Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ajjiye ya zuba ya sanya cokali ya sauka qasa ya ajjiye a gabansa.

Lion eyes dinsa da suka rusuna saboda zafin zazzabi ya daga ya zube mata su,yadan lumshesu kadan sannan ta motsa bakinsa a nutse yana miqa mata hannu

"Taso nan" jiqaqqun idanunta ta daga ta kalleshi,sai ta saukesu qasa a hankali,ta yunqura da karyayyiyar zuciya jikinta a mace,ta fara takawa a hankali. Idanu ya bita dashi yana kallon takunta,tausayinta yana ratsashi a hankali a hankali,sai ya miqa mata hannu kafin ta qaraso yana gyara mata inda zata zauna.

Sosai ra zauna a gabansa ya gyara mata skirt din jikinta,ya dago bowl din ya ciro cokalin ciki ya debo abincin yakai bakinta

"Bismillah" ya furta,saita maimaita itama ta bude bakinsa ya saka mata. Ta runtse idonta tana tauna abincin a hankali.

Da gaske komai da zai fito daga hannunsa dabanne a wajenta da bakinta,me hakan yake nunawa?. Duk yadda take ganin zata iya,zata iya ci ita kadai zata iya gamsar da kanta da buqatunta a hankali a hankali sai komai yake neman qaryatata. Me yasa take gazawa akan komai?,me yasa kasawarta ke fito akan komai da komai?

"Ba zaki iya ba sai dashi" wani sashe na zuciyarta ya bata amsa kai tsaye cikin sallamawa daga lamarin gaba daya. Maganar ta tsaye mata a rai,da gaske hakanne ko kuwa?.

Tana tsaka da wannan tunanin ta daga idanunta,sai taga ashe ita yake kallo shima,ya ritsata da idanunsan nan da a yau kallon cikinsu ya haifar mata da wani irin abu da bata taba jinsa ba,a take kuma idanunta suka hada hawaye fal har hakan ya nuna cikin qwayar idanunta masu sheqi.

"No...... don't cry" ya fadi a tausashe,sai ya zaro tissue daga gefansu yana miqa mata. Bata musa ba ta saka hannu ta karba ta fara tsane idanunta

"Kin qoshi?" Ya tambayeta yana dubanta. Kanta ta gyada a hankali

"Good" ya fadi yana maida ragowar tissue din cikin kwalin. Ruwa ya tsiyaya ya miqa mata,ta miqa hannunta zata karba hannunsu ya hadu waje daya. Dukansu shida ita babu wanda baiji wani abu a jikinsa ba,yayi saurin sakar mata ruwan wanda saura kadan itama ya subuce daga hannunta. Kamar kullum ya hada kan kayan guri guda,ta bishi da satar kallo ta gefan ido. Tana jin kamar tace masa kada ya fita daga dakin,amma kuna tana jin nauyin fadan haka.

Bayanta ta mayar jikin kujera tana lumshe idanunta gami da fidda numfashi a hankali.tanason tuna daidanta da kuma kuskurenta,a cikin wannan tunanin nannauyan bacci yayi awon gaba da ita,dukka jikinta ya sake saboda qoshin da tayi,wanda tun ranar qarshe daya bata abincin rabonta data qoshi haka.

Lokacin da ta farka tayi mamaki sosai ganinta kwance saman gado kuma lullube cikin duvet,ta dudduba jikinta a hankali mamakin dai bar barta ba haka ta sauka tana duba lokacin sallar azahar. Lokacin bai qure ba amma dab yake da fita,wannan ya sanya ta qara azamar shiga toilet.

Tana idar da sallah wayarta ta dauki tsuwwa,ta miqa hannu a nutse tana jawo wayar. Number goumar ne,don haka ta daga kiran.

Muryar batoul ta fara ji,cike da karsashi take magana

"Mummy assalamualaikum" murmushi ya subuce mata,muryarsu na daya daga cikin abubuwan da suke sanya mata nutsuwa a wannan lokacin

"Wa'alaikummussalam B" murmushi ya qwacewa yarinyar,har tana jin sautinsa ta wayar

"Mummy ina kwana?" Karyar da kai sultanar tayi tana jin dadin jin muryarta

"Lafiya lau B.....amma yanzun ba safiya bace,ko bacci ama ta barku kuka dinga yi?" Dariya ta qyalqyale dashi

"A'ah,yanzun nan mamy tanja ta gama gasa mana cake.... uncle goumar yaje ga siyo mana whipping cream strawberry flavor ta saka a ciki" murmushi ya qwace mata,yaran badai son cin dadi ba,bakinsu yasan kwadayi qwarai,ko don sun saba tun suna qananu?,saidai kuma duk da hakan bai sanya an barsu sun sangarce ko kuma sun miqe da samun duk abinda sukeso ba

"Ma sha Allah,a yiwa mamy tanja godiya sosai"

"Mummy.....we missed you.....don Allah ama tace mu tambayeki muzo mu ganki?" Maganar ta sanya sultana jin nauyi da kunya,me ama ke nufi?,ya zata hana yaran zuwa?,ita kanta marmarin ganinsu takeyi,inda da hali ma kuma da zaiyiwu aman ta bata dasu zatafi kowa farinciki da hakan,amma ta sani wannan magana bame yiwuwa bane,koda wasa kuma ko a mafarki ba zata ce a bata su batoul ba,don sun zama halak malak din ama da aba,mallakinsu ne ko duniya ta shaida

"You are welcome BB" ta fada a gajarce don batasan ko ama tana wajen ba.

Ihunsu taji daga cikin wayar da muryar mutumin nasu goumar,sai kawai ta ajjiye wayar tana murmushi. Batasan wanne qarfin qauna goumar din yakewa yaran ba,ba wani abu da yake barinsu su nema su rasa,real definition of uncle ne shi din.

Samun kanta tayi da tunanin me zata samawa yaran suci a matsayin barka da zuwansu?. Ta dinga tunani daga qarshe ta yanke abinda zata basun,tasan ba abinda suke so irin kayan maqulashe,don haka ta qarfafa jikinta ta miqe tana zare hijab dinta ta lullube kanta da madaidaicin mayafin daya dace da rigar jikinta.

Har cikin ranta takejin walwala sosai,ta dinga takawa cikin lobby din don ta wuce zuwa kitchen din,daidai sanda taga qofar dakin dake daura da nata a bude. Idanunta saman qofar dakin tana qiyasta a nan ya koma kwana kenan.

Dab da zata gifta dakin ta soma jin sautin muryarsa,cikin calmness dinnan nashi

"In sha Allah next week ko upper week zamu shigo Niger din......"

"Lafiya ko?" Daga cikin wayar ta jiyo sautin muryar uncle umar yana tambayarsa

"Neman aure oncle......nigeria da kuma niamy in sha Allah"

"Hasbunallah" ta fadi tana gifta dakin da sassarfa tana jin qafafunta kaman ba'a jikinta suke ba.......tana qoqarin sarrafa tashin hankalin da takeji cikin zuciyarta tana kuma tuhumar kanta me ya kaita tsaiwa jin maganarshi cikin waya.

Da qyar ta qarasa kitchen,ta samu stool ta zauna saiga hawaye kamar ana tunkudosu.......auren zaiyi da gaske?,meye makomarta kenan?, meye matsayinta a gurinshi?,a ina ya ajjiyeta?.

"Sultana......ki fitar da kanki daga sabgar nan......kiyi ta kanki kiyi ta rayuwarki......taki qaddarar ce qila kiyita haifa masa yara babu cikakken zaman aure.....ki sauke wannan daga nan ki samawa kanki mafita...... zaiyi aure saboda baki da wani matsayin komai a wajensa....baki kuma isa komai ba.......ki zama jaruma....ki zama jajirtacciya......ya hado laila ayana da dukka danginsa ya aura mana" zuciyarta ke gaya mata hakan cikin tsawatarwa.

Kokawa sosai ta dinga yi da zuciyarta tana wassafa yadda zata iya handling maganar. Maganar tafiya neman aure kenan ya kira suhail da sardauna yayi musu?,zasuyi masa rakiya kenan?,su zasu zame masa abokan ango?. Kifa kanta tayi a tafukan hannayenta tana wassafa girman tashin hankalin da takeji cikin zuciyarta,yayin da tsoro ya mamayi zuciyarta,anya zata iya jurewa wadannan abubuwa?,tana tsoron kada wani abu ya samu dan tayin halittar dake kwance qasan mararta......halittar da takejin wani matsanancin soyayyarsa banbanci da abinda taji a cikinsu benazeer,ko don su din bata gama sanin me ake nufi da gundarin abinda kalmar d'a ke nufi ba?,ko don a sannan batasan ciwon kanta ba?.

Ta sake shafa mararta a karo na biyu tana sake addu'ar ubangiji ya tsare duk abinda take dauke dashi. Mamakinta kuma yana sake linkuwa,me zata haifa haka da duk irin tashin hankalin da takeji daga zuciyarta zuwa gangar jikimta bata taba jin wani alama na akwai wani mummunan abu da yake faruwa dashi ba?,bata taba jin alamun girgiza daga zamansa qasan mararta ba?,tabbacin wata ajiya ce ta ubangiji dashi kadai ya barwa kansa sani.

_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400
BIYU_800
UKU_900
HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875
Musaa Abdullahi safiya
Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261


*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku kudin*

09033181070


*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂GUDUN KADDARA
Chapter: B00K O2 PAGE 137
*_GUDUN KADDARA_*
*HUGUMA*


'ya'yanta data tuna ya
bata wani irin qwarin gwiwar cilli da kuma tunkude kowacce kalar damuwa. Ta mige tana garfafawa kanta gwiwa ta soma duba duk wani abu da takeso tana hadawa waje guda.
Girki tayi sosal irin wanda
ta jima batayi irinsa ba, duk da yadda gamshin wasu abubuwan ke neman galabaltar da ita amma tuna benazeer din da batoul kadal yana saka mata qwarin gwiwa.
Koda ta gama bata fidda komai ba ta barshi cikin kitchen din, ta gyara komal yayi mata yadda takeso, sannan cikin kasala ta juya zata fice a kitchen din.
Yana tsaye ya harde
hannayensa yana kallonta, kuma dukkan alamu sun nuna yadan jima tsaye a wajen don har ya jingina sosal da bakin gofa. Suna hada ido ta kauda kai, batason taci gaba da kallonsa bare gazawa ko rauni ya mamayeta.
Ci gaba tayi da takowa, yayin da yaci gaba da kallonta yakuma d'ana mata tarko har zuwa lokacin data iso dab dashi.
Sosai yaso dauke kanshi daga gareta, ya ja numfashi har zuwa cikin hunhunsa amma zuciyar. tagi daidaita daidal da matakin da yakeso. Ba tare daya shiryawa hakan ba, ba kuma tare da yaso hakanta kasance ba ya sanya hannunsa ya fusgota cikin jikinsa.
Sanda ta isa ga
faffadan girjinsa sai taji kamar an yaye mata wani abu dake lullube a girjinta. Sassanyan gamshin nan nasa da a yanzu a duk duniya babu abinda takeso take kuma gaunar shaga... gamshin ainihin fatarsa laushinta da duminta ya mamayeta.
"Kin gama kuka dazun......yanzun kuma kinzo kina girki..... banason dukka wadannan dabi'un
please.... ko meye kikeyi abinda yake cikinki yana sane dashi" kaman jira takeyi dama yace wani abun ko kuma yayi wani motsi sai kawai ta cusa kanta cikin gir jinsa ta fashe da wani irin kuka. Kuka me wani irin sauti daya rudashi ya kuma daki zuciyarsa lokaci guda. Ya dagata daga jikinsa yana rige kafadunta da dukka hannayensa biyu
"What's happening?....mene kuma?" Ba zata iya cewa komal ba don tana ganin ta katse kukan bame yiwuwa bane...... yaga alamun hakan shima, don haka bai sake tambayarta ba ya rigeta da kyau ya fita da ita falon. Saman kujera ya azata
ya koma yasa a gabanta ya zauna dirshan yana kallonta. Bai rogeta ta tsaida kukan ba, saboda yadda take kukan kadal ya tabbatar masa daga zuciya ne.
Bai ce da ita komal ba
sai daya tabbatar dai dai lokacin zuciyarta tayi sanyi
"Me ne kuma ya faru?, ko har yanzun dal na matsa miki?, ina takuraki?, ko kina bugatar wani space dinne sama da haka?" Dukka tambayoyinsa sai suka bata masifan haushi, tama rasa gane masa gaba daya?, me yasa bazai fahimceta ba?, baya ganewa ne?, baya gane yanayinta ne?, anya ba da gangan yakeyi ba?, bayan kuma ya tabbata yafi kowanne mutum iya karantar badininta daga tsakiyar idanunta?.
"Kina da wata matsalar dani ne?, idan akwai ki gayamin zanyi gogarin kauce ma hanyarki...... na miki algawari ne kuma ina gogarin cikawa.... please let me know
idan akwai wani matsala". Dukka maganganunsa suna nuna bai
fahimta komai ba, da gangan ne ko kuma iya gaskiyarsa kenan ita bata sani ba, abu daya ta sani, dukka wadannan maganganun ba su take burin ji daga bakinsa
"Kaine matsala!" Shine abinda taketa son gaya masa amma kuma batasan da wacce siga zata fasa mishi maganar ba.
Bayan hannunta ta saka tana sake goge fuskarta,sai ya sanya dukka hannunsa biyu ya zuba tagumi yana kallonta. Can gasan ransa kaman ya saki mata dariya amma yana cijewa. Ka nema abu da kanka amma kuma kazo ka buge da bawa kanka punishment?, shi kam bai taba ganin wannan abu irin na sultana ba.
Gajeruwar hanya me saugi amma ta maidata doguwar tafiya. Shi din mutum ne daya ci burin samun ingantacciyar soyayya zazzafa
daga wajen matarsa...
....ba
kowacce kalar soyayya ba wadda bata amsa sunanta ba, so me sunan so wanda ya gunshi sadaukarwa abota da kyakkyawar fahimtar juna .....wannan ya sanya a tarihinsa bai taba budurwa ba a baya.....ba wanda ya isa yace ga budurrsa..... don kowacce mace ya kalla sal yaga kaman ba zata bashi abinda yake bugata ba ta hanyar haquri dashi ta kuma mallaka masa zuciyarta da rayuwarta dama gangar jikinta gaba daya...... auren dole yana daya daga cikin abinda ya yiwa mummunar tsana......ya kuma yiwa kansa algawarin bazai taba auren macen da babu soyayyarsa cikin zuciyarta ba
"Ki sake gayamin me kk bugata haidar zai kiyaye...."
"Idan nace kai nake bugata nayi daidai banyi kuskure ba?" Ta gwada fadi cikin zuciyarta, saidal a fili kuma idanunta ta lumshe. Batasan ya zatayi masa bayani ba.....batasan yadda zai fahimceta ba ba tare data furta komai ba.
Bell din da aka kada ita
ta katse komal a tsakaninsu, ya waiwaya a hankali yana duban qofar kafin ya dawo da dubansa kanta
"Wipe your tears please baby gurl.... kada na je su ama ne ki sanya suyimin dukan tsiya..... naga har yanzu basa yina kedin dai ke sukeyi" ya fada yana dan ranqwafawa kadan ta saman kanta kamar me rada mata bayason wani yaji abinda yake fada din.
Jikinta ya bata su batoul ne, don kamar tana dan din muryarsu kadan kadan, ta jawo tissue tana sake tsane idanunta tare da gyara zaman mayafin kanta tare da gyara zamanta.
Ihun da suka saki yaran
ya sanyata duban bakin qofar bata shirya ba, dukka sun saki kayan hannunsu sun dane uban, shi kuma ya dagasu dukka su biyun kamar bayajin nauyi da girman da suke sakeyi kullum. Ya diresu suna gaidashi, benazeer tadan bata fuska tana cewa
"Ina mummy?" Da yatsa ya nuna musu ita, sannan ya ranqwafa a tsakiyarsu gasa gasa yana cewa
"Kuyi magana a hankali mummyn batason hayaniya......kuzo mujeku tayani bata haquri, wai haushina takeji" ya furta shima kaman garamin yaro yana dan bata fuska.
Agaba ya sakasu har
suka isa gabanta, sun tsareta da idanu kamar yadda itama ta tsaresu da idanun, sai ta bude musu hannuwanta, da gudu kuwa suka fada kanta.
"fais-le soigneusement (yi a hankali), karku buge baby" ya fada yana janyesu daga saman gafafunta.
RA
Batoul sarkin magana ce ta
daga kai da hanzari ta kalleshi
"Daddy ina babyn?" Ta fadi tana zare idanu. Hannunsa ya dora daman cikinsa sannan ya nuna mata sultana. Tsalle ta buga tana rigeshi da kyau
"Baby zata siyo mana daddy, mu xama mu haka?" Ta fadi tana daga yatsunta guda hudu.
"In sha Allah" ya fada yana murmushi. Harara sultana ta jefawa benazeer sanda ta juyo da niyyar mata tata tambayar, hararar ta sanya benazeer ta tsuke bakinta tsaf, daidai nan goumar ya shigo da sallama.
Zuwan nasu shi ya sake debe mata damuwa me yawa, tayi yogarin sakin jiki dasu, yayin da goumar uban tsokana yaketa son kwasarta amma kuma idanun maina ya hanashi. Duk motsinta akan idanunsa yake, ya lura kuma tana sane tana basarwa ne, kaman batason kallon idanunshi ne bataso kuma shima ya kalli nata.
Tare sukayi sallar magariba cikin falon dukansu, yana kuma sane ya hanasu tafiya da wuri ya jasu har magaribar saboda ita.
Bayan sallar magaribar abincin da yayi musu order daga wani gidan abinci ya iso. Kowa da zabinsa, ta mige ta wuce kitchen yaran suka bita don dauko spoons da plates, sai ya bisu da kallo yanaji a ransa Inama wannan yanayin ya dore har abada?. Sanda ya dauke idanunsa sai suka hada ido da goumar, dariya ta tasowa goumar din amma ya toshe fuskarsa da wayarsa, sai ya zabga masa harara yana dauke kanshi.
"Ka shirya Next week ko upper week zamu wuce Nigeria, ina tunanin adadin bukukuwan zasu dadu, so nake a hade bikin duka lokaci daya idan zai yiwu" maina ya fadi yana bude wayarsa da sago ya stigo, daidai sanda kuma take fitowa ita da yaran daga kitchen din
"Bukukuwa yaa maina.....bikin waye?"
"Ka fito da passport dinka kawai, ka gayama ama ta fiddo nasu benazeer zan duba mana ticket, idan munje zaka gani"….*_GUDUN KADDARA_*
*HUGUMA*
B00K 02 PAGE 138

Goumar daya ga isowarta
gurin ya daga kanshi ya kalleta, suka hada idanu saita kauda kai tana ajjiye abincin data dauko musu a hankali.
"Mun gode" goumar ya fadi cikin sanyin jiki. Dukka juriyarta da yogarinta ta tattaro ta aza saman fuskarta ta kuma fidda murmushi
"Aunty najma zata biya bagin buzu" duk da yana cikin yanayi na rashin
Jin dadin zuciyarsa amma sai daya maida mata murmushinta. A nutse kaman bataji komal ba ta juya, duk kuwa da cewa zuciyarta na wani irin rawa.
"Zan shiga daki zaku zauna wajen uncle goumar?"
"Zamu biki dakin" benazeer tayl saurin fada. Bata hanasu ba suka bita a baya, benazeer tana gaba batoul na binta a baya ita kuma tana bayansu.
Ko cikin dakin sun sake abinsu sunata dara, tana zaune kawai tana binsu da kallo, yayin da zuciyarta tayi nisa sosal da gangar jikinta. Tana jin wani rauni yana mamayarta, da gangar ya kasa fatimtar ta?, ko kuma da gaske yake bai fahimceta din ba?, zata kuwa iya jurewa wannan hukuncin da ya yanke musu me gaba daya ita dashi?.
Qarar wayarta ya dawo da ita hayyacinta, ta kalli wayar daga inda take zaune, abun mamaki sai taga goumar ne, ranta ya bata ko akwai wani abu me muhimmanci ne ya sanyashi kiranta.
Da sallama a bakinta cikin
raunanniyar muryarta, ya amsa sal kuma shuru ya biyo baya tsakaninsu
"Sultana" ya kirayeta da sunan data manta rabonshi da kiranta.
"Na'am" ta amsa masa a sanyaye.
"Kinsan waye maina kuwa?" Yayi mata tambayar da ta rasa abinda zata ce masa, sal shuru daya ratsa a tsakaninsu
"Why sultana?..... me yasa ba zaki yafe ba?, me yasa komal bazai wuce ba?, me yasa ba zaki bayyana masa soyyaya ba?.. kinsanadadin yadda yaa maina yake mutuwar sonki?, kinsan yadda ya daukeki a rayuwa?, kinsan adadin soyayyar da ya baki?, kinsan iya matsayinki da matakinki a rayuwarshi?.......
yana bugatar wata soyayya wadda bata uwa ba....yana bugatar wata soyayya wadda bata 'ya' yanshi ba..
...sultana pl......
Maganarsa
ta yanke sanda take jiyo muryar maina ta cikin wayar, da alama ya shigo gurin da goumar din yake zaune, alamu kuma sun nuna baya wajen sanda yayi kiranta
"Ki turo su batoul zamu fita" goumar ya rufe maganar tashi da wannan.
Sauke wayar tayi tana
jin idanunta suna mata zafi, kuka takeso tayi amma kuma batason ta karya farincikin da yaran suka samu ta sanadinta.
"Kowa ya sanya cap dinshi, uncle goumar yana kira" da saurinsu suka maida p_caps dinsu da suka cire garin tsalle tsallensu, suka kuma ruga suna rige rigen fita daga dakin.
Rub da ciki tayi qwalla na silalo mata, da gaske ne dukkan abinda goumar ya fadi mata?, da gaske ne komal goumar ya fadi a kanshi tattare da ita?, ta yaya ya kamata ta fuskanceshi?.
Da wannan tunanin ta
dinga juyi saman gadon tana tuna abubuwa da yawa cikin kanta. Tun tana zuba ido tana lissafin sanda zataji motsin dawowarsu har taga
dadewar tayi yawa, tun tana kawaici har sai data daga waya ta kira goumar.
"Yanzun muka wuce gida, ama tace mu dawo dare yayi"
"Ku gaisheta" ta bawa goumar amsa
tana aje wayar.
Minti goma minti ashirin
minti arbain shuru bata ji motsin
dawowarsa ba, har ta share awa daya awa ta biyu ta wuce. A hankali wannan kasalar tayi mata rubdugu a jikinta, wani nannauyan bacci da bata shiryawa zuwansa ba ya ziyarceta, baccin da bata farka ba sai washegari daidal sallar asuba.
Ko da akayi sallar asuba
ma wani irin bacci ne ya sake surarta, saidai duka duka bata wuce awa biyu ba ta farka. Toilet ta shiga tayi wanka, ta tito ta tsaya gaban madubi tana duban lotion din da take amfani dashi. Ta budesti amma kuma ta kasa tabuka komal, qwagwalwarta tanata wassafa mata yadda zata fuskanceshi.
Handle din dakin ta ji an murza sannan aka tura gofar aka shigo. Aliyyu maina ne cikin wasu suit da suka karbeshi matuga da gaske.
Tsahonshi da mur jewar jikinsa dukka sun bayyana. Sumarnan baga sidik tanata shegi saboda gyaran da take samu a kowanne lokaci. Lion eyes dinnan nasa yau fes suke, sun sake wani haske da kuma girma kaman ya diga musu wani abun.
Sallama yayi yana motsa jajayen labbansan nan masu daukan hankali idanunsa tsaye car saman girjinta da ya zauna sosal, gefe guda kuma yana kokawar dauke idon nasa gudun kada ya kasa sauke abinda ya niyyata.
Muryarsa kawal ta saka
zuciyarta tayi rauni, amma duk da haka ta hana hakan bayyanuwa saman fuskarta. Ta jawo towel tana dorawa saman kanta ta yadda zai lullube mata kafadunta da girjinta da suka fito tana amsa sallamar.
Rarasawa yayi a nutse ya ajJiye complete kayan breakfast din daya shigo mata dasu kaman yadda ya saba "Ina kwana?" Ta gaidashi tana fatan samun damar yin wata maganar daban dashi bayan galsuwar
"Kin tashi lafiya?" Ya bata amsa cikin nuna kulawa, can yasan ransa kuma yana jin ba dadi kan yadda ta haramta masa ganin kyakkyawan fatarta dake gara wani sulbi da
"Athamdulillat"
"Zan fita.....
•zan zama busy sosal a
kwanannan.....idan kina da wata damuwa ko wata bugata kiyi magana akai" ya furta cikin salo na bada dama gareta. Bakinta ta motsa tanason tayi magana amma sai ta kasa furta komai din, ya motsa kadan yana cewa
"Abdulhamid zai kula da
abincinki in sha Allah, duk sanda kk da bugatar wani abu let me know... zaki iya serving abincinki da kankiko?, ina sauri zan iya makara" kai ta gyada masa, sai ya juya a hankali yana furta
"Fi amanillah" da idanu ta bishi har ya fice daga dakin, tana jin kamar ta dawo dashi ta zaunar dashi a waje daya.
*****Kamar yadda yace mata ne, cikin kwanakin duka busy din yayi. Amma hakan bai hanashi dubata da safe ba. Sau tari kuma Lokacin da zai dawo wani kasalallen bacci yayi awon gaba da ita, don haka bata sanin lokacin da yake dawowar.
Duk yadda takeson space takeso kuma ya bata sai wannan abun ya gundureta, ta dinga blaming kanta da kanta, me yasa?, wal me yasa?.
Duk da yanayin da take ciki me wahala amma hakan bal hanata hada program dinta ba. A ranar da ya zamana washegari ne ranar da zata shiga Tv station, takai har garfe goma na dare a zaune tana hada komai cikin laptop dinta. Ta kammala ta tattara komal ta aje gefe tana duba agogo, baccin da takeyi da wuri ne kenan ya sanya bata gane daren da yakey kafin ya dawo gidan ba?.
"To ina yake zuwa?, har yakeyin dare?" Ta yiwa kanta tambayar.
"Laila......ayana" ta tuna
sunayensu, wani abu kuma ya darsu a zuciyarta, abinda ya sanyata taji kanta ya Sara kenan, ta saka hannunta daya tadan tallafi kan nata tana lumshe idanunta.
Tsation mintuna goma
sha biyar tana zaune a haka ta ji garar motarsa. Ta sauke hannunta a hankali tana kallon yadda hasken fitilun motar ke ratso labulayen dakin nata. Tana iya jin muryarsa gasa yasa da alamu waya yakeyi, ranta ta ji ya sosu, ta maida idanunta ta lumshe sai kuma ta mige tana wucewa toilet.
Fitsari tayi don a yanzun
ba wani rige fitsari takeyi sosai ba, sai kuma ta daura alwala kaman yadda ta saba duk sanda take da niyyar yin bacci, ta dauko garamin towel don tsane damshi sannan ta nufo waje.
Yana tsaye tsakiyar
dakin, hannunsa guda cikin al jihun wandonsa, dayan kuma dauke da wayarsa yana dannawa. Suit dinshi na saman yana rataye a kafadarsa. Haske

Please Login or Register in order to submit comment