Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ta amsa mata da

"Alhamdulillah" tunda musulma ce,shuru nadan sakanni ya biyo baya tana qoqarin fidda takardar gwajin daga cikin takardunta data taho dasu.

"Ina tayaku murna madam......" Ta fadi da fara'a tana miqawa ama takardun. Daurewa kan ama yayi,amma sai tayi tunanin kamar bataji abinda ta fadi bane da kyau,ta miqa hannu tana karbar takardun sanda take sake cewa

"Dole tayi haquri da wasu canje canje da zata dinga ji,daga wadannan satittikan har zuwa sati sha biyu sha biyar har sati na ashirin ga wasu matan" idanu kawai ama ta zuba mata,mamakinta yana sake ninkuwa,ita sam bata fahimci inda zanca dr ya dosa ba,saboda bayanan dr kaman tana bayani ne ga mutumin dake kiwon kaji?.

"Kaman yaya dr?" Ama data kasa buda takardun ta tambayeta

"Votre fille est enceinte(yarku tana da juna biyu)" wani duka maganar tayi saman kunnuwan ama da wani dirar mikiya naban mamaki

"quoi ?(what?)" Bakinta yayi subutar fadi ba tare data shirya tambayar ba. Kai dr ke gyada mata har yanzu fuskarta da murmushi,don ta yarda da tarbiyyar mutanen dattako da nutsuwarsu harma da kamewar yarinyar,tayi imanin cikin da ta gani tattare da yarinyar zaiyi wahala ya biyo ta baragurbin hanya

"Eh madam". Tattaro dukka wani busashen yawu dake bakinta ama tayi,ta kuma aro murmushi ta jefi dr dashi

"Na gode sosai da wannan albishir dr"

"Ba komai.....sai a kula da ita da kyau,duk sanda akaji wani abu kuma da ba'a yarda dashi ba hanya a bude take kada ayi jinkiri a sanarmin koda bana gida"

"In sha Allah,na gode" ama ta sake jaddada godiyarta,tana bin dr kawai da kallo. Duk yadda taso yi mata tattaki koda zuwa bakin qofar falonne ta kasa,tana jin qafafunta sun mata nauyi da wani irin dan banzan mamaki mara adadi.

Saida dr ta fita sannan taji tana da muradin kiran sultana,amma sai taji kamar muryarta ba zata kai ba. Sai a yanzu ta samu kanta da wani matsanancin fargaba da wani mummunan tunani daya rikito mata

"Ciki?,na waye?, yarinyar data shekara shida rabonta da d'a namiji?, innalillahi wa inna ilaihi raji'un..... Sultana ba zata taba aikata alfasha ba,amma kuma cikin waye a jikinta?,shin akwai boyayyar alaqa tsakaninta da maina?" Dukka wadannan tunaninkan suka dinga bugun kan ama har ta rasa hanyar da zata kira sultana din ma

"Ya Allah.....Allah kasa boyayyar alaqar ce" ama ta samu kanta da furtawa a sarari bakinta yana rawa,tsoro da fargaba kamar zasu dulmiyar da ita a wajen.

Sai sannan idanunta ya fada kan tanja,ta tabbatar zaiyi wuya ta fahimci duk maganar da sukayi da dr tunda kaf da harshen faransanci ne,wanda nata harshen baiyi nunar da zata fahimci duka komai ba

"Tanja kiramin sultana" ta fada tana fasa kiran nata datayi niyya,wayarma saita sulale daga hannunta. Da dan mamaki saman fuskar tanja din ta miqe tana nufar dakin sultana.

Ta gama salla kenan da hijabinta a jiki tanja ta isar mata da saqon,gabanta ya sake faduwa kaman dazu,sai ta miqe kawai ba tare da tsaiko ba tabi bayan tanja.

Tunda ta sanya qafafunta ta fito daga dakin ama ta soma qureta da wani irin asababben kallo da bata taba ganin tana mata irinsa ba,abinda ya sake qara yawan faduwar gabanta,ya kuma saka dukka gwiwoyinta sanyi,a haka ta isa gaban ama,sai ta samu kanta da sulalewa ta zauna sosai a gabanta. Kasa cewa sultanar komai tayi saici gaba da kallonta da tayi,don ta rasa da wanne harshe ma zatayi tambayar,da hausa koda turancin ko kuma da faransanci ko da yarensu na abzinanci?.

"Sultana" ama ta kirata sosai

"N....na'am" ta amsa mata tana dan daburcewa,don sosai takejin shigar kallonta

"Cikin waye a jikinki?,kuma wata nawa?" Kamar da wadda ta yiwa magana da yarbanci haka taji,don kwata kwata sai taji sautin ama kamar me koyon magana a yau din. Gefe guda kuma kamar an sharara mata ruwan zafi haka taji,wannan ya sanya ta dago a firgice tanason tabbatarwa ita ama kewa wannan tambayar?, don tana jin kamar bata da alaqa da tambayar,meye hadinta juna biyu kuma?.

Idanun ne suka sauka kan takardar gwajin quru quru kafin takai ga kallon ama din,abinda yayi gaggawar fusgo tunaninta da hankalinta ya maido mata jikinta,maina ya fado mata a rai,dararensu dama sauran ranakunsu da BOYAYYAR ALAQARSU......

*_huguma ta gantale ko?,😂, afuwan,Allah kadai yasan nake squeezing nake muku rubutun nan,Allah ya saka muku da aljanna mutanen kirki da haqurinku gareni,in sha Allah muma mun kusa yin sauka,na gode_**_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 122


Kamar an kaba labbanta na sama da qasa an datse haka taji,gaba daya kowanne harafi da zatayi bayani dashi ji tayi yayi qaura daga bakinta. Wani mugun nauyin ama da bata taba jin makamancinsa ba ya saukar mata,taji koda wasa koda sau daya ba zata iya hada idanu da ama din ba,sai tayi qasa da qwayoyin idanunta da basa Gani da kyau saboda ruwan hawayen da ya cikasu.

Jinta takeyi tamkar ba zaune take cikin falon ba,kamar gangar jikinta ce kadai a zaune a wajen,amma ruhinta baya tare da gangar jiki nata gaba daya. Har yanzu idanun ama suna kan sultana,kaman yadda zuciyarta da qirjinta basu bar bugawa ba. Bata zargin sultana,amma kuma tana fatan taji wani abu daga bakin sultana da zai sake bata nutsuwar zuciya.

Jiki a sanyaye ama ta waiwaya bayanta jin takun mutum. Aba ne sanye da jallabiyya hannunsa dauke da key din motarsa,da alama yayi mantuwa ne a ciki zai fita ya dauko.

Yadda ama ta bishi da idanu haka shima ya bisu da kallo,fuskarsa na bayyanar da zallar mamaki a cikinta

"Ya dai?,me ya sameta hamdiyya?" Yayi tambayar yana duban fuskar ama da alamun tuhuma sosai a ciki. Kallon tuhumar da yake mata ya sanya ta kasa cewa komai,sai kawai ta zare takardun gwajin dake zube saman cinyarta ta miqa masa,ta hada hannayenta kawai ta rungume ba tare da tace komai ba.

Yana kaiwa qarshe ya zare glass din idanunsa,sannan kuma ya samu kujerar da tafi kusa dashi saboda wani iri da yaji jikinsa yayi masa. Sai daya zauna sosai sannan ya iya maida idanunsa akan fuskar sultanan

"Yi shuru,daina kuka hakanan......ki nutsu" muryar aba din sai ya zame mata kamar fami ga zuciyarta da kuma raunin dake ruhinta. Wai da gaske cikin ya maina ne a jikinta a karo na biyu?. Totally tayi disappointing dukkan wani qoqari na aba kenan?,da gaske ta bulawa aba qasa a idanu?,to wai da wanne bakin zatayi bayani?,da meye zata kare kanta?.

A qalla mintuna biyar aka sake sharewa cikin falon ba wanda ya iya cewa uffan,shidai aba ya bata space ne akan ta nutsu aji ta bakinta,gefe daya kuma zuciyarsa nata nanata masa sunan

"Maina ne....maina ne" to amma Ina maina din?,a ina ya ganta?,idan bai manta ba tun a Nigeria da suka rabu bai sake ganin alama ko samun information din yana qasar bama gaba daya bare ya sanya a ransa shine ya lallabo ya sake aikata wannan aika aikar a karo na biyu.

Ganin kamar ta daidaita kanta ya sanyashi gyara zamansa yana duban ama. Hada idanu sukayi,sai ama din tadan dauke kanta gefa,don tanajin kamar case din yana son ya fita daga hannunta,don gaba daya jikinta ya gama bata inda komai ya dosa,to amma kuma tanaso sultana tayi bayanin da dukansu zasu fita daga duhu,cikin saukar da murya da tausasa harshe ta sake maimaita

"Sultana.....ya akayi hakan ya faru?,juna biyun maina ne ko?" Ama ta bata tambayar me hade da amsa.

"Nawa ne ama......salamu alaikum warahmatullah" muryarsa ta bayyana tar a falon da bayyanannen amo daya wadaci dukkan falon.

Da aba da ama dukkansu suka waiwaya zuwa bakin qofar,yana shigowa ne riqe da hannun batoul da benazeer hagu da damansa,bayansa kuma goumar ne janye da luggage.

Sautinsa da amsarsa kusan lokaci guda suka daki zuciyarta dama kunnenta,ta daga jiqaqqun idanunta itama tayi duba zuwa qofar falon.

Aliyyu haidar MAYAK'I,jinin abzinawan nijer,mutumin da ta kwashe sati uku cif! Bata sakashi cikin qwayar idanunta ba,mutumin da duk yabi ya gallabi rayuwarta,yayi dashe a kowanne lungu da saqo na rayuwarta,ya maida kansa jinin dake gudana cikin jiki da jiyoyinta ta qarfi da yaji,ya dasa wani irin alaqa me matuqar qarfi tsakaninta dashi,irin alaqar da duk yadda taso ta kankareta kota gogeta HAR ABADA! Ba zata taba goguwa ba,ya maida dukkan rayuwarta tashi,fitar numfashinta da dukka motsinta.

Ama ce ta fara kauda kai tana jin kamar dariya ko murmushi zai kubce mata don nata mamakin gajere ne qwarai. Ita ta haifi abinta,tasan duk abinda zai aikata dama wanda bazai aikata ba,tayi shuru ne kawai ta sanyawa kowa idanu,amma jikinta ya jima yana bata,saidai kawai hausawa sunce dan yau ka haifeshi ne ba tare da ka haifi halinsa ba......sannan wayo da dabara ta yarda dukka ya nuna mata irin nasu na 'ya'yan zamani,amma ta jima tana suspecting haka,ta dade hasashenta yana bata,abubuwa da dama sun jima suna bata alamomi da sai yau haskensu ya fito tarwai.

Idanu aba ya bishi dashi kamar yaga wata sabuwar halitta,sai kuma ya janye kallon nasa daga kan maina din yana dawo dashi cikin falon kan sultana,ya zuba mata idanu kawai kamar me tunanin abinda zai gaya mata.

Tana jin idanun aba ainun a kanta,duk wata kunyar duniya da nauyi sun tarar mata. Tana tsammanin idan yazo zata samu sassauci da rangwamen kunyar data yi mata rubdugu,amma shigowar nasa bai rage mata komai ba saima nauyin daya qara mata da irin amsar da ya basu ta hanyar kai tsaye babu kwaskwarima.

Kwata kwata aba ya rasa me zaice?,ya rasa me zaya fada?,gaba daya kalmomin bakinsa sun dauke tsaf,ya rasa hukunci zaiyi ko meye?,idan hukunci yace zaiyi akan waye zaiyi?,kuma akan wanne dalili?,wanne kuma laifi aka aikata da za'a yi hukunci a kansa?.

Abu daya da yazo masa a rai shine,babu uwa kamar bibi,me hangen abinda zai wakana shekaru goma ma gaba.

Tun daga bakin qofa ya tsugunna yana zare takalman qafarsa,sai yara suka duqa suna tayashi cire guda dayan,ya daga kai ya kallesu ya sakar musu murmushi,kowacce ta dauki guda daya suka soma takawa zuwa gaban aba.

Zubewa yayi a gaban aba din saman dukka gwiwoyinsa,ya zube kansa a qasa ya kuma hade hannayensa waje daya

"Indai faruwar hakan laifi ne aba.....gani a gabanka ka yanke dukka hukuncin daya dace dani......saidai don Allah ina roqonka,kowanne irin hukunci ne ya zama taqaitacce aba.....kada yayi yawan da zai sake ruguza kowanne irin gini da nake yunqurin ganin na aza..." Qafarsa yadan janye,gaba daya kunya ta masa wani irin dabaibayi,ya sake dan ja baya kadan sannan ya miqe yana dubansu benazeer

"Muje ciki ku tayani hira,tun dazu nake dakon dawowarku,na ajjiye muku abun dadi" Da murnarsu suka ajjiye takalmin suna bin bayansa,sai daya sanya yaran gaba suka wuce sannan aba din ya tsaya,ba tare da ya waiwayo ba ya furta cikin muryar bada umarni

"Ka dauki matarka ku tafi duk inda zakuje mara kunyar banza" daga haka ya taka zuwa gaba yana bin bayan yaran.

Dauke idanunta ama tayi daga kan aba din tana sake danne dariyar da a yanzun ta tabbatar idan batayi da gaske ba saita kufce mata. Sai kuma idanunta ya fada kan maina dake duqe a inda aba ya barshi.

Kunya ce ta kamata itama da nauyi,ga idanunshin nan daya tsareta dasu,saita sake tsuke fuska da kyau itama

"Meye kake kallona?,bakaji abinda yace dakai ba?"

"Naji ama" ya fada a mugun marairaice kamar marayan daya rasa danginsa gaba daya. Saidai kuma can qasan zuciyarsa wani irin mahaukacin farinciki ke ratsashi

"D great victory ✌️! Da sauri haka?,wannan d'a ko 'ya tabbas ba qaramin qaunarsa suke ba......yana da hope na samun cikin,amma kuma babu tabbaci sam sam sai addu'a". Kasa ce masa komai tayi sai kawai ta kwashe wayarta tabi bayan mijinta.


*_Allah sarki sultanarmu ta mutunci_*🥹😥😥*_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 123


Tuni tanja tabar falon tun shigowar aba,don ita wannan gwaji ya biyata,ya kuma gama yi mata komai. Don haka a yanzu sai falon ya zamana ba kowa,daga shi sai ita,sai kuma ayana dake maqale bayan labulen dakin. Tun fara drama din ta farka daga baccin data kwanta tayi bayan ta dawo daga makaranta. Idanunta tamkar su fado haka takeji,kaman yadda zuciyarta ke wani irin bugu cike da mahaukacin kishi,kebewarsun yanzun ya sanyata sake lafewa da kyau tanason kunnuwanta su ida jin abinda zai sake gudana tsakaninsu.

Tsaye kawai tayi yana nade hannayensa a qirji yana qare mata kallo da zagayayyun lion eyes dinshi da a yau suke lumshewa da kansu suna budewa sau babu adadi,ya zuba mata dukka idanuwan yana kallonta,wani irin narkakken kallo dake cike da shauqin soyayya da tsumammiyar qauna irin wadda ta jima da narka zuciya gami da yi mata illa.

Yanajin sautin kukanta har cikin zuciyarsa da ruhinsa,saidai kuma bayason abinda zai katse kallonta da yakeyi. Yayi kewarta......yayi kewarta kamar hauka........yayi mutuwar kewarta har baisan iya adadi ba......yayi kewarta kamar ya karya tsari da lokutan daya diba kafin ta sake ganinsa,shi da ita baisan waye yafi wani gasuwa ba.

Kunnuwansa ke sake dawo masa da furucin aba

"Ka dauki matarka ku tafi duk inda zakuje....." Sai wani tattausan murmushi ya kubuce ma kumatunsa. Zai iya cewa kawo zuwansa duniya zuwa yau bai taba jin wani umarni me gardin wannan ba.......qwaqwalwarsa ta lula wani irin tunani me zurfi,yana laluben wai a duniya a wanne shiyya zai ajjiyeta?,a wanne muhallin ne zaciyoyinsu zasu samu dukkan hutu da salama?,a wanne tsibiri tudu ko tsauni ne zaiyi shimfidar rayuwarsa da sultanarsa?, diyarshi?,rainonshi......matarshi?,uwar 'ya'yanshi?. Dukka wadannan tunanikan yana daga tsaye yake tsarasu cikin qwaqwalwarsa,kafin ya sauke hannuwan nasa yana takawa zuwa gareta. Yanaso ya dakatar da wannan kukan,sai ya dinga ji kaman abinda ke kwance qasan mararta ma tayata kukan yakeyi,ya gaji.......yanason tsaida wannan hawayen da sukayi shekara da shekaru suna zuba,ya kamata su tsaya hakanan.

Gabanta ya qarasa cikin nutsatstsen takunsa dinnan, baiyi qasa a gwiwa ba ya zauna sosai sannan ya tanqwashe qafarsa yana fuskantar ta har gwiwarsa tana taba tashi.

Taji isowarsa,ta kuma ji hucin dumin jikinsa,sai lallausan qamshin nan nasa da a yau takejin ya zama sabo cikin hancinta,har sai da qamshin ya tilasta mata fidda BOYAYYAR ajiyar zuciya,tana jin kaman ta shaqi wani abu me sanyi da ya dinga sauka har saman zuciyarta yana wanke mata zaciyarta.

"Sulthana" ya kirayeta a tausashe yana qoqarin leqa fuskarta ta qasan hijabinta.

Ta fahimci me yakeso,fuskarta yakeson gani,sai ta cusa kanta tsakanin cinyoyinta da kyau saboda ta hanashi wannan damar. Wani qaramin murmushi ne ya subuce masa daga siraran labbansa,hakan da tayi sai ya tuna masa da little sultanarshi ta shekarun baya,ya sanya tafukan hannunsa cikin na juna yana mutstsukawa a hankali cikin wani salon nishadi,idanunshi kuma a kanta

"Am so sorry......ya maina bai kyauta ba.....don me zaiyita zura qwallo a raga ba tare da permission din goal ba?" Hakan da ya fada sai ya zama kamar tiri a gareta,ta kuwa sake sakin kuka mai qarfi tana jin takaicin sa. Ya sanyata abun kunya,irin abun kunyar da bazata taba mantawa dashi ba,ya goga mata kashin kaji,shi kuma nan ba ruwanshi gashi nan,da wanne baki zata kare kanta ne wai?,mutanen da suketa fadi tashi a kanta suke qoqarin ganin sun qwato mata 'yancinta?.

"Ki daina kuka please baby sultana(ya kirata da tsohon sunan da yake kiranta tun lokacin da batafi girmansu benazeer ba

".....nima duk kunya ta kamani,ashe ina tsallakesu ina tafiya dakin 'yarsu ina turmusheta" ya qarasa fadi yana kashe ido daya dariya nason taso masa.

Kalmarshi ta qarshe ta mata girma ta kuma sake tunzurata,ta rasa ma meye zatayi masa ta huce,saita fara shureshi da qafa. Kamo qafafun nata yayi ya aza saman cinyarsa yana cewa

"Indai wannan zai sanyaki ki huce sultana yita shureni har sai zuciyarki tayi sanyi......kiyi iya son ranki......eheenn" ya fadi yana sakin jikinsa da kyau. Ba haka takeso ba,tanason masa abinda zaiji zafi ne,amma it seems ma bai damu ba ko kadan?,muddin taci gaba da zama a wajen haukatata zaiyi,don haka ta miqe tsam taba kubce masa tayi hanyar daki.

"Ina zaki?,bayan aba ya bani damar tafiya da matata?" Ya jefa mata tambayar. Ji tayi ba zata iya jurewa ba wanann karon don haka ta waiwayo tana kallonshi da fararen idanun da suka jiqe sharkaf da hawaye

"Ba inda zan bika,ni ba mara kunya bane" yadda tayi maganar da zallar quruciya dukka da yarinta a mode dinta yaso bashi dariya,amma a yanzun yana jin ba lokacin dariya ko wasa bane,lokaci ne da zai nuna mata qarfin qwanjinsa,ya kuma murda tashi mazantakar,aba da ama sune rauninsa,idanunsu ke masa gate suke kuma kawo masa tsaiko wajen maidata qarqashin umarni mulki da kuma ginin gidansa,a yanzun kuma ya samu cikakken izini koda da gatse aba ya fada,koda ba da son ranshi ba.

"Ni kuma ba kunya gareni ba......don aba kanshi yasan haka,yasan waye haidar......muddin yaci gaba da riqe masa mata yanzun ba juna biyu kika samu ba?,to idan ana daukan ciki kafin a haife wani zakiyita daukan ciki a gabansu........bana iya barin abinda nakeso.......zuciyata bata iya son abu da wasa ba kota fara so tayi sassauci a ciki......saboda idan ta fara son tana yin wannan soyayyar ne da gaske......batasan wasa ko ha'inci ba" ya gama kashe mata duk wani qwarin gwiwa da kafiya da takeji tana dashi,saqon kuma da idanunsa ke isar mata yafi wanda yake furta mata da bakinsa tsanani da kuma tarin kaifi,don haka ta juya da nufin ta isa dakinta ta kulle kanta da kanta,don duk tsanani ba zata iya binsa haka siddan don aba ya fadi wannan maganar ba,wala'alla ma yayi ne don ya gwadata,daga ya fadi magana sau daya sai ta tattara ta bishi kaman dama tana jira?.

Abinda ta manta shine maina din tamkar uba yake a wajenta?,haifanta ne kadai baiyi ba,amma dukka halayenta ya gama da saninsu daya bayan daya,don haka ya kausasa murya yana bata umarni nakai tsaye wanda ba wasa ko sassauci a cikinsa

"Kikayi kuskuren kulle qofa bayan kin shiga zaki gane baki da wayau kwata kwata......zaki fahimci kuma maina aliyyu ne,bashi da sassauci......ina fatan baki manta yadda ya dinga iskeki duk dare ba koda bayan kin rufe qofa ne....." Ya isar mata da saqon da ya sanya ta kasa maida qofar ta kulle kaman yadda ta niyyata,sai kawai ta buge da wucewa dakin da gudu gudu,ta kuma fada saman gado tana fashewa da kuka. Gaba daya ya sanyata a tsaka me wuya,jin laifi takeyi a kowanne sashe na jikinta,tasan koda zata hadiyi qur'ani ama da aba ba zasu taba gasgatata cewa ba ita ke kawo aliyyu ko kuma ita ta bashi fuska ba. Abun kamar almara?,wai ciki a jikinta?,cikin maina again?,bayan duk wahala da fadi tashin cikinsu benazeer da ba zata taba mantawa dashi ba?.

Idanunsa ya lumshe yana furzar da numfashi,sai kuma wani murmushin ya sake kubce masa. Wannan karon koda bori zata hau.....koda aljanu zata tayar sai ya tabbatar mata da cewa shi din likitane,zai banbance mata zaqin soyayya da kuma banbancin kulawarshi a kanta sama da kulawar kowacce halitta.......wannan soyayyar da yayi nasarar haukatata tayi bishiya me manyan jijiyoyi da rassa tsakiyar qwaryar zuciyarta cikin sati uku kaman yadda ya tsara kuma lissafinsa ya tafi dai dai.......zai finciko wannan qaunar.......zai tasheta daga dukkan wani bacci da tayi. Ya sake lumshe idanunsa yana budesu murmushi na sake fita akan fuskarsa kamar me aljannun murmushi. Iya abinda qwayar idanunta ya gaya masa a kanta,baiyi tsammanin aikinsa zaiyi wannan uban tarin nasarar a sati uku kacal ba,tanata wahal da kanta......tanata qaryata kanta akan abinda gaskiyarshi kenan,ita dole ba zata yarda ta kamu ba?,ba zata taba yarda ta fara mahaukacin son maina d'a ga hamid da hamdiyya ba?

"Zakisha mamaki" ya fadi a fili siririyar dariya tana kubce masa.

Miqewa yayi a nutse daya tuna shigarta daki ba abinda zai sameta tanayi sai kuka tabbas kuwa,kukan kuma a matsayinsa na likita yasan baya haifar da d'a me ido ga mace me yaron ciki kamarta

"Tana buqatar kulawa da kwanciyar hankali......ina buqatar healthy baby" yayi wannan maganar shi da zuciyarsa

"Baby ko babies?" Ya tambayi kansa

"Ya rabbb......babies girls or boys.....ko mix dukka inaso" dukka shi kadai yake maganar can qasan ransa kamar wani zautacce,sai ya sake yima kanshi da kanshi murmushi. Bai taba sanin haka yake da son yara ba sai yanzu,koda yake d'an kanka daban yake da komai,zaka yita mamaki ace wannan wani yanki ne daga gareka?.

Qofar dakin ya maida ya kulle,sannan ya isa a hankali gabanta yana kallonta,sai ya zare hannuwansa daga aljihun wandonsa,ya zauna daga gefan gadon,ya sanya hannunsa dukka biyun yana qoqarin dagota zaune

"Tashi muyi magana......ki tsaida wannan kukan....." Yadda yayi maganar da sassaucin murya da kuma girman nan da tasan yana mata shi a baya yasa ta sassauta kukan. Dakin ya dan dauki shuru,sannan yayi gyaran murya ya jefa mata tambayar

"Me kike da buqata?" Muryarsa ta daki zuciyarta sosai,har wata yar shesheqa ta fita daga hunhu zuwa hancinta a sanyaye,tanason ko yaya ne shima yaji bacin ran data ji,rana tsaka ya jawo aba ya mata koran kare a gidansa?,ama kuma da alama itama bayi bayansa?.

"Bana sonka" ta furta zuciyarta na qaryatata amma labbanta sunason cewa gaskiyarta ta fadi.

Har qahon zuciyarsa yaji maganar,karo na biyu kenan data gaya

Please Login or Register in order to submit comment