Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Kaman yadda ya yiwa ama haka ya miqe cikin zafin nama ya tari gaban aba sannan ya sulale a gaban nasa.

"Waye wannan?,ku gaya masa ya matsa daga gabana!" Aba ya furta da wata irin kakkausar murya da duk sanda ta fita da irin wannan sautin......duk wanda ya sanshi to yasan cewa yakai maqurar fushinsa kenan

"Don Allah aba.....don girman Allah......!" Bai barshi ya qarasa magiyarsa ba sai saukar zazzafan mari da sautinsa ya karade falon. Kaf dinsu jini ya dauke a jikinsu,don ba wanda ya tsammaci irin wannan zazzafan hukuncin haka tashin farko daga wajen aba,kasancewarsa mutum ne bame yawan kaiwa koda yara hannu ba bare maina da a yanzun ya zama cikakken mutum

"Kaci gaba da tsayamin bisa hanya kaga yadda zamu kwashe dakai mahaukacin banza!......zaka matsamin ko sai na tattakaka a wajen?" Aba din ya kuma fadi cikin fushi. Cikin hanzari oncle umar ya miqe ya janye maina wanda ko gezau baiyi ba,hasalima baiso oncle umar din ya janyeshi ba,zaifi masa dadi ya barshi a wajen aba yaci gaba da dukansa wataqila ita daya ce sassauqar hanyar da aba din zaiyi saurin sassautowa ya saurareshi.

"Zauna nan,kada ka sake tsaiwa masa a hanya aliyyu" oncle umar da zuciyarsa shima ta fara motsawa ya fada cikin nasa fushin.

Kafeshi oncle umar din yayi da idanu,kaman yadda oncle bashar da oncle issoufou suka kasa motsawa,idanunsu dukka akan maina din,saboda wani abu ne da yazo musu a bazata gaba dayansu.

A hankali idanuwansa suke sauya launi saboda abinda ke motsa masa cikin zuciya,wani irin yanayi maras dadi qunci da zafin zuciyar da shi daya yasan me yake fuskanta.

"Yaushe ka dawo?, yaushe ka shigo gidan?" Oncle bashar yayi qarfin halin tambayar maina. Sanda ya dago fuskanshi da zummar amsa masa dukkansu saida kowa yasha jinin jikinsa. Wani irin yanayi fuskar tasa ta sauya,gaba daya kamanninsa sun canza.

"Yanxu oncle......yanxu na shigo,ama taqi saurarona tace saidai na sameku...... shima aba haka"

"Ba zasu saurareka din ba,don bakayi abinda zasu saurareka haka ta sauqi ba aliyyu" oncle umar ya fadi da wannan yanayin nasa dake nuna zafinsa. Idanu maina ya maida kan oncle umar din yana da zafi shima qwarai,har wani lokaci bibi ke ganin ta wajenshi ya gado zafi da kafiya,saidai nashi zafin da ya tashi ya ninka na dukka uwayen nasa. Duk da zafinsa idan ya gama spark ya sauka yana da budaddiyar zuciya,yana da zuciyar sauraro dake iya fahimtar mutum ta kuma bashi uzuri,yana da kafiya da qoqarin fahimtar da aba harma da bibi a duk sanda suka hau dokin naqi,ya hangi nasara ya idanuwa da bangarensa,don haka ya zamo a hankali ya gurfanar da kansa a gabansu

"Bansan da wanne baki zan fara baku haquri ba......bansan wadanne kalmomi ne zasuyi tasiri a kanku wajen wanke fushina dake zuciyarku ba...... abinda zan iya fada kawai shine......ina me neman afuwa da yafiyarku akan yanayin dana sanya zukatanku.....zullumi da fargaba dukka.......sannan gani a gabanku kuyimin dukka hukuncin da kuke ganin ya dace kan cutarwar da na yiwa jikarku" kalamansa sun dakesu sosai sun kuma sanyayar da jikkunansu. Dakin ya dauki shuru,kaman yadda basuce komai ba hakanan shima bai motsa daga tsugunnon da yayi ba,har sai da oncle umar ya magantu

"Koma ka zauna maina" kasa motsawar yayi yana jin nauyi da kunyarsu,yanajin nauyin abinda ya aikata din da yayi sanadin barinsa gida,yanajin kamar a yanzune komai ya faru,har sai da oncle issoufou ya kama hannunsa sannan ya matsa gefe ya sake zama sosai.

Fada sosai oncle umar ya balle masa dashi,don dama shidin baya barin ko ta kwana,sha yanzu magani yanzune ko akan waye,sai da yayi mai isarsa bashar da issoufou suna tayashi sannan ya rufe da fadin

"Abinda ya faru tsakaninka da matarka za'a iya cewa me sauqi ne inda ka zauna baka nuna ragwantaka ba...... za'a iya cewa rabo ne ya kawo haka,shi kuwa rabo baya tsallake rana da loakcinsa......ba kuma wanda ya isa ya hana wannan rabon fita sai ya fita a sanda ubangiji ya tsara......abu mafi muni shine tafiyarka,tafiya bata sati daya ko biyu ba,bata wata daya ko biyu ba,bata shekara daya ko biyu ba.....shekaru aliyyu,shekaru a qalla biyar?,wanne irin rago ne aliyyu?me yasa ba zaka tsaya ka fuskanci koma meye ba?,duk tsiya ba haramun dinka ka afkawa ba,me yasa ka tafi?" Ya jefa masa tambayar da alama tafiyar tasa tana daya daga cikin abinda ya sosai zuciyarsa.

Tabbas yasan cikin bacin ran dake danqare aran oncle umar ne kadai ya sanyashi ya jefeshi da kalmar RAGWANTAKA......saboda duk gidan yafi kowa sanin TSORO yana daya daga cikin abubuwan da bai baiwa muhimmanci a rayuwarsa ba JA DA BAYA basa daga cikin kafatanin dabi'unsa,duk yadda zai musu bayanin yadda yaji a sanda abun ya faru.....duk yadda zai kwatanta musu yadda qaddara ta dinga janshi tana tilasta masa ficewa daga gidan ba zasu gane ba.......daga bayan barinsa gidan kome daya faru dashi ya sakashi a mizanin wannan QADDARAR da tayi sanadin fitarsa a gida..... wanda yayi imanin banda hakan ta faru......da tuni a yanzun ba shine ALIYYU MAYAK'I da ake magana a kai ba,da tuni ba shine MAINA da yaketa qoqarin binne daukaka da matsayin da ya samu ba,bayan tarin qalubalen da ya gamu dashi sanadin fitarsa a gida

"Dukka ka yiwa kowa laifi,amma tamu me sauqi ce,kuma mun yafe maka,a yanzun babban qalubalenka, zamuyi iya abinda zamu iya wajen nema maka sasaauci,amma saukowarsu wannan tana hannunka,tunda bamu isa mu tilasta musu su yafe maka ko mu goge abinda ke ransu ba......" Ko iya wadannan kalaman na oncle umar kadai sun samar da wani sasaauci cikin gurbin zuciyarsa,sun kuma haifar da wani dan qaramin hope

Baisan ta yadda zai gode musu ba, matsayin nagartattun kawunnai a wajensa,ya miqe da zummar barin falon,yana kuma wassafa ta inda zai fara tunkarar wannan gundumemiyar matsalar........ babban yaqi da zai zama madubin rayuwarsa muddin ya cimma nasara.

"Kaje zuwa da safe koma meye zamu qarasa magana akai......gobe daurin auren qannenka biyu"

"Waye da waye?" Ya samu kansa da jefawa oncle umar tambayar saboda wani fargaba daya kamashi. Dukka sai suka dan tsaya suna dubansa kafin oncle umar din ya bashi amsa

"Aminata da yasmine" qas yayi da kansa kuma yana jin nauyinsu,yana jin kamar yayi tambaya akan makomar aurensa da sultana......to amma kuma hakan kamar zai zama da gaggawa,karbarsa da sukayi bawai yana nufin yanzun shi bame laifi bane a wajen kowa ba...... a'ah......yasan sun karbeshi ne saboda tsananin zumunci irin nasu da yadda suka tashi da soyayyar junansu data yaran da suka fita daga tsatsonsu.

"Aliyyu" oncle issoufou ya kirayeshi da sassaucin nan nasa,don shi din mutum ne da bashi da zafi sam,duk cikinsu yafi kowa sanyin hali

"Ka kama bibi,ka tabbatar ta zame maka tsani" kai ya girgiza wani busashen murmushi na fita daga saman labbansa,tamkar oncle issoufou din ya shiga zuciyarsa,bibi ce kawai last hope dinsa da yayi imanin tana da power din da zata maida komai bisa saiti,ko meye zatayi duk wani borenta bazai bari ya dameshi ba,zai runtse idanunsa,zai kuma gwada mata shi dan yau ne,domin yasan halin bibi sarai,zuma ce sai da wuta,amma kuma yana da babban yaqini a kanta.

Daidai inda sukayi kacibus ya kalla sanda yake fita a falon,yaja dogon numfashi daya sauka har tsakiyar hunhu da zuciyarsa

"SULTANA" ya maimaita sunan kamar yaune ya fara jinsa. Akwai babban game tsakaninsa da ita,yana tunanin itace abu na qarshe da zai cimma,a yadda ya tsara itace zata kasance matakalar qarshe,yaya zaije mata?,ta yaya zai risketa?,dukka bai san wannan ba......abu daya ya sani,ya kuma haqiqancewa kansa shine........duk RINTSI......duk yadda za'a je a dawo ba zaya taba yarda da abinda zai shafi igiyoyinsa ba

"Idan suna nan har yanzu?" Wani sashe na zuciyarsa ya jefa masa tambayar data tilasta masa riqe hannun almu dake zaune zuwa yanzu a gefan qofar falon saman wasu qananun kujeru dake wajen don ya gaji da tsaiwar jiransa

"Idan har yanzu sashe na yana nan......ina buqatarsa,ka gyaramin koda iya wajen da zan ajjiye kayana" ya fada adan birkice,don har yanzun bayajin cikakkiyar nutsuwa a jikinsa. Kai almu ya gyada yana miqewa,har yayi taku biyu mainan ya kirashi,sai ya dawo ya tsaya cak gaban maina yana kallonsa

"Bayan tafiyata ciwon kurumta ko bebantaka ya sameka ne?" Ya masa tambayar yana duban idanunsa. Kai ya girgiza sannan ya matso taku hudu da sauri ya fada jikin mainan yana cewa

"Barka da dawowa ya maina,Tu nous manques(munyi kewarka)"

"merci(na gode)" ya ambata da raunanniyar muryar nan yana daga almu daga jikinsa yana kallonsa. Shima almu din kallon fuskar maina yakeyi,yana mamakin yadda ya mainan nasu ya sake komawa. Babban mutum da wani irin shinfidadden kwarjini da nutsuwa saman fuskarsa. Abinda shima maina ke wassafawa a ransa kenan,almu din da ya tafi ya bari da sauran quruciya ya zama saurayi

"Ka girma almu,ina fata zaka taimaka wajen kawo wani haske komai qanqantarsa tsakanina da ama"

"je promets in sha Allah(nayi alqawari in sha Allah)" kai maina ya jinjina,yana a tsaye har almu ya tunkari tsohon sashensa da baiga wani abu daya sauya ba ta wajen,saima gyara da wajen ya samu da kuma kulawa.

A yadda idanunta suke a rufe sam bataga bibi dake zaune cikin falon ba tana kallo saboda raguwar jama'a daga sassan nata. Sanda ta shigo din daga kai kawai bibi tayi ta bita da kallo,yanayin taku da tafiyar sultanar dukka ba sune tattare da ita ba

"Ikon Allah" bibi ta fadi har zuwa sanda ta tura qofar dakin dake kusa da ainihin dakinta ta shige

"Allah ya kyauta.......itama wannan ja'irar na fuskanci ta zama baudaddiya" ta fadi a bayyane tana maida toothpick din data zaro bakinta taci gaba da sakacenta.

Kamar daga sama taji sallamarsa,saita maida dubanta da hanzari bakin qofar qawataccen falon nata. Yadda ya zuba mata idanu haka itama ta zuba masa tana jin kamar cikin mafarki take ko kuma majigi take kalla

"Wannan kamar maina" ta fadi cikin tantama duk da yaqininta yafi yawa akan tabbas shi dinne. Qafafunta dake saman kujera ta sauke,har yanzu bata dauke dubanta daga kanshi ba kamar wadda taga fatalwa. Ta waiwaya kadan tana qwala kiran sunan

"Tanja!,ke tanja!!" Tanja tana kusa,don tana kitchen din bibi din zata zuba abinci taci,saita saki abinda takeyi din,don yanayin kiran da bibi ke qwala matan baiyi kama da kiran lafiya ba,uwa uba kuma tanata juya dawowar maina a daidai wannan lokaci.

Dashi idanunta suka fara cin karo,yana tsaye abinsa qyam daga bakin qofar,a dan rude ta kalli tanja

"Wancan dake bakin qofar a tsaye ba aliyyu maina bane?" Tayi tambayar bihaqqi tana neman sani.

Tanja bata ma dubi wajen ba ta bawa bibi amsa

"Shine" kammala fitar haruffan guda biyar yayi daidai da miqewar bibi tamkar bame fama da ciwon qafa lokaci lokaci ba,sai kawai ta soma jan zaninta tana daurin qirji dashi idanunta fes bisa fuskar maina da sai data miqe din take sake qare masa kallo abinda daga maina din har tanja suka gaza gane abinda take nufi da hakan

*_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400
BIYU_800
UKU_900
HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875
Musaa Abdullahi safiya
Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261


*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku kudin*

09033181070


*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂*_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

Book 02 page 54


Idanunsa fes bisa kanta,yasan dukkan wani kalar rigimarta,yasan meye zata iya aikatawa da wanda ba zata iya aikatawa ba,yasan kuma lagonta qwarai da gaske.

"Billhuwallazi lailah illa huwa idan ma fatalwa ce ba aliyyu ba ni bibi nafi qarfinta.......idan kuma har da gaske kaine.......da idanuwanka guda biyu a bude na rashin kunya ka iya dawo mana cikin gida to dai dai nake dakai,shege ka fasa ni da kai" ta fadi cikin daukaka murya tana sake gyara daurin zaninta da kyau tamkar me shirin yin dambe dashi. Dolen dole badon yaso ba murmushi ya subuce masa yana kallonta,da gaske take tattara dukkan qarfinta kamar wadda ke shirin yin dambe da qaddararta.

A yanzun ba bibi kadai ba, kusan duk wanda keda ruwa da tsaki da rayuwarsa yasan a tunzure yake dashi,bazaiyi wani abu kuma da zai sake tunzurata din ba don yanzun tamkar itace sitiyarin gidan gaba daya,samun kanta shine samun kan kowanne mutum dake cikin gidan,don haka yaci gana da takawa yana nufarta

"Au......ba zaka dakatamin a nan ba?,la'ilaha illallahu......da gaske dai aliyyu ne!, jama'a kuzo ku ganemin ikon ubangiji na" ta sake fada cikin daga murya tamkar tanasom tara masa jama'ar gidan gaba daya

"Bibi kibi a hankali,ba fatalwa bane na gaya miki maina ne" tanja ta furta adan daburce ganin yadda bibi ta dage lallai saita hada masa jama'ar gidan. Shikam ko gezau be fasa takawa zuwa wajenta ba,yayin da taci gaba da kwakwazo da jan salati iri daban daban.

Yana isa dab da ita baiyi wata wata ba ya sanya hannu ya riqeta da kyau

"Sakeni,sakeni nace" ta fadi yana qoqarin qwace hannunta daga nasa cikin fada da hargagi

"Kiyi a hankali,tunda dai baki samu damar hadamin jama'ar da kikayi niyya ba aisai ki haqura ki zubawa sarautar Allah ido ko?" Ya fadi yana qoqarin zaunar da ita. Dukka sauran qarfinta ta sanya ta tureshi cikin fusata tana cewa

"Gafara can ka bani waje,wato nice marainiyar wayonka,ka tsallake katanga.ka shigowa mutane cikin gida a sirrance zaka zo.ka cuceni,banga alamar akwai wanda yasan da shigowarka cikin gidan nan ba" qaramin murmushi ya saki yana sake yunqurin riqota

"Allah ya kiyaye.......da lalacewa ta sameni,na gudu daga gida......na tashi dawowa na biyo ta katanga?.....ai kuwa da nayi asarar suna,kuma da daga yau na ajjiye sunan Aliyyu na koma aliya"

"Ahaf.......lalacewa kuma ta nawa?,duk dan da zai tsallake albarkar iyayensa yabar gida shekara da shekaru ai lalacewa ta gama samunsa" ta fada tana sake qoqarin tureshi . Har cikin zuciyarsa maganar tata ta bashi dariya,saidai boren nata yayi imanin mataki ne na nasara,nasarar da ya tabbata tana da alaqa da addu'ar da ya tsananta yi tun kafin ya sanya qafafunsa cikin gidan.

"Kina batan lokaci ki zauna ki marabceni kawai" ya fadi yana sanya qarfinsa cikin tausasawa ya maidata ya zaunar saman kujera,sai ya waiwaya yana duban tanja

"Jeki abunki kija mana qofa miji zai gana da matarsa" dan qaramin murmushi me hade da hawaye ya qwacewa tanja,tayi missing maina qwarai,bama ita ba,kowa dake gidan idan zaiyi magana ta tsakani da Allah zai fadi haka. Duk da zamantowarsa me zafi fushi da kuma zuciya......amma kuma shi din mutum ne me dadin mu'amala qwarai da gaske.

Gadon bayansa ta kaiwa dundu da dukka qarfinta tana fadin

"Allah ya kiyaye Allah ya sawwaqe nayi miji da kai,mijina jarumi ne,bai tana ja da baya ba" ta fadi tana yarfa hannunta,don dukan data kai masan ba shine yaji zafin ba itace taji,ita dimma bata ankara da wautar da tayi ba na kai masa dukan sai daya zauna ya babbake a gabanta sannan ta qare masa kallo tsaf. Ya zama ingarma dake da wani irin ginanne kuma tsayyen jiki da nuna zallar qoshin lafiya da cikakken qarfi,ko ina a murde alamun daga qarfe sosai sun bayyana ga jikinsa,duk da cewa cikin sutura yake cikakkiya.

"Bafa mainan da kika sani a baya bane kike dukana haka bibi?"

"Na sani mana.....wannan wani shashashan maina ne,gudajje daga gidan iyayensa bayan yaso ya kashe 'yarsa kuma 'yaruwarsa sannan matarsa" ta fadi masa cikin fushin zuciya,tana jin takaicin yadda bata da cikakken qarfin tureshi ta tashi a wajen ta daina kallonsa. Wani qasaitaccen murmushi ya saki yana sadda kanshi qasa kafin ya dagoshi

"Kowa na gudu.....kowa guduwa nayi.......bien(da kyau),duk kuci gaba da fada,ba laifi tunda abinda idanu suka gani kenan,amma nan gaba kadan zan tabbatar muku da sabanin fahimtarku" ya qarashe maganar yana jan siririn hancinta me tudu kadan wanda kusan dukansu irinsa suka gado,wani irin hanci me kyau dake qarawa fuska kyawu.

Hannunta ta saka ta buge hannunsa tana cewa

"Ka fita ka bani waje tun banci mutuncinka ba,ko kuma na kira ubanka ya fiddamin da kai,tunda naga alama shi kake tsoro" idanu ya fiddo waje,sai ya sulale qasa yana riqe dukka qafafunta hadi da dora kansa saman qafafunta,yayi laushi qwarai da muryarsa cikin sigar tausayi

"Indai ba bindigeni kikeso aba yayi ba kiyi haquri kada ki kiramin shi,dazun nan ya gama kwakwadamin mari,bibi kaman zai tsinemin,ama taqi koda kallo na,kema nazo kin juyamin baya bayan ko meye ya faru ke kika dauremin qarqashin aikatawa......." Bakinsa ta kaiwa bugu da sauri,saidai kuma bata sameshi ba don ya kauce yana boye dariyar dake subucewa tun daga zuciyarsa,fiye da rabin tsoro razani da quncin da yake ciki a yanzun baya jinsa tunda gangar jikinsa ta gamsu da cewa yana cikin gida...... yana cikin family dinsa,yana cikin ahalinsa iyalinsa

"Ni nace kaje ka yiwa diyar mutane fyade?,ka kusa kasheta?,ka illata mata idanu maina?" Ta fadi adan rude. Maganarta ta qarshe ita ta dakeshi,har ta sanyashi daga idonsa yana kallonta,dan siririn murmushin da ya soma samu saboda tubura bibi da yakeyi ya bace bat daga saman fuskarsa

"Illata idanu bibi?, yaushe?,garin yaya?" Tambayar tasa ta sanyata daga hannuwanta dukka biyun ta zuba masa ranqwashi da qasusuwan yatsunta da dukka qarfinta,ta yadda tazan zafin zai ratsa tarin sumarsa ya kuma isa ga ainihin tsakiyar kansa. Idanunsa ya runtse gam,saboda da gaske zafin ya isa har fiye da inda taso yaje din

"Ni zaka yiwa tambayar yaushe ka illatata din?,sanda ka aikata aika aikarka wa kayi shawara dashi?,oh.....ni 'yar nan naga ta kaina......ban sake yarda lallai baka da kunya ba sai yau aliyyu......tashi ka bani waje,kada ka sake shigomin guri,ban gayyaceka ba,daka dawo bani ka dawowa ba,tashi nace" ta fada tana tureshi da gasken gaske. Yaga fushi da motsuwar bacin rai saman fuskarta,amma kuma ta wani sashen da batayi zato ba akwai farincikin ganinsa danqare qasan zuciyarta wanda batasan wannan hasken yana bayyana akan fuskarta ba.

Tsam ya miqe din yana dubanta na wasu sakanni ya qare mata kallo,sai ya zuba hannayensa a aljihun wandonsa yana magana a nutse,duk da qasan ransa akwai razanin jin cewa ya yiwa idanun sultana illa,saidai yana mamakin ta ina?,don baiga wani nakasu cikin fararen zagayayyun idanun nata data jefa masa kallo dasu a makka da kuma dazu dazu ba cikin falon aba

"Zan tafi bibi,amma bawai na tafi kenan ba,zan dawo koda zaki yayyanka ni ki sakani a tukunya.......kafin na karbi kowanne hukunci ya kamata a bani damar magana koda ta minti daya ne,zan bayyanar da kaina a gobe gaban kowa,zan kuma karba kowanne hukunci da kuke tunanin na cancanci ns karbeshi" daga wannan ya soma takawa don barin falon,amma kuma idanunsa manne da bakin qofar dakin,dakin da bazai taba mancewa dashi ba......dakin da yasha mafarkin gashi a cikinsa.....wancan din daya faru yana maimaita kansa har sau babu adadi.....cikin kowanne dare da zaizo ya shude. Cikin jikinsa ya dinga ji tana cikin dakin,amma koda wasa bibi na wajen bazaiyi gangancin shiga ba,a yadda take a fusace ya tabbatar tana iya tayar da boren da a yau aba da bibi ma basu isa sunyi bacci cikin gidan ba.

Dai dai lokacin daya fita din ta sulale qasa tana jingina bayanta da qofar dakin bayan ta gama kallon komai dake faruwa tsakaninsa da bibita qaramar hudar da akayi don hangen wanda ke waje. Tana ganinsun,amma kuma bata iya jin abinda duke fadi a tsakaninsu. Tun dazun hawaye ya gama wanke mata fuskarta gaba daya,saita qarasa zama dirshan qasan dakin tana rufe fuskarta da dukka tafukan hannayenta.

Duk da batajin me bibi ke gaya masa amma kuma sai tayi mamakin yadda bibin ta tsaya saurarensa koda kuwa kanainayetan yayi. Ta dauka zata sanya qafa tayi fatali dashi,ta zaci zata sanya madoki tayita dukansa har sai ya fice musu a daki da qafafunsa,duk wani action na bibi bai burgeta ba duk data fuskanci bore tayi masa,so tayi bibin ta masa irin tarbar da zaiji baya da sauran sha'awar sake zaman gidan.

"Ke sultana!.....,kukan meye kikeyi?,kin manta yanzun ke ba sultanar baya bace?,kin manta a yanzun ke wata sultana ce ta daban?,a baya min xubda masa hawaye,a yanzun bai cancanci kici gaba da xubda masa wannan hawayen ba,ki qarafafawa kanki gwiwa,ki gayawa kanki da kanki a yanzun damuwa bata cancanceki ba.......kiyi moving forward,kada ki bari ya sake maidoki inda kika riga kika wuce" kaifafan maganganun da suka dinga kai komo kenan a tsakiyar qwaqwalwarta.

Sosai taji ta gamsu,ta yadda yanzun shi din ba kowan kowa bane cikin rayuwarta,bashi da kaso ko misqala zarratin a rayuwarta,me yasa zata bari ya dameta?. Da wannan tunanin ta isa gaban madubi tana kallon kanta da kanta. Da gaske ta canza,da gaske ba sultana yarinya qanqanuwa bace wadda zai yiwa qarfa qarfa......wadda zai yiwa.kama.karya......wadda zai yiwa dukkan abinda yaga dama yakeso,a yanzun ta girma......ta kuma mallaki hanakalin kanta,koda jama'ar dake kewaye da ita wadanda zata rayu dasu sai wadanda taga damar zama dasu ta kuma zabesu.

"Dole ya sani ya kuma shaidawa kansa da kansa da da yanzu ba daya bane" ta furta a fili qasa qasa tana motsa jajayen labbanta. Bandaki ta shiga,ta raba kanta da kayan jikinta ta watsa ruwa hade da alwala. Sakakkun kayan bacci ta saka don tafi sakewa,duk wani motsi nata tana furta

"La'ilaha illa anta subhanaka inni kuntu minazzalimin" saboda zuciyarta tayi sanyi. Hijab ta sanya har qasa,ta isa qofar dakin nata ta murza key don kada ma su dawo su dameta,tun dacan dama bata kwana da kowa dakinta don batason takura ko hayaniya,yanzun ma bata son kowa ya dameta shi yasa ta rufe dakin,ta shimfida abun sallah tahau ta kabbara salla shafai ds wuturi sannan ta dora da nafiloli.

*_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400
BIYU_800
UKU_900
HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875
Musaa Abdullahi safiya
Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261


*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku kudin*

09033181070


*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂*_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

Book 02 page 55



Idanunsa suna kan kowanne sashe na sassan nasa,yana nan kaman yadda yake,ba abinda aka sauya ba kuma wani abu daya lalace kamar bai dauki wadannan shekarun baya nan ba.

Duk inda ya gifta ba abinda ke dawo masa sai shekarun samartakarsa, abubuwa da yawa ya dinga tunawa har ya ratsa falonsa yakai ainihin bedroom dinsa.

Yana shiga almu yana ajjiye mop stick din daya gama goge masa tiles din wajen,suka hada idanu da maina din,sai yadan sadda kansa kadan. Abun almu din yana dan bawa maina mamaki,duk ya maidashi wani baqo qarfi da yaji,duk

Please Login or Register in order to submit comment