Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

don bata sanya vest ba ganin rigar me kauri ce, underwear ne kawai a jikinta.

Da idanunta da suka qara laushi ya kalleta, muryarsa a dan sarqe yace

"No" yana girgiza mata kai,sai ya shammaceta ya zuge zip din gar zuwa gwiwarta.

Dukka numfashinsa yaso yayi qaura,farar bra din jikinta zuwa farin underwear dinta sun sauka sun xauna kuma dai dai saman farar lallausar fatarta da a kullum take cikin gyara da kulawa. Albarkatun qirjinta dukka suka tsone masa idanu,ya kasa janye dubansa daga kansu,cikin wani irin zafin nama ya jawota zuwa jikin nasa numfashinsa yana kai komo.

Kyakkyawar runguma yayi mata,ya miqa hannu yana ware band din kanta,hakan ya bawa sumar kanta damar bajewa saman kansu shi da ita gaba daya. Cusa kansa yayi tsakanin wuyanta,da muryar rada yace mata

"Karkiyimin gardama please,i want a peace please,am sleepy" daga haka bai barta ta qara sukuni ba ya dauketa cak ya nufi sofa da ita rigar da mayafin da takalminta dukka suka zame a wajen.

Sosai ya kwanta saman cinyarta hankalinsa kwance bayan ya cire suit din jikinsa sai fara qal din vest dake jikinsa dake fidda lallausan qamshi,gaba daya yayi mata kane kane saman cinya tamkar yaro yaso rigima saman cinyar mamansa.

Hankalinta gaba daya a rarrabe yake,yanzun idan akayi mata knocking fa?,wanne amsa zata basu?. Idan kuma tsautsayi yasa akayi tsammanin shurun da za'a ji bana lafiya bane akayi attempting shigowa fa?.

"Don Allah...... nan din fa ba gida bane wajen aiki ne"

"Ban gaya miki stay at home ba?,na baki izinin fitowa?......duk wanda ya miki knocking ki gaya masa kina tare da mijinki" yayi lafazin yana yin wani irin juyi,ya koma rub da ciki yana gyara kwanciyar kansa saman cinyarta tare da miqa hannunsa ya zagaye qugunta ta baya. Idanu ta sake fiddawa tana mamakin qarfin hali irin nasa,saidai kuma tana tsoron cewa wani abu,don gwara wanann punishment din nasa akan me gaba dayan. Bata gama wanann tunanin ba taji ya kamo hannunta ya dora tafin hannun nata saman tattausar sumarsa yana cewa

"Bacci......bacci nakeyi mummyn twins" ya qarashe fada yana lumshe idanunsa yana jin yayi comfortable yadda ya kamata.


_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400
BIYU_800
UKU_900
HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875
Musaa Abdullahi safiya
Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261


*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku kudin*

09033181070


*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂*_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 98


Yadda yayi ruf da ciki saman cinyarta ya sanya take iya jin bugun zuciyarsa sosai. Bugawa takeyi fiye da kima,sai hakan ya zama tamkar wani Aiken saqo ne zuwa ga gangar jikikta gaba daya.

Sannu a hankali taji bugun zuciyar tasa yana dai daita zuwa matakin da kowacce zuciya ke bugawa,a hankali taji numfashinsa yana fita a hankali,ya soma sauke numfashi da wani irin nutsuwa,saidai lokaci lokaci yana sauke ajiyar zuciya tamkar wanda yayi tsaren gudu,ga kuma qanqame qugunta da yayi sosai kamar zata bace masa.

Nauyi da nutsuwar daya qara yi saman cinyoyinta ya tabbatar mata bacci ya daukeshi,hannuwanta dake saman tattausar sumarsa ta kalla,ta kasa janyesu,sai kallon yatsunta da suka nutse cikin sumar tasa takeyi. A hankali ta soma motsa yatsun nata suna sake nutsewa cikin sumar tasa,wani irin taushi da santsi take dashi. Sannu sannu yadda hannunta ke shigewa cikin sumar sai ya tuna mata da wasu shekaru can baya da suka shude,lokacin da yake daukanta saman wuyansa,ta riqe gashinsa da kyau tana dariya,duk da tasan akwai zafi amma baya nuna mata hakan,lokacin da yake kwanciya saman pillow tayita jagwalgwalata da sunan kitso zatayi masa,wani lokaci ta hanashi bacci har sai ya tashi,wani lokaci kuma yayi baccin dole da bai shirya ba.

Wata ajiyar zuciya ce ta kufce mata,sai ta dauke hannuwan nata a hankali tana maida kanta saman makarin kujerar,duk jikinta ya mutu murus,babu wani sauran laka a jikinta itama,ya gama saukar mata da kasala me yawan gaske,gefe guda ga sammakon da tayi itama bayan kuma bata samu yin isashen bacci ba a daren jiya.

Idanunta a lumshe taji vibration na wayarsa dake ajjiye dab da cinyarta kusa da kanshi. Bude idanun nata tayi a nutse tana kallon wayar.......sunan laila ne ya fito radau saman wayar. Batasan me yasa ba sai taji an motsa zuciyarta,ta zubawa sunan ido yanata yawo saman wayar,tanason ta dauke kai da idanunta amma ta kasa,wai wacece wannan laila din?,tanason sanin wacece,haka kawai takeso ta sani din,tanason taji muryarta koma wacece ita.

Zuciyarta na gargadarta akan ta dauke kanta daga wayarsa amma ta kasa,haka ta miqa hannu ta dauki wayar daketa fidda qamshin tsumammen turarensa daya kama jikin komai da yake tu'ammali dashi. Tayi shipping ta daga kiran sannan ta sanya wayar a kunne, zuciyarta haka kurum na wani irin luguden duka

"Helloooo dear...... good morning,ina hanya in sha Allah,bazan wuce awa daya ko biyu ba zan iso paris......amma champs elysees din ko zaka sa azo a daukeni please ko ka qaraso da kanka?" Ta qarasa maganar a shagwabe da kuma karyar da murya da alama tanason karya taurin kansa ne

"Bacci yakeyi saman cinyata" ta samu kanta da fadi zuciyarta na mata zafi,ranta kuma yana raya mata abubuwa da dama. Dif laila tayi daga daya bangaren,dukka wutarta ta dauke daga bayyanar sautin muryar sultana dake bayyana zallar kamun kai da ajin dame muryar ta mallaka. Qarfin hali tayi ta tattara dukka dauriyarta gabanta yana faduwa tare da mamakin wacece wannan da zatace yaa haidar yana bacci saman cinyarta?,ba zata tana mummunan tunani a kansa ba,don ita kadai shaida ce akan tsarkin zuciyarsa,tsahon zamansu da shekarun da sukayi tare dashi ko kallon banza bai taba yi mata ba bare akai ga batun wani maganar banza

"Ke din wacece?" Laila ta jefawa sultana tambayar. Tambayar saita zowa sultana da salon rainin hankali,ita din zata kalla tace wacece?

"Idan ya tashi kina iya tambayarsa" ta amsa mata a taqaice,sannan ta saki siririn tsaki tana katse wayar?. Kasa aje wayar tayi ta dinga kallon number din,sai taji tana da sha'awar duba cikin wayar,to amma kuma ta riga ta shiga security wayan. To wacace wannan laila din?,zata iso paris nan da awa daya ko biyu?,it means kenan akwai wani boyayyar alaqa a tsakaninsu?,me zatazo tayi masa tana baligar mace yana baligin namiji tun daga wani waje?,a gidansa zai sauketa?. Tambayoyin dukka taji sun mata girma da yawa,ranta yana sake baci,ta motsa kadan tana leqa fuskarsa.

Fayau take dauke da wani irin kwantaccen kyau,komai na fuskarshi na aje cikin tsari da baiwar iya halitta ta ubangiji. Mix take gani na kamannin batoul da benazeer saman fuskarsa,abinda duk tsahon shekarun bata taba gani ba sai yanzun. Kamar jira suke ya dawo rayuwansu dama,suna ta juyewa zuwa kamanninsa.

"Ki rage fada please" taji ya fada qasa qasa kaman me mayen bacci

"Ki maida wayan silent,ki kuma daina picking mini call" ya sake fada yana gyara kwanciyarsa sosai hankali kwance.

Mamaki yadan kamata,kada dai ace yana sauraren abinda duk take fadi?,bai bata dama ta biyu ba ya saka hannu ya jawo hannunta sai gata gaba daya ta kifo saman kansa tayi masa rumfa

"Sleep please......na sani kema baki samu cikakken bacci ba" ya hanata motsawa ya hanata sakat,haka taci gaba da yi masa rumfar,tun tana qananun tunanuka har idanunta suka soma mata nauyi,sannu a hankali bacci yayi awan gaba da ita.

A haka suka shafe awa guda da rabi,gaba dayansu jikkunansu da numfashinsu sun gama gauraya da juna. Shine ya fara farkawa,ya bude idanunsa a hankali yana dubanta. Kyakkyawar fuskar rigimammiyar qanwarsan nan baby sultana,yau din ta zama madam sultana,duk wani sirrin kyau nata ya bayyana,irin kyawun da bai taba gani ba tsahon zamansa da ita. Hannu ya miqa saman lips dinta,yana da muradin taba bakin tsiwa.

Cikin jikinta taji yanayin da take ciki ya sauya sosai,ta bude idanunta a hankali,sai kuma ta qarasa budesu da sauri,a lokaci guda kuma tayi wani irin hantsilawa a tsorace sai gata ta zauna sosai sama sofa din. Idanu take bubbudewa cike da mamaki,ita dake a zaune kanshi a saman cinyarta ya akayi ta koma a kwance,ta matse sosai cikin jikinsa saman doguwar sofa guda daya,wanda koda da yaro ka kwanta sai jikkunanku sun matsi na juna?.

Yadda ya zauna calmly yana qarewa santala santalan hannayenta da dogon wuyanta kallo,yadda baqar sumarta me tsaho da santsi ta baje a sassan jikinta ta sake zama ado a tattare da ita ya tuna mata jikinta ba kaya,ba komai sai bra da underwear.

Da azama ta cure waje daya tana kifa kanta saman cinyarta,itakam wannan wanne irin abun zub da mutunci yake jawo mata?. Siririn murmushi ya saki yana kada kai,duk da bai gaji da kallonta ba bazai kuma gaji din ba,amma dazun kafin ta farka daga bacci ya morewa idanunsa kallonta yadda ya kamata,ta kuma tayar masa da feelings dinsa qwarai,to amma bayason ya cika zaqe mata ko matsarta da yawa dashen da yake da niyyar yi cikin zuciyarta ya rasa kyakkyawan gurbi da muhallin da yake fata.

Tsam ya miqe yana fadin

"Tashi ki bani abinci......am starving" yayi maganar yana dosar toilet dinta. Ta tsakanin gashin kanta da ya lullubeta take satar kallonsa har ya shige toilet din,ta miqe da mugun hanzarin ta doshi bakin qofa ta rarumi abayanta ta maida,saita soma laluben key din office din bayan ta dauki handbag dinta.

Sama da qasa ta rasa maqullin,sai a sannan zuciyarta ta soma raya mata ya boye ne,cak ta tsaya,tabbas xai aikata,tunda har yana iya gane komai saman fuskarta data shirya,kaman yadda yasan tsaf meye zata aikata da wanda ba zata iya yi ba.

Dole ta koma saman kujerar ta zauna tana furzar da iska,saita daga kanta a nutse tana duban agogo

_nan da awa daya ko biyu zan iso paris.....ko zaka qaraso da kanka ka daukeni please_ muryar laila ta fado mata a rai. Agogon ta jefawa harara ta janye idanunta tana jan tsaki.

"Rashin kamun kan yayi yawa" ta fadi qasan ranta tana kuma jan qwafa,ta maida dubanta ga wayarsa kamar me jiran shigowar wani kiran. Can qasan zuciyarta kuma sai takejin babu me laifi sai shi,don meye?,don meye ya fito daga family na mutunci zai dinga jaye jaye?. Lumshe ido tayi abun yana tsaye mata a rai,yanason bata musu sunan family kenan?

"Sunan family ko sunan 'ya'yanku?" Ta jiyo sautin tambayar data sanyata bude idanunta gaba daya tana neman amsarta.


Sosai ya hakimce mata saman sofa din,ta dinga zirga zirgan debo abincin dake shirye cikin tray wanda batasan ma ya akayi ya samu shigowa office din ba,harda kuma wai abincin da ta tabbatar daga kitchen na station dinnasu aka kawo mishi. Ta qasan idanu yake qare mata kallo,bata da abun cewa sam bakinta ya kullu,to meye ma zata ce masa?,ya riga ya gama kulle mata baki,itakam zuwa yanzun ma tsoro yake bata,ta yadda duk yadda tayi qoqarin kaucema qaddarar haduwa dashi hakan bashi samuwa. Lallabawa takeyi ya fice gurin lafiya lau ba tare daya daura mata jinyar ciwon jiki ba(nace gulmammiya,anaso ana kaiwa kasuwa).

"Koma ki zauna" ya fadi sanda ta ajjiye abincin a gabansa,yana zaune sosai saman dan center carpet dan madaidaici da aka qawata office din dashi. Dubansa tayi kaman zata saki kuka,to amma yadda yake dubanta ya sanyata zamewa ta zauna sosai a a gabansa.

"Oya.....saka hannunki....", Ya bata umarni yana tattare dogon hannun shirt din suit dinsa,ya sanya nasa hannun cikin abincin ya fara kaiwa baki a nutse. Kasa motsawa tayi,cin abinci tare dashi cikin kwano daya wani tsohon al'ada ne data manta rabonta dashi,batajin zata iya sam,don haka taci gaba da duban kwanon sanda yake kai abincin cikinsa hankali kwance. Wani mugun nishadi ne ma yake saukar masa,duk sanda zasu kasance qarqashin inuwa daya kaman hakan,yakanji kaman ya tsaida lokaci ya hanashi motsi,abinda ya kasa bawa kansa amsa har yanzu shine,wai dama can wannan matsanancin son yakewa sultana?,ko kuma bayan faruwar wancan abun a wancan lokacinne mahaukaciyar soyayyarta ke yagalgalashi?.


_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400
BIYU_800
UKU_900
HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875
Musaa Abdullahi safiya
Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261


*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku kudin*

09033181070


*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂*_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 99


"idan kika bari na rigaki gama cin abincin nan.......dura zanyi miki" ya fadi yana kada yatsansa dan manuni. Itakam a yanzun ko meye yace zaiyi zai aikata ta sani,don haka ta rufawa kanta asiri ta matso,ta sanya hannu ta dauki spoon. Hannunsa ya miqa ya karbe yana fadin

"Um um......yau da hannu zamuci,mu samu albarkaci junanmu" cikin ranta ta tabe baki

"Wanne albarka mutumin da yake da side chics dinsa?" Ta fadi qasan ranta

"Me kika ce?" Ya jefa mata tambayar yana tsareta da idanu

"Ba komai" ta fadi qasa qasa tana tura baki gaba. Murmushi ya saki,lallai da gasken tsoro ya sanya ta fara gyara wasu abubuwan,ya sani akwai abinda tace,amma shakkar tasa ya saka ta kasa fadi masa a sarari,wanda inda ada ne ya tabbatar zata fadi mashi ne,ko meye zaiyi saidai yayi.

Koda ya gama sai ya koma da baya yayi relaxing yana kallon taunarta,idanunsa can qasa,ba zaka taba kawowa ita din yake kallo ba. Wayarsa ya jawo sanda ta fara ringing,ya saki murmushi ganin sunan goumar,yana dagawa muryar benazeer da batoul ne ya soma masa sallama.

A handsfree ya sanya wayar yana fitar da murmushi,muryarsu fes cike da doki da zumudin mahaifinsu. Hira suke masa sosai hayaniya hadi da shirmensu,ya sakankance sosai ya biye musu

"Daddy munyi missing naka,uncle goumar yace mu tambaya zai kawo mu office dinka?" Tsaiwa tayi da hadiyar lomar tana kallonsa qirjinta nadan bugawa,ko kusa ko alama batasan kowa yasan suna tare,kowa dinma irin goumar?,ta tabbatar daga ranar ta kade daga ita har ganyenta,kai wala'alla ma bakinsa bazaiyi shuru ba saiya gayawa ama, itakam ai da ta kade,da wanne ido zata kalleta?.

Shima din ita yake kalla,kuma salon kallon da yakeyi mata tamkar yana jefa mata tambayar na basu izinin zuwa?ne a fakaice.

Rau rau tayi da idanunta tana tsame hannunta daga abincin,sai ya zame idanunsa yana cewa

"No kuyi zamanku,nayi alqawari anjima kadan zamu kasance tare" ihun murna suka saki,yanata sakin lallausan murmushinnan nasa kafin daga bisani yace su bawa goumar wayar.

Magana sukayi kadan sannan ya kashe wayar,ya miqe ya nufi inda suit dinsa take ya saka,ya maida takalminsa,yana daura agogonsa ya dubeta

"Zaki wuce gida yanzun......daga yau kuma duk sanda kika sake fita bada izinina ba......" Sai bai qarasa ba ya maida kansa ga daura agogonsa.

Afakaice ta harareshi,kaman yaji hakan cikin jikinsa sai ya waiwayo,saura kadan su hada idanu tayi hanzari dauke kanta ta maida ga agogon bangon office din nata.

Lokacin yayi daidai da sanda yarinyar tace zata iso paris,hakanan taji wani abu ya tsaye mata a wuya.....lokacin tashinsu daga aiki da saura,don meye don zaije ya dauko wata can daban zai matsa mata tabar office yanzu?, bayan ya hana mata yin duk wani aiki,har yanzu program din da zata next week bata shirya komai game dashi ba,saboda ya hana mata sakat,ya hanata motsi,ya kuma hanata nutsuwar da zatayi aikinta.

"Are you with me?" Ya tambayeta yana qoqarin daukan wayarsa. Wani tunani da yazo mata ya sanyata miqewa ba tare data kalleshi ba

"Zanje na danyi submitting wani abu,bazan wuce minti biyu ba" ta fadi tana jin dacin yadda wai saita nema excuse a gurinsa kafin tama fita

"Hope ba wajen namiji bane?" Tambayar ta quleta,sai taji kaman kada ta amsa masa,amma tana tsoron hukunci,don haka ta gyada masa kai kawai.

Sai data tsaya tsaf ta maida komai nata inda yake sannan ya barta ta fita din. Qwafa taja bayan ta fita tana cewa

"Ai idan kasan wata bakasan wata ba" office na qarshe a lobby din ta shiga,tasamu baturiyar matar cikin aiki kace kace,amma kasancewar suna girmamata saita tsaida komai ta saurareta.

Dan qaramin hutu ta buqata a kwanakin,ta basu uzurin tanason ta shiryama next program sosai a gida,don mamanta ita zata taimaka mata da wasu research akan culture din da zasuyi magana akai. Ba wani damuwa ta tura request akan buqatarta,ta kuma bata dama a take ta rubuta letter ta tura,sukayi sallama ta fita a office din.

Fes takejin ranta sanda ta baro office din,kome zaiyi daga nan zuwa gida ba zataji haushinsa ba,don tasan abinda ta shirya din shi daya zai mata maganinsa.

Ko a cikin motar yaga ta saki fuskanta sosai,bata damu kaman yadda take damuwa wancan lokacin ba idan ya yanke zasu wuce gida tare a motarsa.

Duk da hankalinta ya dauke daga kanshi,amma lokaci lokaci sai ta dinga duba agogon hannunta,abu daya ranta dai keci gaba da bata zayaje daukota,tanaso tayi tsaki amma tana gudun yinsa a sarari.

Kama ko yaushe ya tsaya daga farkon street din nasu ya bude ya fito ya zagayo inda take zaune yana miqa mata key din

"What do you want to me to do to you tonight?" Ya tambayeta yana dage masa girarsa guda daya hadi da kashe mata ido. Wani abu ya zubawa gangar jikinta,saboda tsananin kusancin dake tsakaninsu yayi yawa,abinda take gani kuma a idanunsa yana son shallake yadda ta daukeshi

"Ki gayyaceni mana yau dai daya da kanki please madam" ya sake fadi yana sassauta mata murya da salon dake narka zuciya.

Saura kadan ya dauke mata numfashi da wani irin tsananin kunya da kuma nauyi daya saukar mata. Ya fahimci ne taji,don haka ya miqe daga durquson da yayi ta jikin window din yana watsa hannayensa gami da dage girarsa sama

"I don't know what's wrong with me,am so addicted to you.....see you tonight" ya fadi da tataccen turancinsa tamkar baisan wani abu waishi yaren faransa ba. Takowanne bangare gwanine,Allah ya bashi baiwar harshe qwarai da kuma salon sarrafa kowanne harshe,idan France yakeyi zaka zaci shine kadai yaren da ya sani,hakanan idan ya juya English.

"Tonight?" Ta maimaita kalmar bayan ta soma gangara motar sosai cikin layinsu. Kai ta gyada murmushin mugunta yana qwace mata

"You will see tonight kuwa" ta sake fada qasa qasa.

Hannayensa ya saki yana juyawa zuwa inda matashin ya aje masa motarsa kamar kullum. Daidai nan wayarsa ta dauki flute ringing me sanyi. Ranshi yadan hade kadan,sai kuma ya daga kiran yana sanyawa a kunnensa.

"Almost over one hour ina jiranka yaa haidar.......bakasan na iso ba ko?"

"Me yasa kika taho laila?,aunty din tana Paris dinne?" Ya tambayeta don baiga ta inda zai bari tayi masa masauki cikin gida ba.

Ajiyar zuciya ta saki,har yanxu tana jin dacin maganar da matar data daga wayanshi dazu ta gaya mata,so amma yanzun ba muhallin da zata tambayeshi bane

"Tacemin yau suna hanya in sha Allah,so ko zakamin alfarmar zama cikin gidanka na wasu awanni kafin su iso?" A yadda sautin nata ya fito ya nuna kaman wani abu ya sosa zuciyarta. Sardauna da daddy sune mutanen daya tuna,ya kuma tuna halacci da gudunmawar da suka taka a rayuwarsa

"Ki tsaya a wajen,zanzo nayi picking naki"

"Alright, thank you" ta fadi. Ya sauke wayar tausayinta yana dan kamashi,shi da ita dukka yana tunanin jirgi daya ne yayi jigilarsu,son maso wani da hausawa ke kira da qoshin wahala,ya juya a nutse ya koma matar yana tayar da ita idanunsa kan hanyar da sultana ta wuce.

Daure da babban towel da kuma qarami ta fito daga toilet. Haka kawai tunda ta dawo gidan gaba daya hankalinta yana kansa,duk kuwa da cewa duka duka basu zarce awa biyu da rabuwa ba. Duk bayan wasu mintuna sai ta tuna da kiran LAILA. Sunan da ma yarinyar gaba daya sun tsaye mata a rai,tayi masifa tayi fada ita da zuciyarta dama ranta gaba daya kan shiga shirgin da bai shafeta ba amma abun yaqi barin zuciyarta.

Tanata ture tunanin tana shirya kanta cikin wani sassanqan material,so take tayi keeping kanta busy yau sosai,tanason ta zauna cikinsu ama da yaran ta basu lokacinta,daga magrib zuwa ishai kuma tana sanya ran ta qarar dashi wajen binciken al'adun qabila daya cikin tarin qabilun Nigeria wato qabilar KANURI.

Fes fuskarta ta fita ta tsakiyar turban cap data sanya fara qal,ta matsa jikin bed Side drawer dinta dake daura da window dinta,haka kawai sai taji sha'awar bude window din.

A nutse ta miqa hannunta ta yaye labulen,ta kuma sake zura hannunta ta janye glass din. Fes ta cikin window din take hangar gidan,gidan da take da tabbacin cikinsa yake rayuwa. Tana qoqarin sakin labulen motarsa ta tsaya qofar gidan,sai ta samu kanta da gaza sauke hannun nata, idanunta tamkar wadanda aka yiwa majanyi

Please Login or Register in order to submit comment