Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

wani box. Kallonsa tayi sannan ta sanya hannu ta amsa. Madararta ce,madara mafi soyuwa a gareta,madarar da tana begenta amma kuma tana nisantata da rayuwarta saboda tuna mata da takeyi dashi

"Gashi inji benazeer da batoul da baki tambayesu ba,sunce suna gaidaki" wata irin kunya ce ta saukar mata,tanason tambayarsun amma batasan ta yaya zata fara tambayar tasu a gaban ama da aba din ba,uwa uba ga bibi a gefe,ga kuma dan sanya ido goumar

"Ace ina gaidasu" ta fada da sassanyan muryarta

"Basa amsawa,sai da aka roqa musu" goumar ya fadi cikin salon tsokana. Harara kawai ta samu damar binsa dashi saboda tashin da motar tayi bata samu daman maida masa raddi ba.

Duk wata kujiba kujiban zuwan masu visiting lokaci yana yi aka rufe gate din makaranta,doka kuma taci gaba da aiki. Suna saman gadonsu kowa na kintsa wajensa da gyara kayayyakin da aka kawo masa daga gida,dakin nasu fal kaya saboda dukkansu kusan daga gidan iko da wadata kowacce ta fito,babu wadda ta fito daga qaramin family.

Da wuri sultana ta gama komai,tana daga saman gadonta ameena aleeyu ta qaraso da box dinta ta miqa mata

"Ga box dinki nan" binsa tayi da kallo tana jin shakkar amsa,sai ta maida dubanta ga ameena

"Bansan waye ya aiko dashi ba,ki ajjiyemin kawai zan nema maishi saina karba"

"To ya wuce saurayinki?" Ta tsokaneta tana dariya. Dukanta maganar tayi har tsakiyar zuciyarta,sai ta daga kai tana kallonta gami da jefa mata harara

"Ba saurayi ba dattijo" ta fadi cikin hushi. Yanayin yadda tayi maganar gauraye da harshen qasar nijer cikin kuma fushi dukkansu ya basu dariya,bata sake ce musu komai ba ta janye qafafunta zuwa gadonta ta juya musu baya.

Iyakar tunaninta kaf ta gaza canko wanda zai iya aiko mata da saqon

"To kodai goumar ke yimin wasa da hankali?" Tayi tunanin haka daga qarshe,sai ta cije lebanta tana jin qamshin gaskiyar hasashenta. Tabbas da ta tuna hakan kafin su tafi saita yayyaba masa magana,ta fuskanci kamar yana yawan son yiwa rayuwarta shishshigi.

*_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400
BIYU_800
UKU_900
HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875
Musaa Abdullahi safiya
Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261


*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku kudin*

09033181070


*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂*_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

Book 02 page 36



**********Sannu a hankali rayuwa taci gaba da tafiyar mata,tana sake hankali tana kuma sake fahimtar me ainihin rayuwa ke nufi kadan kadan.

Sosai kwanyarta take budewa,a hankali kuma ta fahimci gatan da ama tayi mata data kawota makarantar. Kafin takai ga zuwa ss3 ta zama wata sultana ta daban. Azkar ya kama bakinta ainun,karatun qur'ani da wata nutsuwa dake nuna sanin haqiqanin rayuwa. Tabbas! Ilimi wani irin haske ne da babu irinsa,wani abu ne dake busawa zuciya da rayuwa wani ruhi na musamman. Hatta da kamanninta sun sauya,sun cika da wata irin nutsuwa da wani sirtaccen kyau nata dake boye. Idan ka kalleta a sannan babu abinda zakaji cikin zuciyarka dangane da ita sai tsananin burgewa,saboda wata kamala annuri da kwarjini da ilimi ya zuba mata,komai nata sai ya zama cikin nutsuwa da kuma kamun kai. Kalaman bakinta sun canza sosai,hakanan mu'amalarta,saidai kuma tun wancan sanyin da tayi.....tun wancan sauyawar......tun a wancan lokacin har zuwa yanzu sai ta zama me matuqar sanyi,miskila mara yawan surutu hayaniya ko kuma kwarafniya kwata kwata.

Tana S.S3 ama ta saka su benazeer a free nursery,surutu da wayonsu ya isa,wani irin wayo ne dasu da yafi na shekarunsu,duk da batoul nada kalar nata miskilancin,amma tun kafin shekarunsu su fara nisa kamanceceniyar halayya wajen yawan surutu rigima da rawar kai na sultanan can baya benazeer ta kwafe tsaf!,wannan ya sanya ama tafi maida hankali akan benazeer din sosai,tanaso dukka wadannan halaye da Tayo gadonsu su kasance kan tsari da kuma cikakkiyar kulawar tarbiyya. Saboda kwadayin ingantar tarbiyyar yaran ya sanya gaba daya ama ta daina tunanin komawa nijer,tafison a nan din inda suke suyi tasu quruciyar da wayon,saboda itace babbar shaidar banbancin tarbiyyar da qasashen biyu ke dashi.

A shekararta ta qarshe a makaranta ta yiwa kanta gata me tarin yawa. Tayi joining classes da akeyi na musamman bayan wadanda suka zama wajibi. Litattafai ake musu na addini masu yawa,zazzafan karatu ne da ya sanya da yawa daliban basu fiya joining ba sai masu wayo da masifar nacin so karatu irin sultana. Yadda zazzafar qiyayyar karatu ta juye mata zuwa zazzafar soyayyar karatu tana bawa ama mamaki. A duk sanda sukayi hutu tazo gida yakan zamana kamar ba hutu ta samu ba. Duk bayan kowacce daqiqa tana maqale da litattafai,wani lokaci hadda takeyi wasu lokuta kuma tilawa. Ta samu hadisai sosai,wasu ta haddacesu ne,musamman wadanda keda alaqa da mu'amala da kuma rayuwa,wasu kuma a yayin da aka karanta mata ta iyasu a rubuce kuma tana tsintar wasu tana amfana dasu. Kosu benazeer bata basu lokacinta kamar yadda take bawa litattafanta. Sai ya zamana ba wata shaquwa bace can can a tsakaninsu da ita. Da ama suka budi idanu,ama itace mommansu,ita sultana AUNTY kawai suke kiranta,kuma suna mata kallon auty dinsu ce,saboda tsakaninsu hukuntawa ne da tsawatarwa idan za'a yi ba dai dai ba tamkar na qaramin yaro da babbar yayarsa.

Watannin qarshe da suka rage musu a makarantar,dab da zasu fara jarabawa sukayi saukar alqur'ani me girma. Kyawawan qira'o'i dukka guda bakwai din da muke dasu babu wanda bata iya ba. Karatu take tartilan babu gargada,babu bata,zakayi tsammanin ta jima da saukeshin a yanzun maimaici kawai takeyi. Tana cikin zaqaquran dalibai guda goma na farko da aka fidda cikin ajinsu.

Sanda suka fara jarrabawa dukka tunaninta sai ya sake fadada akan qara nisan zangon karatunta,batajin zata zauna haka,yanzunne ta soma jin gardin ilimi,ashe ilimi dadi ne dashi har haka?,ashe muddin kana da ilimi kuma kana aiki dashi basai an zauna ana fama wajen gyaraka da saitaka ba?. Sau tari idan su ameena aleeyu sukaga tana zaune guri daya tana murmushi sukan cika da mamakin meye yake sata nishadi yayin kadaicewa ita daya?. Murmushin ta kan fita ne a duk sanda ta tuna da quruciyarta,ta tuna da rayuwarta a niamy,ta tuna irin tabara da rashin hankali da zallar wauta data tafka,yadda ta qaunaci rawa,xuwa party zuwa birthday kamar hauka,a yanzun idan dukka ta tuna wannan sai kunya ta kamata. Ta sake tabbatarwa da lallai komai lokaci gareshi,komai kuma yana zuwa ya shude ne cikin rayuwa tamkar a allon majigi.

Abu guda daya ke zuwa ya tsinke kyakkyawan zaren wannan tuna baya nata,idan ta tuna da MAINA. Komai yana shafewa a zuciya da ruhinta,komai yana shafewa daga tunaninta amma banda abu daya,banda MAINA banda yadda ya yiwa rayuwarta da mutuncinta dirar mikiya,banda yadda ya wargaza mata kyakkyawar rayuwa yabar mata wata rubutacciyar qaddara a rayuwarta,ya kuma shura qafafunsa ya bace battt daga sararin duniya tamkar zuwan walqiya da daukewarta. Komai ya sauya cikin rayuwarta amma wannan tabon yana nan a zane radam......wannan tsumammiyar qiyayyar tana nan a rubuce dara dara bata kauce ba,daga qarshe takan buge da xubda hawaye me tarin yawa.

Takan jaye jikinta daga cikinsu fateema Ahmad duk lokuttan da suke hirar samarinsu,soyayya ko hirar data shafi 'yammatanci,saboda a sannan kowacce ta soma cika mace,takai kuma ganiyar 'yammatancinta. Cikin jiki da ruhinta takejin kwata kwata bata cikin sahunsu,to meye zai zaunar da ita a cikinsu ana hirar da ba layinta ba?.

Su kuma dukkan wannan sun azashi ne cikin zallar miskilanci irin na sultana,son zaman kadaici da zaman shuru,kamewa da rashin son hayaniya. Takan saki siririn murmushi da jerarrun fararen haqoranta a duk sanda suke mata tsiya

"Kin fiya shuru shuru wallahi,ke ba dama ki zauna ayi hirar arziqi dake."

"Baku riski sultana a sanda take sultanan ta ba,kun samu sultanar nijeria ne,sultanar hassan Ibrahim gwarzo,sultanan ama,auntyn benazeer da batoul.......ba sultanan nijer ba,sultanan bibi da aba,da hirar tsiya ma duka sai anyi,saikun nema wajen fakewa daga gareta" takan raya haka ne cikin zuciyarta.

Ta riqi sallah sosai,ta kuma koyi azumin litinin da alhamis a gida ko a makaranta,tun daga sanda suka karanta hadisin dake bayanin falalar azumin litinin ko alhamis basu taba ruskarta tana da cikakkiyar lafiya ba tare da tayi azumin nan ba. Saidai har yanzu jikin nan yana nan ba wata qiba,amma kai tsaye ba zakace a rame take ba,sai tsaho data qara,duk wata halitta tata ta qara cika,kyawun nan na cikakkiyar buzuwar asali,jinin NADEEYA MUHAMMAD MAYAK'I ya hudata sosai,ya zamana har hirarta akeyi sashi sashi cikin makarantar,domin kaf cikar makarantar da batsewarta babu wata diya mace data isa ta tsaya a tudun mizanin kyau tare da ita,wannan ya sanya take sake kame kanta da kuma fita a dukkan shirgin da ba nata ba. Sai kuma Allah ya zuba mata farinjini da kwarjini wajen juniors,bata da mugunta ko kadan,hasalima cikin sabbin shigowar nan duk yarinyar da ta gani ne rawar kai iyayi da surutu sai taji tana tausaya mata,wani lokaci kuma ta saki murmushi don suna tuna mata da shekarun baya da suka shude mata.

*_GRADUATION DAY_*

Rana ce me matuqar tarihi cikin rayuwarta,ranar data sanyata xubda hawaye me yawa,ranar data sakata dana sanin zaman da tayi ba karatu a wadancan shekarun,ranar kuma data sakata a godiyar Allah me tarin yawa daya fiddata daga duhu zuwa haske.

Taro ne akayi gagarumi na saukar dalibai tare da yayesu,tana cikin dalibar farko da aka kira aka karramata har hawa uku gaban dubban al'umma,gaban familynta,gaban mutanen da suke tamkar iyaye a wajenta,gaban mutanen da suka debe tsammanin zamantowarta a yadda take a yanzun.

Duk inda ta motsa kyaututtuka ne na yabawa da karramawa. Da yawa mutanen dake wajen da sukasan family din MAYAK'I sun mata kyaututtuka na alfarma,har sai da goumar ya taso ya dinga tayata karba.

Data dawo mazauninta ta zauna kasa jurewa tayi,taja hijab dinta ciki ta boye fuskarta tana kuka. Abun mamakin sai batoul ta kalli benazeer cikin kwabe fuska kaman zata saki kuka

"Benz(haka take kiranta don bata iya kiran full name din ya mata tsaho da nauyi),waye yasa aunty kuka?" Waiwayowa benazeer din tayi ta zubawa sultana idanu,itama sai ta kebe baki kamar zata sanya kukan tana duban goumar

"Oncle.......ko itama aunty ta tuna da daddynmu da kace yayi tafiya?" Sosai maganar ta doki qirjin sultana,har batasan sanda ta fidda rabin fuskarta ba tana duban goumar. Kamar dama ya shiryawa hakan,shima ita yake kalla,suka zubawa juna idanu na wasu lokutta suna kallon kallo. Tanata hadiye bacin ranta da maganganun da takeson gaggaya masa saboda cikin bainar jama'a suke. Wato kebewar da yake da yaranta har gaya musu yakeyi suna da wani daddy da yayi tafiya?,waye ya sashi?,shi awa?,meye hadinsu da daddyn da yake musu maganarsa?, tabbas ba zata qyaleshi ba,sai tayi warning nasa,kada ya sake bari wannan maganar ta shiga kwanyar yaranta,bata buqatar hakan.

Wannan maganar kawai ta dauke hawayen fuskarta,sai suya da zuciyarta keyi mata tana fakon goumar tana jira su samu matsawa daga wajen ta amayar masa da abinda ke cikin ranta.

Bata samu wannan damar ba sai da suka tashi komawa gida,bayan taro ya watse,makaranta ta sallamesu sai kuma zuwa karbar result na exam dinsu. Ta gama koke koken rabuwa ita dasu fateema Ahmad da ameena aleeyu,aminan qwarai da ba zata taba mancewa dasu ba,sunyi exchanging phone numbers da full address nasu,har Adress dinta na nijer dukka ta basu saboda batasan me rayuwa ta tanadarwa gobenta ba, al'amuranta bata fiya basu amana ba,ta fahimci caccanjawa sukeyi a duk sanda sukazo hakan,koda yake umarni ne daga rabbussamawati.

Ita da aminata,najma da yasmine su ya dauka a motarsa wadda bai jima da siyenta ba bayan kama aikinsa baya bayan nan da kammala karatunsa. Kusan duk wani hali da dabi'a na maina yana dasu. Har rabon motoci aba ya yiwa samarin cikin dangi yace bazai amsa ba,yafison ya fara hawa wadda ya siya da guminsa. Kusan aqidar maina ne,neman nakai,ya tsani a masa alfarma,ya tsani ya rabu da wani ya dinga cin albarkacinsa,wannan dalili ya sanya har yabar gida baida motan hawa na kanshi,duk da cewa akai akai yana bisa hanya duk kusan sati ko sati bibbiyu tsakanin niamy da marad'i.

Ta fahimci akwai wata kyakkyawar alaqa tsakaninsa da najma,saidai a yanzun ba komai take magana akai ba shi yasa batace komai ba,amma tunda su aminata sukazo ta karanci akwai gulma fal bakinsu,bata dai tsaya ta basu lokaci bane,amma ta tabbatar sai sun fesa mata koda ba zata saurara ba.

Kyawawan 'yammatan buzayen da suketa daukan hankulan jama'a suka jera reras su hudu bayan tashin motarsu aba suka wuce zuwa inda goumar ya ajjiye motar tasa. Hirar suke amma sultana bata fiya sanya musu baki ba,don burinta kawai ta fesarwa goumar abinda yake cikinta.

Akwai takadda guda daya ta sultana da ya tafi karbowa don haka suka dan tsaya suna tattaunawa daga bakin motar tasa kafin ya iso ya bude musu.

Yaro ne da duka duka bazai wuce shekara sha hudu ba ya iso gurin. Fari ne siriri,yana da dan tsaho kadan,yanayin zubin fuskarsa kadai zai shaida maka bafulatanine usul. Sanye yake da wata dakakkiyar shadda sai maiqo takeyi fara qal,kanshi sanye da jar dara sosai irin ta ainihin bare bari. Kana dubansa kasan daga gidan gata ya fito,kuma alamun jikinsa da fatarsa na nuna ainihin jin dadi da yake ciki.

A gabansu ya tsaya yana sallama fuskarsa a sake. Dukkansu suka daga kai suna dubansa,aminata ta amsa masa,sai sultana ta maida kanta tana daidaita qananun litattafan azkar dinta data qarasa debowa daga drawer dinta ta jikin gadonta don bawa 'yan ss2 da zasu maye gurbinsu damar cin gadonsu da kyau. Gaishesu yayi sannan yace musu

"Wai anason yin magana da wannan" ya fadi yana dan murmushi hadi da nuna sultana da yatsa. Kusan dukkaninsu sai da wuta ta dauke musu na wucin gadi,ba sultana kadai ba,su kansu saida tsoro da fargaba ya cika zukatansu. Suka zuba mata idanu dukkansu,yayin da ita kuma ta zubawa yaron nata idanun ba tare da sanin takamaimai amsar da zata bashi ba.*_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 37
______________________________
https://chat.whatsapp.com/CKY0xZDtpby6MTkGrPkXLr
____________________________


"wai inji wa?" Najma tayi qarfin halin tambaya da alamun sanyi qwarai cikin muryarta

"My broz....gashican,yace idan ba damuwa zai qaraso.....don Allah aunty ya qaraso din,mun gaji so muke mu aurar dashi mu huta" ya fada yana qyalqyala dariya,da alama akwai sakewa sosai tsakaninsa da wanda ya aikoshi din.

Dukkansu suka maida dubansu inda yaron ya nuna musu. Baiyi qarya ba,matashin saurayine fari tas da yayi zubin buzaye yarensu,saidai su da yake suna shaida duk wani da sukejin harshe daya dashi take suka shaida bafulatanine shima tamkar qaninsa. Yana sanye da shadda da hula sak irin ta qanin nasa,komai nasu irin daya kamar yadda suke kama da juna

"Kaje kace masa matar wani ce" muryar goumar ta ratsa kokwanto da walagigin da zukatansu suka shiga na yadda zasu kaucema wannan kiran.

A birkice ta daga kai tana kallon goumar

"Matar wani?" Ta furta a fili amma a hankali. Juyowa goumar yayi wanda yaji fitar lafazin nata yana duban qwayoyin idanunta kamar yadda ta kafeshi da nata

"Eh..... qarya nayi?" Ya fadi kanshi tsaye yana sake kafeta da kallonsa. Mummunan faduwa gabanta taji yayi. Tsahon kwanakin watannin da kuma shekarun bata taba tuna cewa wai har yanzun itadin matar aliyyu bace,bata sake tuna har yanzun a sunan matar aure take ba,bata sake tuna akwai igiyoyin aurensa guda uku qwarara a kanta ba.....to wai zaman meye takeyi da igiyoyin auren maqiyinta kuma makashinta?,me ta zauna tana yi dasu tsahon shekara hudu?. Kai ta jinjina tana zare kallonta daga kan goumar,taji daci qwarai har saman harshenta,saidai kuma taji dadi da yayi mata tuni da wani muhimmin al'amari da ya kamata ta tuna dashi ta kuma kawo qarshensa cikin rayuwarta gaba daya.

A yanzun ita din wata sultana ce ta daban data fara sanin dadin rayuwa,kyawun rayuwa da kuma cikakken 'yanci da rayuwa ke dashi,tanaso tayi rayuwa kamar kowa,tana so tasan me duniya da rayuwa suka qunsa?,tanason ta fita tayi gwagwarmayar da al'umma zasu amfaneta,dole ta kawo qarshen wannan maqalallun igiyoyi da ko daya bataga amfanin barinsu a sarqafe ba.

Najman ce a gaba dukkansu suna baya su uku,tana iya hango yadda fuskar saurayin ta canza sanda qaninsa ya iskeshi a sanyaye yana labarta masa,batasan ya suka qarke ba,tadai ga yabi bayan motarsu da kallo har suka fice daga makekiyar harabar makarantar.

Cikin motar kanzil bata ce ba,aminata da yasmine sunta hirarsu,goumar da najma da batasan me suke fadi ba suma tasu hirar suke,sai ita daya da suka fari da hannu dafe da gefan kanta tanata zane saman bangon littafin dake cinyarta,wanda ita kanta batasan me take zanawa ba saboda tsabar tunani.

Iska ta shaqa sosai da suka shiga tangamemiyar harabar gidan aba dake garin abuja bayan jirgi ya saukesu a airport. Tadan bi harabar gidan da kallo yadda ya qawatu matuqa da gaske. Sabon gida ne da basu jima da tarewa ba,duka duka sati biyu. Cikin shekarun nan wani irin tumbatsa arziqin aba dama na hamdiyya ABDU ME KANO wato ama keyi,kaman an sake yiwa dukiyarsu yayyafin albarka,mahaukatan kudi kowannensu yake samu. Yanzu haka sun budewa benazeer da batoul manyan manyan boutique cikin garin abuja har guda uku,wanda kowanne kudade ya lasa ba qananu ba,saboda girman boutique din ya kusa wani mini supermarket din B&B BABY DREAM. Komai nasu na dabanne saboda ana sarrafashi ne daga wani kebantaccen kamfani dake sanya tambarin B&B a kowanne kaya,shi yasa kayansu ya fara zama na daban,ya kuma samu karbuwa qwarai da gaske,karbuwar kuma tana da nasaba da yaran da Allah ya hore musu wani irin farinjinin mutane.

Randa sultana tazo wani hutu ta amshi wayar yaran da ama ke musu amfani da ita tana duba account nasu na insta abun ya bata matuqar mamaki. Followers suke dasu masu yawan gaske. Account ne na musamman da ama ta bude kawai saboda yaran,ba abinda take dorawa sai hotunansu. Tun sultana tana kallon pics din har ta gaji saboda yawansu,ta aje wayar kawai tana murmushi

"Kakar zamani" tayi gulmar ama a ranta tana dan dariya qasa qasa.

Motar goumar ya tsayar a farfajiyar ajiyar motoci dake gidan wadda gari ne kusan guda,ya kalli najma

"Samomin wani abu me dan sanyi,ki tahomin da BB(benazeer da batoul)zamu fita dasu wani guri"

"Okay sir" ta fadi tana murmushi sannan ta bude motar ta fice.

"Akwai abinda na riqe miki ne madam?" Goumar ya fadi yana gyara qaramin pillow din dake gefan kujerarsa. Sai data sanya qafafunta waje sannan ta waiwayo

"Goumar" ta kirashi kai tsaye wani irin tsauri na fita daga cikin qwayar idanunta

"Na'am madamme" ya amsa fuskarsa a sake ba komai

"Karka bari ka barar da sauran mutuncin dake tsakaninmu"

"Tofa!,ikon Allah,me kuma nayi?"

"Da batoul da benazeer basu da wani abu a duniya yanzun,kayi qoqari ka daina yi musu tilawar abinda babu wanzuwarsa a duniya......haka nima......ni ba matar kowa bace,ba matar wani bace ni" wata siririyar dariya ya sake mata,ba abinda yake ganowa a idanu da fuskarta sai zallar quruciya da har yanzun shi baiga ta fita kwata kwata a jikinta ba

"Basu da uba a duniya.....ke ba matar kowa bace to kece kika kashe musu uban?" A kaikaice ya waiwaya tana dubansa,maganar tasa ta sake tsaya mata a wuya kamar mulmulallen dutse. Gaba daya abinda ta fahimta goumar kallon shashasha kuma yarinya yakeyi mata,baima dauki maganarta da muhimmanci ba.

"ko ya mutu koma ya rayu wannan duka ba abinda ya shafi sultana bane,abu daya sultana ta sani,bata da wani hadi ko alaqa ta kusa kota nesa dama ko waye" ta fadi da salon tsiwar nan tata data jima bata taba ba

"Ashe dai da sauran bakin har yanzu" goumar ya fada qasa qasa yana dariya sanda take fita a motar. Ta jishi sarai,bata kuma gama fahimtar abinda yake nufi ba,saidai duk da haka ta juyo ta zabga masa harara,ta murguda qaramin bakinta tace

"Baqin ba'abzine,Allah ya qara gwara da Allah ya barka a baqinka" ta buga murfin motar ranta yana suya da ambatar mata sunan maina tana qarawa gaba zuwa cikin gidan cikin sassarfa.

Dariya sosai ya kwashe da ita yana duban hanyar da tabi

"Baki gama laushi ba kenan,hali zanen dutse" ya fada a ransa yana gyada kai gami da ci gaba da dariyarsa sannan ya sanya hannu yana daga glass din motar zuwa sama tare da duban hanyar dawowar najma.*_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

Book 02 page 38


Tunda sukayi maganar nan da goumar walwalarta ta sake daukewa tsaf,duk yadda ta motsa sai zancan goumar ya fado mata a rai

"Matar wani" kalmar data dinga jin nauyinta qwarai,take kuma dugunxuma mata rai. Abun ya tsaye mata qwarai a rai,ashe duk duniya kallon da ake mata kenan?,ita din matar maina Aliyyu ce?. Cikin jikinta ta dinga jin qyamar danganta kanta da matar maina,ta dinga jin ranta da zuciyarta sunqi su yarda da wannan batun.


******K'arfe takwas ne da mintuna na dare, cikin kebantacciyar wajen da aka killace aka kuma zuba masa dining table na alfarma da daukan hankali. Ama ce keta qoqarin serving aba da bibi,wadda tunda tazo bata koma nijer din ba saboda wani likitan gargajiya da take gani cikin kano. Ciwon qafarta ne ya soma matsantawa ama tace ta zauna ayi masa magana,ta fara zuwa kuma alhamdulillah sauqi ya samu,a hakan rigimar komawa nijer takeyi nan da kwanaki masu zuwa.



Please Login or Register in order to submit comment