Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

murda qofar dakin tana shiga. Babban dakine da yafi kowanne girma da kyan furniture,aman tana tsaye da wani folder a hannunta tana dubawa,ta amsa sallamar tana kallon sultana sannan ta miqa mata takardun tana cewa

"Ba hutu,ba zama,sun kusa gama daukar dalibai,aba yace ki duba,cikin universities din wacce ce tsarinsu yayi miki?"

"Allah sarki ubana na kaina" ta fada hawaye yana cika idanunta. Hannu biyu tasa ta karba tana kallon folder din. Itakam dai kawai tayi rashin mahaifinta hamani ne,amma zata iya cewa iyayenta sun maye mata gurbinsa har fiye da haka,batasan wani abu waishi maraici ba,bata taba ji ko ganin zumunci irin nasu ba,tasan indai ana batun dacewa da family itakam ta dace

"Amma ki kula ki duba location na kowacce university ki zabi wadda ba zaki dinga shan doguwar tafiya ba"

"In sha Allah ama". Ta fadi farinciki yana cika zuciyarta fal,burinta ya kusa cika na zama 'yar jarida,ta rungume folder din tana fita daga dakin.

Tsabar zumudi ya hanata tsaiwa ta kintsa dakin ta zauna duba jami'o'in,tanayi tana browsing a wayarta da babu layi a ciki duk kuwa da tsadar wayar,akwai wifi da suka samu a gidan don haka bata buqatar komai don research din.

Har tanja ta gama abinda ya dace tayi ta biyo ta dakin tana nade tsakiyar gado tana aikin canki canki. Cikin zolaya tanja tace

"Wai sultee kamar yanzu zaki fara zuwa makaranta a rayuwarki,wannan zumudi haka?,xuwa makarantar ma kamar yafi komai yi miki dadi" tashi tayi ta zauna tana yatsina fuska saboda yadda bayanta ya riqe sakamakon rub da cikin da tayi na kusan awa daya tana cewa

"Ji nakeyi kamar yanzu aka haifeni tanja,kaman yanzu ne na soma rayuwa,ai da can ba rayuwa nakeyi ba tanja,rayuwar da babu ilimi a ciki?,meye marabarka da gawa?"

"Irin wannan lokacin maina yakeson gani,shi yayita burin gani tattare da ke,ya Allahu ko ina wannan bawa naka ya shiga?" Qwaqwwaran motsi sultana batayi ba,sai tayi kaman bataji abinda tanja tace ba,inda sunsan adadin dimuwa da qyamatar da ruhinta ke yiwa sunansa kawai bama shi din kansa ba.......da babu wanda zaiyi kuskuren sake kiran sunansa a gabanta

"Bari na kintsa miki wajen kafin ki gama" a hankali ta motsa labbanta tace

"To" tana maida hankalinta ga wayarta cikin tsananin nutsuwa,yayin da zuciyarta taci gaba da motsa da wani irin sautin tsana da qiyayya duk sanda kunnuwanta suka tuna mata sautin kiran sunansa da tanja tayi.

Satinsu daya suka gama huce gajiya,sai ama ta fara diban jikokinta suna fita shan iska. Kullum da inda zasu,sai idan sun dawo kaji labari cakwai a bakin benazeer,don ba kasafai batoul ke da surutu haka ba. Hasalima ita saita nema debo dabi'un abbanta sak da sak,tana da wani irin miskilanci da kuma basarwa. Haka kawai idan taso saita tashi da 'yan shirun, benazeer tayi hirar duniya taqi kulata,idan taga haka tasan tana nufin yau ba zasuyi wasa ba ko ifce ifcensu da suka saba ba sai tahau tsokanarta,ba kuwa zata qyaleta ba har sai ta sakata kuka,sau tari sai ama ta shiga tsakani,ko kuma idan suka cikawa sultana kunne ta leqo shikenan sai benazeer din tayi laqwas ta shiga taitayinta.

A irin wannan lokacin ama kan zauna kawai tana binsu da kallo, zuciyarta tana mata haske tana kuma mata fari,wani lokaci kuma damuwa ta cika zuciyarta,dukkansu su biyun sun dauko attitude na mutum biyu ne, benazeer sak SULTANA tana yarinya,batoul kuwa MAINA ce har yabar gabansu.

Duk da garine dake da ababen kallo sosai,gari ne dake da ababen sha'awa amma ita bata sha'awar fita ko ina. Zaman kadaicin da taketa yi ya sanyata karance karance a matsayinta na wadda keson fadawa harkar karatun jarida,a hankali har abun ya zame mata jiki. A nan taga wata makarantar koyar da girke girke na qasashe daban daban,koda ta duba kudin registration din sai taga yayi yawa,don haka ta maida site din ta rufe bata sake budeshi ba. Ranar ama ta karba aron ipad dinta taga ta soma register,ta fahimci yawan kudin ya hanata qarasawa. Murmushi ama tayi,sultana..... sultana,akwai barin kashi a ciki,ba zata taba bude baki tace ga matsala ko damuwarta ba,sai ta shiga site din ta qarasa komai ta biya kuma kudaden,sai gayawa sultana tayi ranar da zata fara zuwa.

Nauyi da kunyar ama suka sake kamata,tana kunyar yadda ta azama kanta dukkan nauyinta,komai nata itace,bata qyashin kashe mata ko nawa ne, ba'a maganar su benazeer da suke fuskantar wani irin gata,idan akace gata ana nufin gata na qarshe,irin gatan da ake kwatance dashi. Komai nasu me tsada ne,komai nasu kuma na musamman ne,hatta kuwa da brush da zasu wanke haqoransu. Amma kuma duk da gatan da ake gwada musu hakan bai sanya sunyi lako lako da tarbiyyarsu ba. Sosai suke samun kulawa da tarbiyya,don ama da kanta take koya musu qur'ani. Da yake sunyi gadon kwanya,sai gashi da qananun shekarunsu sunyi nisa a alqur'ani,hadda kuma tartilan cikin qwaqwalensu. Ta siya musu kayan karatu kala kala da zasu taimaka musu, harshensu kuma ya fara juyewa da qira'ar sheik imam khusari.

Makaranta me kyau aba ya duba ya sakasu,inda suke karatu da dukka harasa biyun, French da English harda qarin larabci.

*_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400
BIYU_800
UKU_900
HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875
Musaa Abdullahi safiya
Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261


*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku kudin*

09033181070


*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂


*_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 41



Cikin watanni biyu aba yayi settling komai ta fara zuwa makaranta. Qaramar mota ya siya mata daidai d'iya mace,ta kaita makarantar koyon tuqin mota ya zube kudi ta koyi tuqi da kyau suka bata license. Hakan ya mata dadi qwarai,don ta huta da tafiya railway ko kiran taxi.

Shigarta makarantar ya sake sanya idanunta suka bude da rayuwa,ta qara sanin mece duniya?,tarin al'umma mabanbanta masu mabanbantan halaye da dabi'u. Ta sake sanin tabbas duniya tana da girma da fadi,taga kalolin tarbiyya iri iri al'adau dabi'u da kuma halaye,wanda kusan kullum idan ta dawo sai ta bawa ama labari. Murmushi kawai ama keyi,itama sai yanzu take sake tabbatar da quruciyarta,lallai a baya in banda quruciya da tabara babu abinda sultanan ta sani. Duk da haka suna biye kuma suna kula da ita,ko don girman igiyoyin dake saman kanta,wanda tun wancan lokacin da bibi tayi magana ba'a sake tada zancan ba.

Suna exam semester farko aba ya ajjiye musu visa dinsu na zuwa umra. Ranar kasa bacci sultana tayi. Hakanan Allah ya jarabceta da son zuwa madina da makka,tun daga sanda ilimin addininta ya fara zurfi ta fahimci muhimmancin gurin gaba daya zuciyarta ta tafi can.

Washegari goumar ya dira a Paris,sai a sannan tasan dashi za'a yi tafiyar. A sannan tana parlor tana duba wasu litattafai nata door bell tayi qara,tanja ta bude masa ya shigo riqe da jakarsa. Daga benazeer har batoul yarda abun wasan hannunsu sukayi sukayi kansa kamar zasu shide saboda murna,shi kuwa ya tattarasu duk da girmansu ya dagasu yana zagaye dasu.

Har suka gama abinsu tana zaune bata daga kai ba,sai da suka nutsu suka zauna tanja ta ajjiye masa drinks da snacks tana gaya masa ama tana bandaki,sai ta fara tattare litattafanta da zummar barin wajen idanunta na kallon litattafan nata tace dashi

"Ina yini,kana lafiya?"

Gwanin tsokana baya fasa halinsa,tabe baki yayi yana cewa

"Nidai ban roqi gaisuwa ba bare a wulaqantani ehe,meye wani ina yini kana lafiya?" Tsaiwa tayi da abinda takeyi ta xuba mishi fararen idanunta, kwanyarta na mata tariyar tarin kamanceceniyar halayya dai da uban dakinsa sarkin zalunci da mugunta wato maina kaman yadda ta rada masa

"Kaidai ba'a iya maka wallahi,Allah ya sawwaqe" saita dauki kayayyakinta a hannu tana yin gaba

"Ya kyauta mana gaba daya,mutum se shegen qunci da dacin rai kamar wanda aka kashewa diyan fari" ya qarasa fada yana galla mata harara. Tasan halin goumar,baiqi su kwana sunayi ba,don haka ko waiwayoshi batayi ba ta shige dakinta,amma ranta cike fal dashi,tana kuma tunanin hanyar da zata bi ta taka masa burki,yadda yake shige mata sharafi ya soma isarta hakanan.

Bata qara bari sun gamu ba sai ranar da zasu wuce. Tafiyar tasu dukkansu ce,harda tanja,amma sai ya zamana duk cikinsu sultana din tafi zumudi saboda a wajenta tamkar zuwan farko ne.

Tafiyar awanni tara bayan yada zango a wani qasar Wizz Air Malta ya saukesu a filin tashi da saukar jiragen sama dake garin madina don can suka fara sauka. Wata ajiyar zuciya me qarfi ta sauke kamar wadda aka finciki zuciyarta. Ta furzar da iska daga bakinta tana jin daukin ganinta cikin masallacin ma'aiki. Daga wankansu cin abincinsu a masaukinsu zuwa fitowarsu masallacin duk sai taji kaman basa sauri,ji take kamar duk duniya ita daya keda buqata,kamar duk duniya ita keda damuwa a qirjinta,kamar kowa baya da matsala sai ita kadai. Tana ganinta a raudha kuwa kuka ta saki sosai,saidai qasan ranta taji nutsuwa tana saukar mata,wannan ya taimaka ta samu nutsuwa tayi addu'a sosai.

Dukka kwanakin da sukayi a madina babu wanda bata amfaneshi ba da tarin addu'o'in da ita kanta batasan adadinsa ba. Sai gata a yau wai itace da yiwa ummanta NAFESSA da mahaifinta HAMANI addu'ar samun rahamar ubangiji,lallai hankali da nutsuwa ya samu,madalla da wannan rayuwa data samu sauyinta.

Randa suka sauka a garin makka kuwa kayanta kawai ta ajjiye tayi wanka ta fice,ko ama su benazeer ta barwa sallahu su gaya mata ita ta wuce harami. Ta kasa nutsuwa don masaukin nasu daga nan idan ta bude window din dakinsu tana gano harami sosai,saita dinga ji kamar ana fusgarta.

Sanda suka fito ma ita ta bace cikin masallacin,don haka ama ta fara tata ibadar, benazeer da batoul ma sukayi nasu waje,wanda ama batasan ma ina sukaje ba sai da suka dawo hannu dumu dumu da siyayyan kayan zaqi,tunda kafin su fita dama already aba ya basu kudi a hannunsu.

Da rigima suka dawo,mutuniyar batoul tayi kicin kicin da fuska tana harara benazeer,tambayar duniya taqi bayani sai ice cream da ta saka a gaba,ita kuwa benazeer ba abinda ya shafeta ta zauna ta bude abinta ta fara sha tana dariya. Da kallo ama ta bita,sak yadda sultana ke cakar da yara zamanin quruciyarta da shegen tsokana da yiwa yara dariya. Daqyar ama ta lallasota ta gaya mata

"Mutane take kulawa ama,sai kuma tayita basu labari mu 'yan nijer nigeria da paris ne" waiwayawa aman tayi tana duban benazeer,suna hada idanu jikin benazeer din yayi sanyi saboda tasan kalar wannan kallon na ama

"Bana hanaki dogon surutu irin haka ba benazeer?,kina so na saka wuqa na rage miki tsahon bakinki?" Da sauri ta girgiza kai idanunta na hada hawaye

"To daga yau na hana,idan zakuje siyan abu kuje ku dawo,ba ruwanku da kowa kina jina?" Kai ta gyada mata tana lanqwashe qafafunta taci gaba da shan sanyinta. Dariya taso qwacewa ama,wato tsoratar da itan da tayin bazai hanata qarasa shan kayanta ba

"Gado ba karambani ba" ta furta can qasa tana sake tuna mata da sultana da qananun shekarunta cikin qasar nijer mansion house na MAYAK'I family.

Da wata irin kasala mutuwar jiki data zuciya rungume da dardumarta take fitowa daga masallacin. Idanunta sun tasa sun kuma yi jaa saboda yawan kukan da tayi a gaban ka'aba. Rabin kanta sarawa yakeyi saboda abincin da bataci ba wunin yau din gaba daya sai zam zam data dinga sha sosai kaman ba gobe.

Sanye da baqar jallabiyya yake takawa a farfajiyar wajen. Tsahonsa bayananne ne,hakanan nannadaddiyar sumarsa.

Bata lura dashi ba kamar yadda shima din da alama bai lura da ita ba yana cikin gaggawa ne,wannan yayi sanadin da saura kadan kafadunsu su hade waje guda,abinda ya sanya sultana janyewa gefe zuciyarta na wani irin mahaukacin bugu saboda qamshin turarennan da hancinta ya shaqa qwarai da gaske fiye da yadda take jiyo qamshin daga nesa a mabanbantan gurare..........qamshin yaja hankalinta ta waiga a hargitse tana duban wanda ya giftata din........

*_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*


BOOK 02 PAGE 42


Rufewar da idanunta sukayi,da kuma irin bugun da zuciyarta keyi ya sanya idanunta suka nuna mata shi a matsayin maina,daga bisani kuma a hankali ganinta ya washe,ainihin kamanninsa suka fito mata

"Sannu ko?,yi haquri don Allah" ya fada yana daga Mata hannu da sassauqar muryarsa dake bayyana zallar sauqin kansa,ya bata haqurinne da hausa kawai don baya tsammanin ko kadan zataji me zaya fada,don kuwa koda alama batayi masa kama da launin jinsin hausawa ba. Kanta ne yayi wani mummunar sarawa,sai data sake matsawa nesa kadan dashi sannan ta gyada kai tana furta

"Ba komai" a wahale sannan ta juya da sasarfa tana barin gurin,don ko kusa bata qaunar sheqar qamshin wannan bala'e'en turaren

"Uhmm......nace ba,don Allah ko zan iya sanin masaukinku?" Taji ya fadi a bayanta bayan ta baro wajen sosai,don tayi tsammanin ma inda suka tsaya din daga nan ba lallai ka hangoshi ba. Muryar tasa ta sanyata waiwayowa sai suka hada ido. Kai ta girgiza masa alamun a'ah,sai ya marairaice yana ci gaba da binta

"Don Allah,kada kice a'ah" hannuwanta dukka ta sanya tana dage doguwar rigarta tana kuma qarawa qafafunta karsashin yin sauri,don burinta ta tsere masa daga wajen. Ba abinda yake sake hadsasawa zuciyarta sai wani irin bugawa

"Please" ya sake fadi ba tare daya dakata da binta ba

"Ka daina bina,nan din waje ne me alfarma"

"Na sani,ni dinma alkhairi nake nufinki dashi,bata yadda zan miki magana a nan kuma zuciyata sharri ne a cikinta game dake"

"Na gamaka da girman gurin da wanda ake bautawa a wajen ma dakata" ta sake fada daidai sanda ta hangi goumar yana nufo wajen,yana riqe da hannun BATOUL tana bashi labari,shima kuma da alama dukka hankalinsa yana kan batoul,saidai hango sultana da wani na biye da ita ya sanyashi dauke dukka hankalinsa a kan yarinyar ya maido kansu batoul.

Bata fasa sassarfar tsere masa idanunta nakan fuskar Goumar data tabbatar sai yayi mata shishshigi,kaman yadda bai fasa binta yana mata magiya ba,hakanan goumar bai fasa nufosu ba fuskarsa da idanunsa na nuna wani irin emotion.

Ta karanci abinda ke fuskar Goumar,kaman ma a fusace yake ainun,yau kam sai tayi maganinsa taga idan akwai abinda zai iya,don haka suna zuwa dab dashi ta dakata,ta kuma karantawa matashin Address na hotel harda number dakinta

"Na gode sosai,sunana suhail kefa?"

"Sultana" ta fadi a taqaice tana juyawa ta rabe goumar ta wuce.

Sai data fara nisa da gurin suhail ya maida dubansa ga goumar da yayi tsam ya zuba masa wannan idanun nasu me matuqar kwarjini da haiba irin na maina,idanun buzaye dake da wani irin sirri da kuma launi na daban.

A idanu suhail yaga suna kamanceceniya da sultana,saidai shi din baqi ne sosai kuwa akan kalar fatar sultana dake jazur kamar ta fito daha yankin larabawa,wannan kama da ya gani yasa ya miqa masa hannu yana fadin

"Assalamualaikum" girman kalmar da sanin ma'anarta kadai ya hana goumar qin miqa masa hannu. Ya bashi hannun,saidai kuma ya bar masa saqo yana fadin

"Ita din matar wani ne,kada kayi gangancin shiga gonar da ba taka bace,kada kuma kayi yunqurin keta dokar Allah" sosai sai jikin suhail yayi sanyi,amma a yadda karo daya yake jinta cikin kowanne sassa na zuciyarta daga kallon farko,sai yaji kalaman goumar basu shigeshi ba

"Ni jikina sam bai bani haka ba,idan ma kai din rival ne saidai nace maka kayi haquri na riga na kamu,ma'assalama" ya fada yana yin gaba.

Tun daga ranar sai goumar ya dauke mata wuta tsaf,ta daina ganin koda haqoransa,itakam hakan yafi mata dadi,don dama so take ya fita a sabgarta kuma ya fita din,takance a ranta

"Aikin banza aikin wofi,koshi wanda kakeyin abun saboda shi bai isheni kallo ba,bai kuma isa yace zai damu rayuwata ba bare kai"

Suhail kuwa tasha ganinshi a hanya ko cikin masaukin nasu da alama ita yake nema,saita bace masa kota koma har sai yabar wajen. A daidai lokacin lokacin ubangijinta kawai take dashi,ita kanta cikin zuciyarta taji nutsuwa da gamsuwar lallai tayi ibada iya yadda ubangiji ya bata iko,fatanta kawai ta zama karbabba,muddin kuwa ta karbun tayi imanin zata cimma dukkan nasara da kyautatuwar rayuwa.

Sati uku sukayi suka koma Paris ta rungumi karatunta,wanda babu abinda take gani sai budi da nasara,duk wani nasibi da budi data roqo akan karatunta tana ganinsa,karatun tamkar ana buda kwanyarta ana zuba mata shi,nan da nan kafin ma su kammala ajin farko sunanta ya fara yin fice cikin makarantar tsakanin dubban dalibai dake department dinsu.

Duk yadda takai ga janye jikinta da rashin son jama'a sai Allah ya bata farinjini sosai cikin makarantar,kowa ta zauna dashi dai ya qaunaceta,duk da miskilancinta bata iya wulaqanci ba sam,sannu sannu sai gashi ta fara dan sakewa da jama'a. Koda ba zatayi mu'amala dakai ba amma zata maka murmushi saman fuskarta,wannan sai ya sake zama abun burgewar jama'a a wajenta.

Tun wannan zuwan da sukayi sai zuwa umrar ya zame musu tamkar jiki kamar yadda aba yayi mata alqawari. Abun sai ya zama kaman ya tsara musu kanshi da kanshi,duk sanda suka samu hutun makaranta ita dasu benazeer to a saudiyya suke yin abinsu,suyi wata guda suna ibada sannan su dawo kuma a soma shirye shiryen komawa bakin karatu.

Ta riqi karatunta gam da matuqar muhimmanci,tana bashi dukkan lokacinta,saidai kuma hakan bai hanata ibada ko koyon wasu abubuwa da suka shafi rayuwa ba wandada tasan tana da naqasu ta bangaren,kaman koyon girke girke,hanyoyin kula da kai da kuma gyara kai da wata balarabiyar oman ke koya musu. Macace me baiwar sanin ilimin halittar diya mace,shiga ajin matar ya faranta mata ainun,don ya sake maidata wata irin 'yar gayu..... mace me aji,irin macen kuma da tasan kanta ciki da waje. Sai a sannan ta karanci ama cikin hikima. Wato ita ama ba'a banza ba ta fita daban a zuciyar aba,duk da cewa aure qaddarar wasu mazajen ce,to amma bata tunanin tana cikin qaddarar aba,wasu abubuwan ma da yadda take kula da rayuwarta da kuma kanta dukka sai yanzu hankali da ya game sultanan take karantarta,wasu abubuwan tayi qoqarin daukesu,wasu kuma su bata kunya.

Abinda bata sani ba ama din ta fita zurfin nazari sanya idanu da qwaqwqwafi,tuni ta fahimci sultana,sai bata nuna mata ba,amma itama saita sakata a nata ajin na yadda mace zata amsa sunanta mace a idanun mata 'yan uwanta dama maza abokan cudayyarta. Ta sake salute na ama,ba banza ba ta sake fita daban da faccalolinta,tun tale tale komai na ama dabanne,she's so classy,har kuma a yanzun dabi'arnan tana nan,shekaru da fara zuwan girma bai sanya ta canza ba.

Ta zame mata mentor sosai ta fanni da dama,ita kadai data kalla ya sake sanya mata sha'awar koyon girke girke iri daban daban. Ama din kamar half cast za'a kirata,uwa uba kuma ita din tayi zaman qasashe tun zamanin quruciya har zuwa yau,wannan ya sanya ta iya nau'ikan abinciccika kala daban daban,kuma da kadan da kadan sai da sultana da iya da yawa daga cikinsu.

*_KOMAI NISAN DARE gari zai waye_*


Cikin babban dakin taron dake mallakin makarantar,cike yake da dalibai irinsu sultana dake murnar amsar sakamakonsu na kammala karatun aikin jarida fanni daban daban,sai kuma manyan baqi iyaye da 'yan uwan daliban dake qasashe da kuma garuruwa daban daban cikin paris da wajenta.

Tana sanye da academic regalia data dora saman wani tattausan lace da ya lashe kudade masu ciwo da ama ta siya mata,ta kuma bayar akayi masa dinki me aji. Lite make-up ne a fuskarta wanda zaka iya rantsuwa da Allah ba komai saman fuskarta saboda nutsuwa da kwanciyar da kwalliyar tayi a saman fuskartata.

Tun daga takalmin qafarta har zuwa mini handbag da medium mayafinta idan akayi lissafi a qalla zasu tada jari me qarfi ga wani. Komai nata me sanyi da tsari,kaman yadda halittar ta take da daukan hankali da saukar da wani irin nutsuwa.

Siririn kwallin da aka sanya ma fararen qwayoyin idanunta da kuma red lipstick da ta shafa ya fidda mata wata haiba da kwarjini na musamman.

Tana zaune a inda aka tanada saboda dalibai,amma gaba daya hankalinta yana kan batoul da benazeer da aka yiwa kwalliya sosai cikin wata red gown da tayi masiiiifar kwanciya a lafiyayyar fatarsu da hutu da gata ya jiqa sosai. Sai kai kawo sukeyi suna 'yan guje gujensu tsakanin mutane,duk kuma inda zasu gifta din sai sunja hankulan mutane. Wasu su jasu suyi hotuna,wasu su basu qananun gift da ba'a raba baturen mutum dasu.

Kiransun da aka fara yi daya bayan daya ya sanya dole ta haqura da lura da kai kawonsu,duk da tasan idanun aba ama goumar harma da bibi da tayi tattaki tun daga nijer domin ganin yadda gudaliyar tata a yau zata karbi sakamakon da zai bayyanata a cikakkiyar 'yar jarida.

Sanda sunanta ya fita a cikin mic haka

Please Login or Register in order to submit comment