Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

saki Ummu Salma, duk wanda ke gidan nan ya san waye Habib domin zuwa goma in Ummu za ta yi shi zai kawo ta ya kuma zo ya ɗauke ta kuma duk zuwa sai ya shigo ya gaida Ummi da Baba, tun kafin auren su ma bayan auren ma sai ya zama ɗan gida nan zai zo ɗaukan Ummu su zauna a falon Ummi da shi da Baɗɗo da Ummun suna ta hira suna dariya.

Kowa sai jinjina lamarin yake yi, abin mamaki abin tausayi ga rayuwar Ummu, da wayar da Ammah ta yi da Ummin ikki ko minti talatin ba a yi ba sai ga Hamma Abdullahi bakwai saura mintina ya iso gidan yadda ya shigo kawai za ka san shima labarin ya dake shi, jallabiya ce a jikinshi a baibai ya sako ta ma domin yana barcin nan na bayan asuba ya samu wayar Baffa labarin da ya faɗa masa ne ya sa ya diro daga kan gado bai shirya ba, ya razana da jin wai mijin Ummu ya sake ta! Har ya kariso gidan Ummin ikki yana tunanin to me ya sa zai sake ta? To ta yi masa wani abu ne?

Daga Ummin har Baɗɗo da hijaban jikinsu suka bi Abdullahi takalma kawai suka saka, suna tafe a mota Ummin ikki na sake kwashe ma Habib albarka Baɗɗo na daga baya tana ta sharan ƙwalla tausayin halin da Ummu take ciki a daidai wannan lokacin.

"Ummi to wai me ya sa zai sake ta? Ko ta yi masa wani abu ne?

Abdullahi ya tambaya jin yadda Ummin ke mgana da alamu ta san wani abu.

"Ba ka san abin da ya faru kwanaki ba ne Abdullahi?

"Ban sani ba Ummi, Baffa bai faɗa mini ba, haka ma Ammah."

Nan fa ta warware masa komai mamaki ya kama shi sai ma ya kasa mgana wato shi ya sa kenan ya ga Baffa Umaru ya zo har da mijin Ummu da ita kanta ashe lokacin duk matsalan ne ya ta so.

"Wai ba ya son ciki ka ji fa, sai ka ce shi uwarsa ba cikin ta yi ta haife shi ba wataƙila daga sama ya faɗo"

Ummin ikki ta faɗa cikin takaici da haushi.

"Allah ya kyauta."

Kawai Abdullahi ya ce amma maganganu na yawo a cikin ranshi, ta ya ya mutum zai auri macen da yake so kuma ya ce ba ya son ciki? Cikin kuma  na shi ne, daga karshe hadda saki? Kai gaskiya yana tamtama an ya mijin nan na Ummu Salma yana son ta kuwa? Domin wanda ke son ka ba zai yi maka wannan tozarcin ba.

Bai sake magana ba har suka isa gidan, a bakin flat ɗin Ummu suka yi parking ɗin motar, dukkansu kuma suka firfito, abin mamaki ƙofar falon Ummu ma a buɗe take har ga labule nan a waje shi ya sa kawai suka faɗa, Baɗɗo ce ta shige gaba da sauri Ummi a bayanta Abdullahi kuma sai ya tsaya daga waje bai shiga ba, a tunanin shi ko Habib ɗin na gidan abin da ba su sani ba tun wajen shidda da rabi ya tattara kayan shi kaf ya bar gidan a motar shi baya son ma wani cikin yanuwan Ummu su gan shi tun da abin da ya haɗa su ya raba baya fata ko son sake haɗuwa da duk wani abu da ya shafi Ummu Salma. Tunda ya ce ya gama da ita, to har abada ya gama da shafin ta.

Yadda Baɗɗo ta ga Ummu Salma ya sake tsinke mata zuciya tana zaune a in da ta yi salla kanta jingine da wardrope, ta yi kuri kawai ba ta magana ba ta kuma kuka amma fuskarta da idanuwanta sun kunbura babu kyan gani.
Rumgumeta ta yi ta fashe da kuka tana faɗin" Allah ya saka miki Ummu, da ikon Allah Habib sai ya ga sakamakon shi."
 
Ummu ba ta mgana tana dai kallon Baɗɗo kawai, Ummin ikki ta kasa mgana saboda tausayin Ummu har tana ƙwalla.

"Baɗɗo kamata ta tashi, ki kaita falo ki zo ki ɗan haɗa mata kayan sawan ta."

Da to Baɗɗo ta amsa, ta taimaka ta miƙar da Ummu tsaye ta riƙe ta zuwa falo, ta zaunar da ita a saman kujera ta zauna kawai tana kallon ta, bakin ma ya ɗinke ba mgana sai dai kawai ido.
Baɗɗo na kuka ta juya ta koma ciki tare da Ummin ikki suka cika akwatin Ummu huɗu da kayan sawan ta, Ummin ikki ta ce duk a cire zannuwan gadon kar su yi ƙura a tusa su cikin wardrope kafin a ga abin da Ubangiji zai yi, Baɗɗo ce ta yaye zanin gado sai ga takarda ta faɗo ta ɗauka ta buɗe ta karanta.

"Ummi."

Ta faɗa cikin ƙaraji lokacin da ta gama karanta takardan sakin Ummu Salma.

"Mene ne ya faru?

Ummin ikki ta faɗa cikin tashin hankali tana kallon Baɗɗo..

"Ummi saki uku fa Habib ya yi ma Ummu."

Ta faɗa tana nuna mata takardan hannunta

"Innalillahi wa'inna alaihirraju'un."

Ummin ikki ta faɗa kanta har yana sarawa.
"Wannan wani irin sakin wulakanci ne da tozarci?
Ta faɗa tana hawaye, Baɗɗo ba saki ukun take yi ma kuka ba illa maganganun da Habib ya rubuta masu alamu da tozarci da wulakanci bayan sakin

Karɓan takardan Ummin ikki ta yi ta ce bari ta kai ma Abdullahi bayan ta umarci Baɗɗo da ta yi sauri ta naɗe zanin gado ta kuma jawo akwatunan Ummu zuwa falo.

Abdullahi na tsaye jikin motar shi yana waya da Hamma Jibo.
Jiya sai wajen goma na dare suka isa, yana shirin zuwa wajen aiki ne Abdullahi ya kira shi yana sanar da shi mugun labari, shi ne  suke tattaunawa yana ba shi labarin halin da ya je gidan Ummu ya same ta a ciki har zuwan  da suka yi  shi da Baffa gidan waliyin Habibun ashe duk bai ji ba shi ne ya yi mata sakin wulakanci, sai a lokacin Abdullahi ya tuna wato ranar da ya ga Baffa da Hamma Jibo sun tafi ashe can suka je.

"Ni fa Hamma duk ban san abin da ke faruwa ba, kwanaki dai na ganta a gida duk ta rame to ni ban kawo cewa mata matsala ba ce."

Abdullahi ya faɗa yana nusar da hannunsa a cikin sumar kansa.

"An ɗauka za a iya gyara lamarin ne ashe bai zai gyaru ba."

Hamma Jibo ya faɗa daga can bangaren cikin damuwa da tausayin ƙanwar tasu.
Kafin Hamma Abdullahi ya sake magana Ummin ikki ta fito wajensa tana mika masa takardan hannun ta.

"Abdullahi ka ji tozarcin da wannan yaron ya yi mana? Saki uku fa ya yi ma Ummu?

Har Hamma Jibo ya ji abin da Ummi ikki ke faɗa a tare shi da Abdullahi suka saki salati cikin  firgici.
Kashe wayarsa Abdullahi ya yi yana mai karɓan takardan hannun Ummi ya fara karantawa a bayyane.

"Ni Habib Idris Mai Imani na saki matata Ummu Salma Hadi Baba saki uku, da ita da cikin jikinta bana ɓukatar su a rayuwata. Na sake ta ne saboda ni ban aure ta domin ina son ba, saboda jikinta na aure ta kuma na samu abin da nake so, shi ya sa na rabu da ƙwallon mangwaro na huta da kuda. Maganar ciki kuma sai da na ce ta zubar da shi ta yi taurin kai da a ce ta ji magana ta da ba haka ba, to ina so ku sani abin dake cikin Ummu Salma ba ni da alaqa da dashi har abada ba ni da danganta da abin da za ta haifa ballanta wata rana a neme ni saboda shi. Ni da Ummu mun rabu,rabuwa ta har abada ku ɗauka ma kamar ba mu taɓa sanin juna ba."

"Hasbunallahi wa'imal wakeel"

Ummi ikki ta faɗa tana mai riƙe kanta cikin baƙin ciki da takaici.

Abdullahi ya ma kasa mgana ji ya yi lamarin ya yi masa nauyi wannan wani irin tozarci ne, lalle wannan yaron bashi da mutumci duk yadda Abdullahi ke da saukin kai sai da ya fusata ya harzuka da wannan sakin wulaƙancin da Habib ya yi ma ƙanwarsu.

"Lalle wannan yaron ba shi da mutumci ba ɗan arziƙi ba ne. "

Ya faɗa yana jin wani irin zafi a cikin zuciyarsa. Baffa da Ammah kawai yake tunawa, in ya tuna da Ummu sai ya ji ya karaya, ya take ji yanzu? A wani hali zuciyarta take ciki, ya cuceta, ya cuce su sai dai Allah ya saka musu kawai.


*littafin Fargar Jaji na kuɗi ne a manhajar Telegram akan #1k. Tura Kuɗin karatun ku ta wannan acct ɗin 9069067488 JAMILA UMAR OPAY sannan sai ku tura shaidar biya ta waɗanan lambobin kamar haka.*

09069067488.
08032773332.

*Yan kasuwa masu buƙatar a tallata muku hajojinku a cikin wannan kayattacen labarin za ku iya tuntuɓata kai tsaye ta wannan lambar 09069067488 Na gode.*




*Janafty*
*FARGAR JAJI.*

*Wattpad:JamilaUmar315*
*Arewabooks:JamilaUmarJanafty*

"To Hajiya Hauwa'u Inuwa Aminu (Anty Hairi) with love and gratitude"

https://chat.whatsapp.com/LsC7Rjmei7J6Hd11e95nNS?mode=gi_t

*11*

*TUSHE, MAFARI*.

Mafarin ya fara daga Abdullahi(AUDU BABA) bafillace haifaffan garin Mubi. ita kuma Mubi ƙaramar hukuma ce daga cikin Jahar Adamawa Yola. Garin Yola nan ne maƙyanƙyasan sa tun daga kakkannin shi dai bai san wani asalin tarihin iyayen shi ba sai da ya san su a haifaffun jahar Adamawa, wasu suna cikin yankunan dake zagaye da Adamawa kamar irin su girai, funfore, ganye da dai sauran su amma shi asalin iyayen iyayen shi a garin Mubi sukai rayuwa shima anan aka haife shi anan kuma ya yi rayuwarsa har zuwa auran shi na fari da bafillatan matarsa mai suna Asma'u.

A matsayin shi na bafillace tsantsan na gaba da baya, kamar wajibi ne ya auri bafillatana yar'uwansa sannan da yake ba karatun boko matan suke yi da wasu mazan ba to ana yi musu aure ne suna da ƙananun shekaru, in har ka ga namiji ya yi karatu to sai in har fita ya yi cirani daga nan sai ya faɗa harkan neman ilimi , shima hakan ne ta kasan ce da shi yana da ƙarancin shekaru ya yi auran shi na fari kafin ya sake yin wani auren na gani ina so.

Lokacin ya fara shiga jahohin Nigeria domin fatauci ya faɗa garin Daura na Jahar Katsina a can Allah ya haɗa shi Ummu Salma(Gwaggo) ita ɗin haifaffiyar baƙar bafillata ce yar nan garin Daura ce ta uwa da ta uba, tunda Audu Baba ya ƙyalla ido ya ga Ummu Salma ya ji duk duniya ba wacce yake so irin ta a lokacin itama shekarunta ba su wuce sha biyar ba yarinya ce ƙarama ya ɗauka zai sha wahala kafin ya same ta amma sai ga shi cikin lokaci ya samu abin da yake so, tun ballanta da Ummu Salman take son shi ta ga dogon bafillace jajir tas a tsaye jarumi kuma Sadauki tuni ta ce shi take so, su kuma iyayenta ganin duk tushe ɗaya ne sai suka aura ma Audu baƙo Ummu Salma ya tafi da ita can garin su Mubi.

A lokacin ƴa'ƴan shi da Asma'u huɗu Hamza, sai Umaru, Salihu da Sha'aibu. Zuwan Ummu Salma ya sanya suka haɗe kansu suna zaune lafiya Ummu Salma ta ɗan jima ba ta haihu ba sai da aka yi ta karɓa mata taimako wajen shekaru biyar da auran su sannan ta haifi babban ɗan ta namiji wanda Audu Baba ya yi ma huɗuba da Hadi bayan shi kuma ba ta sake haihuwa ba har sun cire rai ma gabaɗayan su sannan ta samu Fatima wanda tsakanin su da Hadi shekaru sha bakwai ne. A lokacin da aka kawo Ummu Salma wacce kowa ke kiran ta da Gwaggo akwai wata maƙociyarsu da aka yi ma Gwaggo uwar ɗaki da ita tun lokacin da aka kawo ta Daura wacce ake kira Nenne tsada saboda hasken fatan ta duk yankin a lokacin ba mai jan ta, shi ya sa ake kiran ta Nenne tsada ita ta zama kamar uwa ga Gwaggo tun kawo ta garin zuwa yanzu komai nata da na ƴa'yanta Nenne take shigewa gaba ita Nenne Allah bai ba ta ɗa Namiji ba duka ya'ƴanta mata ne sannan in ta haihu sai su yi wabi a cikin yara goma da ta haifa huɗu kawai suka tsaya mata, Balki ce babba sai Salamatu sai A'i, sannan autar ta Jamila wacce a lokacin yar shekaru goma ce to bayan Jamilan ma ta sake haihuwa sau uku suma suna yin wabi su kaɗai ne ta samu suka tsaya mata, tunda da daɗewa megidanta ya rasu ita kaɗai ce ke gwagwarmayan riƙe marayun ƴaƴan nata.

A lokacin Gwaggo tana cewa ta kama ma Hadin ta Jamila matsayin mata, tun ana ɗaukan maganar wasa har dai Gwaggo ta tabbatar da ita ba wasa take yi ba. Tun Jamila na ganin Hadi tana gudunsa har ta daina domin shi bai taɓa ɗaukan maganar Gwaggo da muhimmamci ba tun ballatana a lokacin shi ɗan gayu ne tunda yana makarantan boko, Jamila kuma karatun allo suke yi a lokacin sannan tana da wata Aminiya da suke tare tun suna yara mai suna Aisha. Gida uku ne ya raba tsakaninsu duk in da za su je tare ne sannan makarantan allo ɗaya suke zuwa iyayensu su san juna, ko kaya ne in za a yi ma Jamila sai an yi ma Aisha haka itama gidan su Aisha ba sa nuna cewa Jamila bare ce, Aminci ne mai karfi a tsakanin su tun suna yara har kuma girman su sai da Ubangiji ya saka aminta da yarda har a tsakanin ƴaƴan su.

  Jamila na da shekara sha shidda a duniya bayan ta yi saukan Allo aka saka ta a lallen aure ita da Hadi. Shi a lokacin yana da shekaru ashirin da shidda ne, kuma yana gama sakandiri amma bai cigaba da karatu ba sai dai yana yin noma sannan yana kiwo. Auren gata aka yi musu auran da har bayan shekaru masu yawa suke zaune a ƙarƙashin kulawan iyayen su a garin Mubi suka fara gudanar da kyakyawan rayuwarsu a farkon auran su Hadi ba ya son Jamila amma da tafiya ta yi tafiya sai ya ji ya gode ma zaɓin Gwaggo har bayan ranta in ya tuna da abin alherin da ta yi ma rayuwarsa sai ya gode ma ta sannan ya yi mata addu'an samun haske a cikin kabarin ta.

A shekaran auran su Jamila ta haifi yaron ta na farko mai suna Jibril ana haihuwan shi Gwaggo ta ce an samu Jibo shikenan sunan ya bi shi har girman shi, Jibo ya taso tsakanin iyaye da kakanni ne shi ya sa Jamila(Ammah) ba ta sha wahalan renon shi ita kaɗai ba sunan da Hadi(Baffa) Ammah ce ta fara kiran shi da Baffa har ya kama bakin yaran gabaɗaya, bayan Jibo ta sake haihuwan Mustapha tana da cikin Mustapha suka saka Aminiyarta a lalle Aisha ta yi aure a garin Girai duk da ba ta son auren amma hakan nan aka kaita kuma ta zauna sai ya kasance ba a gari ɗaya suke aure da Jamila(Amma) ba.

Haka dai rayuwa ta cigaba da gudana cikin farinciki, Nenne ta fara rasuwa maciji ne ya sare ta a makewayi sai dai gawarta aka iske a kwance shike nan su Ammah sun zama marayu Allah ya sa ma dukkansu sun yi aure a cikin garin Mubi shi ya sa sai maraicin ya zo musu cikin gata Ammah ta fi kowa jin mutuwar Nenne amma samun Baffa kusa da ita ya sa ba ta daɗe ba ta warware uwa uba ga Gwaggo ga Baba ita yar gata ce gaba da baya ba sa barinta ta yi kukan rashin wani abu saboda soyayya da gata. Ga ƙanwar Baffa Fatima da kusan a tare suke rayuwa tun da ba wani tserayan shekaru ne a tsakanin su ba.

Ta haifi Mustapha ko shekara bai yi ba suka sake samun wani rashin na rasuwar Audu Baba shima lafiya lau ya kwanta da asuba rai ya yi halin shi tsakanin shi da Gwaggo kwana arba'in, da man tun rasuwar Baba ba ta da lafiya ashe itama ajali ne Baffa da Ammah sun fi kowa shiga cikin tashin hankali gaba da baya maraici ya sarƙe rayuwarsu yanzu ba su da mai kula da su, Ammah ta rasa mai duba ta, mai kula da ya'yanta da duka rayuwarta sun yi kuka kamar ba za su daina ba. Ga Fatima da take ƙarama a lokacin abin tausayi da Baffa ya so ya karɓi riƙon tilon ƙanwarsa amma sai dangin Gwaggo da suka taho daga Daura suka ce za su tafi da ita saboda ita mace ce sannan Baffa kuma ba kai girman da zai iya rike wani ba shima yana da iyalansa tunda Baba baya raye yana ji yana gani suka tafi da Fatima Daura ko gadon su na Baba da Gwaggo da aka raba su suka tafi da shi, shi kuma ganin ba Gwaggo ba Baba sai ya fara tunanin barin Mubi duk da akwai Umma(Asma'u) da sauran ƴan'uwansa maza amma duk da haka sai garin ya yi masa ƙunci Ammah ma duk ba ta cikin walwalarta tun ballantana da Fatima ta bar Mubi zuwa Daura rashin ta dameta sosai tana kuka tana cewa za ta iya riƙe Fatima me ya sa Baffa ya bari aka tafi da ita? Lallashinta ya yi ta yi saboda shima bashi da tacewa a lokacin a matsayin sa na ƙarami sannan su Hamma Hamza a lokacin ba su hana ba to shi ma bai isa ya ce komai ba.

Da kuɗin da aka raba musu gado Baffa ya fara bin matasa garin da sukan shiga cikin birnin Yola kasuwanci yana ɗan taba harkoki a can farko ya ɗan faɗa harkan siyar da siyarwa ne daga baya kuma ya fara haɗawa har da cinikiyar dabobbi irin su shanaye da raguna, duk abubuwan dai ba su tafi daidai ba sai ya faɗa harkan siyan tsoffin ƙarafan motoci ya fara daga ƙananun karafa ne sanadiyar wani abokin kasuwancin sa da suka haɗu a garin Yola shi ya ba shi tabbacin harkan ana samu sosai kawai sai ya faɗa kuma bai rufe shekara ba ya ga haske a cikin lamarin, yana daɗewa baya gida tunda ba iya Yola yake harkokinsa ba ko'ina har Lagos da ibadan suna haurawa neman ƙarafa sai dai in ya ga mai zuwa gida ya tura ma Ammah da su Umma saƙo wani lokacin sai ya yi wattani biyar ba ya gida amma duk da haka bai manta da tilon ƙanwarsa ba yana tura kuɗi can gida Mubi ya ce in an samu mai zuwa Daura akai ma Fatima sannan duk salla yana yi mata sutura tunda suna kawo ta salla ƙarama in kuma sallar layya ce Baffa da Amma ke zuwa can Dauran saboda dai kar Fatima ta yi maraicin rashin iyaye da ƴan'uwa.

Kuma Alhamdulillah Fatima ta samu iyayen riƙo na gari. Wanda ke riƙon ta ƴaya maza suke da Gwaggo Madibbo shi Allah bai ba shi haihuwa ba ne har sun fara tsufa shi da mai ɗakin sa, sannan yana aiki a gidan Sarkin Daura shi ke kula da bargan dawakai na cikin masarautan gabaɗaya. Fatima ba ta yi karatun boko ba amma tana yin karatun addini. Shekaran su Gwaggo uku da rasuwa Baffa da Ammah da yaran su biyu suka yi ƙaura daga mubi zuwa garin Yola acan Baffa ya kama musu haya suka fara zama saboda harkokinsa suna daɗewa a can shi ya sa ya ga gwara ya ɗauko ta, ta dawo kusa da shi amma in salla ne ko aka yi wani abu ba su manta da mafarin su ba suna zuwa Mubi tunda can ne gabaɗayan yan'uwan suke Ammah ma duka yan'uwanta suna Mubi ga Aminiyarta dake aure a Girai sai dai har lokacin ba ta haihu ba amma in dai Amma ta je Mubi ta kan karisa can Girai su zumunci da amincewar Baffa kamar yadda ya saba bata dukkan wata dama ba ya tauye mata haƙƙin ta na aure ta kowani bangare godiya take yi ma Allah da ba ta auri Baffa ba da ta zama mai asara a cikin mata.

Baffa da kansa ya je Daura ya taho da Fatima ya kawo ta Yola ta ga in da suke da zama ta yi kwanaki da su kafin ta koma kuma lokaci bayan lokaci tana zuwa duba su musamman Baffa zai tura mata kuɗin mota domin ta zo, yana ƙaunar ƙanwar shi, itama tana son yayan ta guda ɗaya da suka haɗa uwa saboda yana kula da ita sosai. Tana da shekaru sha bakwai kwatsam mariƙinta Madibbo ya aiko masa da cewa ya zo Daura yana son ganin shi akan Fatima ne ba ɓata lokaci ya shirya ya tafi yana zuwa sai ya ji labarin da ya girgiza shi wai Fatima ta samu miji, amma mijin ba kowa ba ne sai yaron Sarkin Daura. Sarkin Daura a lokacin Alhaji Muhammad Shitu Daura ne sarki na 49 a lokacin.

Kuma ɗa ne ga sarki Alhaji Bashar Daura sarki na 39 a wancan zamanin, Sarki Alhaji Muhammad Shitu  yana da tarin ƴa'ƴa amma duka duka yaran shi maza guda biyu ne Babban ba shi da lafiya ana ta raɗen raɗen an haife shi da ɗan matsalan ƙwaƙwalwa, sai kuma na biyun Muhammad Nasiru(Hakimin Daura kuma Yarima mai jiran gado) domin tun a lokacin ana tunanin shi ne zai gaji sarauta daga mahaifinsa saboda zamowarsa tushen masauratan Daura. Mahaifiyarsa Hajiya Ruƙayya(Fulanin Daura) duk da fa a wancan lokacin ba ita ce uwargidan Maimartaba Alhaji Muhammad Shitu ba, Hajiya Rakiya Muhammad Shitu ce(Magiyar Yamman Daura) amma ita ce mafi soyuwa a gare shi tunda ita ce mahaifiyar Hakimin Daura sannan Yarima mai jiran gado.

Labarin ga shi dai mai daɗi ne amma kuma ba shi da daɗi a mahanga da yanayin tsarin rayuwarsu na talakawa, ina Fatima ina Yarima mai jiran gado! Ai haɗin ma bai yi ba akwai tazara mai yawa su da ba kowa ba, sai talakawan gari ina su ina haɗa kafaɗa da masu garin gabaɗaya nan da nan Baffa ya nuna bai amince ba shi bai ma yarda son Fatima yake yi ba domin bai ga ta in da suka haɗu ba, ballanta har rayuwarsu ta haɗu waje ɗaya. Amma mariƙinta ya dage da cewa Yariman Daura mutumi ne na gari mai taimakon talakawa, mai alheri ga matasa mai son talakawaa kuma mutanen garin Daura suna son shi kamar yadda ake son mahaifin shi.

Sai dai duk da haka Baffa bai amince ba duk sun faɗa masa a gidan Sarkin Yariman Daura ya ga Fatima lokacin da ta je kai ma Madobbi abinci kuma ya ji nan duniya ita yake so ya kuma je ya yi magana da mahaifinsa. Shi kuma Sarkin Daura a lokacin Marigayi Alhaji Muhammad shitu ya sa aka kira Maddibo mariƙin Fatima ya yi magana da shi a cewarsa da talaka da mai kuɗi da mai sarauta duk Allah ne ya yi su, sannan tunda dai Muhammad Nasiru ya ce yana son ta shi kuma ya yi alƙawarin samar masa da duk abin da yake so amma duk da haka Baffa bai amince ba haka ya dawo Yola cikin damuwa da Amma ta tambaye shi sai ya sanar da ita abin da ke faruwa itama ta ce gaskiya abin ma bai haɗu ba ta ina Fatima za ta kai kanta a matsayin auran ɗan sarkin? Sarkin gobe itama ta goya masa baya kan hukuncinsa saboda haka ma ya ce zai ɗauko Fatima ta dawo hannun shi ya saka ta a makaranta ta yi karatu nan gaba Allah zai kawo mata mijinta ta yi aurenta amma ba ya jin zai yi kasadan wasa da rayuwarta wajen kai ta in da ya fi karfin zuwan ire-iren su.

Ba ƙwace Fatima ya yi daga hannun mariƙanta Modibbo ba amma dai ya nuna zai karɓe ta riƙon ta ya dawo hannun shi tunda Allah ya rufa masa asiri shi kuma Madibbo sai ran shi ya ɓaci da ganin kamar Baffa ya raina masa ne sai ya tara yan'uwansu dangin Gwaggo ya faɗa musu halin da ake ciki nan aka ba ma Baffa rashin gaskiya suka kuma hana shi ɗaukan Fatima daga ƙarshe suka yanke shawaran tura wakilan Sarki can Mubi wajen su Baffa Hamza domin su yi mgana tunda suma suna da haƙƙi, Baffa ba da yawun shi aka aminta da auran Fatima da Yarinman Daura ba lamarin bai yi mishi ba tun ballanta da yaji auren a matsayin auren sirri ba wanda zai ji labarin auran daga Daura a cewar Maimartaba saboda

Please Login or Register in order to submit comment