Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

izza isa da iko.

Hannu ta sanya ta tattare dukkan abinda ke saman gadon,kama daga zanin gadon da ya gama baci da jini zuwa pillow din da tuni ya zame daga cikin gidansa, blanket dinta da shima jini ya taba,sai kayan sawarta da suka gama zama tsumma.

Sanda take rungume da zannuwan gadon zuwa toilet din sai taji zuciyarta tayi nauyi,data waresu cikin toilet din ta fara wankesu kuwa dukka qwalla da zafin da zuciyarta keyi wanda taketa riqewa sai ya gaza riquwa. Wata siriryar qwalla tabi ta gefan idanunta tana bin jinin da kallo,tausayin sultana ya tsargama zuciyarta irin wanda bata taba ji ba. Wannan zallar rashin imani aliyyu ya gwada mata,wanne laifi tayi masa da zafi haka daya zabi yiwa rayuwarta wannan ta'addancin?,ba zata qyale maina ba koda kowa kuwa zaice a daga masa qafa. Zaiyi wuya a yawan jinin data gani jikin zanin gadon yarinyar bata buqaci qarin jini ba. Cikin raurawar zuciya ta dinga wanke zanin gadon zuwa blanket din,abinda tsahon rayuwarta bata taba yi ba da hannuwanta.

Cikin mintuna arba'in ta kammala wankesu tas duk kuwa da nauyinsu,ta koma ta kintsa dakin shima tamkar ba hamdiyya abdu me kano ba. Tana kammalawa bibi na turo qofar dakin,sai ta saki siriryar boyayyar ajiyar zuciya da bibin bata isketa tana tsaka da wanke kayan da haidar din yayi aika aikarsa akai ba.

*_wanda bai samu guri a HUGUMA CLOSET ba yayimin magana na sama masa 08187255862_**_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

*BOOK 02 PAGE 03*
_______________________________

*_Shin kin isa mace?,don magana akeyi ta ISASSUN MATA_*

*_SUTURA ABAR TUNQAHO_*

*_Ado da kwalliya shine cikar 'YA MACE_*

_Magana akeyi ta_

*UMMU MAHNOOR LUXURIES*

*UMMU MAHNOOR LUXURIES*

_GIDAN QAWA ADO NA KECE RAINI_

*_INA AL'UMMAR KADUNA ABUJA SULEJA DAMA NIGER......HAR MA FADIN NIJERIA GABA DAYA_*

*_KIN SHIRYA FITA KUNYA?_*

*_MAZA HANZARTA KI LALUBI KALOLIN SUTURAR DA TA DACE DAKE,KAYAN ADO MASU_*

*KYAU*

*QUALITY DA DAUKAN HANKALI*

*LACES NE,SHADDA CE,ATAMFOFI NA 'YAN QWALISA*
*GA KUMA DESIGNERS TAKALMA DA JAKANKUNA NA ALFARMA DA FITA KUNYA*

*_ZAKU IYA SAMUN MAMALLAKIYAR KAMFANIN KAI TSAYE TA WANNAN NUMBER WAYAR_*

08135142610

*INSTAGRAM* UMMU_MAHNOOR_LUXURIES

*FACEBOOK* MUSA GARBA SHIFA

*_Ga wadanda ke cikin garin abuja kuma zasu sameta kai tsaye a_*

*_system property Nefelix estate,near amasco,galadimawa roundabout_*

*_KARKI BARI A BAKI LABARI,KARKI KUSKURA KI ZAMA 'YAR KALLO_*

*TASTED AND TRUSTED*👌👌👌
_______________________________



Ido suka hada da bibi,dukkansu sai aka rasa me cewa dan uwansa wani abu,duk kuwa da cewa alamu sun nuna kowanne bakinsa cike yake fal da maganganu.

Qarasowa bibi tayi ta zauna tana duban ama,ba tare data buqata ba ama ta sulale ta zauna aqasa tana duban bibi

"Har yanzu kunqi yimin cikakken bayanin meye maina ya yiwa sultana?"

"Ya karbi budurcinta ne bibi ta qarfin tsiya" ama ta amsa mata kai tsaye kanta a qasa tana me matuqar jin nauyin bibi din,don babu magana kwatankwacin hakan data taba ratsawa a tsakaninsu,uwa uba babu wani buqatar ci gaba da boyewa bibi din,don kuwa me afkuwa ta riga data afku.

Dif bibi tayi tana juya abun cikin ranta,duk da ta riga ta gama hasashen komai cikin ranta da zuciyarta

"Bansan da wanne baki zan fara neman gafararki ba bibi...." Katseta bibi din tayi ta hanyar daga mata hannu

"Daga haidar har sultana waye bare?,waye zan ware nace ba nawa bane hamdiyya?" Ta fada da wani irin tune na sarewa da sanyin gwiwa

"Ni babu abinda zancewa da ubangiji na saidai ALHAMDULILLAH har da ya haskamin,ya kuma hanani nutsuwa sai dana tabbatar na maida sultana halalinsa. Yau inda ace ita din ba halalinsa bace ya aikata mata hakan nayi imanin zuwa yanzu wala'alla ina kushewata......saidai duk da hakan......." Ta fadi daga qarshe muryarta na karyewa da wani irin yanayi

"Duk da hakan abinda yayin banbancinsu kadan da fyaden bibi......sultana nawa take bibi?,duka duka shekarunta nawa?,a musulunce ya kamata a nufeta a haka?,bibi....... kinsan dinki nawa aka......" kasa qarasa tayi saboda yadda zuciyarta ta karye hawaye ya sake tsargo mata a karo na biyu.

"Akul......kul kika sake bari hawayenki ya fita akan wannan batun,idan ba haka ba zamuyi mugun samun sabani ni dake,kin manta masifar hawayen uwa akan d'anta?" Bibi ta gada a hargitse kuma cikin gigicewa.

Ba aliyyu takewa kuka ba sam sam sam, a'ah tana tuna girma da masifar zafin stitches ne koda jikin babbar mace bare sultana da duka duka bata wuce raino ba.

Sau uku tana zirya sashen maina don ganewa idanunta ko ya shigo gidan kafin ta fita amma bataga alama ba,haka ta shirya duk wani abun buqata ta dauki daya cikin masu aikinta da driver dinta suka koma asibitin.

A hanyar komawar dai duk sammakal,tunda ta zauna cikin motar zuciyarta ta lula a tunani. Fuskar aba take hangowa kawai,har ta fito daga gidan babu wata magana data hadata da shi,ta tabbatar kuma abunne yake dukansa kamar yadda yake dukanta.

Cikin qanqanin lokaci moudu driver ya sauketa cikin asibitin. Shi ya fiddo komai da tazo dashi. Abinci ne tasa zunnira ta shirya cikin qananun warmer's masu kyau,saboda batasan sanda sultana zata farka ba,kada ta farka cikin dare ta kuma buqaci abinci,sai kuma kayan sanyawar sultana din da wasu qananun kayan buqatu nata.

"Idan ba damuwa kaje ka shirya ka dawo,ina da buqatar ka kwana cikin asibitin tare damu,don bansan meye zai iya tasowa ba na gaggawa" tace da moudu sanda ya gama kwashe kayan tsaf ya shigar mata dasu ciki,ta furta maganar tana fiddo kyawawan qafafunta dake sanye cikin wani rufaffen takalmi maras tudu

"To ba damuwa ma'am in sha Allahu" ya amsa mata a ladabce.

Akwai taqaitar zirga zirgar jama'a sosai cikin asibitin,abinda ke alamta maka cewa lallai dare ya soma tafiya. Cikin wani irin kasala mutuwar jiki da rashin jin dadi jiki da kuma na zuci take takawa har ta isa dakin.

Ta iske qwararrun nurses biyu zaune a dakin,suna hirarsu qasa qasa ta yadda ba zata damu mara lafiya ba bare ta tadashi.

Sunfi kowa sanin ita din wacece cikin qasar nijer,don haka girmamawa ta musamman suke bata. Sannu tayi musu cikin halin sauqin kanta idan taso,suka amsa mata,sannan suka sake duba komai,kama daga file din sultana,ruwan dake shiga jikinta da sauransu suka tabbatar komai yana kan order

"Zamu wuce ma'am,duk abinda kk da buqata akwai waya da zaki kira(ta fada tana nuna mata inda wayar take a girke)"

"merci(na gode)" ama ta furta idanunta akan sultana

"c'est bon" suma suka maida mata amsa sannan suka nufi qofa suna mata sallama.

A hankali ta matsa gaban gadon tana sake dora idanunta akan fuskar sultana. Kyakkyawar baby face dinnan,wadda bata rabo da tsiwa da rashin kunya gaba daya ta canza,qaramin bakinnan da baya rabo da murgude murgude yau din gaba daya a kumbure yake. Kyawawan idanunta masu wani irin maiqo kaman an diga ruwa a yau din ba sosai kake hangosu ba saboda kumburin da gefansu yayi. Wani abu taji ya motsa zuciyarta,karo na babu adadi taji abun ya sake taba zuciyarta sosai. Inda ace saddi mace ne kwance haka cikin wannan halin wani d'a namiji yayi masa haka ya zataji?. Tambayar data sanyata jawo kujera ta zauna sosai gaban gadon tana ci gaba da kallon fuskartq zuciyarta kuma na hakaito mata yadda abun ya gudana tsakaninsu,wani nauyi na sake sauka mata a qirji. Fuskar nafessa take hangowa

"Ya rabbbb.....kada ka kamani da laifin gudun qaddarar da nayi,ya ilaheee ASTAGFIRUKA" ta furta a fili saidai can qasa hawaye suna cika idanuwanta.

A hankali sai zuciyarta da kuma tunaninta suka fara komawa baya suna mata tunin wasu abubuwa da suka faru shekarun baya da suka shude.

*_WANNE QULLI NE ZARGE QARQASHIN WANNAN IYALI DAKE DADADADDEN TARIHI?,SANIN KOMAI DANGANE DA TARIHIN WANNAN AHALI SHINE TAMKAR MADUBI HASKE KUMA FITILA TA LABARIN GABA DAYA_*


*_WHO DIED? WHO LIVES?_*


*_MUHAMMAT MAYAK'I_*


Dattijon arziqi shine sunan da jama'a da yawa ke kiransa dashi cikin ainihin mahaifarsa dake qasar nijer garin AGADEZ. Garin da ya zama tushe kuma makafar buzayen dake qasar nijer din.

Babban family garesu wanda yayi tambari sannan yayi suna ta fannin ilimi siyasa da kuma arziqin kansa. NADEEYA na daya daga cikin mutanen da suka sake sanya sunan family din MAYAK'I yayi shuhura. Qasaitacciyar 'yar boko 'yar kasuwa,wadda Allah ya huwacewa baiwar kwanya basira da iya sarrafa rayuwa. Gefe guda kuma tana daya daga cikin matan da koda cikin buzaye kyawunsu na dabanne. Wani irin kyau da akayi ittifaqin har xuwa yanzu shike bibiyar jininta,'ya'ya da kuma jikokinta. NADEEYA din ta fita daban,saidai a yanzun za'a iya cewa HAMDIYYA ABDU ME KANO wato AMA ita ke biye da sawayen NADEEYA da dukka tarin wadannan abubuwan da nadeeya din ta mallaka tamkar dama can ama ta fito daga tsatson nadeeya dinne. Saidai Sam,ita kanta ama batasan nadeeya da idanu ba wadda su aba ke kira da granny saboda ita din kaka ce a wajensu.

Ko cikin mata nadeeya ta dabance,wanann ya sanya ake tunanin ya zame mata kambun data riqa wanda ta zauna gaban Bobbi wato kakansu aba ita daya tal!,har zuwa lokacin da bobbi din ya rasu ya barta. Ita daya taci gaba da kula da 'ya'yanta cinsu shansu karatunsu har zuwa tarbiyyarsu. Allah ya albarkaceta da yara maza ne gaba daya su biyu,tayi mata sau biyu suna rasuwa,duk yadda takeson ta ganta da 'yar budurwa haka ta haqura. Allah ya raya mata yaranta rayuwa me kyau. ABDALLAH shine babban d'anta da ya zame mata gishiqi kuma madogara,wanda ta dora bisa dukkan wasu hanyoyi nata saboda halin rayuwa. Ya kama kuwa fiye da yadda ma takeso,wannan ya kwantar mata da hankali,saidai duk da haka bata nutsu ba har sai data tabbatar ta aurar dashi shi da me binsa wato ABDURRA'UF.

ABDALLAH ya auri bibi nana halimatou asalin bafulatana kuma buzuwa 'yar asalin garin AGADEZ. Kafin ya samu daukar halimatou bibi yasha fama a lokacin saboda wani irin farinjini Allah yayi mata,hakan kuma itama baya rasa nasaba da zallar kyau da Allah ya huwace mata,uwa uba tana da wata irin nutsuwa kamun kai da cikakkiyar tarbiyyar da takai duk yammatan unguwarsu idan an tashi kwatance da ita akeyi musu.

Gida guda nadeeya ta gina musu ita da yaranta,saboda tana da sha'awar su rayu tare. Wani irin gini tayi musu mahadi ka ture,ginin da saidai gidan sarakuna da manya manyan attajirai irinta.

Rayuwarsu na tafiya kaman yadda nadeeya ke buri,tsufa yana dada kamata,amma kulawar da take samu ya sanya take da cikakkiyar lafiyar da ciwo dai saidai irin wanda me dattijan da shekaru suka soma musu rubdugu basa rabuwa dasu.

A hankali bibi ta soma hayyafa,saidai faccalarta aseeya har zuwa lokacin shuru. Ba wanda ya daga mata hankali ko ya daga nasa hankalin,saboda dukkansu masu aiki da ilimi ne.

Dukkan me rai mamaci ne,sanda bibi keda yaranta maza har guda shida a lokacin ajali ya saukarwa granny nadeeya,lafiya lau akayi sallama da ita da dare ta tafi ta kwanta aka wayi gari babu ita. Sunyi kuka,sun kuma shiga tashin hankali sosai,saboda tsanani sabo da shaquwa da kulawar da suke samu daga yaran nata har jikokinta. Tayi masifar dasa musu wata irin qaunar juna a tsakaninsu,bawa juna kulawa da damuwa da damuwar juna, dabi'ar data bi jininsu qwarai da gaske,ta kuma zarce cikin jikin jikokinta har zuwa sanda suka zama cikakkun samari.

MOHMOUD da HAMIDOU sune yaran da bibi ta haifa da tazarar shekara hudu a tsakaninsu,batayi haihuwa ta uku ba kuma sai data shekara biyar ra haihuwar HAMIDOU(ABA) sannan ta haifi MUHAMMAT,sai oumar bashar sannan issoufou autah.

Babban tashin hankalin da suka fuskanta bayan rasa nadeeya shine na rasuwar mahaifinsu alhaji ABDALLAH wanda gaba daya sunansa yafi fice da sunan kakansu na ainihi wato MAYAK'I. Rasuwar da tayi mugun girgiza su,ta kuma daga musu hankali,don shi dinma kamar dai nadeeyan,babu wani ciwo,face dai tunanin da suke rasuwar mahaifiyar tasa ya maqale a rai har ta zame masa ajali. Hakanan cikin wani irin ciwo da rashin rabo sukaci gaba da rayuwa,cikin rashin jin dadi da kuma walagigi saboda basu saba rayuwa haka ba su kadai,don kuwa a sannan baaba ABDURRA'UF yayi nisa da agadez,bama agadez ba gaba daya nijer,tun bayan rasuwa granny da aka bashi gadonsa ya lula duniya fatauci.

Tun bayan tafiyarsa sai matsalolin rayuwa suka dinga taso musu,wadansu mutane sabbin fuska da basusansu ba,kowa yazo zaice yana bin nadeeya ko abdallah abu kaza,sai sunyi duba da wani abu me qwari cikin dukiyarsa suce yayi jinginarsa a garesu. Babu wanda bibi ta tsaya ja'inja dashi,ta barsu kawai,a sannan mohmoud yaso ya taka birki duk da kwata kwata shekarunsa a sannan basu goma sha biyar ba amma bibi ta hanashi

"Zukatan mutane a yanzu sun qeqashe da son abun duniya,komai na duniya a nan aka sameshi kuma a nan za'a barshi,yau ina wanda ya tara dukiyarma?,ka barsu nafi buqatar taka rayuwar akan abinda aka tara muku,watan watarana sai kaga Allah ya albarkaceku da abinda yafi abinda kuka rasa" qananun shekaru da kuma zantukan bibi ya sanya hakanan suka zuba ido,basu qyalesu ba saida suka tabbatar sun rabasu da manyan kadarorin da mayak'i ya mallaka.

Shekarar da mohmoud ke aji na biyu na university,hamidou (aba) yake ajin qarshe na secondry school rayuwa ta tsananta a garesu,gidan da suke ciki ma ya soma niyyar gagararsu zama a ciki. MOHMOUD wani irin halitta ta daban Allah yayi masa,bibi tasha daga hannu ta godewa Allah da ya bata kyautar mohmoud a matsayin d'a. Yana da kyakkyawar zuciyar da zai iya yin kuka saboda kawai wani yayi dariya. Yana da kyakkyawar zuciyar da zai iya hanawa kansa saboda wani ya samu,yana da kyakkyawar zuciyar da zai iya wanzuwa cikin radadi rudani da firgici muddin wani zai wanzu cikin walwala nutsuwa da kuma sukuni. Wanna dabi'a tasa bawai iya cikin gida ba har zuwa ga mutanen waje.

Ranar da abun yaci tura ranar da ya kammala jarabawarsa ne daga aji biyu zai shiga aji uku,sakamakon jarabawar hamidou kuma ya fito,an gama komai na cuku cukun tafiyarsa jamia,amma kudin da ake da buqata don yiwuwar hakan basu babu dalilinsu.

Idanunsu jajur yayi zaune gaban bibi yana gaya mata ya ajjiye karatunsa,ya yanke shawarar bidar kudi kota halin qaqa kota kuma wacce hanya muddin wannan hanyar halastacciya ce don ya kula da ita ya kuma kula da rayuwar qannensa

"Amma mohmoud ta yaya?,karatun naka dake sake nisa ta yaya zaka ajeshi?" Kai ya girgiza

"Sam sam karatuna a yanzu bashi da amfani,koda na yishi bazanyi farinciki ba mahaifiyata da qannena da basu da kamata suna cikin matsi da buqatar rayuwa" daga bibi har hamidou tsit sukayi suna duban mohmoud,ya fadi maganar ne har tsakiyar rai da zuciyarsa. Daga kuma randa ya furta wannan batu ya fara aiwatar da abinda ya tsara din kamar yadda yace.

Tinja tinja aka dinga yi tsakaninsa da hamidou,yace shi kuma sam bai yarda ba,bazai zama silar rujewar farinciki da kuma burikansa da shi yafi kowa saninsu ba. MOHMOUD bashi da wani babban buri a duniya da ya wuce ya zama cikakken likita,ya shaidawa bibi shine zai tallafi karatun yayan nasa,idan yayan nasa ya gama shi yayi nasa.

Wani kallo sheqeqe ya watsawa hamidou,har yanxu wannan kyakkyawar soyayyar da qaunar da granny nadeeya ta dasa musu yana biye da jinin jikinsu

"Saboda gani babban banza ko?, bakaji mr bahausa suka ce ba?, babban wa magajin uba ko?,to gwara ka soma shirin tafiyarka makaranta,don ko bakaje din ba dama karatuna tangal tangal yakeyi ai, karatun lafiya sai dan wane da wane kai kafi kowa sanin haka,ni ba babbabn kwabo bane ra zan zauna qanina ne zai tallafi buqatun qannena dana mahaifiyata ba,indai nayi hakan meye amfani na?,meye amfanin girman da Allah ya bani?".

Tun daga lokacin da ya ajjiye karatunsa ya shiga neman kudi idanu rufe saidai bisa tsaftatacciyar hanya,baya raina abinda zaya kawo masa kudi komai qanqantarsa koda kuwa kwasar kashi ce. MOHMOUD dan gayu dan gata sai gashi tashi daya rayuwa na tamaula dashi tana sauya masa kamanni da tsarin rayuwa. Yasha dawowa gida ya kasa bacci saboda ciwon jiki ciwon kai ko ciwon qafafu,amma baya bari kowa ya sani. Saidai kuma wannan dashashiyar qaunar tana nan tana kewayawa,duk wani motsin MAHMOUD din bisa idanu da kiyayewar HAMIDOU ne, hamidou din yasha boyewa yayi kuka saboda ganin yadda yayan nasu ke bautar da kansa saboda su,iya yadda yake tunanin yaa mohmoud yana sonsu sai a yanzu ya tabbatar abun ya zarce haka,ya kuma shallake hankali da tunaninsa. MOHMOUD ne faskare, MAHMOUD ne tura ruwa, MAHMOUD ne dako, MAHMOUD ne share share goge goge da wanke wanke a gidajen saida abinci duk don kada karatun hamidou ya samu tangarda,kada karatun su oumar ya tsaya,kada bibi ta buqaci wani abun ta rasa,ya gwammace shi yayi kuka muddin su zasuyi dariya. Ranar da ya gaza jurewa ganin dan uwan nasa ahaka cikin wani darene da MAHMOUD din ya kasa bacci saboda radadi da hannunsa ke masa saboda yawan itacen daya faskara duk don ya qarasa hada kudin registration din hamidou.

Yana ganin hamidou din ya motsa yayi saurin boye hannuwansa,saidai kuma tuni shima ya kama hannuwan yana kalla. Wasu hawaye suka zarto daga idanunsa yana dubansa

"Hamma....wannan abun da kakeyi a kanmu yayi yawa,ka sassauta gangar jiki da zuciyarka don Allah hamma" hamidou ya fada yana hawaye. Jawoshi kawai mohmoud yayi yana bubbuga bayansa

"Inajinku ne tamkar 'ya'yan da suka fita a ciki na,zuciyata da ruhina ba zasu taba samun nutsuwa ba muddin dayanku na cikin buqata" sun jima a daren hamidou yana gasa masa hannunsa,tun kuma daga ranar yasa ya masa alqawarin daina boye masa wasu abubuwan,sannan wasu lokutan tare suke fita ayyukan,amma yanayin karatu ba kasafai yake barin hamidou din binsa ba. Shima kuma MAHMOUD din yafison hakan,yace yafison yayi zamansa ya maida hankalinsa akan karatunsa shi shine farincikinsa.......*_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

*BOOK 02 PAGE 04*
_________________________________
*_Shin kin isa mace?,don magana akeyi ta ISASSUN MATA_*

*_SUTURA ABAR TUNQAHO_*

*_Ado da kwalliya shine cikar 'YA MACE_*

_Magana akeyi ta_

*UMMU MAHNOOR LUXURIES*

*UMMU MAHNOOR LUXURIES*

_GIDAN QAWA ADO NA KECE RAINI_

*_INA AL'UMMAR KADUNA ABUJA SULEJA DAMA NIGER......HAR MA FADIN NIJERIA GABA DAYA_*

*_KIN SHIRYA FITA KUNYA?_*

*_MAZA HANZARTA KI LALUBI KALOLIN SUTURAR DA TA DACE DAKE,KAYAN ADO MASU_*

*KYAU*

*QUALITY DA DAUKAN HANKALI*

*LACES NE,SHADDA CE,ATAMFOFI NA 'YAN QWALISA*
*GA KUMA DESIGNERS TAKALMA DA JAKANKUNA NA ALFARMA DA FITA KUNYA*

*_ZAKU IYA SAMUN MAMALLAKIYAR KAMFANIN KAI TSAYE TA WANNAN NUMBER WAYAR_*

08135142610

*INSTAGRAM* UMMU_MAHNOOR_LUXURIES

*FACEBOOK* MUSA GARBA SHIFA

*_Ga wadanda ke cikin garin abuja kuma zasu sameta kai tsaye a_*

*_system property Nefelix estate,near amasco,galadimawa roundabout_*

*_KARKI BARI A BAKI LABARI,KARKI KUSKURA KI ZAMA 'YAR KALLO_*

*TASTED AND TRUSTED*👌👌👌
_________________________________________



*HAMDIYYA ABDU ME KANO*

Yarinyar da tafi kowa kyau cikin school din,ajjiye kyau a gefe,idan ana batun gata za'a iya cewa kaf makarantar babu diyan da ya kaita gata wala mace ko namiji.

Ita din diya ce ga attajiri alhaji abdullahi me kano,mashahurin dan kasuwa wanda inda arziqi yana yawa za'a iya cewa nashin har yayi yawa. Arziqi da aka nemeshi da zuciya da kuma qwanji,aka tara shi cikin albarka iyaye data al'umma. Yaranshi uku kacal a duniya,tajuddeen da ake kira da taj,sai mebi masa abdulhakeem sai kuma 'yar daya daya 'yar gatansu kuma 'yar gaban goshin kowa wato hamdiyya(ama). An haifi hamdiyya ne a lokacin da kowa ya fidda rai daga sake samun haihuwar mahaifiyarta hajiya aisha a duniya,bayan wasu shekaru harsu abdulhakeem sun fara yin hankali,don a qalla a cikinsu babu wanda ya bata qasa da shekara goma. Tazo a dai dai sanda suke da kwadayin qananun yara a gidan,kuma tazo a jinsin diya macen da basu da ita,wannan ya sanya gata yayi mata rubdugu tako ina,kowa kawo nashi gudunmawar gatan yakeyi. Idan akace gata ana nufin gata me sunan gata,gatan da ya sanya take cike da haushin yadda rayuwar sultana take,domin kuwa idan za'a dora mizanin gatan da sultana ke samu da wanda ita ta samu a zamanin quruciya zata iya cewa sultana din bata samu kaso daya cikin goman nata gatan ba,saidai natan bai hanata samun cikakkiyar tarbiyya da kulawa ba. Sam sam alhaj abdullahi da aishatu matarsa basa cikin jerin sahun mutanen da suka aza dukiya a gaban tarbiyya yaransu. Sau da dama yanayin tarbiyya yaran alhaji abdullahi na bawa daruruwan mutane mamaki. A yadda mahaifinsu keda kudi ruwa ruwa kamar su kasheshi,ko kadan ba zaka taba tsammatar samun tarbiyya haka daga yaransa ba,sakamakon yadda ya zama kamar wani tambari ko al'ada na yaran da iyayensu ke da hali,sukan tashi a sangarce,babu ganin girman babba bare akai ga sanin haqqin qarami,gaisuwa ma kam ba kowanne ke tashi da iyata ba,wanda wannan babban kuskure ne ga rayuwa,domin da 'ya'ya da dukiya dukka amana ce kuma jarrabawa ce,idan ka jagorancesu ta hanya me kyau kaci moriyarsu cikin kwanciyar hankali da farinciki,idan ka jasu kuma ta akasin hakan lallai bone da nadama yana nan tafe.

Hajiya aishatu mahaifiyar ama itace haifaffiyar qasar NIJER, CIKAKKIYAR buzuwa gaba da baya wadda har rayuwa tayi mata zurfi cikin nijeria bakinta baya fidda hausa tar kamar yadda ya kamata.

Sun rayu kuma tashi da tsananin zumunci,daga dangin mahaifi har na mahaifiya babu wanda suka bari a baya wajen sada zumuncinsu,wannan ya sanya alaqa me qarfi tsakaninsu da dangin mahaifiyarsu dake nijer. A duk sanda suka samu hutu suna ware lokaci sosai da zasuje ga dangin mahaifiyarsun suyi masu kwanaki su juyo,wannan ya sanya nijer taso janye hamdiyya banda tsananin son da suke mata da tuni zamanta a Nigeria ya zama labari,saidai duk da hakan bayan ta kammala secondry school kakarta ta dauketa da zummar hutu kawai zatayi ta dawo,sai gashi zama ya miqa,duk da yadda abbanta dama su abdulhakeem ke jelen ta dawo

Please Login or Register in order to submit comment