Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

magantu

"Ina zaka kaini?,nan ba hanyar bace" juyowa yayi idanunsu suka hadu waje daya

"Nace miki fyade zanje nayi miki karo na biyu tunda wancan ya amsa sunansa" yayi maganar yana dauke kan motar suka shiga wani titi na daban da wani irin zafin nama.

Ido kawai ta zuba suna ci gaba da wuce wurare har suka iso babban ginin daya tsaya a gabanshi yana karbar binciken security kafin wucewarsa ciki.

Idanunta ta daga tana qarewa ginin kallo,sunan data gani daga qarshen sunan dake kafe a tsororuwar babban ginin ya sanya gabanta harbawa

"Hotel?,to me sukazo yi s hotel?" Ta tambayi kanta da kanta. Kafin ta lalubi amsa har ya gama da security ya wuce cikin babban harabar hotel din.

Ko ba'a gaya mata ba da ganin tsari da girman wajen tasan hotel ne na manyan mutane masu hannu da shuni,komai bisa tsari tun daga farfajiyar har tsarin ginin wajen

*_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400
BIYU_800
UKU_900
HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875
Musaa Abdullahi safiya
Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261


*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku kudin*

09033181070


*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂*_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 71


Bayan ya daidaita tsaiwar motar,ya zare seatbelt dinsa yana dubanta,kaman zaiyi magana sai kuma ya fasa,ya bude side dinsa ya fice. D

Bata koda kalli sassan da yake ba har sai da taji ya maida murfin ya rufe, second biyu ta bayar ta waiwaya da kanta tana duban gefanta.

Cikin takun nan nasa me cike da ginshira da qasaita yake takawa zuwa main entrance na hotel din,hannunsa guda daya zube a aljihun wandonsa,daya hannun kuma wayarshi da key din motar ya riqe. Idanunta ta kawar tana tabe tana jan tsaki,tana mamakin irin qarfin halinsa,yanayin komai kamar baisan ya aikata komai ba,kamar kuma bame laifin komai ba,yanata maimaita kalmar fyade zaiyi mata kamar wata kyakkyawar kalma me dadin ji da sauraro?,baya ma ko kunyar idanunta bare abinda ya aikata a baya da ita har yanzun sunan fyade ta bashi?,duk da ta fahimci da gasken ba fyaden bane,sadakinsa na saifa daya bayar ya sauyawa abun suna a musulunce. Yanxun daya kawota nan din me zaiyi a ciki?, Tambayar data yiwa kanta kenan kuma bata da amsarta.

Tunaninta ya katse sanda kira ya shigo wayarta,ta bude handbag dinta ta zaro wayar tana gyara ajiyar cards dinta masu amfani dake ciki. Yasmin ce sarkin zaquwa da gaggawa

"Shuru.....shuru sultana lamarinki sam babu kara fa" yasmine ta fadi cikin zumudi

"Afwan yasmine...... kin ganni nan......" Da sauri ta katse abinda da farko tayi niyyar fadi,sam ta mance,tana shirin dabawa kanta da kanta wuqa

"Ina hanya bazan wuce awa daya ba in sha Allah"

"Shikenan,ina jira,aminata ma ke take tsumayi"

"In sha Allah" ta amsa mata tana lumshe ido saboda bacin rai daya taso.mata. gaba daya ya sauya mata akalar tafiya?,wai anya ma ba sassauci ya gani saman fuskarta yake neman rainata har haka ba?.

Tana katse kiran tare da qoqarin sauka daga call logs dinta taji ya bude murfin motar a hankali. Sam batasan da isowarsa wajen ba don hankalinta baya kai. Idanunta ta daga a hankali ta sauke dubanta a kansa. Yana tsaye gabanta,cikin cikakkiyar tsaiwar nan tasa dake sake fidda diga da zatinsa. Cikakken tsayayyen ba'abzine dogo fari tas. Shima ita din yake kalla,hasken rana daya haska qwayar idanunta dake da sheqi kamar an diga zaiba sai ya bada wani irin haske me kyau,abinda ya masa kwarjini qwarai,mazantakarsa ta sanyashi shanyewa,ya sassauta kafin nasa qwayar idanun cikin nata kadan,sannan ya rusuna yana dauke handbag din take saman cinyarta,wanda kafin tayi kowanne yunquri ya soma takawa yana barin wajen

"Taso mu qarasa"

"ina?" Ta tambayi kanta tana fidda ido waje. Ganin bai waiwayo ba ci gaba yakeyi da shiga ciki,ga idanu da sukayi yawa a kanta dole ta zura qafafunta waje tabi bayansa. Tana biye dashi saidai ta cika tayi fam da bacin rai da baqinciki

"Wai me wannan yakeji dashi ne?" Ta yiwa kanta da kanta tambayar. Yadda suka dinga wuce security ana checking nasu duk inda suka wuce ya sanya ta sake shiga nutsuwarta sosai amma kuma ranta cike yake fal da fargabar shigarta wajen,batasan me yazo yi ba,batasan me ya kawosu yi ba.

Elevator taga ya nufa,ya danna ta bude ta shige,sai a sannan ya waiwaya yana kallonta. Ja tayi ta tsaya,abun ya isheta haka,ya maidata kaman wata raqumi da akala?. Yana tsaye daga bakin qofar ta yadda bazai bata daman rufewa ba ya kuma tsareta da ido.

"Idan kika qara minti daya a nan wannan karon nine zan miki ihu na kuma tara miki mutane kaman yadda kika yimin wancan karon" hanjin cikinta taji ya dunqule guri daya,daga yadda taga wajen yadda yake cike da matakan tsaro idan ya aikata mata hakan ta kade daga ita har ganyenta

"Idan kin damqani a hannun police har na kwana ni a hannun da zan damqaki ko?......." Bai qarasa ba illa yatsansa daya nunata dashi wani shu'umin murmushi na mugunta na kubcewa daga saman labbansa.

Babu shiri tayi taku biyu xuwa gaba,sai yayi taku biyu baya har ta shiga elevator din ya rufe dasu suka fara wucewa zuwa floor din daya zabar musu.

Tana tsaye daga bakin qofar dakin take qarewa dakin kallo. Babban daki ne wanda aka wadatashi da komai na alatun rayuwa. Kana ganinsa kasan vip suit ne na isassun mutane. Idanunta ta dauke daga kallon dakin ta maida kansa sanda yake qarasawa ciki yana ajjiye key din motar saman bedside drawer din dake dauke da bed lamp. Wani abu ta sake hadiyewa me tauri daya tsaya mata a wuya tun dazun

"Amma dai kasan inda zanje ko?" Ta jefa masa tambayar muryarta na bayyanar da bacin ranta

"Na sani......ina da buqatar na huta tukunna kafin mu wuce"

"Bana buqatar wani hutu.. wannan abun da kakeyimin ya isheni haka,ka bani key dina na tafi,idan kaso ka bari sai wata shekarar sai ka taho wannan ba damuwar sultana bace" ta fada tana yarfa hannu cikin fusata. Sosai ya zauna saman sofan dake dakin,ya kuma dora qafanshi daya saman daya yana qare mata kallo tsaf har takai aya.

Murmushin gefen baki ya saki yana kada kai

"Taurin kai da rashin kunyar nan naga alama da sauranta har yanzu......yayi kyau......haka nakeson gani" ya fadi yana sauke qafafunsa qasa,sai ya miqe cak abinsa ya qarasa bakin window din dakin,ya zuge labulen yana hangen view me kyau daga nan cikin dakin. Abun sai ya fusata ta,wato ya maidata wata mahaukaciya ma,ta hasala sosai,kawai sai ta fara masifa idanu rufe. Yi yayi kaman baiji ba har minti kusan biyu. Ya saki labulen ya juyo a tsanake. Kallo days yayi mata sai yakau da kai,ya sanya hannunsa a nutse ya fara balle botiran rigarsa.

Da farko bata ankara ba har sai daya gama ballesu tas,fara qal din vest dinsa dake ciki ta bayyana kanta,ya saka hannunsa ya fara zare rigar a nutse,ya cireta tsaf ya ajjiyeta a gefe.

Kallo daya tayi ma qirar jikinsa wata shakkarsa me qarfin gaske ta shigeta. Murdadden jiki me cike da baqa sidik din gargasa. Ba tare da yace mata kanzil ba sai gashi dukka maganganun da take zubarwa tana musu muhalli tare da maidasu cikin cikinta ragowar da bata ida furtasu ba. Tsoro sosai ya shigeta sanda ya zare ragowar vest din data rage a jikinsa ya waiwayo kuma yana dubanta.

Guri daya idanunsu suka sarqe,ya lumshe idanun nasa yana mata nuni da dogon wandon jikinsa yana riqe hannunsa a qugunsa. Ba qaramar yarinya bace ita,hakanan tun ba yau ba yayi mata sabo da body language,don haka sarai ta fahimci me yake nufi. Cikin dakiya ta aje masa wani kallo zuciyarta na tsananta gudu kaman zata fasa qirjinta ta fito

"Muqulli na kawai nake da buqata......kada ka yarda kaci gaba da shiga hurumin........" Bata qarasa ba ta tsinceshi gabanta,yayi mata katanga da faffadan qirjinsa. Dukka tsahonta ya shanyeshi,bata kuma tsaya ko ina ba sai daidai qirjinsa dake a waje cikin ni'imatacciyar lallausar suma.

Baya tayi niyyar ja da sauri,saidai kuma kafin takai ga aiwatar da hakan ya sanya hannu daya ya fusgota. Batayi masauki ko ina ba sai saman qirjinsa,fuskarta ta samu kyakkyawar tarba tsakiyar kwantacciyar sumar qirjinsa. Wani dogon matsoracin numfashi taja wanda ke cakude da sassanyan qamshin dake fita daga cikin gargasar tasar. Kafin tayi tunani na biyu ya sanya dukka hannuwansa biyu ya warware mayafinta tas.....bai barta ta gama nutsuwa ko tattara hankalinta waje daya ba ya sauke mata dankwalinta,wanda cikin sa'a ya hada harda ribbon dinta,abinda ya bawa doguwar sumarta daman bajewa gaban fuskarta zuwa gadon bayanta.

Tana cikin qoqarin tattara sumar nata cikin tashin hankali da tunanin me yake shirin aikatawa,fit......taji ya sauke zip din gaban rigarta gaba daya tun daga sama har qasa,abinda ya sakata sakin gashin nata kenan a muqar gigicewa da kuma razanin yadda ya iya aikata hakan kamar qiftawar idanu

"Mm......meyeh.....haka?,wanne abunne wannan?" Ta tambayeshi a gigice tana qoqarin tattaro gaban rigar tata don hana bayyanuwar jikinta muraran

"Ladabi zan sakeyi miki,don na fahimci yara biyun ma da kika haifa basu sanya kin sauya hali ba...... karatu kawai kikayi ba ilimi ba, yanzun zan baki cikakken ilimi,and yanzun yara uku nakeso na baki ajiya!"

"Maina!...... don't......" taja sunansa da wani irin amon sauti me dauke da tashin hankali......Sai ta kasa qarasa fadin abinda takeson fada din saboda tsintar tausasan tafukan hannayensa da tayi cikin ainihin fatar jikinta yana yawo dasu daga saman cikinta ya zagaya har zuwa gadon bayanta sannan ya zarce yana neman maballin bra dinta

"Don't what?.......ehhh?,ba zaki daina bani warning akan abinda yake halali na ba?,karki damu wannan karon nayi hankali nima,na sake girma.......you will enjoy it......babbabn ALBISHIR dinma tare zamuyi rainon cikin,tare kuma zamu shiga labour room din".

Rawa dukka jikinta ya dauka cikin matsanancin tashin hankali,bakinta ya kulle gam,sai kawai ta sakar masa muka sanda taji d'as! Ya balle bra din. Jikinta ta cukuikuye waje guda tana girgiza masa kai sanda taji yana qoqarin zare rigar da bra din duka daga jikinta,yana nufin ya ganta a tsurarta kenan?,abinda bata taba yi ba gaban wani d'a namiji

"Please......don Allah,i beg you.....kayi haquri" ta jefa masa roqon ba tare data shiryawa hakan ba tana girgiza kai kaman ba gobe.

Cak ya dakata daga abinda yake shirin yi,yayi komai ne akan plan da son cimma wani abu na sanyata ta sakeyin laushi,amma kuma sai abun ke neman zame masa na gaske,don ba wata kafa a jikinsa da bata mutu ba,gaurayuwar jikinsu waje daya da kuma yadda fatarta keda tsananin taushi sulbi da wani irin qamshi na musamman sun masa wata irin mummunar illar da basuyi masa a baya ba cikin qasa da minti daya.

Sake mata komai yayi sannan ya juya a nutse abinsa yana wucewa toilet. Da gudu gudu sauri sauri ta dinga maida komai muhallinsa,ta mayar din amma kuma komai a hargitse ta maidashi,ta lullube jikinta da mayafinta,saita sulale a wajen tana sakin qaqqarfan kukan da take ta riqewa.

Ya jima sosai a bandakin sannan ya fito,sanye da gajeran wando zalla abinda ya sanyata sake cusa kanta tsakanin cinyoyinta tana jin wani bacin rai da weakness suna ratsata. Baice da ita komai ba ya isa ga windows din dakin dukka ya sauke labulayen,abinda ya qarawa dakin duhu kenan,ya isa ga makashin qwayaye dukka ya kashesu,sannan ya qarasa saman gadon a matuqar kasalance yabi lafiyarsa yana cewa

"Zan huta na wasu mintuna daga bisani na kaiki.....ki kwanta ki huta kema" ya furta yana tattare pillows din saman gadon ya matsesu gam a jikinsa yana sauke numfashi a wahale.

Bata amsa masa ba,hakanan bata motsa ba,taci gaba da rera kukan bacin rai a hankali. A qalla mintuna ashirin da daukan shirun da dakin yayi,wayarta data watse a gefe ta soma haske. Kaman ba zata daga ba sai kuma ta miqa hannu ta janyota

"Ama ta" shine sunan dake yawo saman screen din. Riqe kukanta tayi da kyau tama share hawayenta da bayan hannunta sannan ta daga kiran

"Karki jima sultana sosai,ki dawo da wuri ki fara hada kayanku,kwana biyu kawai ya rage mana zamu koma" kamar bushara haka taji maganar ama,ta bude idanunta da suka jiqe da hawaye tana hangensa daga inda take a zaune,wani irin farinciki ya soma mamaye damuwarta,lokaci yayi da zata sake masa nisa,nisan da idan tayishi ba zata sake bashi daman zuwa kusa da kta ba bare ya dinga walagigi da rayuwarta yana mata Iko yadda ranshi yakeso ba

"In sha Allah ama" har ama din ta buda baki zata tambayeta inda ta tsaya don yasmine tace bata qarasa ba sai kuma ta fasa ta yanke kiran. Wata wawiyar ajiyar zuciya ta saki fuskarta na kallon sama

"Alhamdulillah" ta samu kanta da furtawa,tana ji a nan kusa zata yakiceshi ta huta. Bashi da communication me kyau da ama bare aba ballantana ya isketa a inda take din. Sai ta miqe a hankali ta taka zuwa qofar toilet din tana ji har jikinta da zuciyarta ta samu qwarin gwiwa.

_ba'a nan naso tsaiwa ba,amma yanayin yazo a haka,in sha Allah idan na samu yadda nakeso hutun zai kasance asabar da lahadi ne zuwa litinin kawai,daga nan zamu dora_


_da alama qullalliya sultana ke shirin qullawa maina ta hanyar amfani da ama ba tare da ama din tasan da haka ba,shin ya zata kasance?_

_ayi sallah lafiya cikin aminci,ubangiji ya maimaita mana ya karbi ibadunmu ameen ya hayyu ya qayyumu_*_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE page 72


Alwala ta daura ta goge fuskarta da kyau cikin toilet din,ta fidda powder da bata rabo da ita ta shafa,ta kuma gyara lips dinta. Har cikin zuciyarta tana jin sanyi,bacin ranshi kuma ya ragu sosai,tunda tasan kwanaki biyu rak suka rage mata tayi adabo dashi.

Tayi zaton data fito zata sameshi a shirye ko yana ma shirin su tafi din,maimakon haka samunsa tayi a kwance lakadan abinsa,kamar ma wanda ke bacci. Ta saci kallonsa sai tayi hanzarin kauda kai,saboda ta tunashi da shegen saurin karantar mutum. Taci alwashin ba zata ce dashi komai ba,don haka ta koma saman kujera ta zauna,ta fidda wayarta daidai sanda take ringing kira ya shigo.

Ko data duba sai taga kiran yasmine ne still

"Ya salam" ta furta cikin damuwa,don batasan amsar da zata bata ba

"Oya..... bani wayar nan" muryarsa can qasa kaman wanda yasha wani abu ya ratsa kunnenta. Tadan tsorata don ta tsammaci bacci yakeyi,amma sai ta tada kai tana dubansa. Bai ko kalli wajen ba,amma hannunsa suna saitinta yana jira ta kawo din.

Har tsakiyar zuciyarta taji zallar raini kawai yayi mata,banda haka meye hadinsa da wayarta dama ita kanta da zai dinga qoqarin control dinta da komai nata

"Kada na maimaita fa?" Ya furta har yanzun muryarsa da wani mugun laushi. Bacin rai ya kawo mata iya wuya,ta motsa qaramin bakinta da niyyar masa tsiwa kuma saita maida dukka maganganunta ta hadiye,don tasan furtasu bazai haifar mata da d'a me ido ba,kuma a wannan wajen da suke komai ma zai iyayi mata babu me ganin laifinsa. Wannam tunanin ya sanya ta tattara duk wata tsiwa tata da bacin ranta ta hadiye,ta kuma yunqura a nutse tana isa inda yake din.

Wayar ta miqa kamar yadda ya miqa hannunsa ba tare da tace masa komai ba,tana kuma qudurcewa a ranta ba zata ce masa ta iso ba,duk sanda ya juyo ya ganta.

Hannunta da aka cafka ya sanya zaren tunaninta katsewa,kafin ta sake tuna komai ya jawota zuwa saman gadon ita da wayar gaba daya.

Birkitota yayi sosai yana zare wayar a hannunta ya danna switch ya kasheta,idanunsa a lullumshe muryarsa na dauke da wani irin lallausan amo yana cewa

"Ba zuwa nayi kawai na kashe kudin daki kina niamy ina marad'i ba.....dole ki tayani hutawa,bacci nakeji sosai.......baccin da kikayi shekara da shekaru bakya barina inyisa cikin nutsuwa.......duk sanda na jefar da kaina na kwanta to tabbas sai wannan muryar taki me cike da tsiwa ta biyoni har cikin mafarkina tana sake jaddadamin abinda ta gayamin a baya......zaimin fyade.....Allah ya isa ban yafe ba...... it's so annoyed" ya qarashe fadi da salon muryartata sannan ya cusata tsakiyar qirjinsa a tausashe yana maida hannuwansa ya lullubeta da kyau.

Wani irin abune taji ya mamayi dukka ilahirin jikinta wanda ya haifar mata da tsatstsafowar gumi ta kowacce kafa ta jikinta

"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" ta furta jikinta yana rawa,wani irin tashin hankali yana rufto mata

"Shshshsh!" Ya fadi da qaqqarfan sauti yana dora yatsansa saman lips dinta,wanda a sannan fuskokinsu sunyi matuqar kusaci da juna. Ji tayi kaman zata shide sanda ya busa.mata iskar bakinsa a fuskarta,iskar dake dauke da qamshin mint na mouthwash ne kona meye bata sani ba.

Dukka qarfinta ta tattaro ta turashi baya,sai ya ware lion eyes dinsa yana kallonta

"Ehnnm......bance miki fyade zan miki ba dama?,yanzun wa zaki kira cikin wadanda ke tare miki?,uhmmm?" Ya sauke maganar yana duban tsakiyar idanunta dake kawo gudunmawar hawaye. Labbanta rawa suke tanason fidda maganar dake zuciyarta tare da qoqarin qwatar kanta,sai kawai ya saki siririn murmushi ya maida kansa ya kwanta bayan ya tabbatar ya zagayeta da hannayensa. Ya barta taci gaba da yunqurin qwatar kanta,bai hanata ba bata fasa ba har sai da dukka qarfinta ya qare,yayi amfani da wannan damar ya jata jikinsa sosai,sai ta fashe da kuka ganin babu sauran wata dama data rage mata kenan,bata da sauran zabi sai hada numfashi dashi,ba wata mafita ko garkuwa saita hada gangar jiki dashi,abinda bata sake mafarkin faruwarsa ba,abunda take gani bazai taba hadata dashi ba har qarshen numfashinta. Wanne irin tsaurin ido gareshi haka.,wanne irin taurin kai da kafiya ce dashi da har ya ya iya zare duk wani tanadi data yiwa haduwarta dashi?,ya yake neman rusa komai ya kuma ci galaba a kanta?. Abune da ba zata taba bari ya faru ba yayi iya yinsa na yau ne kadai,saidai duk yadda yakai ga qwarewarsa wajen yaudara bai isa yakai inda yake hari ba.

_nikam nace mmmm🤐

Tun tana lissafa minti biyu biya har goma sai gashi ta tafi lissafin awa daya,sannu a hankali awar tana shudewa tana zarcewa awa ta biyu. Idanunta fes tana zagaye da cikin dakin tana muma biye da fitar numfashinsa da kuma bugun zuciyarsa. Ko yaya ta motsa da zummar zare kanta sai taji ya sake maqaleta da kyau,murya can qasa kuma ya furta

"No" har abun ya fara bata tsoro,a qa'ida ya kamata idan baccinsa yayi nisa dukkan gabbansa su saki ta yadda zata iya zare kanta,amma nasa qawa zucin bai bar hakan ya faru ba.

Tayi kuka tayi kuka har dantsensa daya dora kanta akai ya jiqe,idanunta dukka suka tasa saboda tsabar bacin ran da takeji cikin ranta,ga wayarta daya kama ya kashe mata,tsoronta daya kada hankalinsu ya tashi da neman inda take tunda dai ita bataje gidansu aminata din ba,sannan kuma bata koma gida ba.

Dai dai sanda muhtarin sallar la'asar ya shiga ya motsa. A hankali ya bude zagayyayun idanunsa da duka qara girma suka. Dan kada kadan ya zubesu akan fuskarta. Kamar an qara mata qarfi saboda yadda zuciyarta ta motsa da rainin hankalinsa,shi ashe ma baccinsa yakeyi da gaske?. Sanda yake qoqarin tashi saita rigashi tashin,tana tunanin shammatarsa ne batasan miqewa shima zaiyi ba. Tsam ta miqe tana gyara dankwalinta da mayafinta,sai ya miqe a nutse ya zauna ya zuba mata idanunsa. Can qasan ransa dariya ce sosai take kamashi,yasan ya gama da ita,wannan din wani assignment ne ya bawa zuciyarta da gangar jikinta,ya basu wani aiki ya kuma ajjiye musu wani yanayi da zaiyita kai kawo cikin kwanyarta koda batason hakan.

Abu na biyu yadda taketa wani gyara jikinta tana gyara yafen mayafinta tamkar wadda taga wani muharraminta. Taurin kanta da yadda har yanzu take masa kallon ba mijinta ba yana burgeshi,don yana hango ranar da zai sanyata ta qaryata hakan da kanta,ba da bakinta ba,zata qaryata ne tun daga qasan zuciyarta har ya bayyana a dukka ayyukanta.

Kau da kansa yayi kaman baiga abinda takeyi ba ya miqe a nutsensa ya wuce toilet yana boye dariyarsa,ya azawa fuskarsa wata muguwar daurawa da cin mur.

Har ya fito ya maida rigarsa ya dauki key zai fita tana zaune,sai da taga da gasken yayi hanyar fita sannan tayi hanzarin miqewa

"Ina zaka tafi ka barni?" Tayi masa tambayar wadda a zahiri murya da fuskarta dukka sun juye sun koma kalar shagwaba,irin tsohuwar shagwabar nan tata da take tatawa sanda take ganiyarta,yayin da can qasan zuciyarta kuma ba shagwabar bace. Wata tsana da haushinsa ke yunqurin hallaka zuciyarta. Muryartata saita kashe masa jiki gaba daya,ya daki handle din ya tsaya sosai yana kallonta,kaman zaiyi magana sai wani abu ya fado a ransa,sai yasa hannu yaja qofar ya rufe yayi gaba. Duk taku daya kunnuwansa na cikin dakin yana wani murmushin mugunta,zayaso wannan LOKACIN ya qaraso,sanda zai dafa zuciyarta da gangar jikinta da soyayyarsa,yana tausaya mata,daga mata qafan da yakeyi a yanzun yana yinsa ne kawai saboda yanason ya fara sauke zafin kanta da kuma zafin fushin da zuciyarta ke ciki a kansa.



Please Login or Register in order to submit comment