Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

take yi a kanta cewa tunda yanzu ta zama bazawara ba ta bukatar ta.

Tana ta hawaye ita kaɗai tana zaune da waya a hannunta.
Jikinta ya fara karkawa ne lokacin da hoton ƙasa suka buɗe. Sai ta ga kamar ko idanuwanta ke yi mata gizo ba gaskiya ba ne. Har sake murza idanuwanta ta yi ta sake ƙura ma wayar idanuwanta cikin fitan hayyaci.

Zuciyanta ne ya tsaya da bugu na lokaci ɗaya.
Me take gani haka?
Shamsiya ce da Habib cikin shigar alfarma a cikin hotunan nan guda biyu.
Ɗaya ya kwanto ta bayanta ya haɗe hannayensu a saman cikinta. Dayan kuma tana zaune a kan kujera shi kuma ya tsaya a bayanta suna masu kallon juna suna mirmishi cikin yanayin da amarya da ango kan yi a lokacin yin hotunan pre-weeding pic, tamtama take yi kamar ba Habib ta gani a jikin hoton ba sai dai kuma ina shi ne domin ba za ta taɓa mantawa da kamaninsa ba har abada.
Habib ne mijin da Shamsiya za ta aura?

"Kai gaskiya sun dace."
Ta ga saƙon wata Hamdiya"

Kar dai a ce Shamsiya Habib za ta aura tunanin da take yi kenan zuciyanta na sake tsinkewa.
Ko ba ta san Habib ba ne? Ko ba ta san Habib shi ne mijin da ta aura ba? To ai in mijinta ne a da a yanzu ba mijinta ba ne sun rabu. Ba kuma za ta ce Habib bai san Shamsiya ƙawarta ba ce, ba kuma za ta ce Shamsiya ba ta san Habib ba.

Dukkansu sun san juna, kuma shi ne za su yi aure! Da man shi ne mijin da ta samu lokaci kaɗan? Ko da man shi ne dalilin da ya sa ta ja baya da ita. Ta sani ta san Habib ne za ta aura ta sani kuwa.
Zuciyan Ummu ya daina aiki kwata-kwata kanta na sarawa ta ma rasa tunanin da za ta yi, wayar na hannunta addu'oin fatan alheri ke ta shigowa ga Shamsiya da mijinta Habib, tun tana tunanin mafarki take yi har ta gasgata a zahiri ne yake faruwa. Ta kashe wayarta yafi sau uku tana sake kunnawa amma still in ta sake shiga hotunan take gani hoton Habib da Shamsiya a cikin yanayin farinciki.

Ta kasa zama ta kai gauro ta kai mari a cikin ɗakinta. Tana jin har abin da ke cikinta yana juyawa tsabar halin datake ciki.

"A'a Bestie ba za ta auri Habib ba."

"Ba za ta aure shi ba."

Take faɗa tana kallon hotunan lokaci ɗaya tana faman girgiza kai. An ce kuka ma Rahama ne ta kasa kuka amma a kasan zuciyanta take jin wani irin zafi zafin da ba ta taɓa jin irin shi ba har ya ninka irin zafin da ta ji lokacin da Habib ya sake ta. Ta kasa gasgata gaskiyan abin da ta gani, in har auren ne da gaske to watakila Shamsiya ba ta san Habib ba ko shi ne bai gane Shamsiya kawarta ba ce, ga shi dai zuciyanta na cigaba da hasko mata hotunan su a lokutan da Shamsiya da Habib suka sha haɗuwa tun kafin aurenta da shi har ma bayan auren amma wani shashi na zuciyanta faɗa mata yake kila dai kuskuren fahimta ne ba abin da idanuwanta ke ganin mata ba ne.

Saboda ma ta samu tabbacin abin da ta gani sai ta sake duba katin bikin ga sunan Habib Idris Mai imani nan raɗau a jikin katin tare da na Shamsiya.

"Aa No.."

"Ba gsskiya ba ne."

Ta faɗa kamar mahaukaciya. Ba ta yarda ba zuciyanta ba ta aminta da abin da ta gani ba tana bukatar wani ya yi mata karin bayani
Jikinta da hannunta na rawa ta lalubo lambar Shamsiya ta kira ta amma kira sama da sau goma ba ta ɗaga kiran ta ba, in wayar na ringing tafiya yake yi da bugun numfashin Ummu Salma tsabar tashin hankalin data ke ciki.

Ganin da ta yi tana ɓata lokaci a daran nan a wannan lokacin take son karin bayani take kuma son sanin gaskiyan komai tun kafin zullumi da fargaba su saka zuciyanta bugawa. Wani dogon hijabin da take salla ta raruma ta saka a saman bakar doguwar rigar jikinta.
Har ta fito falo sai ta tuna ba ta ɗauki kudi ba sai ta koma da gudu ta yayo mu ƙaramar jakarta dake saman madubin dakin, tunda ta dawo daga asibiti ta ajiyeta a wajen wayarta na hannunta ta fito, takalmin Ammah dake kofar ɗaki wani na roba na zirga-zirgan tsakar gida ta zura ta fice daga gidan ba tare da tunanin komai ba, tana jiyo hiran Ammah da Baffa a turakansa amma ko waiwayowa ba ta yi ba, a lokacin hankalinta ya bar  gangan jikinta. So kawai take yi ta buɗe idanuwanta a cikin na Shamsiya ta nuna mata hotunan da ta gani ta ji shin abin da ta gani gaskiya ne ko ƙarya ne?

Ba ta ko ganin gabanta kafin ta isa titi ba ta san adadin sau nawa ta ci tuntuɓe ba, amma ba ta damu ba Kekenapep ta tsayar ta shiga ta ce ya kai ta barraks road suna tafe amma ji take yi kamar ta yi tsuntsuwa ba ta taɓa ganin nisan gidan su Shamsiya ba sai a ranar suna isa tun daga kofar gidan ta san ana sha'ani domin get ɗin gidan ma yana buɗe ne ga motoci nan birjit a haraban gidan wasu har waje, ba ta damu da kowa ba, ita dai ta san ta fiddo kuɗi da ba ta san ko nawa ba ne ta mika mai nepep ɗin daga nan sai kawai ta tsinci kanta a falon gidan su Shamsiya akwai mata ga sunan da yawa amma idanuwanta ba su tsaya tantance fuskokinsu ba. Waige-waige kawai take yi ba wacce idanuwanta ke son gani irin Shamsiya.

"Wa nake gani kamar Ummu Salma."

Ta ji an faɗa daga bayanta tana juyowa sai ta ci karo da Anty marikiyar Shamsiya.
Mirmishin dole ta yi mata wanda ya tsaya iya saman fuskarta.

"Ni ce ina yini Anty"

Ummu ta faɗa tana sauke numfashi.

"Lafiya lau sannu Ummu Salma."

Ta faɗa tana kallonta daga sama har ƙasa.

"Ai na yi ta cewa Shamsiya za ta rako ni gidanku na yi ma Umman ki jajen abin da ya faru ban samu dama ba."
Ummu ta sunkyar da kai, amma tana ta kalle kalle domin hango ta in da za ta ga Shamsiya.

"Allah ya kyauta na gaba. Allah ya zaɓa mafi alheri."
Ko amsata Ummu ba ta yi ba domin ba ta ita take yi ba.

"Kin samun kin rarafo kenan? Da man da na ga ban ganki ba Shamsiya ta ce ai kin yi nauyi."

Da gaske kenan Shamsiya za ta yi aure, amma dai da tabbacin Habib za ta aura ne ba ta sani ba kuma shi ta zo ta sani daga bakin ita Shamsiyar.

"Shiga ciki tana cikin ɗakinta ba ta ma daɗe da dawowa daga wajen gyaran kai ba"
Ko kafin Anty ta gama magana Ummu ta wuce ta zuwa cikin ɗakin Shamsiyar da dama ta san ɗakin.

Kofar ma tana buɗe suna ta hayaniya ta san ta shiga cikin ɗakin kuma ta ga harda yayyen Shamsiyar a ciki amma wacce idanuwanta ke son gani ta nema sai ko suka haɗa ido tana zaune gefen gado ta buɗe kanta yan'uwanta na duba gyaran kan da aka yi mata.

"Kai Ummu kin rarrafo kin zo?

Badawiyya yayar Shamsiya ta faɗa bayan duk hankula ya dawo kanta.
Ita dai kawai tana yaƙe ne amma hankalinta da natsuwarta na kan Shamsiya.

Wato ta ce ba za ta samu zuwa ba ne saboda ta yi nauyi to ai ba ta yi ƙarya ba tabbas ta yi nauyi tunda ga nauyi nan a gabanta tana fama da shi.

"Bestie sannu da zuwa."

Shamsiya ta fada bayan ta taso zuwa gare ta har tana riƙo hannunta.
Ta kuma ja ta har gefen gado ta zaunar da ita, ita kuma kamar gaula ta zauna.
Suna ta yi mata sannu ta kasa amsawa kawai Shamsiya take kallo ko a jikinta sai jikinta ya bata wata kila ba gaskiya ba ne Shamsiya za ta yi aure amma ba Habib ne mijin da za ta aura ba.

"To mu je ko mu bar Bestie ta gana da Bestien ta."

Badawiyyya ta faɗa tana tattara sauran yan matan dake ɗakin, wasu ta san su yan'uwan su Shamsiya ne wasu kuma ba ta ma tsaya iya gane su ba. Tunda in dai na kusa da Shamsiya ne ta san su kamar yadda itama ta san duk wani da ya shafe ta. Kamar yadda Shamsiya take zuwa gidansu itama haka take zuwa nan gidan wajen Shamsiya tun ma kafin ta yi aure.

Dukkansu suka fita sannan suka rufe ƙofar, suna fita Shamsiya ta kalle ta, tunda daman ita Ummu tunda ta shigo take kallon ta.
Mirmishi ta yi mata irin mai ƙayatarwa nan kafin ta ce" Tunda na ganki na san cewa zuwa yanzu kin ji komai ko kin ga komai."

Ta faɗa tana mai yi ma Ummu wani kallo.
Cikin wani yanayi Ummu ta ce" Na ji mana, na ji za ki yi aure amma ba ki faɗa mini jibi ne bikin ki ba."
Ta faɗa kafin ta ɗan ja fasali.

"In ba ki so na zo bikin ki Bestie ba sai kin ɓoye mini ba nima a wannan halin ba zan zo ba ballatana har na na ɓata miki bikin ki."
Ta faɗa cikin rawan murya, tunani kawai take yi ba gaskiya ba ne , ko dai ita ce ba ta gani daidai ba ko kuma an samu wani kuskuren.

Shamsiya ta sake kallonta kafin ta kwashe da dariya.
Ummu ta yi jagale tana kallonta ganin tana yi mata dariya

"Wai akan me kike magana?
Ta faɗa lokaci ɗaya tana mikewa..
"Kin ce ma su Anty na yi nauyi shi ya sa ba zan samu zuwa bikin ki ba, alhalin ni ba ki faɗa mini ranar bikin ba."
Shamsiya ta sake kwashewa da dariya tana nuna Ummu kafin ta ce" Wai da man ba abin da nake tunani ya kawo ki ba?

"Me kike nufi?

Ummu Salma ta tambaya cikin shan jikin jikinta.

"Ba ki san abin da na ke magana akai ba?
Ko dai kin sani kin zo ki tabbatarwa ne kina yi mini alaye"
Ta faɗa tana mai kallonta cikin kurullah.
"Me me kenan?
Ummu Salma ta tambaya har bakinta na harɗewa.
Shamsiya ta dauko wayarta a gaban madubi ta yi danne danne ta miƙa ma Ummu wacce ta yi tsai tana kallonta.

"Karɓi ki duba."

Hannunta na rawa ta karɓa. Tana dubawa, sai gata ta sake ƙamewa a zaune.
Ba sabo ba ne a idanuwanta hotunan nan ne dai da ta gani ɗazu ta kasa gasgatawa.

"Ki yi ta yin gaba, hotuna ne ne ni da mijina in sha Allahu"
Hannun Ummu na rawa zuciyanta na bugawa, haka ta rika wucewa tana kallon hotuna kala kala sama da kala goma ba ta ko gama gani ba ta ɗago idanuwanta cikin wani yanayi tana kallon Shamsiya.

"Da ma. Da ma da gaske ne?

Ta faɗa cikin rawan baki da na zuciya.

"To da kin ɗauka karya ne?
Shamsiya ta faɗa tana ɗan dariya.

"Habib ne fa! Ko ba ki gane shi ba ne?

"Habib ne, na gane shi Sweety ba."

Shamsiya ta katseta cikin ba ta tabbaci.
Ummu ta kasa magana bakinta na rawa, tare da jikinta Shamsiya kuma ta ɗaure fuska tana kallon Ummu kallon kasƙanci.
"Ga shaida nan na nuna miki. Jibi uwar haka ina gidan Habib a matsayin matarsa in sha Allahu."
Ta sake faɗa tana sakin wani mirmishi.

"Habib fa! Habib miji."

"Kul ɗinki. Kar ki sake kiran shi da mijin ki domin Habib ba na ki ba ne nawa ne. Ummu Salma."
Ta faɗa tana taso mata a fusace
Kafafun Ummu har gara suka yi saboda jin abin da ba ta taɓa tsammani ba.

"Ban karya ta cewa ke kika fara sanin Habib kafin ni ba, amma zan baki tabbacin ni na baki aron shi har kika aure shi kika kuma yi zaman aure da shi."
Ta dawo gaban Ummu Salma ta tsaya sannan ta nuna cikin jikinta da yatsunta guda ɗaya.

"Ni ce har na baki damar da kike da wannan cikin a jikin ki. In da na so da baki aure Habib ba, in da na so da yau ba ki rigani ɗaukan cikin shi ba"

Ummu ji take yi kamar mafarki amma da ta runtse ido sai ta sake ganin ta a gidan su Shamsiya kuma ga ta a gabanta tana faɗa mata wasu maganganu waɗanda ta kasa yarda da su.

"Ke Habib ya fara gani yana so, ranar da kika nuna mishi a matsayin saurayin ki na ji dama ace shi ɗin nawa ne, bani na fara kai kaina ga Habib ba shi ya kawo kansa gare ni da cewa sai da ya ganni ya san ba sonki yake yi ba sha'awarki ya ke ji, tun a lokacin muke tare muna soyayya a ɓoye, saboda ke ba zan hana zuciyata abin da take so ba Ummu Salma."

"Me ya sa to ya aure ni baI aure ki ba?

Ummu ta samu karfin gwiwan tambayan Shamsiya domin ko hawaye ma ba ta ji ya kawo mata ba zuciyarta ke suka tana hasaso mata wasu abubuwan, au da man Shamsiya ce masoyiyarsa da yake ta magana a kanta ita ko me ta yi ma su Habib da suka zaɓi su yi mata wannan yankar ƙaunar.

"Ina son Habib ina son abin da zai saka shi farimciki. Yana tsananin sha'awarki kuma yana so ya kauda wannan sha'awar ni kuma a gida ba za a bari na yi aure a lokacin ba. Shi ya sa na ba shi daman ya aure ki amma na shekara ɗaya ya yi amfani dake son ranshi ya sake ki zuwa lokacin ni kuma na shawo kan matsalata a gida.  Mun yi da shi ba zai bar ki ki samu ciki ba, amma sai da kika ɓata mana plan din mu."

Nan ta shiga ba ta labarin duk yunkurin zubar da cikin da Habib ya yi mata da saninta domin tare suke shirya komai.

"Ki ma gode ma Allah na baki aron shi, ki kuma jinjina mini yadda na bari kika fara ajiye ƙwaan Habib a mahaifarki kafin ni, saboda haka godiya ya kamata ki yi mini Ummu domin na ba ki aron abin da na fi so a duniya."

Ta gama faɗa tana fuskanta ta. Ummu ta yunƙura ta miƙe tana jin ɗan cikinta na haɗewa waje ɗaya saboda halin da ta ke ciki, cikin ido ta kalli Shamsiya kafin ta ce" Ai ban neme da ki ba ni aron shi ba Shamsiya. Me ya sa kuka yi mini haka? Riban me za ku samu?
Ta faɗa cikin soyewar zuciya.

"Na samu riba, domin Masoyina ya biya bukatarsa, ni ma kuma na samu nawa biyan bukatar, ga shi za mu yi aure."

"Shamsiya mijin da na au"

"Haramun ne? Ai ya sake ki, kuma ko bai sake ki ba zan iya auransa in na ga dama. Amma ni ba zan iya zaman kishi dake ba shi ya sa nace ya sallame ki daga rayuwar mu."

"Da man ba don Allah kike tarraya da ni ba?

"A baya don Allah na ke zaune dake amma daga lokacin da kika auri Sweety na tsane ki Ummu Salma."
Ta dakata tana kallon Ummu da ta koma tana mirmishi kamar mahaukaciya

"Kuma na ja baya dake ne saboda bana son alaqar mu, bana son ki a rayuwata. Ki je ki cigaba da rayuwarki amma ki manta da kin taɓa sanina ballatana Habib. Mu zama kamar mun shuɗe daga tunanin ki."

Ummu ta girgiza kai ba za ta iya fassara a yanayin da ta ke ciki ba.
"Sannan kar ki damu kaf dangina ba su nan kin auri Habib ba, sun san shi ne kawai a matsayin sa na mijina."
Ta faɗa tana kashe mata ido ɗaya cikin dariyan shaƙiyanci.

"Na gode, da man tabbacin nake son sani tunda kuma na same shi daga wajen ki ba komai."
Ummu ta faɗa cikin aro jarumta.
Kawai sai ta juya za ta bar ɗakin tana jin maranta na daurewa a waje daya, ga ɗakin na juyawa mata amma ta daure.

"Ba ki ji ba."

Ummu ta juyo tana kallon ta.

"Na so ki zubar da cikin nan,  watakila da kin iya samun wani wanda zai kwashe ki, amma kika yi taurin kai ki ji be ki fa yanzu? Wa zai kwashi bazawara mai ɗa, ɗan ma mai kama da ɗan shege tunda uban cikin ya ce ba ya so"

Ta gama faɗa tana kwashewa da dariya har tana tafa hannuwanta
Juyawa kawai Ummu ta yi ta fice daga ɗakin tana jan kafa, ita dai ta san ta bar gidan ta kuma yi tafiya mai nisa a hanya kafin ta samu abin hawa.

Ta san kamar hankalinta ya gushe domin ba ta ma san har ta faɗi sunan anguwarsu ba, ita dai an sauke ta a bakin titin gidansu ta sauka ta ba shi kuɗinsa sannan ta yi tafiya zuwa gida da kafafunta.

Ba ta kuka ba ta komai amma tana ji kamar yau za ta bar duniya.
Masallatan anguwan har sun idar da sallar isha'i wasu ma sun daɗe da idarwa.
Ta shiga gida ba ta damu da Ammah ko Baffa su ganta ba.
Ba ta damu da su tuhumeta ba.

Kawai ta faɗa ne kai tsaye.
Hamma Lamiɗo na tsaye wajen ɗakin Baffa yana waya ya juya baya. Ba ta san shi ba ne sai da ya juyo shima ya ji ana ta jefa kafafuwa ne yaraf yaraf shi ya sa ya juyo.
Ido huɗu suka haɗa domin akwai hasken wuta a tsakar gidan.

Mamakin ganinta yake yi ga ciki a gaba sannan yarkace-yarkace kamar ba ta cikin hayyacinta. Ta kalle shi cikin wani yanayi shi dai juyawa kawai ya yi ya cigaba da wayarsa ita kuma ba ma ta shi take yi ba da sauri ta faɗa falon Ammah.

Tana shigewa ya bi bayanta
Da kallo  cikin mamakin me ya fitar da ita a cikin wannan daran? Me ya same ta ya ga kamar ba ta da lafiya. Duk da fa ya daɗe bai ganta ba, ba haka take ba.
Sai kuma ya yi tunanin watakila ciki ne ya mayar da ita haka.

Yana gama wayarsa ya koma cikin ɗakin Baffa abinci yake ci aka kira shi a waya ya ta shi.
Ammah kuma ta shiga ciki ta je yin sallah. Komawa ya yi gaban abincin shi Baffa na gefen shi da man Ammah ce ke hiran bayan ta tashi sai ɗakin ya yi shuru.
Shi Lamido da man bai iya hira ba shi kuma Baffa sanin halin shi ya sa bai ma bata bakin shi ba

Ammah na ɗakinta ta idar da salla ta ji kamar an shigo
Ta fito haka dai daidai lokacin da Ummu ta shige ɗakinta ta rufe kofa.
Sai Ammah ta ɗauka ita ce ta fito falo ta koma, domin ba ta san Ummun ba ta a gidan ba, bayan fitan ta Lamiɗo ya zo suna ɗakin Baffa gabaɗaya.
Daga nan kawai ta fice ta koma ɗakin Baffa.

Ummu ta sulale a kasan cafet tana jin zuciyarta na zafi kamar za ta mutu. Abubuwa suna gilma mata. Shamsiya da Habib.
Me ta yi musu da za su lalata mata rayuwarta haka?.
Shamsiya fa da suke ƙawance tun suna yara ita ce ta ci amanarta da namijin da ta ba ma Amanar rayuwarta.
So take yi ta daina jin zafin da ke ji a cikin zuciyanta.
So take yi duk wani damuwarta da take ji ta daina jin su, so take yi ta bar duniyan nan ko za ta samu yar salama.
Amsar kuwwan Kalaman Shamsiya sun kasa barinta ta huta, sun saka ta jin gwara kawai ta ji shuru gwara ta sama ma kanta natsuwan zuciya.

Miƙewa ta yi tana layi ta isa gaban madubi ta ɗauki reza sabuwa a cikin kwalinta ta buɗe. Rezan ba na ta ba ne na Ammah ne kwali ɗaya take siyab itama shekaranjiya cizgiya ne ya fito mata a gefen hannunta sai ta yi ma Ammah magana ta bata, bayan ta cire sai ba ta mayar mata ba sai ajiye a saman madubin ɗakin.

kallon kanta take yi a madubi tana tunanin yanzu rayuwarta ba ta da amfani hijabin jikinta ta cire ta na kallon cikin jikinta.
Ba amfanin ta haifa ma Habib yaro ko yarinyar dake cikinta domin bai cancanta ba, yadda zuciyanta ke zafi ne take son kawai ta hutar da kanta.

Ba tare da tunanin komai ba ta ciro rezan ta daidaita tsitsiyan hannunta na hagu za ta yanka lokaci ɗaya tana mai runtse idanuwanta hawaye na wanke mata fuska, sai ƙaran vibration ɗin wayarta ya dakatar da ita wayar na kan madubin ne, idanuwanta na ganin duhu amma sai da ta ga sunan mai kira, Sisna Baɗɗo ce take kiranta a lokacin da ba za ta saurare ta ba, a lokacin da ba za ta iya amsa wayarta ba.

Tana mai zubar ƙwallah wasu na fitowa wasu na ƙoran wasu ta sake daidaita hannunta
ta yanka sai ga jini ya tsartsu, ta runtse ido tana jin wani irin zafin azaba na ratsa ta daga ƙafafunta har saman ƙwaƙwalwarta.
Sake yanka hannun nata ta yi a karo na biyu jini ya sake tartsuwa, ta sake runtse ido sabo da azaba mai raɗaɗin da ya dabaibaye jinta da ganinta tana gani jininta na zuba a kan madubi yana gangarawa a kasan cafet da gudu kamar an buɗe famfo.

Azaba take ji amma kuma tana jin daɗi yanzu za ta daina jin abin da take ji a cikin zuciyanta. Gwara ta mutu in ta mutu za ta huta.
Tana mai kallon kanta a madubi tana hawaye ta fara ganin kanta biyu biyu kafin ta ji jiri ya kwashe ta, ta yi baya ta dafa gado amma ina ya rinjayeta, tuni idanuwanta suka hau lumshewa jikinta ya saki da ta kasa iya riƙe kanta
nan ta sulale ta faɗi kasa ta gefen hagu.

Hannunta kuma har a lokacin bai daina zubar da jini ba, ga rezan da ta yanka kanta nan a yashe a gefen ta
Ta ji daɗi domin jinta da ganinta ya tsaya cak zuciyarta ta daina aiki ta daina jin komai ta samu salaman da ta ke fata.
Ta ji ɗif, ta samu natsuwa ta samu hutun zuciyan da take muradi.

*1k on Telegram 09069067488*




*Janafty*
*FARGAR JAJI.*

*Wattpad:JamilaUmar315*
*Arewabooks:JamilaUmarJanafty*

"To Hajiya Hauwa'u Inuwa Aminu (Anty Hairi) with love and gratitude"

https://chat.whatsapp.com/GKzdnJ5Gb62IjjqT6AYpcC


No. 1 online shopping kenan inda zaku sami duk wani kaya da ku ke buƙata, tun daga kan kayan kicin, laceses, atamfofi, shaddoji kayan yara maza da mata ,da uwa uba magungunan supplements wadanda ba su da illa na manyan mata inda zaki fito ki yi das da ke ki zama abin sha'awa, ga kuma Arabian sabaya powder wacce baki taba cin karo da irin ta ba, ke dai maza shigo ki kwashi romon arziki a gidan mutunci da karamci a kai Miki kaya har inda ki ke babu fargaba.

*20*

*DAAMA SPECIALIST HOSPITAL*
NO:70 72 Abubakar Atiku Rd. Jimeta Adamawa.
VIP:Room 23.

Ta daɗe tana jin wucewar iska a cikin kunnuwanta. Sannan kanta ya yi mata nauyi sosai tana ji kamar an ɗora mata katon dutse, idanuwanta take so ta buɗe amma ta kasa ji take yi kamar an danne idanuwanta nata da wani abu mai nauyin gaske. Tana ta ƙokarin motsa gangar jikinta lokaci ɗaya da fitar da numfashi sosai amma ta kasa jikinta ya tamke, ko ɗan yatsanta ba ta iya ɗagawa sai ma take ji kamar wuyanta ya rabu da gangan jikinta ne. Sannan bakinta da wani abu an yi mata takumkumi da ya hanata damar iya sakin numfashi sosai.

Tana jiyo ɗan maganganu daga can nesa da ita amma ba za ta tantance komai ba, tana cikin kamar tsakanin rayuwa da mutuwa ne. Komai daga nesa take jin sa kamar ba a kusa da ita ba ne, tunani take ko dai ta mutu ne tana cikin kabari, tabbas ta mutu ƙasa ne ya danne ta da ya sa ta kasa motsa gangan jikinta.

"Innalillahi wa'inna alaihirraju'un."

Ta furta a cikin zuciyanta, tana ta ƙokarin buɗe idanuwanta ta kasa sai da ta daddage sannan ta samu nasaran buɗe kumburarrun idanuwanta da suka yi mata nauyi kamar an ɗora mata jakan duwatsu a sama, dishi dishi ta fara gani kafin ganin ta ya ɗan fara washe.

Farin POP ta fara cin karo da shi lokaci ɗaya da karamar farar fanka a sama tana gudu sosai, shi ne iskar da take jin ƙaran wucewarsa a a cikin kunnuwanta.
So take yi ta tuna abin da ya faru da ita amma ta kasa tuna komai, tunanin ta ya fi karkata da cewa ta mutu ne, to amma in har ta mutu to nan ba a cikin Kabari take ba, domin a cikin kabari babu rufin ɗaki sannan babu fanka.

A hankali a hankali ganin ta

Please Login or Register in order to submit comment