Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ba."

"To ku kyaleta Baffa ta yi ma kanta illa saboda wani wanda ya cire ta daga rayuwarsa cikin tozarci da wulaƙanci. Ku barta in ba ta kashe kanta ba, ba ta haifu ba."

Baffa ya yi shuru kawai yana kallon ɗan nashi.
"Kai sake ta."
Hamma Abdulrrahman ya ba ma Saddam umarni.
Da sauri ya saki Ummu ya miƙe tsaye, tun kafin ma ya sake magana Ummi da Baɗɗo suka saki hannayen Ummun Salma suka matsa gefe suka bar Baffa kaɗai a durƙushe a gaban ta.

"Baffa kai ma don Allah ka tashi daga durƙushen nan."

"Abdulrrahman."

"Baffa don Allah."

Hamma Abdulrrhaman ya faɗa lokaci ɗaya yana kallon Baffa cikin ɓacin rai,  ba lallashi take bukata ba fata fata za a yi mata sannan za ta dawo cikin hayyacin ta.
Baffa ya ƙi tashi sai da Ammah ta shigo ta kira sunan shi.

"Baffa."

Kallonta ya yi kawai sai ta gyaɗa masa kai, dole ya tashi jiki a sanyaye amma sai da ya kalli Abdulrrahman yana faɗin" Ka yi mata a hankali."
Ya faɗa yana dafa kafaɗan shi ya ɗan bubbuga.
Fita ya yi daga ɗakin ya koma falo Ammah ta bi bayan shi ganin shi cikin damuwa.

Hamma Abdulrrahman ya yi tsaye a gaban Ummu Salma da ta natsu kamar ba ita ce ya shigo ya ga ana rirriƙeta ba, amma yanzu ta yi shuru sai dai kawai hawaye take yi wasu na zuba wasu na karanyowa.

"Kin fasa kashe kan na ki ne?

Ya faɗa yana kallon ta, kawai sai ta fashe masa da kuka.

"Ban hana ki ba, go ahead ki kashe kanki Ummu Salma.".
Ya faɗa yana sassauta fushinsa.

"Hamma.."

Ummu Salma ta kira sunan shi cikin kuka da fitan hayyaci.

"Na ce ki kashe kan naki don Uban ki."
Ran maza ya ɓaci a gabanta ya duƙa lokaci ɗaya yana kallonta.
"Ai sai kin kashe kanki za ki nuna mana kaf ɗin mu ba mu da amfani ko matsayi a wajenki Ummu Salma."
Ya faɗa cikin ɗaga murya. Ta ɗago jajayen idanuwansa tana kallon shi, bai dagata ba ya cigaba da faɗin.

"Ammah da ta yi cikinki na tsawon wata tara ta kawo ki duniya ta rene ki, da Baffa da ya yi ɗawainiyar rayuwarki tun daga ranar farkon ki a duniya har zuwa girman ki. Da mu y'an'uwanki da muka yi rayuwa dake sama da shekara ashirin duk yau bamu da muhimmanci, wannan dai banza a banza da ba ki da amfani a wajen shi, wanda kika haɗu da shi a baya baya shi ne kike ikirarin kashe kanki saboda shi Ummu Salma?

Hawaye kawai ke shatata ta kasa magana, tana so ta yi ma Hamma bayanin yadda take ji amma ta kasa wataƙila ba zai saurareta ba, saboda bai taɓa riskan kansa a cikin halin rayuwar da take ciki a yanzu ba.

"Are you stupit? Ko kuwa kin rasa tunanin ki ne saboda wanda ko shekara biyu ba ki yi da sanin shi ba?  Da kin san shi? Ba ki san shi ba kuma kin yi rayuwa Ummu Salma ba ki mutu ba to yanzu ma haka za ki cigaba da rayuwa ba za ki mutu saboda wani wanda bai dace ya fita daga rayuwarki ba."

Ya karishe faɗa yana kallon ta, duk da tausayinta na kama shi amma ba zai nuna mata ba gwara ya yi mata jan ido domin ya ga ba ta da hankali.

"Za ki cigaba da rayuwarki kamar yadda kika fara tun farko. Bai hallata ki cigaba da kuka ko damuwa akan wanda bai damu dake ba, wanda ya yi miki sakin wulakanci har uku sannan ya sake ki da cikin shi a jikin ki ba tare da ya damu ba. To ki sani in kika sake cewa za ki kashe kanki saboda shi, to kin nuna ma duniya cewa ke ba y'ar halas ba ce."

Shuru ya yi yana kallonta tana ta kuka har da gunji.
"Wanda ke son ki ba zai ƙi haɗa jini dake ba Ummu Salma."
"Ai ya ma ce ba sonta yake yi ba mara mutumcin."
Ummin ikki ta katse shi ya ɗago yana kallonta.

"A takardan sakin abin da ya rubuta kenan maganganu masu muni ai tsakanin mu da wannan yaron sai Allah ya isa."

Ummin ikki ta sake faɗa tana matsar ƙwalla.
Hamma Abdulrrahman ya miƙe cikin mamaki yana faɗin" Ina takardan sakin?
"Ko yana hannun Baffa?
Ya sake faɗa.
Sai Ummin ikki ta amsa mishi da cewa yana hannun Baffa. Da sauri ya bar ɗakin yana zuwa falo ya ga Ammah da Baffa, yana ganin shi ya miƙe yana kallon shi.

"Baffa ina takardan sakin?

Ya tambaya yana miƙa masa hannu, bai yi musu ba ya laluba aljihun rigan shi ya ɗauko ya mika masa. Ya karɓa daga tsayen ya fara karantawa bai ko kai ƙarshe ba ya yi wurgi da jakar hannunsa da takardan yana faɗin.

"Wannan yaron so yake mu nuna masa matsayin mu Baffa."

Ya faɗa a fusace lokaci ɗaya yana ɗauko wayarsa daga aljihun wandon shi, da sauri Baffa ya riƙe shi yana tambayan shi abin da zai yi sanin halin shi rudaɗde ne in ran shi ya ɓaci.

"Abokin aikina zan kira. Baffa dole fa mu yi ƙaran wannan yaron mara tarbiya."

Ya faɗa har jijiyon kansa na miƙewa raɗau saboda ɓacin rai.

"Aa"

"Baffa za mu shigar da ƙara sai  mun yi shari'a da shi sai kotu ta karɓo ma Ummu Salma haƙkin ta."
Ya faɗa cikin ɗaga murya.

"Na ce maka A'a."

Shima Baffa ya katse shi a tsawa ce lokaci ɗaya yana ƙwace wayar hannun shi, Abdulrrahman ya fusata kawai sai ya fara zagayen falon yana ciccijewa saboda ɓacin rai, Baffa ya bishi ya riƙo shi yana faɗin ya je ya zauna ya samu natsuwa.

"Baffa wai ba ka karanta maganganun dake cikin takardan nan ba ne? Raina mu ya yi da zai rubuto mana haka?

Ya faɗa yana kallon Baffa cikin fusata.
Ammah na gefe zaune ba ta yi magana ba daman ta san sai an yi haka don ma ɗayan fusattacen bai zo ba Kabiru ai da Baffa ba zai iya da su shi kaɗai ba.

"Zo ka zauna ka natsu mu yi magana."
Da lallashi da ban baki ya amince ya zauna Baffa ya zauna a gefen shi.
"Kwantar da hankalin ka Abdulrrahaman."
Baffa ya faɗa yana kallon sa ganin yadda yake huci ba abin da ke yi masa yawo wai sai don jikinta ya aure ta kuma tunda ya gama mora shi ya sa ya yada ƙwallon mangwaro ya huta da kuda.

Tuna hakan da ya yi ya sa ya sake miƙewa a zuciye yana faɗin" Kai ina! Bai isa ya ci bulus ba, dole ne mu nuna masa kuskurensa yadda ko nan gaba ya ji an ambaci sunan gidan nan sai ya fara mazari don uban sa."
Da sauri Baffa ya sake riko shi yana ba shi haƙuri.

"Baffa ka bari mu koya masa hankali. Ko nawa zan kashe daga nan har kotun ƙoli so kawai na ke yi na ga ya wulakanta."

Abdulrrahman ya sake faɗa yana ta da jijiyoyin kansa saboda ɓacin rai.
Mirmishi Baffa ya yi kafin ya ce" Abdulrrahman"
Ya kira sunan shi yana mai kallon shi.
"Ba za mu je kotu ba, ba za mu je mu buɗe ma duniya cikin mu ba. Shi fa namiji ne ita kuma Ummu mace ce, ita ce za ta zama abin nunawa ba shi ba. Gwara mu kai shi kotun da ba wanda ya isa ya kwace daga zaluncin da ya yi ba wannan mahaluƙin in dai ka yi zalunci sai ka karɓi sakamakon ka, daidai da abin da ka ka aikata."

Hamma Abdulrrahman ya kalle shi cikin mamakin kalaman shi shi kuma Baffa ya jinjina masa kai kafin ya cigaba da faɗin" Kotun Allah Abdulrrahman. Mu bar shi da Ubangijinsa shi zai yi ma Ummu faɗa shi zai saka mata in sha Allahu."
Sai ya yi shuru yana sauraran Baffa ta wani fannin gaskiya ya faɗa.

"Za mu iya kai shi kotu mu yi nasara amma zafi da baƙin cikin dake zukatan mu ba za su gushe ba Abdulrrahman. Kuma ba za mu iya sauya cewarsa na baya son yar mu ba, duk abin da za mu yi sai dai mu yi ba mu isa mu ƙanƙarema Ummu bakin cikin zuciyarta ba amaimakon mu saukaka mata sai mu sake dagula mata lissafi."

"Haka ne Baffa."

"To ka yi hakuri da maganar shigar da ƙara. Ba wai don ba za mu iya sharia da shi ba ne. Aa sai domin mu taimaka ma Ummu wajen mantawa da shi, shi kuma Allah ne ya hana zalunci kuma ya yi, to ko Ummu ba ta furta Allah ya saka mata  ba wallahi sai Ubangijin adalci ya yi mata sakayya ko a nan duniya ko a ranar gobe ƙiyama.".

"In sha Allahu."

Ammah ta faɗa cikin sanyin murya Hamma Abdulrrahman ya yi ajiyar zuciya kafin ya yi magana Baffa ya dafa kafaɗan shi yana faɗin." Ina fatan ka fahimce ni yanzu ko?
"Na fahimta Baffa. Allah ya kyauta na gaba."
Ya faɗa yana jin fushin sa na sauka.

"Allah ya yi maka albarka "

"Amin Amin Baffa "

Ya amsa a sanyaye shuru na wani lokacin kafin Baffa ya tambaya Ummu.

"Na yi mata faɗa, Baffa ba a lallashi a irin haka, ba ta da hankali sai zuciya ta zuga ta."

"To yanzu dai ka koma ka matsa mata taci wani abu. Amman ku ta ce tunda suka zo ba ta ci komai ba, kuma ka ga ba ita kaɗai ba ce "

"To Baffa."

Ya amsa yana kallon shi.

"Baffa cikin fa? Mu za mu riƙe shi ko bayan ta haihu za a mayar da shi wajen uban shi?

Baffa ya girgiza kai kafin ya ce" A'a ba ka ji abin da ya ce a takardan ba ne?. Ba ya bukatar cikin shima "
Nan Baffa ya sanar da shi yadda suka yi da waliyin Habib da hukuncin da ya yanke.
"Baffa saboda dai ka ƙi yarda ne amma ai Ummu kaɗai muka aura masa ba da ciki ba. Bai isa ya ƙi karɓan abin da yake nashi ba ne ƙaryan shi tasha ƙarya"

"Ba komai. Ai Ummu ce za ta haifi koma mene ne, saboda haka ba za mu ƙi jinin ta ba."

Hamma Abdulrrahman ya jinjina kai amma da ace Baffa zai bari wallahi ba za su karɓi cikin nan ba sai an je kotu alƙali ya yanka mai kuɗin ɗaukan ciki da reno tana haihuwa bayan ta yaye ya zo ya karɓi abin ya ɗiga shi. Rayuwar Ummu ba za ta kare wajen wahala ba tunda ba shi da mutumci.
Umarnin Baffa ya bi ya koma ciki ya iske gabaɗayan su har da Saddam sun tasa Ummu kowa yana bata baki amma ba ta ji ba kuka kawai take yi tana gunji ko tsayawa ma jin kukanta bai yi ba ya ce a haɗo mata tea mai zafi a kawo masa ba musu Baɗɗo ta mike ta je ta haɗo mata daman akwai ruwan zafi a fulas ta ciko wani jug ta kawo ma Hamma Abdulrrahman ba wasa a fuskar shi yana miƙa ma Ummu jug ɗin ta karɓa hannunta na rawa.

"Shanye shi duka ki ba ni Jug ɗin ina jiran ki "
Ya faɗa ba wasa a maganarsa jiki da hannu na rawa ta karɓa ba ko gaddama ta kafa kai ta kwankwaɗe shi ta dire kofi su Baɗɗo na ta murna.

"Yauwa ko ke fa Ummu Salma yanzu ai kya ji dama-dama"

Ba ta gama rufe baki ba Ummu ta yunkura da sauri kafin ta iya miƙewa amai ya biyo baya duk kuma ruwan shayin da ta sha sai da ta amayar da shi a wajen nan Hamma Abdulrrahman ya matsa baya yana rufe hancin sa, saboda ba ya son ganin amai ko ya shaƙa yanzu nan shima zai fara fita ya yi ya ce in sun gyara wajen su sake haɗo mata wani shayin. Hamma Saddam ma ya bi bayan shi aka bar Ummin ikki ta kama Ummu zuwa tiolet ita kuma Baɗɗo tana gyara in da Ummu Salma ta yi aman.

Sai da aka gyara wajen aka kunna turaren tsinke ɗakin ya ɗau ƙamshi ita kuma Ummu Salma wanka Ummi ikkin ta yi mata domin jikin na ta ba karfi sannan duk ta ɓata kayan jikinta kawai sai ta taimaka mata ta yi wanka bayan ta fito Baɗɗo ta ɗauko mata wata doguwar riga cikin kayanta da suka zo da shi. Hamma bai tafi ba ya sake dawowa da wani kofin cike da ruwan tea ya ce Ummu ta sake shanyewa sai ta fara hawaye tana faɗin.

"Hamma zan yi amai."

"Ko sau ɗari za ki yi amai sai kin sha, in dai zai zauna a cikin ki."

Ta san halin shi in yana magana da lalama a yi abin da yake so in ya birkice bashi da kyau dole ta karɓa ta shanye.
Ya karɓi jug ɗin yana faɗin" Good. Ki riƙa cin abinci sosai kar ki bari na ji labarin kina zama da yunwa kin ji ko ba ki ji ba?

Sai ta gyaɗa kanta tana mai zubar ƙwalla
"Ba ki da baki ne?
"Na ji."
Ta faɗa tana danne kukanta.
Sai ya miƙe lokaci ɗaya yana faɗin" In ma kina so ki mutu ne ki yi mutuwar da Allah ya tanadar miki, amma in har saboda wancan  ne to ki sani har abada rayuwarki ba ta da wata amfani a wajen shi. Ki riƙa tuna hakan a cikin zuciyarki."

Daga haka ya fice ya koma falo ya yi ma su Ammah sallama da cewa zai tafi.

"Ka tsaya ka ci abinci mana."

"A'a Amma bana jin cin wani abu."
Jakarsa ya ɗauka ya rataya ya ce zai shigo gobe da safe kafin ya wuce wajen aiki in dai ba ta ci abinci da yamma ba Ammah ta yi masa waya zai sake dawowa da haka suka yi sallama ya fice Baffa ya koma ɗakin sa can ya bi shi suka yi sallama sannan ya fice daga gidan cikin tausayin Ummu har da su Baffa gabaɗaya gwara Baffa na bayyana damuwarsa Amma ce ke ɓoye abu kallo ɗaya ya yi mata ya fahimci ta rame a tsaye cikin yini ɗaya.

  Ranar sai dare Abdullahi ya kai Ummin ikki gida. Daman da ya dawo da yamma tare da matarsa Adda Suwaiba da Madibbo ya zo. Ita ce tare da Baɗɗo suka zauna da Ummu suna ta ɗan ba ta baki ta daina kuka sai dai suyan zuciya kawai. Baɗɗo nan ta kwana tare da Ummu matar Abdullahi sai wajen sha ɗaya na dare suka koma gida.
Washegari ma wajen ƙaryawa sai da Baffa ya zauna ma Ummu ta ɗan sha tea kaɗan shi ma ba daɗewa sai da ta yi aman shi, da rana faten wake Amma ta yi mata amma ba ta iya ci ba sai da Hamma Abdulrahman ya zo ya tsaya mata sannan ta tsakura haka da daddare ma sai da ya tsaya mata tunda suna gidan har dare tare da Adda Suwaiba kowa Ummu yake tausayawa. Habib kam ya sha tsinuwa da mugun baki Ummin ikki ma tana gidan har dare ita da Kaltume washegari kan Ammah ta fara karɓan baƙi masu zuwa mata jaje, yayyen Baɗɗo dukkansu sun zo Iklima har dare sannan ta tafi. A waya ma Ammah tana ta samun wayoyin sauran yaranta da matan su.
Hamma Jibo ya ce sai karshen sati Hamma Mustapha dai ya ce sai karshen wata za su shigo har Baffa duk sun kira suna mai jajanta musu da wannan lamarin da ya faru su da yake suna da sauƙin kai sun ce hukuncin Baffa ya yi daidai. Kuma duk sun yi magana da Ummu Salma ta wayar Ammah suna ta bata baki amma har yanzu Ummu ba ta daina kuka da damuwa ba.

Hamma Kabiru ne ya yi ta masifa a waya yana faɗin ba za su karɓi wannan cikin ba, ba wanda ya saurare shi daga AmmaH har Baffa sanin halin shi shi ma dai ya ce yana tafe a karshen satin nan.

Saboda hankula ba'a kwance yake ba shi ya sa Amma da Baffa suka manta da maganar kwaso kayan auren Ummu Salma.  Sai da su Umma Balki suka zo daga Mubi suke maganar kwaso kayan tunda duk Ammah ta sanar da su, abin da ke faruwa.

Da Ammah ta yi masa mganar kwaso kayan Ummu sai Baffa ya ce za a je a kwashe in zukata sun samu natsuwa. Kwanan su ɗaya suka juya cike da alhini.
Baffa ma ya sanar da su Baffa Umaru kowa ya ji labari sai jikinsa ya yi sanyi barin ma in suka zo suka ga yadda Ummu ta koma cikin kwana biyar ta faɗe ta rame ta lalace abinci in ba Baffa ko Hamma Abdulrrahaman suka tsaya mata ba, ba ta ci in kuma ta ci ba ya zama a cikin ta za ta amayar da shi. Sannan Baɗɗo ta ce Ummu ba ta samun barci da daddare.

Abdullahi shi kan shi ya ga ɗashewar Ummu Salma ya ce ya kamata a kaita asibiti a duba lafiyanta. Shima Baffa ya ga haka saboda komai ta ci baya zama a cikin ta.

Ranar Jumma'a da Safe Baɗɗo da Ummin ikki da Hamma Abdullahi suka kai Ummu Salma asibiti Boshin clinic in da take da fayel, suna zuwa likitoci suka riƙe ta acan suka ba ta gado likita na ta faɗa jininta ya hau ga maleria ga rashin cin abinci. Yana ta faɗan cewa yanayin zai iya zama barazana ga cikin jikinta.

Baɗɗo suka bari da ita, Ummin ikki da Abdullahi suka koma gida suka sanar da su da halin da ake ciki sannan suka zo da mata da wasu kayan sawa sai fulas ɗin ruwan zafi da kayan tea. Kwanta ɗaya a asibitin sai ga Hamma Kabiru ya zo shi kaɗai ya shigo garin daman Baɗɗo ne ta kwana tare da ita da safe Ummin ikki ta je tana taya ta zama sai Adda Suwaiba da Adda Ummu Sulaim da suka zo da rana su ɗan taya su zama.

Hamma Kabiru ya zo har asibitin ya duba Ummu Salma shi da Abdulrrahman da Saddam nan suka bar ma Saddam ɗin suka tafi, tana ta barci saboda an yi mata alluran barci tana ta samun barcin da ta yi kwanaki ba ta samu ba.
Hamma Kabiru da Hamma Abdulrrahman suka koma gida suka samu Baffa shi Hamma Kabiru faɗa yake yi don mai Baffa zai ce a karɓi ciki ai tun da dai ya amince shi ya ɗiga shi to bai isa ba.

"Baffa Ummu ta koma kamar wata horror tsabar rama da fari."
Ya faɗa cikin damuwa.
"Nima na ce Baffa ya bari a yi ƙararsa amma ya ce ba za mu yi ba."

"Baffa ka bari mu yi amfani da kuɗinmu mu jijiga duniyarsa kamar yadda ya jijjiga rayuwar ƙanwar mu."

Baffa dai ya yi shuru yana jinsu suka gama bambamin faɗan su suka sauka sannan ya yi magana da su kalaman dai da ya faɗa ma Abdulrrahman shi ya faɗa ma Kabiru ya dai bar maganar ne amma ba wai don ya fahimci Baffa ba, ai tunda ya nuna shi ba shi da mutumci gwara suma su nuna masa yan zamani ne, bai karanta takardan sakin ba amma duk kalaman dake ciki Abdulrrhaman ya karanta masa tun yana Jalingo.

Ba kwana zai yi ba a ranar yake so ya koma amma ya ce zai dawo tare da Adda Safinatu da yara su duba Ummu su ɗan kwana biyu. Hamma Abdulrrahman ya tafi saboda akwai in da zai je shi kuma sai ya shiga falon Ammah su sake gaisawa tun da lokacin da ya shigo gidan tana da baƙi, labari kamar ana ta aike maƙota duk sun ji labari ana ta shigowa yi ma Amma jaje har Baffa in ya fita haka za a tsayar da shi ana masa jaje, to ai tunda lamarin ya faru ba wanda ya isa ya hana a yaɗa labarin

Ko Ammah abin da Hamma Kabiru ya ke faɗa mata kenan ta lallashi Baffa ya bari su yi ƙaran yaron nan.

"Baffa ba zai amince ba Kabiru ku bar maganar nan kawai."

"Ammah to sai ya kashe mana ƙanwa! Kin ga yadda Ummun ta koma ne?
Amma ta yi shuru tunda ita dai ba ta je asibitin ba Baffa ma ya kasa zuwa amma dai sun yi waya da Ummin ikki ta ce mata ta samu sauƙi tana ta barci dai. Gwara ta samu barcin ko za ta samu yar natsuwa.

"Kawai Baffa ya koma gefe ya bar mana faɗan nan. Wallahi ko ba mu tura yaron nan gidan yari ba sai ya gane ba shi da wayau sai ya san ba a taɓamu a zauna lafiya. Ɗan iska kawai ni da man bai yi mini ba yana wani sunkunyar da kai kamar nagari Ammah ki tsoraci mutum mai kirki da surutun tsiya daga baya sai ya aikata mugun abu. Nonsense kawai"

Amma ta ɗan murmusa ba ta yi magana ba, in dai Kabiru ne da man karatun sa kenan ta kiyayi mutumin da ya cika kirki ba shi da gaskiya. Sake gyara zama ya yi yana kawo maganar da ta wuce wai bai so da man a yi ma Ummu aure ba kamar ya san abin da zai faru daga karshe kenan.

"Yanzu Ammah ina daɗin abin da ya faru? Ummu ƙaramar yarinya ta zama bazawara ga ƙaramin ciki. Haba don Allah in da a ce yarinyar nan ta ji maganar mu da yanzu ta kusa gama Degree ɗin ta da yau ba ta can akwance rai a hannun Allah saboda wani stupid irin yaron da ta aura"

Amma dai ta yi shuru tana sauraran shi yana ta faɗa yana nuna mata harda kuskuren Baffa da itama ma kanta tunda Baffa na jin maganarta ba ta hana a yi ma Ummu aure a wancan lokacin ba.

"Kabiru ka ishe ni fa. Baffan ne ke da laifi? In ya tara sani  zai aura ma ta shi? Kaddara ne kuma mu duka musulmai ne musan karɓan kaddara gare mu wajibi ne."

"Amma ki gane magana ta mana. Me ya sa aka goya mata baya! Da a lokacin ke da Baffa kun dage mata wallahi da ta koma makaranta ta bar ra'ayin aure. But kalli abin da ya faru at the end Ammah Rayuwarta ta da dawo baya fa."

"Haka Allah ya hukunta Kabiru ni ko Baffan ka ba mu isa mu sauya faruwan haka ba"

Shi dai sai wani kawo na shi tsarin yake yi Ammah ta gaji ta yi masa tsawa tana faɗin" Kabiru zan ci maka mutumci ba za ka bar ni na ji da damuwata ba, ka zo kana damuna da turancin ka na banza da wofi."
Domin daga karshe sai ya koma yana yi mata mgana da turanci sai da ya ji Ammah ta buɗe masa wuta sannan ya ɗaga hannuwa sama yana dariya.

"Afuwan Ammah na yi shuru."

Ya faɗa cikin harshen fillanci wata uwar harara ta maka masa da ya sa ya ɗinke bakin shi, shuru na wani lokaci sai da ta sauka don kanta ta tambayi Safinatu da yara, duk da ta kira ta waya ta yi mata jaje, ya ce duk suna lafiya yana tunanin za su zo karshen wata su yi musu ko kwana biyu ne Ammah ta ce Allah ya kaimu ya amsa da Amin.

"Ammah gaskiya ya kamata in Ummu ta haihu ta koma makaranta."

"To Baffa."

Ta faɗa cikin gatse tana hararan shi sai ya yi shuru yana dariya.
"Amma shawara ce fa."
"Ba'a son shawaran naka"
"Allah ya ba ki haƙuri Amman mu."
Ya faɗa yana ɗan mirmishi, sake maka masa harara ta yi shi kuma sai ya kwashe da dariya.

"Allah ya huci zuciyar Amman Lamiɗo"

Kamar ya sani sai ko ga shi ta yi mirmishi dariyan ya sake yi kafin ya ce" Da man na sani sunan Amini ne kaɗai zai saka ki dariya."
Amma ta yi mirmishi kafin ta ce" Kwana biyu ma ba mu yi waya ba. ya ko san abin da ya faru na Auta?
"An ya! Kamar bai sani ba don ko shekaranjiya mun daɗe muna waya kuma ban ji ya yi mini magana ba ina tunanin bai sani ba."

Amma ta jinjina kai kafin tace" Ko jiya na gwada lambarsa ba ta shiga. Haka ma Fatima itama ba na samun ta a waya."
"Mami fa kamar ba ta ƙasar, kwanaki mun yi chart da ita tace mini suna Paris."
Amma ta ce" An yi haka na manta Baffa ya faɗa mini sun yi tafiya. Lamiɗon ne na damu amma tunda har ka yi magana da shi yana lafiya Alhamdulillah."

Hamma Kabiru ya ce" Lafiyan shi lau Amma ga ma wani labari mai daɗi."
"Me ya faru?
"Kin kusa fara ganin ɗanki yanzu akai,-akai."
Amma ta washe baki tana fafin" Kai don Allah?
Hamma Kabiru ya gyara zama yana faɗin." Wallahi a shekaranjiyan

Please Login or Register in order to submit comment