Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ga ƙokarin su Ammah yadda suka yi ma Ummu auren wuri haka a lokacin ta yi ta ce ma Lamido ta yi ƙarama da aure bai ce mata komai ba, ga shi nan ya sake ta ya wulakanta ta da ƙananun shekarunta.
Ta shi ta yi ta ɗau wayarta ta bar ɗakin domin ta san in gogan ya fito ya iske ta ba zai ji daɗin shiryawa ba, shi ya sa ta bar masa ɗakin ta koma ɗayan bedroom ɗin ta ɗan kwanta.

Shi ko bai wani daɗe ba ya fito daga wankan, sai da ya tabbatar da Balkisu ba ta ɗakin sannan ya saki jikinsa da ga shi sai towel ɗaure a kugunsa ya fito ba ya ɓata lokaci wajen shiryawa yanzu ma cikin lokaci ya shirya ya saka farar shadda gezner ɗinkin zamani riga da wando, rigar yau har ta fi sauka masa saboda yau jumma'a za su je masallaci tare da su Baffa, wani nishaɗi yake ji tun safe na tunowa da rayuwar baya amma labarin da Balkisu ta bashi ya ɗan hanashi sukuni.
Taje kansa ya yi da gemunsa da yake tunanin yau zai je gyaran fuska a rage masa gashin fuska. Turare ya fesa kaɗan saboda shi ba ya son kamshin turare ya yi masa karfi da yawa yanzu kan shi zai fara ciwo, ko Balkisu ta cika turare har kansa yake hawa in kuma ya shaƙa da yawa haka zai yini da ciwon kai, bai taɓa ce mata ta daina sawa ba, saboda shi a tunanin shi saboda abin da ba ya so shi kaɗai ba zai tauye mata haƙkinta tunda ita tana so ba.

Shi ya sa ko ba ya son abu ba ya faɗa, gani yake yi kamar son kai ne. In kuma yana son abu shima ba ya faɗa gani yake yi don shi kaɗai yana son abu kaza kamar ya shiga haƙƙi ne ya ce kowa sai ya so abinda yake so ko ya zama irin sa ba.
Sai ita Bilkisun ce da kanta ta gano ba ya son mu'amala da turaruka tunda in ya yi birthday tana siya masa a matsayin gift zai karɓa amma sai shekara ta sake zagayowa bai taɓa amfani da shi ba, uban turarukan dake ɗakin shi kamar za a buɗe shago amma baya amfani da su tun daga lokacin ta fahimci bai cika son ƙamshi ba, ita kuma gata tana son ƙamshi tana mu'amala da turare sosai in ka yi mata kyautar turare ba ta mantawa.

Ba ta daina amfani da shi ba amma in suna tare sai ta yi amfani da mai sauƙin ƙamshi, ita fa koda yaushe jikinta a cikin ƙamshi yake duk bayan wata ɗaya tana zuwa a yi mata gyaran jiki na skin care. Shi ya sa fatar ta kamar ta turawa wajen taushi da santsi sannan ba aikin da take yi, daga zuwa asibiti ta duba patients shike nan ta dawo gida ta kwanta.
Sannan gaba da baya tana cikin jin daɗin rayuwa.

Kan kujeran da ya tashi ya koma ya zauna da wayarsa a hannu ƙiran samsumg ita ce wayar da yake amfani da ita na Family, shi in ba zai yi kira ko an kira shi ba sai ta yi kwanaki bai yi amfani da ita ba, a wajen aiki kuma suna da wayoyin aiki shi ya sa.

Yana so ya tambayi wani labarin abin abin da ya faru amma ba zai iya ba.
WhatsApp ya buɗe ya shiga, 24/7 datar shi tana buɗe ne tun a can ma wajen aiki suna da wifi a Lagos ma haka. Ta kwana a kunne saƙonni su yi ta shigowa amma sai a fi wata bai duba ba. Tun ballatana in yana wajen aiki bai cika duba wayar ba.
Wasu saƙonnin ma sun fi wata biyu bai duba ba.
Ya ga saƙon Mahma tana tambayan lafiyan shi?
Giransa guda ɗaya ya sosa da hannu ɗaya yana jin nauyi , bai kyauta ba ya kamata ya kira Mahma.

Har da saƙon Maimartaba yana faɗin sun ji shuru kwana biyu ba a samun wayarsa Fulani ta damu.
Bai amsa ma wannan ba tunda lokacin da ya koma Lagos ya yi magana da su gabaɗaya.
Ƙasa ƙasa ya yi ta yi, can ne ya gano group ɗin Ammah da Baffa ya dai san an buɗe amma bai taɓa bibiya ba sai yau ya shiga ya ɗan duba saƙonni.

Ya ga Date ɗin da Hamma Jibo ya sanar da labarin da Balkisu take faɗa masa an kwarari wata biyu cikin na uku ma.
Sake sosa giran shi ya yi, haka ne ƙololuwar nuna damuwarsa, tunani yake yi ko shi ya sa daga Baffa har Ammah duk suka rame masa a ido, bai yi magana ba ne amma a zuciyarsa sai da ya ce duk sun rame amma sai ya danganta haka da ɗan daɗewar da ya yi bai gan su ba.

Fita ya yi daga group ɗin, ya je ya nemo KB da sunan shi ke a matsayin Friend a wayar Lamiɗon.
Sai ya ga ma ya yi masa mgana.

"Amini mutanen Jimeta."

Haka ya rubuta masa dubawa ya yi sai ya ga yana online.

Rubutu ya fara yi na wani lokaci kamar zai rubuta wani abu ashe kalma ɗaya ne ya rubuta.

"Amini."
Ya ɗan ja fasali kamar yana ganin sa.

"Me ya faru..?

Ya sake rubutawa ya tura masa sai kuma ya dakata kawai yana kallon wayar.

"Naam Amini ya gajiya! Ya baƙun ta?

"Me ne ya faru kuma!?
A ina?

Duk wayar na hannunsa saƙonnin suna ture juna suka shigo
Sai ya fara rubutu sai ya goge ya yi ya kai sau uku sannan ya samu ya rubuta.

"Ummu Salama."

"Me ya samu Ummun?
Hamma Kabiru ya turo masa cikin mamaki.
Haushin chart ɗin Lamiɗo yake ji magana ba magana ba ya rabata ya ɓata maka lokaci.

Kawai sai ya kira shi Video call kamar ba zai ɗauka ba sai dai ya ɗaga kiran.
Hamma Kabiru ya bayyana a cikin lap na asibitinsu yana sanye da suit da farar rigar lapcot ɗin sa. A jikin lapcop din an rubuta sunan shi..
Kabiru Hadi Baba.

"Amini wai me ya faru da Ummun ne?

Ya faɗa yana kallonsa, shuru ya yi masa yana kallonsa sanin halin shi ya sa ya ce" Wai ko maganar abin da ya faru da sakinta da ɗan iskan yaron nan ya yi?
Sai da ya ɗan lumshe idanuwansa sannan ya ɗan gyaɗa masa.
"Kai ai an kwana biyu Amini, lokacin kana can wajen aiki shi ya sa ban faɗa maka."
Nan shima ya shiga sanar da shi duk abin da ya faru

"Amini na so Baffa ya cire hannunsa mu kai yaron nan kotu amma kasan dai halin Baffa, Ammah ma ta goya masa baya. Ya sako yarinya ga shi ya barta da wahalan ciki tunda ya sake ta an ce ba ta kara lafiya ba, kullum kuka da rashin cin abinci, ita a damuwa su Baffa ma cikin damuwa. Amini da a ce su Baffa sun matsa ma Ummu Salma ta cigaba da karatunta da yanzu duk wannan abubuwan da suka faru wallahi ba su faru ba."

Ya karishe faɗa yana jin haushi in ya tuna cin mutumcin da Habib ya yi musu.
Shuru kawai Lamiɗo ya yi yana jinsa ba tare da ya yi magana ba.

"Wai yaron nan ne zai ce shi ba son Ummu yake yi ba auren sha'awa ya yi da ita yanzu kuma tunda ya gama moranta bari ya yada ƙwallon mangwaro ya huta da ƙuda"
Lamiɗo ya sake sosa giran shi na dama wannan karon kansa ya duƙar ƙasa bai kuma yi magana ba

"Ya ce ba ya son cikin jikinta tunda ya ce ta zubar ba ta zubar ba. Baffa kuma ya ce ta haifa su suna so kuma za su riƙe, ka ji halin da ake ciki ni tun zuwan da na yi ma ban koma ba, ga tausayi in ka ganta amma haushinta zai sa in kana kusa da ita ka yi mata dukan tsiya"
Lamiɗo ya ɗago yana kallon shi.
"Me ya sa?
Ya tambaya a hankali kamar ba ya son magana.

"To Abdulrrahaman na faɗa mini har yanzu tana son wannan shegen bayan ya gama tozarta ta, saki uku fa ya yi mata Amini bayan ya haɗo ta maganganun cin mutumci, shi ne har yanzu take so? Wallahi da ina garin nan sai na taka wuyanta tunda ita shashasha ce."

Sai da Lamiɗo ya motsa bakinsa ya ɗan murmusa.
Amma dai bai yi magana ba shi kuma Hamma Kabiru ya shiga faɗa ta in da yake shiga ba ta nan yake fita ba, shi dai kawai su Baffa yake ba ma laifi da ba su yi ma Ummu aure ba da duk haka bai faru ba ya manta da zanen kaddaran bawa ba ka iya guje masa.

Gajiya Lamiɗo ya yi ya motsa bakinsa ya katse Hamma Kabiru sanin halin shi in ya fara kawo hujjojinsa sai fa kowa ya fahimce sa.
"Ammah ta damu ko?
Shi ya sa ta rame ita da Baffa."
Ya tambaya ɗaya bayan ɗaya.
"Ai damuwa ta zama dole Amini, gwara ma Baffa ana iya gane damuwarsa Ammah ce sai dai ta kunshe ita kaɗai."

Shuru ya yi, Ammah tana cikin damuwa duk ta rame baiwar Allah. Ko saboda Ammah da yana nan aka yi haka sai ya saka an yi ma yaron nan ladabi tun da ya saka Ammah damuwa ita da Baffa.
Lamido gajiya ya yi da tsarin Kabiru ya kashe wayarsa ya ce zai je gida za su je masallacin jumma'a da su Baffa, amma ya ce in ya dawo gida za su yi magana.

Hula ya baƙa saka da wani rufaffen takalmi mai rufewa.
Har ɗaki ya bi Balkisu sai ya isketa ta yi barci har bargon ya ɗan gyara mata sannan ya fita. A falo ya iske su Sultan suka naɗe shi suna kiran sunan shi, kaya ya ce Anitha ta sauya musu tare da su zai fita ba daɗewa aka shirya su Sultan ma kamar ubansa farar shadda ya saka har da hula Beena kuma wata riga ce yar kanti a jikinta pick colour ga takalminta na mata cover mai kalan pick, gashin kanta an kama mata da kananun ribbors masu kala-kala.

Ganin ba a saka mata hula ko hijabi ba ya sa ya ce Anitha ta nema mata hula saboda Ammah za ta yi magana ko Baffa in su ka ganta ba ɗankwali ko hijabi.
Shi ya tuka su zuwa gidan Baffa, Ammah na ganinsa da yara ta tarbesu. Sultan da Beena sun saba da kakarsu suka make suna kiranta da Ammah. Ita kuma ta rumgume su tana murna.
Da su kaɗai Ammah ke wasan jika da kaka domin tana ta ce ma Sultan ya yo wanka yana so ya kwace ma Baffa gwammati a wajenta ko? Baffa ma da ya fito cikin manyan kaya ya ce ina ai ba wanda ya isa ya ture gwamnatinsa.

Ummu na cikin ɗaki tana jin su amma ba ta fito ba.
Tana jin zuwan su Hamma Abdulrrahaman da tafiya su masallaci su huɗu har da Hamma Abdullahi.
Sultan ma sun tafi da shi Beena kawai aka bar ma Ammah tana ta fama da ita, yarinya akwai shagwaɓa ta ce wannan za ta ci sai an bata ta ce wannan Ammah kuma ba ta gajiya.
Kafin su dawo Ummu ta fito ta shigar da ruwa ɗakinta karma ta nema daga baya, ba ta kaunar ma su sake haɗuwa har sai sun tafi.

Nan gida suka dawo a falon Ammah suka ci abincin suna ta hira duk da shi ɗan kasaitar ba a jin muryansa sai dai ta su Hamma Abdulrrahman.
Sai can yamma suka watse, Allah ya taimaketa har suka bar gidan ba ta fito ba kuma ba wanda ya neme ta sai Baffa shima sai bayan ya dawo sallan mangariba ya zo ya duba ta.

Kusan satin su Lamido ɗaya a jimeta suna hutawa. Kullum sai ya zo gidan Ammah shi da yara Balkisu kuma bai wuce sau uku ta zo ba, tana gida tana hutawa amma dai ta leka gidajensu Hamma Abdullahi Lamiɗon ma Ammah ta tura su tare da matarsa ta shi gidan Ummin ikki sun gaishe ta.
Ranar da suka yi sati suka tafi Jalingo gidan Hamma Kabiru kwanan su biyu suka dawo daga nan Ammah ta ce ya kamata su je Mubi ana ta tambayan shi tunda ya daɗe bai je ba, suka shirya tafiyan da Hamma Abdullahi da matarsa sai shi Hamma Lamiɗo da iyalan na shi a helux ɗin Lamiɗo suka tafi suka yini suka dawo. An ce Hamma Lamiɗo ya yi ta rabon kuɗi ga su Baffa Umaru da iyalansu har gidajen su Umma Balki duk ya je haka Hamma Abdullahi ya zo yana faɗa, shi daman mai  wuyar Ammah ta yi magana ko bai yi ra'ayi ba zai je.

Ummu dai ba ta sake bari sun haɗu ba amma dai sun sake haɗewa da Balkisu da yaran tunda ko da yaushe suna gidan.
Lamiɗo bai yi ma Ammah maganar Ummu kai tsaye ba ya dai ce ta daina saka damuwa a ranta kar cuta ta kamata ta ce za ta daina in sha Allahu.

Bai kara ganin Ummu Salma ba, sannan bai sake tambayan wani game da ita ba, suma mutanen gidan ba wanda ya yi masa hiran abin da ya dangan ce ta. Suna da kwana goma da zuwa suka tafi Daura.
Daga can Balkisu za ta koma Lagos da yara saboda aikinta da makarantan yara amma shi Lamiɗo zai dawo ta Jimeta kafin ya koma Lagos.

****

*KATSINA STATE, DAURA.*
*MASARAUTAR DAURA.*

Garin Daura karamar hukuma ce da ke cikin Jihar Katsina. Garin yana cikin jihar katsina ne a arewa maso yammacin Nigeria, kuma ya yi iyaka da jamahuriyar Nijar ta wajen Damagaram daga arewa.
Masarautar Daura Jiha ce ta addini, da ta gargajiya a Arewacin Nigeria.

Sannan an kira Masarautar Daura a matsayin ɗaya daga cikin kasashen hausa bakwai, domin itace tare da Biram, Kano,Katsina, Zazzau, Gobir da Rano. Wanda zuriyar ƴa'ƴan Bayajidda suka yi mulki, tare da Daurama da magira,(matarsa ta farko)Jami'ar calfornia's Afircan. American studies na nufin Daura, da kuma Katsina a matsayin tsofaffin kujeru na al'adun musulunci  da ilimantarwa.
Akwai al'adan da suke gudanawar a garin Daura bikin hawan sallar gani na ɗaya daga cikin bukukuwan da masu sarauta da dawaki ke kece reni a cikinsa, wanda kuma za a iya cewa ya samo asali ne daga Daura sannan garin ya fice wajen gudanar da wannan al'adan.

**

Tun zamanin sarkin Jafaru ɗan Umaru zuru'an su Lamiɗo ke mulkin Daura sama da shekaru sittin da suka gaba ta.
Mai martaba Sarki Alhaji Dr. Nasiru Daura ya yi hau karagan mulkin Daura shekaru talatin baya sannan shi ne sarki na 42 a lissafin masarautar.

Kuma ya samu nasaran hawa karagan ne bayan rasuwar mahaifinsa tsohon sarki Mai martaba Muhammad Shitu.
Masarautar Daura kayattaciyar masarauta ce mai ɗimbin tarihi.
Lokacin da suka iso filin jirgi na Umaru Musa yar'aduwa da yake an san da zuwan su tuni wasu aminttatun Mai maitarba irin su Waziri da wambai tare da rakiyan dogarai sai ƙanin Lamido Saleem(Sardaunan Daura Hakimin Daura) suka zo tarban su. Shi kaɗai ne ke karatu a Nigeria shi ne kuma ke gida Daura tare da Maimartaba kuma yawancin yana wakilta shi zuwa wajen taro ko wani abu da ya shafi sarauta, mutanen garin Daura suna tunanin Saleem(Hakimin Daura) ne zai gaji Sarki duk da yana da karancin shekaru domin bai wuce 26 ba amma yana da hikima da hangen nesa sannan mai fara'a da son mutane saɓanin Lamido da ba shi da fara'a sosai, sannan ba mazaunin masarauta ba, amma shima an yi shaidarsa da kyakyawan zuciya da son takalawa da matasa, duk da kuma shi ke da Sarautan Yarima Daura mai jiran gado hakan bai hana  wasu tunanin Hakimin Daura a matsayin wanda ya cancanta ba, duba da shi jinin Sarauta ne gaba da baya saɓanin Lamiɗo da iya bangaren uba ne sarautarsa take da ƙarfi.

*FARGAR JAJI SECOND PROMO.*


KU BIYA #800 A MADADIN 1K, TURA TA WANNAN ACCT ƊIN.
9069067488.
JAMILA UMAR OPAY.

08032773332.
09069067488.

VALID 24HOURS.

MUN GODE.


*Janafty*
*FARGAR JAJI.*

*Wattpad:JamilaUmar315*
*Arewabooks:JamilaUmarJanafty*

"To Hajiya Hauwa'u Inuwa Aminu (Anty Hairi) with love and gratitude"

*FARGAR JAJI SECOND PROMO.*


KU BIYA #800 A MADADIN 1K, TURA TA WANNAN ACCT ƊIN.
9069067488.
JAMILA UMAR OPAY.

08032773332.
09069067488.

VALID 2HOURS.

MUN GODE.

Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/L6zUax648eTERbvw8Bqyie?mode=gi_t

*18*

A mota ɗaya Lamiɗo da Saleem suke cikin wata baƙar Hilux, tana daga cikin motocin Mai martaba. saboda Lamiɗo ne, ya sa a motocin alfarma ake zuwa tarbansa in dai ya zo Daura. Ba sai Mai martaba Sarki ya yi magana ba kowa ya shaida yadda yake son Lamiɗo ba ga iya ahalin masarauta ba har jama'an gari saboda yadda yake yawan zencen sa ko yana nan ko ba ya nan.

"Ranka ya daɗe barka da zuwa Garin Daura."
Saleem ya faɗa yana mai kallon yayan na shi wanda tunda suka shiga mota suka fara tafiya bai yi maagana ba.
Balkisu da yara suna motar gaban su tare da hadiman Mai martaba.

"Saleem"

Ya kira sunan shi cikin yanayin maganarsa.

"Ranka ya daɗe an iso lafiya?
Saleem ya sake faɗa, sanye yake cikin rawaninsa tsaf ya fito a Hakimin Daura kuma Sardauna.

"Mun same ku lafiya? Ya makaranta?
Lamiɗo ya faɗa yana kallon shi.

"Lafiya lau. Allah ya taimake ka. Allah ya kara maka lafiya da arziƙi Allah ya tsare mana kai Yarima."
Saleem ya gama faɗa har yana jinjina masa hannu.
Mirmishi ya yi har sai da fuskar ta nuna kafin ya jinjina kai.

"Ka san ba na so ko?

"Tuba na ke, a gafarce ni ranka ya daɗe"
Lamiɗo ya yi wani mirmishi mai tsada kafin ya ce" Hakimin Daura"
"Naam Allah ya taimake ka."
Saleem ya faɗa har yana ɗan rusunawa cikin girmamawa.
Kafaɗansa Lamiɗo ya dafa yana sake kallon shi.

"Sardaunan Daura."

Ya sake faɗa a hankali kamar ba ya son magana. Ko direba da Wambai dake gaban motan ba za su iya cewa ga abin da Lamiɗo yake faɗi ba.

"Allah ya ja da zamanin Yarima."

"Ka daina mu'amalanta na kamar sauran mutane."

"Tuba na ke yi ranka ya daɗe."

"Am your brother, mu yi mu'amala kamar yan'uwan juna."

"A yi mimi afuwa. Tuba na ke yi Ranka ya daɗe."
Ya sake faɗa yana mirmishi ba zai dai bari ba kenan.
Lamiɗo ya ɗan sake dukan kafaɗansa ba tare da ya sake magana ba

"Allah ya taimake ka. Tuba na ke yi. Tuba na ke Yariman Daura. Yarima mai jiran gado"

Ya san ba ya son wannan kirarin shi kuma yana yi masa ne saboda ya yi magana. Ba uwa ɗaya suke ba, ba kuma su san juna a shekarun baya ba amma yanzu da suka san shi a matsayin ɗan'uwa na jini suna son shi, musamman ma Saleem ɗin jin Lamiɗo yake yi kamar uwa ɗaya uba ɗaya saboda kyawawan hallayansa duk da ba ya da yawan magana da son hayaniya akwai kyakyawan alaqar Yaya ga ƙaninsa a tsakanin su, suna waya sannan in dai ya zo garin kuma Saleem na nan a lokacin har ya koma duk in za su je suna tare.

Shuru ya yi kawai yana kallon sa ya ɗan kwantar da kansa a jikin kujeren motar. idanuwansa na lumshewa lokaci ɗaya yana kallon hanyar da suke wucewa zuwa Daura, yana jin wani alfahari na samun Lamiɗo a matsayin ɗan'uwa.

Shi ko Lamiɗo hanya yake kallo iska na ɗan shigarsa, wani natsuwa ya je ji na kama sa a duk lokacin da ya zo Daura. Ba domin ba ya son duk abin da ya shafi sha'anin Sarauta ba da ace shi ba ɗan kowa ba ne to da ya ji daɗin rayuwarsa a Daura. Ya yi rayuwa a Jimeta amma yadda yake son yanayin garin Daura da jama'ar cikinta na musamman ne, a cikin zuciyarsa komai na garin ya yi masa damuwarsa ɗaya abubuwan sarautan nan mai hana kunnuwan mutum su huta, in ya je Daura har ya koma cikin ganin jama'a yake yi, in kuma za a yi taron Fada Mai martaba sai ya matsa masa ya je, kafin a gama zaman fada ya shiga mummunan takura a rayuwarsa.

Shi ba ya son hayaniya, ba ya son magana ya fi daraja ya ji duniyar ma ta yi tsit gabaɗaya.
Amma in dai yana amsa sunan Muhammad Nasiru(Yariman Daura) ba zai iya guje ma abubuwan da suka shafi sarauta ba a baya ya yi haka amma jini da sarauta suna cikin jinin jikinsa ne ko ba a Daura ba shi ɗin kasaitattace ne.

Har suka iso garin Daura magana ba ta sake haɗa shi da ɗan'uwansa ba shima kuma kanin na shi ya san waye shi bai takura masa ba shima a cikin motan lamo ya yi kamar baya ciki.
Motocin da su Bilkisu ke ciki kofar shashen cikin gida ta nufa, su kuma direct motar su fada ta nufa, tuni bushe-bushe da kaɗe-kaɗe suka cika fada na zuwan Yariman Daura.

Motarsu ko gama fakin ba ta yi ba dogarai suka yi caa,tuni yar natsuwanr da ya fara samu ta yi ta kanta ga hayaniyar mutane ga busa wanda ya ke sake bashi tabbacin ya shigo garin Daura rayuwarsa ta sauya ya tashi daga Muhammad matuƙin jirgin ruwa ya koma Muhammad Nasiru(Lamiɗo) mai sarautan Yarima mai jiran gado duk da dai shi kam ya san ba wani gadon da ya je jira ba zai iya yin wata sarauta ba domin ba zai iya ba.

A guje dogarai suka buɗe musu ƙofofin motar shi da Saleem, da yake a tawagan da suke je ɗauko shi har da masu kakin masarauta.
Tun kafin ya fito daga motar dogarai suka zube a kasa suna faman kawo gaisuwa..
Daga lokacin ya ji kamar ana sauya shi komai na shi ya sauyawa kamar ba shi ba.
Shi ya sa aka ce in dai kai jinin sarauta ne, duk in da ka shiga ba zaka ɓuya ba.
Tuni Lamido ya rikiɗe ya fito a Yariman Daura sak.

Kafafunsa farare masu cike da gargasa ya fara sawowa waje masu ɗauke da takalma rufaffu bakake na fatar damisa masu kyau, sannan gangar jikinsa ta fito. Dogon Yarima mai ƙwarjini da Haiba. Haka wani dogari ke faɗi kamar zai saka kansa a kasa saboda girmamawa.

Sanye yake da wani baƙin yadi mai ɗan santsi ɗinkin riga da wando amma tazarce, sai ya ɗauki jaket baƙa na saƙin sarauta a jiki ya ɗora a sama. Kansa da hula baƙa ta dara shigar bakake ya yi daga samansa har ƙasa, ya rage gashin fuskarsa sai haibansa ta sake fitowa amma suman kansa na nan domin hulan ma a saman sumar ta zauna sannan gefe da gefen wajen kunnuwan shi kana ganin suman da ya tara da ɗan yawa.

"Barka da zuwa Yariman Daura. Sauka lafiya Namijin fama. Sauka lafiya Yariman matasa. Farin Yarima kake dogo ɗan Nasiru jikan Shitu, barka da zuwa shalelen Masarautan Daura. Barka da zuwa kasaitattacen Yariman Daura. Jama'ar Daura na yi ma dogon Yarima barka da zuwa."

Hannu kawai yake ɗaga musu ba ya magana fuskar nan ta sa ta sake ginshiƙewa saboda jinin mulki ne ya motsa a cikin jininsa.

"Takawarka lafiya ɗan sarki jikan sarki. Angon Balkisu Baban Muhammadu, takawarka lafiya Amintattace, takawarka lafiya mai alheri takawarka lafiya Yarima Allah ya ƙara tsawon kwana Allah ya tsare gaban ka da bayan ka."

"Barka da isowa Hakimin Daura takawar ka lafiya Sardaunan Daura."

Suke ta faɗa kamar za su shiɗe suna mai ƙanƙantar da kan su. Hannu kawai ya ɗaga musu ya wuce tawagan suka bi bayan shi zuwa fadar Sarki Mai martaba Alhaji Dr Nasiru Daura in da yake gudanar da zaman fada a daidai lokacin.

"An gaishe ku. Yariman Daura ya amsa muku."

"An gaishe ku. Hakimin Daura ya gaishe ku."

Haka shugaban dogarai yake ta faɗa. Da irin takunsa na jaruman maza gif! Gif suka shiga fada, suna shigowa suka duƙa gaban Mai martaba da ke zaune kan wata kyakyawan karaga cikin naɗi idanuwansa ne kawai a ake gani su kuma su Wambai suka jeru cikin masu zaman fadan da suka sha rawani.

"Allah ya ja zamanin ka na kawo Yarima gida kamar yadda ka bukaci na jagoran ci haka."
Saleem ya faɗa cikin ɗan rusunawa.
Jinjina kai Mai martaba ya yi alamun gamsuwa, ko da ba a ganinsa fuskar sa amma kowa ya shaida yau yana cikin farinciki.

"Sarki ya gode ma Hakimin Daura. Allah ya ja zamanin Sardaunan Daura."
Lamido ne ya ɗan rankwafa cikin yanayin maganarsa ya ce.

"Allah ya tamaimaki Mai martaba fata duk mun same ku lafiya?
Maimartaba ya sake jinjina kai.
Dogarai suka ɗauka.

"Sarki ya gaisheka Yarima, sannan yana yi maka maraba da sauka a masarautar Daura."

"Na gode. Allah ya kara yawan rai da lafiya mai ɗorewa."

Lamiɗo ya faɗa yana ɗan jinjina kansa.

"Amin Yarima. Allah ya ja zamanin ka, Mai martaba ya amsa."

Ɗaya bayan ɗaya Lamido ya juya yana kai gaisuwa ga walikan fada suna amsawa da an gaishe da Yariman Daura barka da sauka,
Duk da haka fuskar nan ta shi ta nan a ginshiƙe cikin irin yanayin sa.
Yarima ya amsa, Yarima na

Please Login or Register in order to submit comment