Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Gimbiya Shahida uwar gidan Maimartaba da man duka sauran matan na shi.
Sannan Fulanin Daura yadda ta dauki Lamiɗo da muhimmanci haka ta dauƙi Ammah da Baffa. Mami ce tun da ta ce ba ta da alaqa da su haka ɗin take ba ta ma nuna ma ita ta haifi Lamiɗo ballanta wani abu ya sa a sako ta a ciki. Shima kuma ba ya taɓa nuna Mami a matsayin mahaifiyarsa Ammah ce uwar sa har gaban abada.

Lamiɗo kawai suka sani da marikan shi da suke tamkar iyayen shi, shima Lamiɗon ba ya ɗaukan kowa a matsayin iyayen shi sai Ammah da Baffa Mami dai kawai sunan ta uwa ne amma babu shaƙuwar ɗa da uwa a tsakanin su. Dalilin Lamiɗo har Hajji Masarauta ta kai Ammah da Baffa suka je suka sauke farali.

***

Ummu Salma ta kasance a wajen Ammah da Baffa a matsayin yar Auta. Ta taso cikin zaratan yayyen ta maza bakwai ko na ce takwas ga Lamiɗo sannan ita mace, shi ya sa in dai ana maganar gata sai dai a yi kwataance da Ummu Salma.
 
Tun tasowar Ummu ta tsani karatun boko, domin kanta gaskiya ba ya ja, kusan na kusa da na ƙarshe take ɗaukowa a makaranta. Duk gori da zagin da su Hamma Kabiru ke yi mata bai sa ta gyara ba. Kuma makaranta mai tsada take yi ta Ahmadu Ribaɗo Collage a garin Yola. Amma sai a saran kuɗi ake yi kwaƙwalwar Ummi ba ta fahimtar komai har gwara ma bangaren islamiya shi ba laifi amma na bokon nan ne sai a hankali. Ita kawai karatun boko na wahalar da ita ne, duk ko yadda ba ta iya shan inuwa ɗaya da su Hamma Kabiru a cewar su daƙikiya ce ita kar  Hamma Lamiɗo  ya ji labari ita tun zaman shi a gidan su jininsu bai taɓa haɗuwa ba, wata maganar arziƙi ba ta taɓa haɗa su ba shi ba ya magana ma. In ka gan shi yana mgana to da Ammah ne ko Hamma Kabiru, tun tana yarinya ta san shi ba ɗan Ammah da Baffa ba ne saboda su suna kama da juna amma shi kamininsa na dabam ne, duk da ba ta son shi amma kuma akwai shakuwa a tsakaninta da mahaifiyar shi Mami, wacce ita ta yi renon ta bayan Ammah ta haifeta kafin auranta sannan bayan ta yi aure tana yawan zuwa Kaduna gidan Mami ta yi hutu, Mami mace ce mai fara'a sannan ita da mijinta suna ji da ita in suka je kasashen waje haka Mami za ta ciko mata jaka cike da kayan sawa na alfarma sai wanda ya gani. Ta sha zama ta yi ta mamakin yadda Mami ta iya haihuwan Hamma Lamiɗo ita ba ta ga ta in da ma suka haɗu ba, shi dabam ita dabam ita mai fara'a ce mai kirki da son Jama'a saɓanin Lamiɗo da ba shi da fara'a ba shi da son mutane sannan ba shi da kyakyawan mu'amala.

Ummu Salma ta taso ta ga Aminci tsakanin Amma da Ummin ikki shi ya sa itama Aminta ya haɗa ta da Aisha(Baɗɗo) a yayin da makaranta ya haɗa ta da Shamsiya(Bestie) su suna da son karatu kuma suna ganewa ba kamar ita ba tun da kuma ta fahimci ba ta gane karatu ta ce ba za ta ci a karatun boko ba, daga lokacin ta saka ma kanta tunanin daga sakandiri ba za ta cigaba da karatu ba.
Kuma haka aka yi ba yadda ba a yi ba amma Ummu Salma ta ce ta gama Baffa kuma da Ammah suka goya mata baya. Abu ɗaya Ummu ta fi mayar da hankali shi ne girken-girken zamani, ta bakin Hamma Kabiru ya ce shi kaɗai take ganewa.
Bayan ta gama sakandiri ta je Kaduna ta yi wattani huɗu a wajen Mami saboda tsangwaman su Hamma Kabiru akan sai ta cigaba da makaranta tun ballanta ganin kawayenta Baɗɗo da Shamsiya sun cigaba.

A can kaduna ta yi ta shiga catering School tana samun ƙwarewa  bayan ta dawo Jimeta ma ba ta zauna ba yayyenta sun gaji da magana sun ƙyale ta tun da Baffa yace boko ba dole ba ne, shi bai yi ba Ammah ma ba ta yi ba amma ba su mutu ba sun rayu saboda haka a bar Auta ta sarara. Kadunan ma da ta gudo saboda Mami ta fara zaunar da ita tana kwatance a kanta na amfanin karatu tunda ta ji haka tace za ta koma gida saboda Mami za ta iya jan Ra'ayin ta in kuma hakan ya faru ko ta shiga ba za ta iya ba gwara maganin ayi kar a fara.

Sai da ta yi zaman shekaru uku a gida ba makaranta ba ta da aiki sai girke girken zamani a gida duk abin da ta koya sai ta gwada shi tun ballantana abubuwan da take gani a waya tunda Mami ta siya mata waya Samsumg babba ta zamani, ko da yaushe tana cikin kwabin fulawa ita ce Cake ita ce donot wani abun ta yi ya yi daɗi wani kuma ya lalace Amma ta yi ta masifa Baffa ne mai supporting ɗin ta.

Ummu Salma Bata taɓa tunanin za ta haɗu da Habib ba sai ga shi Allah ya haɗa su, wata rana ta dawo daga gidan su Baɗɗo ya biyo ta. Duk da a ganin farko ta ji ya yi mata ba ta ɗauka soyayyar da ya nema a wajenta zai kai su ga aure ba sai ga shi komai ya faru cikin lokaci. Ummu Salma da Habib sun yi soyayya kamar su lashe juna kafin aure ya nuna mata duk duniya bai so wata mace sama da ita ba, yayyenta suka yi ta mganganun cewa bai kamata a yi mata aure a lokacin ba, amma Baffa ya ce tunda ta samu miji kuma ya bincika yaron nagari ne zai aurar da Ummu sun yi adawa sosai amma kuma sun haƙura daga karshe. Cikin wattani biyar aka yi auran Ummu Salma da Habib auran ya zama abin kwatance kowa na ganin Ummu ta gama yin dace, ko bayan auran Habib ya nuna ma Duniya Ummu Salma ce duniyarsa, zaman lafiya da soyayya da ƙauna shi ya rike su a cikin wattani takwas ɗin da suka yi da aure. Duk masu adawan auren ta sun haƙura ganin tana zaune lafiya da mijinta.

Ummu Salma ta ɗauka ta gama dacewa. Ta ɗauka bayan ita da wahala a samu mace irin ta a cikin tsara. Sai ga shi cikin wattani uku Habib ya yi ma rayuwarta juyin waina daga sama ta koma kasa. Cikin wattani tara zuwa goma da auran su ya yi ma rayuwarta katon taɓon da har ta koma ga Allah ba za ta manta ba.


*littafin Fargar Jaji na kuɗi ne a manhajar Telegram akan #1k. Tura Kuɗin karatun ku ta wannan acct ɗin 9069067488 JAMILA UMAR OPAY sannan sai ku tura shaidar biya ta waɗanan lambobin kamar haka.*

09069067488.
08032773332.

*Yan kasuwa masu buƙatar a tallata muku hajojinku a cikin wannan kayattacen labarin za ku iya tuntuɓata kai tsaye ta wannan lambar 09069067488 Na gode.*

*Janafty*
*FARGAR JAJI.*

*Wattpad:JamilaUmar315*
*Arewabooks:JamilaUmarJanafty*

"To Hajiya Hauwa'u Inuwa Aminu (Anty Hairi) with love and gratitude"

https://chat.whatsapp.com/LsC7Rjmei7J6Hd11e95nNS?mode=gi_t

*12*

Hamma Abdullahi ya ɗauko  Ummin ikki a mazaunin gaba na motarsa sai Baɗɗo da Ummu dake zaune a gidan baya akan hanyar su ta zuwa gidan Baffa. Baɗɗo ne ke ta kuka saboda in ta kalli Ummu sai ta ji rauni ya dabaibaye ta, ita ma Ummin ikki hawayen take yi tana sake rantsuwan ba za su yafe ba sai Allah ya yi ma Ummu sakayya akan tozarcin da Habib ya yi mata.

Hamma Abdullahi ko baya magana tuƙinsa kawai yake yi amma in da za a tona zuciyarsa da wataƙila an fahimci halin baƙincikin da yake ciki, takardan sakin tana cikin aljihun jallabiyan jikinsa har wani ɗaci yake ji a ran shi na tozarcin kalaman Habib yanzu ya ya Baffa da Amma za su ji? Ummu ma ba a maganar ta, tana zaune kawai ta ƙura ma gabanta idanuwana sai ta daɗe ba ta kyafta idanuwana ba kamar wacce ta zama gunki ba ta kuka ba ta motsi sannan babu hawaye sai dai ido kawai yana kallonta, ta cikin madubin motarsa na gaba gabaɗaya jikinsa ya yi sanyi kamar an masa wanka da ruwan sanyi, addu'a kawai yake yi mata Allah ya ba ta ikon cin wannan jarabawan domin jarabawan mai zafi ne sai wanda ubangiji ya so zai iya tsallakewa.

Har suka isa gidan Baffa dake Zone 3 suna cikin wannan yanayin har cikin haraba Hamma Abdullahi ya shiga da motar Baɗɗo ta kama Ummu ita da Ummin ikki suka shiga da ita cikin gida yayin da Hamma Abdullahi ya buɗe boot ya kwaso akwatin Ummun guda huɗu ya bi bayan su da shi. Amma na zaune a falonta tun bayan fitowarta daga wajen Baffa ba ta koma ba, ba ta so ya fahimci tana cikin gigita shima kamar ya sani sai ya bata lokaci tunda suka gama waya da Aminiya take zaune cikin mutuwar jiki da na zuciya na tsawon lokaci kafin ta ji sallama a tsakar gida zumbur ta miƙe jikinta ba in da ba ya rawa ɗago labulen da aka yi ne yasa Amma ta yi saurin komawa ta zauna tana ɗan daidaita yanayin ta.

Lokacin da suka shigo da Ummu a riƙe kallo ɗaya Amma ta yi mata ta ji ta sare, kafafunta sun yi mata nauyi da ta kasa ma miƙewa Ummu ce ta koma haka! Idanuwa sun kumbura fuskarta ta yi wani irin jajir, tana zaune kawai tana kallon su, suka zaunar da ita a saman kujera Baɗɗo ta zauna a gefenta ta jawo ta a gefen kafaɗanta tana ɗan tapping bayanta alamun lallashi, duk in da aka bi da ita can take bi kamar wata doluwa ko yarinya ƙarama.

Ummin ikki ta ƙarisa kusa da Amma ta zauna tana faɗin" Aminiya yau mun tashi cikin jarabawar Ubangiji."
Amma ta kalleta kafin ta ɗan motsa bakinta a hankali tana faɗin" Allah ya sa hakan ya zame mana alheri gabaɗaya"
Ummu ikki ta amsa da Amin kafin ta fara goge ƙwalla tana cigaba da faɗin" Wannan yaro ya cuce mu. Da ikon Allah sai Allah ya saka mana."

Ta faɗa tana kallon Ummu har a lokacin kawai waje ɗaya take kallo ko kiftawa babu, kafin ta sake cewa wani abu Hamma Abdullahi ya yi sallama ya shigo cikin gida sun amsa sannan ya shigo falon Ammah, sanda suka taho da su Ummin ikki Hamma Jibo ne ya kira wayarsa shi ya sa ya ɗan dakata suka yi magana ya sanar da shi ya kawo su gida yanzu. Akwatin hannunsa ya jera anan tsakiyar falon Ammah ko zama bai yi ba ya kalli Ummu na wani lokaci kafin ya ɗan girgiza kansa.

"Ina kwana Ammah."

Ya faɗa cikin sanyin murya.

"Lafiya lau Baba ya iyalan naka?

Ta amsa masa amma ba ta kalle shi ba kanta na ƙasa ba ta so shima ya fahimci halin da take ciki, ko ba ta fito ta nuna ba ko ta ɓoye Ammah fa uwa ce ga Ummu Salma yadda lamarin nan zai daki kowa barin ita ne.

"Suna lafiya."

Ya faɗa sai kuma ya yi shuru, Ummin ikki na ta sharan ƙwalla Baɗɗo ko hawaye ne wasu na zuba wasu na sake tunkuɗowa.

"Ba komai in sha Allah zai wuce."

Hamma Abdullahi ya faɗa domin a lokacin shima ya rasa kalaman da zai faɗi falon ya yi shuru kamar mutuwa ta gifta tun ballanta shessheƙan kukan Baɗɗo da na Ummin ikki. Ummu dai ba ta kuka da man an ce wani baƙin ciki in ka yi kukan daga baya in kukan ya ɗauke shike nan sai dai zuciya ta dinga ƙuna da raɗaɗi to hakan ce take faruwa da Ummu tunani take yi kamar ba gaskiya ba ne abin da ke faruwa gani take yi kamar komai a mafarki ne in ta farka za ta ganta a cikin ɗakin auren ta, tare da Habib amma ina duk lokacin da ta kifta idanuwanta a falon Ammah take sake ganin ta.

"Ammah Baffa fa?

Ya faɗa ganin Ammah ta yi shuru kanta na kallon ƙasa.

"Yana cikin ɗakin sa."

Ammah ta amsa masa cikin ajiyar zuciya.
Ya kama hanyar barin falon ne sai ga Baffa ya shigo da sallama daidai lokacin da Hamma Abdullahi ya ɗaga labulen falon Ammah sai ya koma da baya ya ba ma Baffa waje domin ya shigo.

Baffa ya shigo har falon Ammah ya yi tsaye kawai yana kallon Ummu Salma sanye yake da manyan kaya tun da ya saka ne zai je masallaci da asuba.
Tun ɗazu ya ji shigowarsu amma ya kasa tashi ne, bai san adadin hawayen da ya share a ciki kafin ya fito ba. Bai san a wani hali zai ga Ummu ba! Abin da ya faru da ƙanwarsa Fatima ya dawo masa sabo, shi kaɗai ya san dararan da ya ɓata idanuwan shi biyu yana kukan tausayin Fatima tausayin jarabawan rayuwan da ta faɗa sai ga shi kwatan kwacin haka ya sake faruwa da gudan jininsa Ummu Salma, amma bai yi butulci ba sai ya yi ma Allah godiya domin ba wai ba ya son bayin shi ba ne don ya sake jarabtansu, ya yi haka ne domin ya sake jaraba imaninsu, yana fata da tunanin in Habib ya zama mafarin Ummu Allah ya kawo mata wanda zai wanke mata duk wani dattin zuciya da Habib ya sanya mata.

  Ko da yake tsaye a gaban ta, ba ta nuna alamun ta san ma yana wajen ba, kawai gabanta take kallo babu ko ƙyaftawa. Falon ya sake yin shuru kamar ba kowa a ciki Baffa ya duƙa a gaban Ummu yana kallon ta amma ita ba shi take kallo ba kawai gabanta ta ƙura ma idanuwa ba ta ko motsi daga in da take zaune Baɗɗo na rumgume da ita.


"Ummu Salma."

Baffa ya kira sunan ta cikin kulawa na musamman.

Shuru ita ba ta amsa ba sannan ba ta kalle shi ba, ya sake kiranta a karo na biyu nan ma ba ta ɗago ta kalle shi ba sannan ba ta amsa ba.

"Ummu Salma."

Shuru falon ya sake ɗauka kowa hankalin shi na wajen Ummu cikin tausayi.

"Kalle ni nan Ummu Salma."

Baffa ya sake faɗa lokaci ɗaya yana riƙo hannunta guda ɗaya, abin mamaki haka ya riƙe hannunta da ya ji sa ya yi sanyi sosai amma Ummu ta kasa iya rike Baffa sai ta ji kamar duka kasusuwan hannun nata ba sa aiki, daƙyar ta iya ɗago idanuwanta ta kalli Baffa. ta ƙura masa ido  ba ko kiftawa tana ta kallon shi.

"Ummu Salma."

Baffa ya sake kiranta yana mai matse hannunta a cikin na shi hannun, yana ji kamar ya fashe da kukan tausayin ta amma in ya yi kuka ita za ta sare a yanzu a wannan kadamin su ne ƙarfin gwiwanta in suka rushe itama za ta rushe.

"Ummu Salma."

Ya sake kiran sunan ta, sai ta motsa idanuwanta. Ta kifta ta sake kiftawa sai ga hawaye sharr sun kwaranyo mata a saman kumatun ta.
Ganin Baffa kawai da ta yi ya duƙa a gabanta yana kiran sunan ta ya sa hawaye ya kawo mata. Ya Baffa zai ji? Wani hali zuciyarsa take ciki? Ta yi aure ta tafi ita kaɗai sai gashi ta dawo  musu da ciki a cikin jikinta, Ammah ma ta san tana cikin firgici kawai tana ɓoyewa ne. Kuka fa ake yi saboda abin da ya same ta. Ita ko in ba ta ce tana cikin bala'i ba me za ta ce?

"Allah ya ba ki dangana Ummu Salma. Sannun kin ji ko?

Baffa ya faɗa yana sake jinjina hannanunta dake cikin na shi. Sai ta sake kifta idanuwanta hawaye suka sake zubo mata.

"Ai gwara ta yi kukan ko za ta samu sauki. Tunda muka je yarinyar nan ke cikin wannan yanayin."

Ummin ikki ta faɗa cikin rawan murya. Baffa ya yi shuru kansa na ƙasa kafin ya saki hannun Ummu ya miƙe yana kallon Baɗɗo na saka tafukan hannayenta tana mai share ma Ummu hawaye.

Hamma Abdullahi da tausayin Ummu ya kama shi sai ya ji kamar ya yi mata ƙwalla amma duk da haka idanuwansa sun kala sun yi jajir kamar gwarwashi saboda bacin rai.

"Baffa ina kwana? Ya muka ji da wannan al'amarin kuma da muka tashi da shi yau?

Ummin ikki ta faɗa tana faman goge ƙwallah.
Baffa ya sauke numfashi kafin ya amsa mata.
"Lafiya lau. Ya za a yi da sanin Allah komai zai wuce in sha Allahu."
Baffa ya faɗa cikin karfin hali kafin ya sake kallonta yana faɗin" Sannu da kokari mun gode sosai Allah ya bar zumunci."

"Amin yiwa kai ne Baffa. Allah ya saka ma wannan yarinyar."

Kowa ya yi shuru bai ce komai ba, sai da Baffa ya sake jan numfashi kafin ya ce" Ba komai. Komai zai wuce."
"In sha Allahu."
Hamma Abdullahi ya faɗa cikin damuwa.

Ammah dake zaune tun ɗazu ba ta ce komai ba ta ɗago tana kallon Baffa kafin ta ce" Baffa ko za ka kira waliyin Habibun. Watakila su shiga ciki su iya gyara al'amarin."
Hamma Abdullahi na shirin magana Ummin ikki ta yi saurin cewa" Tab wani gyara kuma Aminiya?
Ammah ta kalleta cikin mamaki ba ita ba har Baffa ma.

"Saki uku fa ya yi mata."

"Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un."

Baffa ya yi saurin faɗa cikin fitan hayyaci, Ammah kuma sai ta kasa magana amma bakin ta na motsi.

"Wallahi tozarcin da yaron nan ya yi mana kenan. Takardan sakin ma tana hannun Baba."

Ummin ikki ta gama faɗa tana nuna Hamma Abdullahi shi ko bai yi magana ba ya zaro takardan sakin cikin aljihun wandon sa ya mika ma Baffa, hannunsa na rawa ya karɓa haka fa ya karɓi na Fatima shekaru talatin baya yau ma gashi zai sake karɓan na Ummu Salma, Allah kana gani.

Nan take Baffa ya warware takardan ya fara karantawa a bayyana ne, kafin ya gama ya jiƙe da zufa kafafuwansa sun gaza ɗaukansa sai da ya yi ɗan baya ya samu damar jingina da bangon ɗakin Ammah.
Ummi ikki sai ta hau kuka tana jero ma Habib addu'an Allah ya sa, Ammah ko wani nauyi ta ji daga ƙasan zuciyan ta. Ganin ta ya yi duhu sai kawai ta dafe kanta ta kasa mgana.

"Lalle wannan yaron ba shi da mutumci."

Ummin ikki ta faɗa cikin cizon yatsa, Ummu na zaune a yadda take amma abin da Baffa ya karanta ya yi mata fami a gyambon ta wataƙila da Baffa ya san ba ta san abin dake cikin takardan ba da bai karanta kowa ya ji ba, ita ba kanta take ji ba su Baffa ya za su ji? Ita ta riga ta gama Haddace kalaman Habib na baya son ta sannan ta daɗe da fahimtar manufar auran ta zuwa gare shi, su ne suka rage su sani duk kuma yadda ta kai ga yi ma maganar rufa rufa Habib ya fallasa komai.

Baffa ya yi shuru kawai da takarda a hannunsa ya kasa magana. Zuciyarsa na wani tafarfasa in da a ce zai iya wallahi da sai ya yi shari'a da Habibu amma kuma ba zai kai shi kara a kotun duniya ba sai dai ya kai shi a kara a kotun Allah. Ya gama cutar su ya cuce Ummu Salma ya gama da rayuwarta ko da sun yi ƙaran shi a gaban hukuma wani ɓata lokaci ne, sannan tonuwar asirin auran Ummu ne ga duniya amma a ƙotun Allah ne kaɗai zai karɓi sakamakon abin da ya aikata.

"Baffa bai kamata a bar yaron nan ya tafi haka ba gaskiya."

Hamma Abdullahi ya faɗa cikin jin haushi.

"In ya saki Ummu ba mu yi jayayya ba, amma maganar ya bar mata ciki ba shi da alaqa da shi bai ta so ba, tunda har shi ya yi cikin nan bai isa ya ce babu ruwan shi ba in ya yi taurin kai ai akwai hukuma sai mu yi ƙaran shi "

Ya faɗa yana kallon Baffa da ya yi shuru ya kasa mgana.

"Gaskiya magana, ita in mun ƙarbeta tamu ce amma ai cikin na shi ne bai isa ya ce babu ruwan shi ba"
Ummin ikki ta faɗa Baffa dai ya yi shuru bai yi magana ba sai kawai ya zura hannu a cikin aljihun wandon sa ya zaro wayarsa.

"Wa za ka kira Baffa?

Hamma Abdullahi ya tambaya sai kawai Baffa ya ɗaga masa hannu ba tare da ya yi magana ba. Lambar Alhaji Sheriff ya nemo lokaci ɗaya ya kira shi ya kara a kunne tana ta ringing bai ɗaga kiran ba sai da ta kusa katsewa sannan ya ɗaga wayar daga can bangaren da sallama, Baffa ya amsa cikin dattakon sa ran shi a ɓace yake shi ya sa bai tsaya ma wata doguwar gaisuwa ba.

"Alhaji kana da labarin ɗan ku Habibu ya saki Ummu Salma saki uku?

Daga can bangaren Alhaji Sheriff dake zaune a ɗakin da mahaifin Habib ke jinya a cikin gidan su ya miƙe a razane cikin firgici ya ce" Innalillahi yaushe? Wallahi tallahi Alhaji ban sani ba."
Ya faɗa cikin tashin hankali to da man ai ba zai sanar da kowa in zai aikata abu mara kyau ba a yanayin maganar Alhaji Sheriff za ka fahimci bai sani ba sannan maganar kuma ta dake shi matuƙa.

"To ya sake ta saki uku gata nan ma na saka an je an taho da ita."

"Hasbunallahi wa'imal wakel. Alhaji wallahi bamu sani ba. Ba mu da labarin wannan hukuncin da Habibu ya yanke"

Alhaji Sheriff ya sake faɗa cikin ɗimuwa da tashin hankali tare da nadamar yadda ya shiga lamarin Habibu, da yau bai shiga ba tuni bai ji kunyar da ya ji yau ba.

"Ba komai Alhaji kar ka damu na san da man ba ka sani ba, da man dalilin da ya sa na kira ka wani saƙo zan ba ka zuwa ga Habibu sannan na kafa shaidata akan maganata da kai "

Alhaji Sheriff ya ma kasa magana Gwaggo ma ta dawo ɗakin da man ta ɗan fita ne, jin wayar da Alhajin yake yi yana rantsuwan bai sani ba sannan yana ambaton sunan Habibu ya sa ta tsaya ta kasa fita cikin zullumin abin da kuma ya sake faruwa.


"A cikin takardan sakin ya rubuta cewa da man ba son Ummu Salma yake yi ba, jikinta ne ya sa ya aurete kuma yanzu tunda ya gama moran abin da ya aura domin shi, shiyasa ya sake ta."
Baffa ya faɗa yana jin ƙuna a ƙasan zuciyarsa.

"Lailahaillallah."

Alhaji Sheriff ya faɗa cikin tsorata da lamarin Habibu.

"Sannan kuma ya ce cikin dake jikinta ba ya so, shi ya sa ya ce ta zubar amma ta yi taurin kai. To saboda haka ya bar mata cikin kar wata rana a danganta shi da cikin har abada"

"Wannan ne kuma bai isa ba ƙarya yake yi. Tunda har ya amince da cikin na shi ne to ko ya mutu ne sai an danganta shi da wannan cikin."

Alhaji Sheriff ya faɗa cikin fushi mai tsanani saboda ya fahimci Habibu ya raina musu wayau yana wasa da hankalin su.

"Ai ba a dole Alhaji tun da har ya ce ba ya so to ba wanda zai masa dole akan haka. Tunda har da kansa ya yi ikirarin cewa har abada kar mu danganta shi da cikin jikin Ummu, to nima Alhaji Hadi Baaba a matsayina na mahaifin Ummu Salma na yi alƙawarin ko bayan raina kar Habibu ya kusanto ni ko ya kusanto Ummu Salma ko abin da za ta haifa nan gaba kamar yadda ya haramta ma kansa dangantakar shi da cikin jikinta nima na haramta masa ya danganta kan shi da Ummu Salma ballanta cikin dake jikinta, ni da man uba na ke ga Ummu Salma har abada sannan zan sake zama uban abin da za ta haifa. Har abada bana son na sake ganin fuskar Habibu."

Baffa ya gama faɗa yana jin zuciyarsa na tsalle saboda ɓacin rai da baƙin ciki.

Alhaji Sheriff daga can bangaren ya ruɗe yana ƙoƙarin magana amma tuni Baffa ya katse wayarsa ya bar shi tsaye cikin  mutuwar jiki da nadama mai yawa.

"Alhaji me ya faru ne?

Gwaggo ta tambaya cikin tashin hankali.

"Habibu ne ya saki matarsa saki uku."

Ya ba ta amsa kai tsaye ai sai ta saka salati tana ɗauka tana direwa.
"Wai ko Habibu ya fara shaye-Shaye ne?
"Babu abin da yake sha, kawai yaron ba shi da mutumci ne."
Ya faɗa yana ta neman lambar Habibu amma sai dai ta yi ta ɗif ɗif ba ta shiga.
Mahaifin Habibu na kwance yana

Please Login or Register in order to submit comment