Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

qarfi matuqa daga hancinta zuwa cikinta sannan ta fesar,yanayin yadda yayi magana ya ratsata qwarai,har taji kowacce kalma na sauka a kowanne gaba na jikinta,ta dinga jin abinda ya fadi din kamar dahir ne,amma kuma wani sashe na zuciyarta sai taji ya kasa aminta da hakan. Ta ina zai zaqulota?,ta yaya zai taddota?,bayan inda zata shiga din zata guje masa ne da nisan tazarar tafiyar awanni da kwanaki ma?,ba zata taba bari ya zaqulota ba, tabbas!.....itama zata tabbatar ta cika wannan alwashin da taci. Da wannan tunanin ta fito daga bakin bandakin don dama bawai wani abu zatayi a ciki ba,mafaka kawai take nema,ta dawo cikin dakin jikinta na neman mutuwa amma ta bawa kanta qwarin gwiwa,ta sauke suit case dinta guda biyu,ta soma hada komai nata waje daya,tana ji a ranta da zuciyarta muddin yana nijer batasan ranar sake zuwanta ba.

Shi daya cikin mota suna a hanya amma dukka jikinsa ya mutu murus,irin qiyayya da tsanar da yake hanga cikin idanunta tana taba zuciyarsa sosai,baisan me take buqata daga gareshi ba wanda zai wanke dukka laifin da yayi mata. Kamar me magana a radio din yasan me yake tattaunawa cikin ransa ya soma magana kaman haka

_ba kowacce matsala ce tsakanin masoya sulhu ke maganceta ba,wani lokaci sai ayi fada,wani lokacin sai anyi qarfa qarfa an saka qarfin iko_ a nutse ya lumshe idanunsa yana digesting maganar a kwanyarsa,tsahon mintuna kusan talatin kafin wani murmushi ya subuce masa

"Na fahimta" ya furta can qasa yana jinjina kai.

"Me ka fahimta yallabai?" Suhail dake zaune gefansa yana duba newspaper da alama shidin makarancin labarai ne ya fadi yana duban maina. Juyowa yayi suka hada idanu dashi ta cikin eye glasses dinsa

"It's not your own business" idanu suhail din ya dan fiddo sai kuma ya maidasu yana rufe jaridan

"U right.....abinda yafi damuna rashin samun layin crush dina......kaine nake ganin zaka taimaka min kana neman watsa min qasa a idanu,ka qirqiri wasu labarai duk don ka nesantata dani......ni kuma nayi alqawarin bazan bar marad'i ba sai da soyayyarta" ya fadi yana dunqule hannunsa guri guda. Da qyar maina yawu ya wuce ta maqoshin maina,ya dauke kansa a hankali yana qoqarin tausar zuciyarsa kan kada ya yiwa suhail mugun bugu cikin motar,muddin yace zai daki suhail to saidai buzunsa,don ko a qirar jiki suhail din dan kalankashi ne me jikin fulani. Hannunsa ya tura cikin qaramar jakarsa ya fiddo headphones ya dora saman kansa ya toshe kunnuwansa,yayi connecting da wayarsa ya soma sauraren wani abu na daban,sai suhail yayi sak yana kallonsa kafin daga bisani ya dauke kallonsa yana girgiza kai.


**********Washegari sukayi sallama da dukkan wani family din MAYAK'I suka wuce airport suka bar al'ummar gidan cike da kewar iyalan ama musamman BB. Bibi harda qananun qwallar wucewar yaran

"An daukesu an dauke uwarsu" ta fadi cikin falon nata tana qananun qwalla. Kusan dariya ta bawa kowa,bibi din bata iya sabo da mutum ba idan ta tashi sabo dashi din,bare sultana da take tamkar wani bangare na jikinta,ga yaran suma sun dosano farinjininta da kuma soyayyar data samu din.

"Sai da nace ki shirya mu wuce tare bibi,yanzun a miki shiri ki biyo bayanmu?" Ama ta furta cikin lallashi. Kai bibi ta girgiza

"A'ah hamdiyya,barni a nan cikin ahalina,shekaruna turawa sukeyi,na gaji da yawo a qarfen nasara,irin haka ne mutuwa zata riskeka a qasar wasu azo ayita tiri tiri da gawarka,ko mutuwa ne gwara ka mutu cikin sutura a dakinka" maganar tata sai tadan taba zuciyar kowa amma sai suka bita da dariya,sultana tace

"Mutuwa bibi ba yanzu ba,Allah ya qara miki dogon kwana me amfani"

"Ameen" aba dake duqe shima a gabanta ya amsa. Nutsuwa sukayi bibi ta musu addu'o'i sosai sannan suka miqe,har sun fita ta sanya aka kira mata aba,ya dawo gabanta ya tsugunna

"Hamidou"

"Na'am bibi?"

"Rayuwa bata da tabbas,hakanan duk dan adam bai wuce kuskure ba,shine cikar dan adam din,abinda nakeso dakai don Allah ina roqonka ka sassautawa yaron nan koda a iya fuska ne,ya dawo da dukka qwarin gwiwarsa da kuma daidaita rayuwarsa,bai kamata mu rushe komai nasa ba akan kuskuren da ya riga ya afku,kuma Allah ya kawo yankewar komai ba tare da an samu mummunan sakamakon lalacewar rayuwar wani cikin su biyun ba" kai ya gyada a ladabce

"In sha Allah bibi"

"Allah ya albarkaci rayuwarku gaba daya" ya amsa da ameen.

Lokacin da jirginsu ya daidaita a sararin samaniya sai ta furta

"Alhamdulillah" cikin wata cikakkiyar nutsuwa,ta rufe idanunta tana jinta ta zama comfortable, murmushi ya kufce mata,can qasan maqoshinta ta fadi

"Naga ta inda zaka nemo ni" tayi maganar cikin mugunta da jin ta tsere masa har abada.

A nutse ama ta dauke dubanta daga fuskarta tana sauke tata ajiyar zuciyar,tun daxun ta fahimci yadda take cikin walwala da barowarsu nijer,ta sani koma meye zai sakata walwala baya rasa nasaba da gujewa maina,batasan yadda wannan qaddara ta samo asali ba,kuma Allah shine masanin lokacin qarewarta,bata taba ganin irin wannan mummunar rashin jituwar kamar tasu ba,tun abun be damunta har ya soma tabata,abu daya ya rage mata wannan addu'ar zata ci gaba dayi

"Allahumma khir li wakhtarli". Maida dubanta ta sakeyi ga benazeer da batoul,basuyi sallama da mahaifinsu ba don basusan inda zasu koma din wani guri ne da zasu jima basu ganshi ba,duka lissafinsu Nigeria zasu sake zuwa suyi wani hutun na kwana daya ko biyu kafin daddynsu shima ya dawo daga tafiya.

Iska ta kuma furzarwa,Allah ya sani taqi shaida masa ne saboda tana son ya sake sanin maqurar muhimmancin mace a wajen d'a namiji,tanason yasha wahalar samo kanta wadda bai sha ba sanda aka aura masa ita sama taka yana zaune cikin inuwa,tanason ya jigata yadda bazaiyi wasa da ita ba,bazai kuma yi wasa wajen nemo soyayyarta ba. Murmushi yadan qwace mata tana hangoshi sanda zai duba kaf gidan yaga ba ita ba benazeer ba batoul ba kuma sultana din. Ta tabbatar sai yayi musu qaramar hauka,to amma kuma tana dan shakkar anya zaya dauki lokaci mai tsaho me gano inda suke ba?. Ta sanshi farin sani tas ma kuwa,tunda dai ya fita daga jikinta ne,yana da naci da bin qwaqwafi akan dukkan abinda yakeson aiwatarwa ya kuma sanya a gaba,uwa uba ko da can yana da wata fikira da basirar saurin gano abu,to amma koda ya gano inda suke din,tasan bazai gano su a banza ba,dole energy da kudaden aljihunsa suyi aiki,idan yazo kuma ya kawo mata kanshi,don ba zata zake bari yayi aiki qarqashin wasu ba,bayan a abinda kakanninsa ita da aba suka tara masa yana da dukiyar zai dauki mutum Dari aiki a qarqashinsa da cikakken albashin da zai riqe kowanne ma'aikaci da iyalinsa.

Kwana daya rak suka daidaita cikin qasar France a garin paris. Ba wani dauda ko qura me yawa suka samu,don haka cikin awanni qalilan suka gyare komai,komai kuma ya koma kan muhallinsa,abu na gaba data fara shiri shine fara aikinta a sati na gaba a gidan tv ta qasar paris,wanda zata zama jagorar shirin daya shafi al'adun africa gaba daya. A satin suka tura mata kudade masu yawa daga gidan tv din na wardrobe allowance. Bata da buqata ba abinda kuma zatayi dasu,don suttura kam wata ma sai ta shekara biyu bata sakata ba. Ta bangaren aikinta da zata fara kuwa komai aba ya tanadar mata,ga ama itama a gefe data tsaya mata kan ta lissafa duk abinda take da buqata ko takeso,buqata kam saidai idan bata fadi wadda takeso ba,don haka hanakalinta kwance take shirye shiryen kama aikinta.

*_MAINA FA?_**_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 78




*ALIYYU MAINA*


Cikin qwazo da kuma qwarewa ya jagorancin aikin duba kamfanin da gabatar da abubuwan da suka zama dole a buqata a cikinsa don samun ingantattun abubuwa da zasu dinga fitarwa. Haka kawai ya samu hankalinsa da tunaninsa suna karkasuwa kashi kashi,wani a niamy wani a marad'i,duk bayan wasu lokuta sai benazeer da batoul sun fado masa a rai,ta wani gefen kuma sultanan ce gaba daya tayi masa tsaye a rai,yana tuna abubuwa masu yawa da suka faru a tsakaninsu,bama iya sultana kawai ba hatta da yaran,wani abun ya saki murmushi wani ya girgiza kai,daga qarshe yakai tafin hannunsa saman qur'aninsa saitin zuciyarsa ya dafe yana fidda wani sihirtaccen murmushi.

Ya yadda yayi imani sannan kuma ya tabbatar a yanzun sune rayuwarsa,sune Kuma duniyarsa gaba daya,bayajin zaya iya rayuwa ba tare dasu ba,haqurin da yayi na wancan shekarun,ya rayu babu su,a wannan karon baya jin zuciyarsa zata dauke wannan. Wannan tunanin ya sanyashi yin overwork a ranar,suhail nata mitar ya gaji,ba sauri sukeyi ba,me zaya hana su isa masauki su kwanta, gobe su qarasa zuwa jibi,ko gata ne sa koma marad'i din,ai suna da enough time.

Juyawa yayi kawai ya kalleshi,shi daya yasan me yakeji a zuciyarsa,yana ji kaman ya raba zuciyarsa ne gida biyu yabar rabi a marad'i,a wannin da yaketa spending a nan din yana ji kaman ya maidosu marad'i,bazai taba iya kaiwa jibi a niamy ba,yana buqatar komawa ya hada kan iyalinshi waje guda,ayi duk abinda za'a yi a gama,zai rungumi kowanne irin tsanani,don wannan karon bawi da wasa yakeson maidota cikin rayuwarsa ba.

"Ban hanaka zuwa ka kwanta ba......abinda na sani dai kawai shine,gobe in sha Allah a marad'i zan kwana,ko mun gama ko bamu gama ba,bare ma inda tabbacin na sanya dukkan effort dina,gobe azahar yayi yawa mun gama in sha Allah.....idan ka gaji kaje ka huta zan iya kammalawa" bai sake cewa komai ba ya maida kansa yaci gaba da magana da ma'aikatan.

Satar kallon maina din kawai yakeyi,he's so hardworking,tun farkon haduwarsu abinda yaja raayinsa game dashi kenan,bashi da wasa,ko meye ya saka a gabansa sai ya cimma nasararsa. Iya wannan daya tuna din,sai shima ya kakkabe dukkan wata guntuwar kasala ya miqe sosai suka ci gaba da aikin tare.

Kaman yadda ya yiwa kansa alqawari washegarin qarfe sha biyu na rana sun kammala komai,zuwa qarfe daya ya kammala rubutawa daddy report ya tura masa ya kuma turawa sardauna ragowar,kai tsaye suka koma masauki,ya koma toilet ya sake watsa ruwa,ya kuma shirya tsaf cikin wani lallausan farin yadi,saidai kuma dukka wannan gaggawar tashi dole ya jira akwai ragowar lokaci,don jirginsu sai qarfe hudu zai tashi,yana ji yana gani ya fita corridor din dake manne da dakinsu ya zauna samam couch yana duban suhail dake zaune d'ai d'ai abinsa ba alamun shiri tattare dashi.

Kanshi ya dauke yana zuqar numfashi,zayaso suhail din yayi zamansa a nan ba tare daya bishi marad'i din ba,duk da haka sai ya danne zuciyarsa ya tambayeshin yana duban wani guri na daban

"Hala ka dawo gida kenan?"

"Me ka gani?" Suhail dake shan yoghurt ya fadi

"Banga alamun tafiya tattare dakai ba,na dauka zaka kammala hutunka a nan,zamu hade kawai a France"

"Inaaaa" ya furta yana miqewa da hanzari kamar wanda aka mintsina,har sai da maina dole ya juyo ya kalleshi.

Fararen danunsa fes cikin na maina din yana kallonsa

"Banga ta zama ba,ka manta har yanxu ko cikakken magana bamuyi da crush dina ba?,yaya zan koma ban samu soyayyata ba?" Idanunsa ya mayar ya lumshe.

yanajin kamar suhail yana diga masa wani abu saman zuciyarsa,baisan me yasa ba,ba halin suhail bane qin fahimtar mutum da gangan ba,amma sai yaga kaman idanunsa ya rufe a wannan karon

"Idan ma akwai wanda ya sanyaka kakemin haka......ina me baka shawarar kabi a hankali,idan har ka bari na fusata zan manta da matsayinka a wajena,na gaya maka ina kuma sake gaya maka,sultana is my wife......" Yana kaiwa nan ya miqe a nutse yana bar masa wajen. Da kallo suhail ya bishi,shi fa har yanzu yana tantama akan hakan,ta yaya hakan zata kasance?,shekarunsu nawa dashi?,amma koda wasa bai taba zancan wata ba?,yaran da yake iqirarin nashin ne sau nawa suna zancan baisan yaran wanne qasa bane?. Kai ya girgiza,shi kam har yanzu bai gamsu da zancansa ba.

Kafin lokacin ya cika sai ga suhail din ya shirya tsaf harda jakanshi da wasu kayan daya musanyo daga ainihin masaukinsa gidan kakanninsa. Maina din baice masa komai ba,don haka ko cikin jirgi ma kowa sabgar gabanshi yakeyi.

Awa biyu rak ta iso dasu marad'i,cikin drivers na gidan mayak'i daya daga ciki yazo ya daukesu daga airport cikin daya daga cikin motocin maina dake gidan.

"Wanne kalan malalacin tuqi kakeyi ne?" Maina ya tambayi driver din yana kallonsa ta cikin madubin. Waiwayowa suhail dake qoqarin kunna wayarsa yayi ya kalli maina,sai ya maida dubansa ga driver din wanda yake qoqarin take motar ya qara mata gudu

"Kada ka damu tuqinka yayi dai dai ba laifi,muje a haka" sai ya juya ga maina. Ya fahimci kaman bashi da nutsuwa daga jiyan zuwa yau

"Fake wife din naka ka matsu ka gani ne?" Ya tambayeshi cikin muryarsa akwai sautin tsokana me yawa. Wannan karon gaza daurewa maina yayi,ya kaima suhail wani mummunan duka a kafadarsa,saiga suhail din ya gantsare yana runtse idanu hadi dayi masa nuni da driver dake cikin motar. Dukka girarsa ya daga yana nuna masa ko a jikinsa

"Gaba idan ina sabgogi na nida iyalina ka sake shiga,na rantse da Allah da Allah saidai su sardauna suzo su daukeka a kakkarye"

"Amma dai kai mugu ne wallahi,koda yake na fuskanci inda ka dosa,kishi ne yake dawainiya dakai,kuma kada ka manta......ba sauke kafada ba,ko meye zaka yimin idan tace saini saini din" tafin hannunsa kawai ya sanya ya lullube fuskarsa,ya fuskanci ko meye zai cewa suhail bazai daina fadin abinda ke ransa ba,tun ba yau ba,yasan shi din dan kai tsaye ne,amma yanzun ya soma fahimtar abinda yakeyi masan kamar akwai wata a qasa.

Ana kiraye kirayen magarib motar ta daidaita a farfajiyar babban gidan nasu,ya sauke ajiyar zuciya yana dan yawo da idanunsa wai ko zai hangi benazeer ko batoul. Yanason shiga ciki ya gansu,to amma kuma muddin ya shiga din zai iya rasa jam'in sallah,don haka ya daure ya cire agogonsa da sauran kayayyakinsa ya miqawa attah yace ya shiga masa dashi wajen ama. Atta din nason masa bayanin saidai ya kaiwa bibi yaga har ya juya yana amsar ruwan alwala daga hannun daya daga cikin ma'aikatan gidan,don yace bazai qarasa famfunan dake jere a farfajiyar gidan.

Tare suka wuce masallacin shi da suhail almu atta da saddi. Sukayi sahu daya har aka idar,bai zauna azkar ba yasan kafin ya isa gida ya kammalasu a hanya,suka sake rankayawa cikin gida tare.

Sassan ama ya soma wucewa kai tsaye,saidai tun bai isa ba ya fuskanci sashen a kulle yake,ya dubi almu da suke tare

"Ina ama?"*_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 79



"bata nan" ya amsa masa yana dan sosa kanshi,don shi bashi yaso ya shaida masa tafiyar tashi ba kada ya debo rigimar da tafi qarfin shekarunshi. Ido yadan qanqance yana kallonsa

"Kuma aka rufe sashen gaba daya haka?"

"Eh...... zata.....zata danyi kwana biyu ne" dan jim yayi yana jinjina abun,har yanzu ama fushi takeyi ne dashi haka da har zatayi wata muhimmiyar tafiyar da zatayi kwana biyu amma bata gaya masa ba?. Kai ya gyada yana juyawa a hankali,har yayi taku biyu kuma sai ya waiwayo

"Ita da waye tayi tafiyar?,na ganku dukka a gida kai dasu saddi?"

"Benazeer da batoul sai mamarsu......a gida dama mu muke,ba zamu iya dadewar da sukeyi a can ba" ya amsawa maina kai tsaye duk da kaucewar da yaso yi. Duka maganar saita dunqulewa maina waje daya,wanne irin dadewa sukeyi?,a ina kuma suke dadewar?,ina suka tafi?.

"Ina suka tafi?" Ya tambayeshi yana jin fargaba cikin ranshi,don maganar data gaya masa ta qarshe ce ke dawo masa ka

"Da dai Austria suka fara zuwa,amma daga baya sun canza qasa,ban dai tantance ba"

"Hasbunallahu wani'imal wakil" ya fadi cikin ransa,indai hakane kenan ama ta sake debe masa iyali sun yi nesa?,nesan da baisan waye zai masa cikakken bayani cikin gidan ba?.

"Amma wanne iri ne kai?,ta yaya mahaifiyarka zatayi nesa dakai irin haka amma kuma bakasan wanne qasa take ba?"

"Bata gayamana ba ya maina...."

"Okay saita gaya maka?!" Ya tambayeshi a tsawace,tsawar data ratsashi sosai. Qas yayi da kansa yana dan ja baya gudun kada yakai masa duka

"U are not serious at all" ya fadi yana juyawa zuciyarsa na masa susa.

Yana takawa zuwa cikin sashen bibi amma gaba daya hankalinsa a dagule yake,da gaske take kenan da tace basai ya dawo ya sameta ba?,wanann din duka plan ne kenan?,plan kuma harda saka hannun ama?,kenan ama tafi son sultana a kanshi?,tafison farincikin sultana akan nashi farincikin?. Da wannan tunanin a ransa yayi sallama murya can ciki a falon bibi,idanunshi a kanta tana zaune tana amsa waya da wayar hamaissa ta sashen oncle umar.

Zamewa yarinyar tayi ta gaidashi ta soma barin falon,duk da bai jima da dawowa cikinsu ba amma halinsa ba baqo bane sannane ne,kuma har yanzu babu wani abu daya sauya game da halin nasa tunda suna gani.

Zamewa yayi ya zauna sosai gaban bibi kanshi a qasa,kunnuwansa suna sauraren wayar da bibi din takeyi,amma kuma saidai gaba daya hankalinsa yayi nisa da wajen,saidai ya fahimci waya takeyi hankalinta kwance,kenan babu abinda ya shalleta ko ya dameta?.

Kokawa yaketayi da zuciyarsa da kuma harshensa don kada fushi ya sanyashi fadin abinda bai kamata ba. Yana zaune bai motsa ba har ta ida wayar ta aje gefanta tana dubansa. Bacin rai fushi da kuma motsuwar zuciyarsa baya boyuwa a idanunta. Bata kai ga magana ba ya daga idanunsa da shi kansa yakejin sun sauya launi

"Abinda akeyimin bibi ya fara kaini maqura......ayimin hukunci kawai a wuce wajen amma ba'a yimin ba?,sai a dinga yimin wani irin bahagon horo?,zuciyata akeso ta buga?, saboda inata kawaici?" Bude baki bibi tayi kawai tana kallonsa,kafin ta tattara mamakinta tsaf ta alkinta bayan ta tuna waye ALIYYUN

"yanzu wannan baqi da farin da kazo kana ja da waye kake?" Ta furta fana jefa masa wani kallo a kaikaice

"Kun tattaramin matata da 'ya'yana kun cillasu wata duniya,bada sanina ba,bada izini na ba,wannan dai dai ne?" Ya qarashe maganar yana duban bibin. Motsawa tayi tana sake daukar wayar gefanta

"Af.....wannan zancan ai hamidou ya kamata na kira maka saika gaya masa kai tsaye,kasan waqa a bakin me ita tafi dadi ko?" Ta fadi tana lalube cikin wayar.

A nutse ya sanya hannu ya zare wayar daga hannunta,saita bishi da kallo sanda yake aje wayar gefe

"Meye na gaggawa bibi?,zan fadi mishi a sanda na lalubosu da kaina ba tare da neman taimakon kowa ko qarin haske daga gurin kowa ba.....zan tabbatar muku ina matuqar qaunarsu,kuma su din jinina ne....... numfashi na sannan kuma rayuwata.......saidai kuma,daga sanda na nemosu da kaina,a barni da matata saboda halalina ce ita din.....,inason ki isarmin da wannan saqon" baki bibi ta kama tana kallonsa,dukka ya gama sanyata jin kunya da nauyin kalamansa,data rasa abunyi sai kawai ta buge masa da borin kunya

"Nice marainiyar wayonka kenan kazo ka zauna ka sakani a gaba kake gayamin?" Wani malalacin murmushi ya saki,don yanzun bashi da kowanne energy na biyewa bibi akan maganarta,sai ya miqe tsam,ya matsa gaba ya kama hannunta yayi kissing bayan hannun nata a kasalance yana cewa

"Karki rigima dani,don nima gobe zan koma inda na fito in sha Allah" yana ganin yadda jikinta yayi sanyi saboda maganarshi ta qarshe,ya juya a nutse ya fita a dakin.

Bai samu suhail cikin dakin ba,amma kuma yaji tashin muryarsa a harabar gidan shi da security,yasan halinsa dan rudu ne,yanzun haka wata hirar ya samu a can shi yasa yayi zamansa,dadewarsa da yawa kuma ya bashi tabbacin qilan ya wuce wajen mutuniyar tasa wato bibi. Sanda almu ya kawo masa abinci ya tabbatar masa da haka.

Ba wani taste yaji a abincin ba,don ba abincin ba hatta gidan a daren salam yake jinsa,kafin suhail ya shigo dakin tuni ya kade passport dinsa ya sanya a yanka masa ticket,gwara ya koma Paris ya soma rage wasu abubuwan kafin binciken inda sukayi ya kammala,don yaci alwashi yadda yayi mata alqawari to sai ya cika,sai ya zaqulota ko a ina take cikin fadin duniya.

Yayi sa'a qwarai ya samu ticket na jirgin da zai tashi daga abuja zuwa Paris direct kwanaki biyun da zasu zo a gaba,ba haka yaso ba, yaso ya samu wanda zai tashi a gobe,to amma haka dole ya haqura ya karba a haka,saidai iuma yaji yafi masa sauqi ya wuce Abuja gidan daya daga cikin kawunnan nasa ya jira kwanakin, uncle abdulhakeem ko uncle tahir.

Sai washegari da safe yake gayawa suhail zai koma,yayi mamaki suhail din ya kuma tambayeshi me ya kawo wannan tafiyar haka ta gaggawa

"Lokacine yayi" kawai ya amsa masa a taqaice

"Alright,yayi,ni zan qarashe weekend dina a nan gidan,kasan gidan masoyi dadi gareshi,ga kuma sabuwar granny na samu,ina jin kusan sai sabon wata zan taddaka a Paris"

"Allah ya kaimu" ya amsa masa a taqaice. Ya lura akwai damuwa me yawa cikin idanun maina din,to amma yasan hali sarai,ba lallai bane ya bashi amsa idan ya tambayeshi,don haka sai kawai ya tayashi da addu'a cikin ransa.


***********Jiran mintuna kadan yayi bayan ya shaidawa uncle tahir yana cikin filin sauka da tashin jiragen sama na garin abuja aka kirashi da wata baquwar number.

Cikin matuqar yauqi da iyayi take magana ta cikin wayar

"Hello......mr haidar?"

"Yes" ya amsa a taqaice

"Sunana ayana tahir me kano......kana ta wanne guri?,ina jiranka zanyi picking naka"

"Gani nan qarasowa" ya amsa mata a taqaice daga inda yake yana hangota. Idanunsa ya sauke daga kanta,duk da ya jima rabon daya ganta,tun batafi shekara sha takwas ba amma hakan bai hanashi ganeta ba,saboda tsananin kama da sukayi da uncle tahir din.

Straight gown ne a jikinta na wani yadi wine color,ta yane kanta da mayafi gray color me haske. Kana kallonta zakasan ta hada jini da abzinawa sosai,sai ya sanya wayarsh a aljihu ya jawo luggage dinsa yana nufarta.



Please Login or Register in order to submit comment