Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

yi wannan manufar tawa da gaske na ke yi a kan ki."

"Habib kar ka lalata mini rayuwata don Allah"

Ummu Salma ta faɗa tana ji kamar ranta zai fita daga gangan jikin ta.

"Ni kuma in ban yi haka ba tawa rayuwarce za ta lalace ki gane mana. Ni tawa rayuwar ban ma fara ba ke kuma tunda kin fara taki ki bari kawai na ƙarisa lalatata gabaɗaya kowa ma ya huta."

Ya ƙarishe faɗa har yana shafa kumatun ta, kuka kawai Ummu Salma take yi kamar za ta shiɗe mai fitar da sauti. Habib na ta dariyan nishaɗi daga ƙarshe ma sai ya ƙure wakar Auta waziri na Autar mata ba ya son jin kukan ta, tana damun shi har suka isa gida ba ta daina kuka ba ta ɗauka yana ajiye ta sai juya amma ina tana saka ƙafa a bedroom ɗin ta yana shigowa tun da ta ga ya tura ƙofa yana nufota ta san manufarsa.

"Tunda ka ce ba ka sona to jikina ya haramta a gare ka Habib."

Ta faɗa lokaci ɗaya tana kuka samnan ta ƙamƙame jikinta da hannayen ta.

"Allah? To ai saboda jikin na ki na aure ki, kin ga kenan ba ki isa ki hana ni more abin da na biya sadaki saboda shi ba."

Yana gama faɗin haka ya tura ta , ta faɗa saman gado ya bi ta ya danne da ƙarfin tsiya yake so ya haye mata ta fara mutsu mutsun hana shi cimma burin shi a zafafe ya kifa mata maruka biyu a saman fuskarta.

"Saboda jikin ki na aure ki, saboda haka in kika kuskura kika sake saka mini hannu sai na yi miki illah."

Ummu-Salma ta ji kamar duniyar ta tsaya mata cak, tana mai kallon Habib da idanuwanta masu zubar da ƙwalla, ko motsin kirki ba ta ƙara yi ba har Habib ya raba ta da kayan jikinta ya biya buƙatan shi son ran shi ya tashi ya bar ta nan, hawaye ne masu zafi suke zubo mata ta gefe da gefen fuskarta. A cikin zuciyarta take jin wani irin zafi zafin da ba ta taɓa jin irin shi ba tun da Amma ta kawo ta duniya, ta yi kuka ta yi kuka kukan nadama da baƙin ciki sannan a karon farko ta ji ta fara tsanar Habib, tunda har ya iya kai hannun shi jikinta sannan ya haiƙe mata ba da son ran ta ba, ta daina faɗa da shi ne domin a yadda ya zuciya zai iya yi mata illa ita da abin da ke cikin ta, ta fi awa biyu tana kwance tana kuka ta kasa tashi sai da ta ji ana ta sallar azahar a masallatan kusa sannan ta iya jan kafafunta zuwa tiolet ta tsarkake jikinta sannan ta yo wanka da alwala azaune ta iya yin salla har kuma ta gama ba ta daina hawaye ba. Fuskarta ta yi jajir in da Habib ya mare ta har da tashin hannayensa zuciyarta ta yi duhu tana mata suya haka ta yini a cikin wannan halin bai kuma hana Habib dawowa gare ta da daddare ba, ba ta sake ƙoƙarin hana shi ba ta bar shi ya yi duk abin da ya ga dama da ita ya tsallake ta ya barta tana fama da suyan zuciya da hawayen bakin ciki da tausayin kanta. Domin ba ta isa ta hana shi abin da ya aura sabo da shi ba.

Tun daga ranar zaman su ya sake juya teburi. Hatta kayan abinci kaf Habib ya kwashe su a gidan nan ma'ana ta dinga ci da kanta, store ɗin ta bai bar ko ƙwayan abinci ba sai abin da ba a rasa ba da kuma ta gani ba ta yi mgana ba domin ita ta riga ta gama aminta da duka kalaman Habib, da gaske ba ya son ta sannan saboda jikinta ya aure ta kuma tana bashi yana cigaba da mora. Duk lokacin da ya ji bukatarta zai zo gare ta ita kuma za ta kwanta ta buɗe masa har ya yi ya gama abin da zai yi ya tashi ba zai yi mata mgana ba itama ba za ta yi masa ba, tun in yana yi tana kuka har ta samu nauyin zuciya ta daina kuka sai dai idanuwanta na kallon rufin sama tana mai jin suya a cikin zuciyarta. Ta ɓoye ma kowa halin da ta ke ciki har Baffa Umaru sai da ya kirata ta ce masa komai ya daidai ta, ta riga ta gama sarewa da rayuwarta, gwara ta zauna a duk wani tsanani daga Habib kar ta yadda ya sake ta saboda in ya sake ta a yanzu ya gama cutar da ita. Duk wani abu da mace za ta yi taƙama da shi Habib ya ɗauke da ga wajen ta, ba ta da komai sai rai kawai sannan ba za ta koma gida ta bar ma su Baffa abin faɗe a anguwa da dangi ba gwara ta cigaba da zama a yadda Ubangiji ya zaɓa mata rayuwa. Za ta zauna da Habib ta ba shi abin da yake so matukar zai barta ta cigaba da zama da auran shi a kanta

Ko da yaushe Ammah za ta kirata tana tambayanta yadda take sai ta ce suna lafiya haka ma Baffa, har Hamma Abdulrrahman sai da ya kirata yana mata jan ido da cewa Baffa ya faɗa masa an samu masalaha yana ta jan ta mganar cewa in Habib bai daina maganar zubar da ciki ba kar ta ɓoye masa ta faɗa masa shi zai tsaya mata, amma ta ce komai lafiya bayan sum gama waya ta yi ta kuka, da ma a ce za ta iya da ta faɗa masa komai amma ba za ta iya ba suna zaman su lafiya ba za ta zama silan matsala da damuwa ga iyayenta da ƴanuwanta ba. Tun tana jin Habib a ranta har ta daina jin sa kwata-kwata ya tozarta ta ya ci mutumcin ta, ta koma sai ta fita ta siyo dan abin da za ta ci kuɗaɗe ne a hannunta sama da dubu ɗari amma sai da suka ƙare a wajen ciyar da kanta da zuwa asibiti, tunda ta sake komawa cikin ta har ya shiga wattani uku sannan ga shi likita ya ce jininta ya yi ƙasa tana ɓukatar cin ganyayyaki saboda inganta lafiyanta da abin da ke cikin ta, ba saboda kanta ba saboda gudun jinin dake tare da ita, shi take so domin duk halin da ta faɗa saboda kare shi da ta yi ne shi ya sa nan duniya babu abin da take so da ƙoƙarin karewa sai cikin jikinta. Kuma a haka dare na yi Habib zai zo ya biya buƙatar shi da ita ko a jikinsa. Tabbas saboda jikinta ya aure ta, kuma yana moran abin shi son ran shi, Ummu ta gama sakawa a ranta jikin ta ne kuma da man Habib ya kusa kai sa zuwa ga expearing date ɗin shi, gwara ta bar masa komai ya ƙarisa shi tundaa shi ya fara.

Baɗɗo ba ta nan ta tafi gidan kakanin ta a Mubi, Shamsiya kuma ta kwana biyu ba ta ji ta ba, ba ta kiran kowa wanda ya kira ta kuma ta yi masa ƙaryan tana lafiya. Mami ma ta kirata tana ba ta haƙurin cewa ba za su samu zuwa jimeta ba za su je Paris ita da megidanta da yara sai dai in sun dawo ko ita kaɗai za ta zo ta duba su. Sai ta ji daɗin haka domin ba za ta so wani na ta ya zo ya ganta a cikin wannan halin ba, kuma ta tabbata in Mami da diro Jimeta sai ta zo gidan ta kamar yadda ta saba abu ɗaya take yi da ke saka ta farinciki kallon girke-girke a wayanta sai ko salla da karatun Qur'ani amma Allah kaɗai ya san girman nauyin da ke cikin zuciyarta ita kaɗai ta san abin da ke muƙurƙusanta a cikin zuciyarta ƙarfin imani ne kawai ke riƙe da ita.

****

Shafewar sama da kwanaki arba'in Ummu Salma na cikin wannan halin rayuwan Ammah ta kira ta a waya ta shaida mata zuwan Hamma Jibo tare da matarsa da yara. Sai ta yi saurin ce ma Amma za ta zo ta gaishe su, a lokacin ma ba ta da ko sisi ballanta ta yi kuɗin abin hawa, duk kuɗaɗen dake cikin acct ɗin ta ta gama kashe su a hidimar kanta.
jiya ma waken da take dafawa ta haɗa da allaiyahu ya ƙare, kuma tun jiyan ba ta ci komai ba sai ruwan zafi kawai take sha cikinta na ɗagowa. Farkon cikin ne take laulayi ba ta iya cin abinci yanzu kuma da ta ɗan samu sauƙi tana ci ko da za ta yi amai haka likita ya ce saboda abin da ke cikin ta. Ba ta da kuɗi ta kuma rasa yadda za ta yi Allah ya dube ta a washegari Hamma Mustapha ya tura mata 10k kamar ya saka ta a aljannah haka ta ji ta kira shi tana yi masa godiya kamar za ta yi masa sujjuda.

Kuɗin sun zo mata a lokacin da take cikin matukar buƙatar su shi ya sa gari na wayewa ta shirya ta tafi kasuwa. Sai ta kwana uku ba ta sa Habib a idanuwanta ba wata rana ma ba ya kwana a gidan sai ranar da yake da buƙarar ta to tana ganin shi, shi ya sa game da fita neman abin da za ta ci da lafiyanta, in za ta fita za ta ce Allah kana gani na fita da izinin ka domin lafiyata da abin da ke cikina, sai ta saka kafarta ta fita to haka ta yi ranar ta je kasuwa ta kaso dubu takwas sauran ta dawo dasu domin ta yi na abun hawa zuwa gida gobe. Abin da ba ta sani ba tana fita ba daɗewa motar Hamma Jibo ɗauke da Matarsa Nauwara da yara suka shiga haraban gidan su, suka iske ƙofar bangarenta a rufe kuma Hamman na ta kiran wayan ta, tana ringing amma ba ta ɗagawa.

Megadi ya tambaya shi ya ba su tabbacin ta fita amma yana tunanin ba za ta daɗe ba sai Nauwara ta ce su zauna a mota su jira ta. Haka ko aka yi suna cikin mota suna hira Ummu Salma ta shigo gidan tana tafiya kamar za ta faɗi hijabi ne a jikinta amma duk wanda ya santa in dai ya ganta sai ya firgita da raman da ta yi sannan ta ɗan yi duhu hasken ta ya ragu, hannunta ɗauke da ledojin da ta auno shinkafa da fulawa sai wake da manja sai kayan ganye tun da yanzu ta daina cin mangyaɗa saboda ta fahimci in dai ta ci abincin mangyaɗa to ba za ta kwana lafiya ba bayan amai ta yi ta fama da tashin zuciya.

Ko kaɗan ba ta ma lura da motar dake bakin bangarenta ba, har ta nufi ƙofarta ta sauke kayan hannunta tana neman maƙulli a cikin jakar ta sai ji ta yi an kira ta kuma da sunan da aka kirata yan gidan su ne kawai ke kiranta da sunan sannan kuma ta jiyo murya kamar ta Hamma Mustapha.

"Auta."

Da sauri ta juya ba Hamma Mustapha ba ne, Hamma Jibo ne mamaki ya kamata sai da daburce.

"Hamma."

Ta faɗa cikin sauri nan da nan idanuwanta suka kawo ruwa da ta gan shi sai ta ji kamar ta warke da duka matsalolinta. Hamma Jibo ya kalli Nauwara itama ta kalle shi amma ba su yi mgana ba ya fara takawa zuwa ga Ummu sai ya ga ta kwaso gudu zuwa gare shi, ko da take gida in ya zo tana murna da ganinsa har ta zo ta riƙe mishi hannu amma ba ta taɓa faɗawa jikinsa irin na yau ba sannan lokaci ɗaya ta kece masa da kukan da ya ɗaga masa hankali.

"Hamma."

Ummu-Salma take faɗa cikin muryan kuka rike ta ya yi a zuciyarsa yana jin wani iri, me ya samu Ummu ne duk ta rame ta lalace haka?

Ɗago kanta ya yi lokaci ɗaya yana share mata hawaye da tafukan hannayen sa

"Ya isa haka Auta. Ya isa haka."

Ya ke faɗa yana sake share mata wasu hawayen da suka kwaranyo.
Nauwara na gefe ita da su Saudat duk jikinta ya yi sanyi yaran ma sun raɓe a jikinta suna kallon Babansu da Annin su, duk da yara ne amma suma sun ji wani iri fuskar su ta yi ɗif alamun damuwa.

"Me ya same ki Auta? Ko kin yi ciwo ne?

Ya faɗa yana kallon ta, sai ta basar da tambayan tana sakin shi wajen Nauwara ta nufa tana gaishe ta.
"Adda Nauwara ina shirin zuwa na gaishe ku ne fa."
"To ai duk ɗaya ne mu ba ga shi mun zo ba." 
Ta ba ta amsa suna gaisawa ta jawo Saudat jikinta tana yi mata fillaanci sai ta ba ta amsa itama da fillancin amma ta haɗa da turanci. Ummu ta yi dariya ta ba ta hannu suka tafa lokaci ɗaya tana faɗin.
"Lalle za ku shirya da Amma yanzu."
Suka yi dariya gabaɗayan su Ammi na gefe ta yi karaf ta ce itama ta yi iya fillanci Ummu ta ce ta yi mata ta ji, bayan ta tambaye ta ina su Isma'il? ganin ba ta gansu ba da yaren fillanci sai kawai Ammi ta ma yar mata da amsar tambayanta da turanci.
Da cewa suna gidan wajen Ammah.

"Ke kam Ammi za ki ko shirya da takwaran na ki kuwa ?

Ammi ta tura baki tana rantsuwan ta iya, Saudat na cewa ba ta iya ba sai kawai Ammi ta fara kuka sai da Ummu ta rumgumeta tana lallashinta. Hamma Jibo ne ya ce a waje za su cigaba da tsayuwa sannan Ummu ta tuna da suna waje ne  da sauri ta wuce gaba suka bi bayan ta, tana can ƙokarin neman maƙulli Hamma Jibo ya duƙa ya kwaso mata ledojin da ta ajiye a ƙasa.

"Auta Kasuwa kika je ne?

Ya faɗa lokaci ɗaya yana duba ledojin hannunsa

"E Hamma."

Ta faɗa lokacin da ta ɗauko key din tana ƙoƙarin buɗe ɗakin, shi ko jikinsa ne ya yi sanyi har sake leƙa ledojin ya yi ganin abubuwan dake ciki, sai ya sake ɗagowa yana kallon Ummu lokacin da ta buɗe ɗakin tana cewa su shigo,  kallon matarsa ya yi itama ta kalle shi domin tana kusa da shi ne ta ga ƙulle ƙullen su manjan da ke ciki da shinkafa da wake da in an haɗa duka ba su wuce tiya ba.

  Sai da suka shiga falon suka zauna ita kuma ta kwashi kayanta zuwa kitchen sannan ta kawo musu ruwan a jug na famfo ne da ta siya, Hamma Jibo ya sake shan mamaki a ran shi sai yana tunanin ko dai mijin Ummu ya samu matsala ne a wajen aiki?
Nauwara ma tunanin da take yi a cikin ranta kenan amma ba ta furta ba.

"Anni ni swanwater na ke so na sha ba wannan ba"

Cewar Saudat. Da ya ke da Annni ƴa'ƴan yayyenta suke kiranta a matsayinta na ƙaramar uwa a gare su.

Ammi na jin haka itama ta ce" Anni ni kuma hollandian zan sha."
Ta faɗa da harshen turanci, Ummu ta kasa mgana ta yi wani wiƙi-wiƙi  da idanuwana duk Hamma  na lura da ita.

"To yanzu dai ba ni dashi ku fara shan wannan sai na fita na siyo muku."

Ummu ta faɗa cikin yaƙe da dariya.

"Haba. Ƙyale su Auta rigima ce"

"Adda ki bari na fita ko megadi na ba ma saƙo ya siya musu."

Hamma Jibo ne ya saka baki ya ce Aa, yaran ma ya yi musu jan ido ya ce su ɗau ruwa su sha in ba za su sha ba su bar shi, dole suka ɗauka suka sha kaɗan Hamma ma ya sha shi da Nauwara, miƙewa ta yi tana faɗin me za su ci ta dafa musu?
Da sauri Hamma Jibo ya ce" Sai da suka ci abinci muka fito fa, Auta ki yi zaman ki kawai."

"Dad ni egg zan ci "

Ammi ta faɗa kamar za ta yi kuka wannan karon Nauwara ce ta balla mata harara kafin ta ce" Ba shi kike taso kika bari a gidan Ammah ba? Zan zane ki fa"
Ta faɗa mata cikin harshen turanci lokaci ɗaya tana hararanta Ummu duk ta zama wata iri sai yaƙe take yi amma da ka ganta tana cikin damuwa.

"Auta taho nan ki zauna kusa da ni."

Ya faɗa mata yana mai nuna mata kusa dashi jikinta a sanyaye ta zo ta zauna kusa da shi kanta a ƙasa.

"Auta me ke faruwa ne?

Ya tambaya yana kallon ta, sai ta ɗago tana kallon shi cikin yaƙe kafin ta ce" Me ka gani Hamma? Lafiya ta lau na yi ta zazzaɓi kwana biyu ne "
"Haka Ammah ta ce sannu?
Nauwara ta faɗa tana kallon ta, Amma ta faɗa mata Ummu na da ciki shi ke ɗan ba ta wahala wataƙila shi ya sa duk ta rame.

Hamma Jibo ya yi shuru yana kallonta ya kasa magana.

"Hamma ba fa komai Allah."

Ummu ta sake faɗa tana faɗaɗa mirmishinta wanda ba ta san bai boye damuwarta ba.

"Megidan na ki ba shi da aiki ne yanzu?

Cikin mamaki ta ce" Yana aiki me ka gani Hamma?

"Na ga kin siyo abinci Auta."

Ya faɗa kai tsaye yana kallon ta cikin nazarin ta. Sai ta kasa mgana, kanta na ƙasa amma hawaye take yi ganin haka ya sa Hamma Jibo ya ce Nauwara ta kwashi yaran su shiga ciki zai yi magana da Ummu Salma. Da sauri ta bi umarnin sa ta kwashi yaran suka shiga bedroom ɗin Ummu suka zauna.

"Auta ki faɗa mini abin da ke faruwa ni fa ɗan'uwan ki ne, zan yi komai  domin ganin kin yi farinciki."

Kalamansa sake sake ruguza  rauninta ta sake fashe masa da kuka, kanta ya dafa yana ɗan bubbugawa alamun lallashi, sai da ta yi kukan ta ya ishe ta sannan ta warware masa komai amma shima ta ɓoye masa abubuwa da yawa kamar yadda ta ɓoye ma su Baffa, sai dai ta bayyana masa ita ke ciyar da kanta tunda har ya gannin ma idanuwansa ƙarya ba na ta ba ne. Har da haɗa sun da aka yi waje ɗaya kamar an samu masalaha duk ta sanar da shi.

Hamma jibo ya ji wani abu ya kama shi na tausayin ƙanwarsa da jin haushin Habib cikin faɗa ya ce" Kuma kike zaune yunwa za ta kashe ki Ummu ga su Baffa a kusa?
Tana kuka ta ce" Hamma ina son aurena sannan ina son iyayena ba na so na saka su cikin damuwa."

"Ai cutar da kanki da kike yi shi ne zai saka su a damuwa Auta."

Ya faɗa yana kallon ta, tana hawaye ta ce" Ka yi hakuri Hamma."
Kanta ya jawo a saman kafaɗanta yana lallashin ta.
"Ya nuna ba ya jin maganar na gaba da shi tunda an masa mgana ya nuna ya ji amma bai ji ba, sakarai ne shi? Ta ina aka taɓa haka? Kawai sai ya ce sai kin zubar da ciki saboda ba shi da tunani?

Ya cigaba da faɗa Ummu na ta kuka tana faɗin Hamma ka yi haƙuri.

"Ya zama dole su Baffa su sake sanin halin da ake ciki."

Ya faɗa yana sakin ta lokaci ɗaya yana ƙokarin ɗauko wayarsa.

"In ba haka ba wata rana zaki mutu ba a sani ba, kin ga yadda kika rame? Kuma kina da juna biyu in wani abu ya same ki fa?

Da sauri Ummu ta sauko ƙasa ta duƙa tana faɗin" Don Allah Hamma ka yi haƙuri, kar ka sanar ma da su Baffa ba na so hankulansu ya sake tashi."
Tsayawa ya yi yana kallon ta cikin mamakin ta.

"Hamma ina son na tsira da aurena ba abin da ya rage mini a yanzu. Don Allah kar ka bari su Baffa su san abin da ke faruwa."

Ya rasa yadda zai yi da ita ganin tana ta kuka shi ya sa sai ya mayar da wayar shi aljihu yana faɗin" To na ji ya isa."
Ya saka hannu ya ɗago ta yana share mata hawaye miƙewa ya yi yana ce mata bari ya je ya dawo.

"Hamma."

"Zan dawo yanzu."

Yana gama faɗin haka ya fice, nan ta zauna tana kuka Nauwara ta fito ta same ta, tana kuka ba ta tambayi ba'asi ba ta zauna tana ta lallashinta Ammi ta yi barci Saudat ne idanuwanta biyu da ya ke akwai wutar nepa sai Nauwara ta kunna mata cartoon zaman shuru suka yi Ummu ta daina kukan amma ba ta daina ajiyar zuciya ba.

Ba daɗewa sai ga Hamma Jibo ya dawo Allah sarki ɗan'uwa. Kayan abinci ne ya siyo mata mai yawa kuma shi ya dinga ɗauka yana shiga mata da shi cikin store, Ummu ta yi hawaye ta yi kuka tana yi masa godiya ba abin da bai siya mata ba har kayan tea sannan ya tura mata 100k ya ce ta riƙe a hannunta. Ba su daɗe ba ya ce su tashi su tafi da alƙawarin zai faɗa ma Baffa halin da take ciki amma ba zai bari a kashe mata aure ba, sai dai za a sake kiran Habibu a ji dalilin shi na yi mata horan yunwa.


*Janafty*
*FARGAR JAJI.*

*Wattpad:JamilaUmar315*
*Arewabooks:JamilaUmarJanafty*

"To Hajiya Hauwa'u Inuwa Aminu (Anty Hairi) with love and gratitude"

https://chat.whatsapp.com/LsC7Rjmei7J6Hd11e95nNS?mode=gi_t

*09*

Suna tafe a mota za su koma gidan Ammah, Nauwara ta fahimci mijinta na cikin damuwa tun fitowan su daga gidan Ummu fuskar shi ta nuna damuwar da yake ciki, ta fahimci akwai matsala amma ba ta so ta yi shisshigi tunda bai sanar da ita komai ba. Ga kukan da Ummu Salma ta yi ta yi, sannan ga kayan abincin da ya siya mata shima wani alama ne da cewa wani abu na faruwa.

Hannunta ta ɗora saman hannunsa dake saman sitiyari, ta riƙe ta ɗan matsa da ya sa ya kalleta lokaci ɗaya yana ma yar da hankalin shi kan tukinsa su Saudat na baya suna ta wasa ba su ma fahimci abin da ke faruwa a gaban motan ba.

"Ina fatan ba wata matsala ba ne game da Auta ba ko?

Nauwara ta faɗa cikin kwantar da kai tare da kulawa ga mijinta Jibril Hadi Baba.

Kai ya gyaɗa mata kafin ya sauke ajiyar zuciya.

"In sha Allahu komai zai yi dai dai."

"Allah ya sa. In sha Allahu."

Ta amsa masa cikin jinjina masa kai lokaci ɗaya tana yi masa mirmishi,  shima sai ya mayar mata da martanin mirmishin nata, amma gabaɗaya baya cikin natsuwarsa halin da ya iske Ummu Salma a ciki ya gama ta yar masa da hankali shi ya sa suna komawa gida sun ci sa'a Baffa ya dawo lokacin ɗakinsa kawai ya shiga Nauwara kuma da yara suka ya da zango a falon Ammah in da suka iske su Hassan da Hussaini na ta wassani isma'il ne ma ya yi barci.

Baffa ya razana da labarin da Hamma Jibo ya sanar da shi, ya yi masa zuru yana kallon sa cikin ɗimuwa da mamakin labarin da ya ba shi, wai Ummu na yini da yunwa saboda ba abinci ya tuna yadda store ɗin su yake rumbatsa da kayan abinci wani ba ya karewa ake sake kawo wasu, Baffa ba zai iya kirga shekarun da ya ɗauka bai siya hatsi ba, haihuwa ce ta yi masa rana har da ma waɗanda bai haifa ba suna yi masa, amma a ce ɗiyarsa na aure a garin nan amma tana kwana da yunwa saboda son rai da mugunta da zalunci irin na Habibu.

"Innalillahi wa'inna alaihirraju'un."

Baffa ya samu kan shi da furtawa saboda hankalin shi ya tashi matuƙa.

"Baffa wallahi hankalina ya tashi da yadda na ga Auta. Ba zan ɓoye maka ba sam ban ji daɗin ganin ta ba, tunda na baro gidan ta na ke cikin damuwa. Baffa Auta ta sauya tana neman mutuwa a cikin gidan nan ba wanda ya sani."

Ya karishe faɗa kamar ya yi kuka, da man shi yana da tausayi da rauni.

"Baffa ina tambayanta sai kawai ta fashe mini kuka, Baffa ka ga yadda Auta ke kuka, kamar ran ta zai fita amma a haka roƙona take yi kar na faɗa muku wai ba ta so hankalin ku ya tashi ni kuma na ce sai na sanar daku domin dole ne a yi wani abu tun kafin Auta ta samu wata matsalan a dawo ana wallahi tallahi Baffa."

Ya dire maaganarsa yana shafa naman goshin sa cikin damuwa.

"Gwara da ba ka rufe ni ba Jibo. Ai wannan ba mganar da za a yi shuru ba ne. Tunda tun farko mun

Please Login or Register in order to submit comment