Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

masa kalmar gatse gatse,takuma sokeshi qwarai da gaske. Yadan cije lips dinsa,sannan ba tare daya dubeta ba yace

"I will slap you sultana......ni ba sa'anki bane,duk ranar da kika sake cewa you hate me ko?......" Sai kawai ya jinjina kai yana jin zuciyarsa tana motsawa

"Am just asking you me kikeso,saiki ce wani you hate me?.....ba rannan kin fada ba?,yanzun ma kin maimaita ko?,well.....karki maimaita na uku.......nima din na janye kalman i love you....i hate you..... shikenan?" Ya jefeta da tambayar yana dubanta.

Ko sau daya,koda wasa kuma bata taba kawowa a ranta zataji zafi idan ya gaya mata baya sonta ba,amma sai taji wani abu me tauri yazo ya tsaye mata a wuya kamar ma tana neman rasa numfashin shaqa

"So stop telling me......ina da wadanda suke sona,zanyi focusing a kansu.....now ki dauka kina tare da uncle dinki......nemi hijab ki saka muje,dole kibar musu gidansu yadda suka buqata" sai ya miqe kawai ya bude Wardrobe dinta.

Duk abinda yaga ya kamata ya dauka kawai yake dauka din,baima nuna yaji kukanta ba,har sai daya gama hada komai,yana daga tsaye ya fiddo waya ya kira goumar. Kamar me jiran kiran nasa ya dauka

"Qaraso ciki kazo ka fitarmin da kayan nan"

"Okay sir" goumar din ya fadi dadi yana cikashi. Wayar ya mayar aljihu ya waiwaya gefansa yana kallonta

"Idan kina zaton zan nema wani abu a wajenki ki daina wannan tunanin......zanje na kula da ajiyata.....idan kika sauke ya rage naki......yanzun na koma uncle dinki kamar baya,live your life.....banason na sake maimaicen magana dake,ki saka jilbab mu wuce" daidai nan goumar yayi knocking maina ya bashi daman shigowa.

Idanunsa akan sultana gulma tana cinsa,maina yana ankare dashi don yasan halin mutanen nashi,ya jefa masa harara yana masa nuni da kayan,sai ya dauke kanshi yana qusnhe dariya ya daga luggage din ya soma janta,maina ya kira shi ya waiwayo ya jefa masa key din motarsa ya cafe sannan ya juya yana ficewa.*_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 124


Idanunta akan gidan,ta tsammanin can zataga ya wuce amma sai taga ya nufi motarsa. Goumar da ya jima da sanya luggage din a ciki yana tsaye jingine da motar. Zai bude mata maina ya daga masa hannu,yasa hannunsa ya bude mata gidan gaba ba tare da yace komai da ita ba. Kai ta daga ta kalleshi,sai kuma ta maida dubanta zuwa ga cikin motar, zuciyarta na karyewa ta saka kai tana shiga,rauni yana ziyartarta,tana ji a ranta zai nesantata da kowa nata,ta yaya zata iya tafiya tabar ama?,ta yaya zata iya nesa da benazeer da batoul yaran da kwanan da suka dinga yi tare dasu a dan tsakanin ya haifar da wata mahaukaciyar shaquwa a tsakaninsu.

"Banyi sallama da ama ba,banyi sallama da aba ba,benazeer da batoul" ta furta muryarta na rawa,sabon kuka yana so ya qwace mata sanda ya shiga motar seat din driver yana niyyar rufewa. Sai ya fasa tayar da motar,Iska ya furzar yana dan buga steering motar da yatsunsa dake samanshi. Tausayinta yaji ya kamashi,sai ya sanya hannu ya bude murfin motar ya fiddo jikinsa waje gaba daya yana nufar qofar gidan da zummar komawa ciki.


*_ABA_*


Abu uku ke turereniya a zuciyar ama sanda take barinsu a falo tana bin sahun aba zuwa nashi falon. Na farko mamaki dariya kunya da kuma tausayin sultana,dukka sauran abubuwan kuma wa aba takewa. Lallai gaskiyar hausawa da suke cewa ba'a shaidar d'an yau,ta godewa Allah da bata zafafa da yawa cikin lamarin maina da sultana ba lallai tabbas da yau taji kunya,ta sake godewa Allah da aba yabar batun raba auren,inda ya kafe akan hakan Allah ne kadai yasan me zai faru. Cikin biyu dai dole ayi daya,ko ayi cikin a waje wa'iyaxubillahi tunda dai rabo ya rantse,ko kuma aba din ya rasu kuma suci gaba da zaman aurensu.

Dariya ta kusa subuce mata sanda ta isa falon ta sameshi dirshan tsakiyar jikokinsa yana aikin bare musu sweet,abinda duk soyayyarsa da yara baya jurewa,zai dai siya,amma saidai ama goumar ko tanja suyi aikin budewa,yau sau gashi da bare leda ya kusa nawa,idan ya barewa batoul sai ya barewa benazeer. Ya amsa sallamarta yana daga idonsa a kanta,suna hada ido wata dariyar tazo mata saita kauda kai kaman tana neman wajen zama.

Jinjina kai kawai yayi qasan ransa murmushi yana subuce masa,ya sani,dariya take masa,kuma bama ita ba duk wanda yaji zancan shi da ya zaqe da yawa cikin lamarin zai fara yiwa dariya.

"Ku dauki ragowar kukai tanja ta boye muku.....ta saka muku house wear a cire wannan kayan" aba din ya fada yana tattara musu tarkacensu.

Sanda suka fice sai falon yayi shuru daga ita sai shi,sai aka koma satar kallo tsakaninta da shi. A karo na kusan ashirin da suke satar kallon juna daga qarshe suka kama juna,dole murmushin ama me sauti ya fita tana danne dariya kada ta biyo baya

"Aba....how far?" Tayi maganar tana kashe ido hadi da maqe murya. Dariya dole ta kamashi shima

"Hamdi ni kikewa dariya?"

"A'ah,aba ai dole nayi dariya,kaga aikin 'yan zamani ko?"

"Na gani hamdiyya,me na isa yanzu nace?,shi yasa nace ya tattara matarsa su tafi,bansan kuma da wanne ido zan sake muzurai da cika baki akan 'yar marainiyar da naketa haqilo ba"

"You learn a lesson aba......tsakanin miji da mata fa sai Allah,ma'auratan da dukka sun balaga harda 'ya'ya a tsakaninsu,haka kawai sai a turke kowannensu kamar dutse?" Murmushi yakeyi yana girgiza kai

"A'ah......ni na tabbatar daga yadda diyata ke kuka fin qarfi yayi mata..."

"Rape still?,wallahi aba wannan karon bazan yarda a jefawa dana kalman fyade ba,wancan karon nayi kawaici......amma dis time around nima murje idona zanyi......ahaaan......sanda suka daidaita kansu da inda suke jonewa ma baka sani ba aba,amma kazo kana yabonta.....saifa bango ya tsage qadangare yake samun wajen fakewa" ta fadi tana shan mur kamar da gaske.

Dariya sosai ta bawa aba,abun dukka sai ya juye masa nishadi musamman idan ya tuna wai BB nada qani ko qanwa a hanya.

"Maida wannan dogon hancin naki kada ya tashi sama.....wait......ashe dama baki da kara har haka hamdiyya?"

"A nan dai bani da aba.....,yarinya ta kawo maka result.... Ina laifin ma a yabawa d'ana shima?" Dariyar da tafi ta dazu ama ta bawa aba

"Fitinannen dankin nan ba,shekaru shidan da suka wuce da suna tare na tabbata for now mun gani da daukan jikoki ko?" Sai a nan kunya tadan kama ama,ta kauda kai tana dariya qasa qasa gami da cewa

"Oho.....koma dai meye,Allah dai ya sakawa Bibi da alkhairi"

"Ameen ya hayyu ya qayyumu "aba din ya fadi yana jinjina abun qasan ranshi. Wato wani irin rabo ne me zafi a tsakaninsu wanda duk idan ya tashi zuwa baya zuwa da sauqi,ya godewa Allah da rabon baiyi ajalinsa ba. Ama na zolayarsa yasan amsar da zai bawa mutane batoul ta dawo.

"Ama wai kizo" kaman zata tambaya waye sai kuma ta fasa,ta miqe tsam tana bin bayan batoul suka fito.

Yana tsaye tsakiyar falon hannayensa goye a bayansa. Suka hada idanu da ama,yau din shima sai yaji kunya ta dabaibayeshi,yadan yi qasa da kansa,ama din ta gyara tsaiwarta tana hade rai

"Meye kuma?" Kanshi ya sake dagawa a karo na biyu,saidai kuma ya gaza hada idanu da ita,ya karyar da murya yana cewa

"Ama.....kuka take,tace ba zata tafi ba bakuyi sallama ba" tausayin sultana din ya saukar mata,tasan halin d'a namiji,bata kuma cire har d'an cikinta ba,sun qware wajen iya yaudarar diya mace da kalamai,sun muma qware wajen karyo dake su samu biyan buqatunsu idan suka so komai kafiya zafin kai da jajircewarki,ballantana sultana......sultanar da take tashi......sultanar da jinin jikinta ya gaurayu da nashi,sultanar da tayi amanna koda wanin maina ta aura a rayuwarta zai wuya yayi controlling nata yadda maina zaiyi,ta zama shi ya zama ita......kominsu daya ne.....girma da sauyin dabi'unta ya kawo jirkicewar komai a tsakaninsu.

Hijab dinta dake aje saman kujera ta dauka ta zura tayi gaba ba tare data ko kalleshi ba,sai yaji dadi ya saukar masa ganin tayi accepting abinda yakeson gaya mata tun kafin ma ya gabatar mata dashi. Bai bita ba,sai ya doje daga bakin qofar gidan,yana kallon ama sanda ta isa gaban motar ta sanya hannu ta bude murfin motar ta shige.

Sanda taji an bude motar ta dauka shine,don haka tayi banza da ranta tana ci gaba da rera kukanta. Zama sosai ama tayi a seat din driver din tana kallonta. Qamshin turaren ama ya fallasata,saita daga kai da sauri,suna hada ido da aman ta gaza ci gaba da kallonta saboda kayan kunyar da takeji ta debo

"Au.....kuka kika zauna kinayi?,cikin shege kikayi ne sultana?" Maganar ta sanyata maido dubanta kan ama,tanason ta tabbatar da gaske ama bata dauki wani abu ba?,da gaske ba komai bane wajen ama din.

"Ko bashi da uba yana da kaka,auren sunna ne har abada tsakaninki da haidar haka ne?" Wani sanyi ya soma sauka mata cikin zuciya,ta shiga gyada kai hawaye na sake yawa cikin idanunta.

"Ki goge hawayen muyi magana ko na fita na barku" da sauri taja gefan hijabinta tana goge idanun nata tare da tattarawa ama hankalinta.

Tun maina da suka shanya a waje yana kallon motar har ya koma kallon agogon hannunsa yana irga lokaci.

"Wannan maganan yayi tsaho" ya sake fadi a karo na kusan biyar. Goumar yana gefe dariya kaman ya kasheshi,wai dama haka ya mainan yake mutuwar son sultanarshi?,da gaske irinsa dama soyayya haukatasu takeyi a mafi yawancin lokuta?.

"Goumar....ko zaka......" Sai kuma abinda zai gayawa goumar din ya yanke ganin ama na fitowa daga motar.

Tun kafin ta qaraso ya miqe yana jiran isowarta,gaba daya ama din ta zame masa wata boss. Tana isowa goumar ya matsa ya basu waje

"She's pregnant ka sani,akwai wasu canje canjen halaye wajen me ciki.....saurin fushi yawan kuka duk zata iya fuskantarsu,cin abincinta ya qaru,kowanne lokaci tana iya buqatar abinci......gata nan kaman ajiya ce.....kada kaga ance ka tafi da ita ziqau ka dauka ruwa tasha ko kaci bulus.....da sauran gatanta,kuma komai na 'yar gata zamuyi mata kaman kowacce mace.....cikin jikinta ne kawai zai kawo tsaikon wasu abubuwan....."

"Na shiga uku ni maina" ya fadi qasa qasa

"Baka shiga uku ba saika kasa kula da ita" ama ta bashi amsa idanunta cikin nasa

"Bamu hanaka saitata ba......da qin biyema kuskurenta ko son zuciya,tsawatarwa duk yana da kyau......amma ta yanda ya dace....ka cika mata zuciya da soyayyarka......banason na haifi d'an da mace zata kasa mutuwa a soyayyarshi" ama din ta fada kanta tsaye. Mutum ce me matuqar son soyayya,tana martaba soyayya saboda tasan dadinta. Yana daya daga cikin dalilan da yasa ko mutuwa take fata ta fara daukanta ko ta daukesu tare da aba..... namiji da tasan an jima ba'a yi kama tasa ba cikin duniyar iya nunawa matarsa soyayya.....girma shekaru ko tsufa basu sanya ya wofantar da hakan ba......ba wasu shekaru da suka dakushe salon nuna mata kulawa da yakeyi ko kuma soyayya,wannan ya sanya kullum kwanan duniya aba yake na daban a zuciyarta dama rayuwarta gaba daya

(Zuciyar mace 'yar son soyayya ce,komai tsufa da shekarunki kinaso kiga mijinki ya mato a kanki,yana tattalin farinciki da baki lokacinsa da dukka kulawarshi,ba abinda yakai wanann morewa a rayuwar mace).

Yana murmushi yana dosar motar,indai ta fannin winning zuciyar mace ne yayi winning zukatan matan da ba soyayya ne ya hadasu bama ina ga sultana......a nan koda sakewa sultana yayi yace tayi rayuwarta,yayi imanin ba zata taba kubuta daga sharrin tsumammiyar soyayyar daya dasa mata ba.*_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 125


A nutse ya shiga motar,yayi bismillah ya kunnata,ya tasheta suna fita a layin sannu a hankali.

Cikin motar ya dauki shuru,ba kuka takeyi ba,amma kuma baya iya ganin fuskarta,ta cure waje daya kaman maijin sanyi,wannan ya sanyashi miqa hannunsa ya kashe ac din motar gaba daya,ya kuma sake dage glass din sama.

Tana iya jin kowanne motsi nashi kaman yadda qamshin turarensa daya cika motar yake shiga hancinta cikin kowanne numfashi da zata shaqa. Idanunta ta dinga lumshewa,tana mamakin yadda takejin matuqar dadin qamshin fiye da kowanne lokaci. Maganganun da sukayi da ama suna dawo mata daya bayan daya tana sarrafasu cikin kanta. Bata taba tunanin haka ama ta shahara wajen kara ba......haka ama ke kallonta dama?,amma koda a motsin 'yan yatsunta bata taba nuna mata komai ba..... kullum tana bayanta.....kullum goyon bayanta kuma takeyi,hakanan kullum farincikinta takeso.

Duka duka tafiyar minti goma ya bulla wani titi,titi ne dake dauke da wadatar shops iri iri da ke saida abubuwan buqata iri daban daban. Ya ganganara muhallin da aka kebance don yin parking ya ajjiye motar a hankali sannan ya kasheta,ya zare key din,yadan waiwaya ya kalleta. Har yanzu taqi kalonsa,taqi juyawa sashen da yake gaba daya.

"Zaki magantu,zakiyi bayani" ya fadi qasan ransa yana tunanin me ama ta gaya mata haka da ya tsaida kukanta a lokaci guda haka?.

A nutse ya bude murfin motar ya fice,saita samu kanta da satar kallonshi. Yadda yaketa dake mata da yadda fuskarshi keson koma mata aliyyun nan na maradi ke bata mamaki

"Hey madam.....gani ta nan" taji an fadi daga gefanta. Juyowa tayi ga mamakinta yana ta bakin window din da take zaune. Suka hada idanu saita dauke kai don nashi idanun duka suna kanta. Ita batasan ya zagayo ba,da ba yadda za'a yi tabi bayanshi da kallo.

Rumfa taji ya mata gaba daya,ta daga idanu a dan tsorace tana tunanin me zaiyi mata?. Oily eyes dinta suka hadu da lion eyes dinsa suka sarqe waja guda. Tana jin dumin numfashinsa sosai yana sauka saman fuskarta yana kuma gogayya da nata numfashin. Hannunsa ya miqe yana sauke mata kujerar sosai yadda zata iya jingina ta huta yadda ba zata takura ba,faffadan qirjinsa yana gugar nata a hankali,ya lumshe idanun nasa yanayin numfashinsa yana sauyawa. Shi kadai yasan idanunta kadai ke iya illata dukka jarumtarsa.....ina ga kyakkyawan jikinta dake dauke da wani irin sinadari dake kassara duk wani qwarin gwiwa nashi

"Bi a hankali 'yammata,idanuna basu da kyau......kince baki sona.....so ina baki shawara karki yarda ki fada tarkon so na" yayi maganar softly kaman me rada. Kanta ta kawar gefe saboda yadda zuciyarta ke wani irin bugawa. Tana iya jin sautin fitar murmushinsa,ya miqe yana maida mata qofar ya rufe

"Mugu" ta fadi cikin zuciyarta tana lumshe idanunta,qamshinsa yana sake sanya mata nutsuwa a ranta,maganarta da ama tana sake kwantar mata da hankali,duk quncin da take tunanin shiga tana jin babu kaso hamsin cikin darinsa.

Duka duka bai wuce mintuna ashirin ba taji ana bude butt din motar. Ta glass din motar take hango sanda ake zuba siyayya a ciki,ya sallamesu ya dawo ya tayar da motar.

Tafiya suke a nutse kaman bai shirya zuwa inda zasuje din ba. Sun kusa mintuna talatin saman hanya kafin su isa inda suka nufa din.

Daya daga cikin unguwanni ce dake dauke gine gine masu irin wani fasali dake da ban sha'awa kaman cikin qasar turkey. Idanunta qasa qasa amma tana kallon unguwar da duk wani tsari da yanayinta me kyau. Kaman ko ina cikin qasar,itama a tsaftace take cikin tsari,sannu a hankali har ya isa qofar wani madaidaicin gidan dake da madaidaiciyar harabar me qananun katangun da kana iya hangen ainihin ginin gidan dake tsakiya,harabar da aka qawatata ainun kamar wani qaramin garden.

Da kanshi ya sauka ya bude motar,sannan ya saka wani siririn key ya bude gajeran gate din,sannan ya dawo ya shiga da hancin motar ya kuma ajjiyeta daga hannun hagun harabar inda aka saka qaramar rumfa mara girma don ajiye motaocin da bazasufi biyu zuwa uku ba.

"Alhamdulillah" taji ya furta cakude da fitar numfashinsa yana zare key din motar.

A nutse ya ciro wayarshi,yadanyi danne danne sannan kuma yayi kira. Cikin qasa da second biyar aka daga kiran. Kiran sunan suhail da yayi ya tabbatar mata suhail ne

"No...je n'ai besoin de rien(bana buqatar komai)" ya fada a taqaice

"Near Rue de rivoli" ya sake fadi. Dan satar dubanshi kadan tayi,ta fahimci kaman yana gaya masa adress na unguwar ne,don a hanya taga symbol na wannan sunan,saita mayar da kanta gefe. Zuciyarta na qiyasta mata wanne bigiren kuma rayuwa zata kaita yanzu?,a ina rayuwa zata ajjiyeta?,ta yaya zata zauna dashi?,yaya zasu rayu?,a matsayin miji?,ko a matsayin yaaya kaman yadda yayi iqirari?.

Tana jinsa ya bude motan ya fita bayan ya gama wayar,da idanu dai take ci gaba da satar kallonshi har ya isa qaraman veranda,ya sanya maqulli ya bude qofar da zata sadaka da ainihin cikin gidan ya shige.

Ko ina lullube da duhu,sai ya dinga takawa a hankali yana kunna kowacce fitila ta gidan.

Ko ina na gidan tsaf yake kuma fes kaman yadda ya zata,don ya ajjiye me kula dashi na musamman duk bayan kwana bibbiyu. Sai daya gama zagaye ko ina ya tabbatar komai yana kan order sannan ya dawo tsakiyar falon. Yayi tsaye hannayensa cikin aljihun wandonshi yana kallon babban hoton benazeer da batoul da ya mamaye kusan rabin bango ga tsaho ga fadi kamar zasuyi magana. Saidai kuma ba ainihin photo bane,qwararren me zane ne ya zanasu irin zanen da kana kallon frame din kawai kasan yaci kudi bare akai ga farashin zanen kansa.

Wani irin tsarin gini me matuqar tsari da dukan hankali aka yiwa gidan. Gida ne daya ginashi da guminsa da kuma jinin jikinsa. Gida ne daya ginashi tun bai sanya ran ci gaba da rayuwarsa kaman kowanne mutum ba,kamar yadda hoton dake maqale a bangon hoto ne da aka zanashi tun baisan benazeer da batoul mallakinsa bane.....jininsa bane ....kuma 'ya'yansa bane. Tsananin soyayyar da yakewa yaran ya sakashi aka masa zanen ya sanya a cikin gidan da ko sau daya bai taba kwana a cikinsa ba. Sardauna yasha tambayarsa me zaiyi da wannan gidan da har ya kashe maqudan kudade don ya mallakeshi a qasar da ba tasa ba?. murmushi kawai yakeyi,don shi kansa a lokacin baisan me zaiyi dashi din ba,saidai kuma zuciya da gangar jikinsa suna yawan gaya masa ya gina gidanne don iyalinsa

"Wanne iyalin?,iyalin da babu su?" Sai wani sashe na zuciyarsa ya tuhumeshi da wannan,saidai kuma bai taba sarewa ba......yau gashi ashe akwai ranar da wannan tunani nasa zai cika.

Gidan yasha burgeshi shi a karan kanshi,yasha jin kaman ya kwana a gidan.....amma kuma hakanan sai yaga bai cancanci kwanan a ciki ba. Gini ne daya dace da dukka tsarinsa da yanayin rayuwarsa,don ko suhail ma bai taba zuwa gidan ba.

Juyawa yayi a nutse yana fita a falon bayan ya kashe dukka ac din gidan,don ya fahimci kaman sanyi yana takurata.

Yana fitowa ta maida idanunta ta rufe,ya ganta amma sai yayi shima kaman bai gani ba,don yasan meye ya shirya mata,ya saka hannu ya bude murfin motar,sai kawai ya zura jikinsa gaba daya ya daukota cak daga cikin motar.

Tsoro ya kamata sosai irin tsoron da yaro kanji a sanda babba ya daukeshi yana gudun kada ya yada shi,ba tare data shirya ba ta saqalo wuyansa da duka hannayenta tana zaro idanu waje zuciyarta kuma tana karyewa.

"Shshshs" yace da ita ba tare daya kalli idanunta ba,don yasan me yiwuwa dole tace wani abu. Kanta tayi qasa dashi,tana tuna alqawarin data yiwa ama ba za tana musu ba don yanzun matsayin yayanta kuma uba yake a gareta,tsohon matsayi ne da bai canza ba yanzun ya dawo sabo.

A nutse ya dinga wuce gurare har sai daya dangana da daya daga cikin bedroom din. Dream bedroom dinsa ne a duniya ya tabbatar da wanzuwarsa a wajen. Ya kashe kudade ba qananu ba wajen ganin bedroom din ya zama kamar yadda yake a yanzun. Saidai ko sau daya bai taba iya dogon zama a ciki ba,saboda duk inda ya juya yana reflecting masa rayuwar auren da a wannan lokacin bashi da wanda zai tayashi rayata. Yana da tsananin kamun kan da ba abinda ya tsana irin zina,don haka ya nisanci dakin gudun galabar shedan.

Duk da idanunta suna kulle amma suna shiga dakin ta tabbatar ta shigo wani guri na musamman daya banbanta da duk guraren da suka gilma cikin gidan.

Saman wata zagayayyr sofa ya ajjiyeta wadda ta nutse sosai saboda laushinta. Bai tsaya ba ya juya yana ficewa a dakin.

Taji alamun fitarshi wannan ya sanyata bude idanunta a nutse tana qarewa dakin kallo.

"Ma sha Allah" ta fada a zuciyarta duk yadda take basarwa. Iya canopy bed din dake dakin kadai ya isa ya sanya maka sha'awar kayi bacci. Ta gama bin ko ina da kallo,ko ina din yana burgeta.

Har yanzu maina din na dabanne,ba abinda ya sauya nashi saima sake gaba da yayi. Yasan me gayu yake nufi kaman yadda tsafta da ado suka zame masa jinin jikinsa,yadda ya fita daban a family din MAYAK'I haka ya fita daban da dabi'unsa dama komai nasa.

A qalla mintuna arba'in yayi kafin ya dawo,duk lokacin nan tana jiyo motsinsa a can babban falo,wanda daga shi zaka taras da

Please Login or Register in order to submit comment