Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

dama a nan balcony ta xauna tana sharban kwalla, Heedayah dai da Farida na xaune kusa da Mami sun yi kukan har sun gaji, Hajiya Zuwaira ta mike ta nufi gun kaka ta dagota cikin sanyin murya tace "Addu'a xa ki yi mata kaka Allah ya gafarta mata" Kaka ta kara rushewa da matsanancin kuka ta rungumeta tace "Wllh matar kirki ce Maryam, duk abinda aka ga tayi bai kai xuciyarta ba xugar shegu ne, kaf shekarunmu da ita bata ta6a tanka ni ba, bata ta6a min rashin kunya ba, duk tsiyata da fitinata shiru take min, kuma anjima baxata fasa xuwa ta min magana ba, ita dai idan ka xauna wajenta cikinka ne xai gaya maka amma wllh ko kallon banxa baxata maka ba balle maganan banxa, kaf surkaina bbu me raga min sai ita, kuma ba dai kaga ta canxa fuska ba don Amadu xai yi maka abu ko xai baka abu, bbu ruwanta da wnn wllh wllh, ita dai kawai girki ne bata son yi balle ta baka ka ci ka koshi, yanxu Maryam ta rasu?? Jiya jiya fa ta sallame mu da yamma wai xata koma wai Amadu yace kar ta kwana, har Yakumbo ke ce mata ta bari gobe yamma yayi ashe ajali ke kiranta, yanxu ya isilin marayun nan da ta bari ni Patuu??" Kuka sosai Kaka ke yi Hajiya Zuwaira na lallashinta, Hajiya Amina hawaye ya kasa tsaya mata haka kishiyarta, ba karamin girgixa su mutuwar yyi ba, daga karshe Hajiya Zuwaira ta fitar da kaka daga parlon. Sosai aka ji rasuwan Mumy, ba 'yan uwa ba, ba makota ba, yawanci kuma duk kyawawan halinta ake fadi, kaka dai ta dage a kan bata ta6a mata rashin kunya ba, ko kallon banxa bata ta6a mata ba, yunwar da ta barta da shi ma ta yafe mata duniya da lahira, har kwana uku kaka bata daina kuka da jimami ba, ana xaxxaune parlor a kwana na ukun, Hajiya Sadiya ta shigo tare da Hajiya Balarabe, Sadiya ta rushe da kuka tana rufe fuskarta da Hijab din jikinta, kaka tayi mitsi mitsi da ido tana kallonta, Sadiya ta karaso tana goge hawayen idonta ta xauna kasa tace "Innalillahi wa Inna ilaihi raji'un, Allah ya ji k'an Maryam, Allah ya gafarta mata, Allah ya yafe mata" Kaka na mata wani kallo daga sama har kasa tace "Sai yau kika ji rasuwan kenan?" Sadiya ta ki dago kanta tana matsar kwalla tace "Eh wllh, na yi tafiya naje Sokoto, garin da naje bbu network sai yau na dawo kaduna, ina dawowa aka sanar min wai Allah yyi ma Maryam rasuwa" Tana kai wa nan ta saki kuka da karfi, Kaka ta mike tana rike da carbinta tace "To tashi ki fita, algunguma mayya yar jaraba, Allah ya isa tsakaninmu da ke...." Da sauri Sadiya ta mike har tana neman faduwa ta nufi kofa Balaraba ma ta mike ta bi bayanta da sauri, kaka ta fashe da kuka tace "In sha Allahu karshen ku baxai yi kyau ba, duk ku kuka gurbata tunanin Maryam, mata me kirki bbu ruwanta da mugun abu kai dai idan xaka xo gidanta to ka xo da shirin dinga shiga kitchen ka nema ma kanka abinda xaka ci, amma tsinannun mutane kawai kun nemi hallakata ku ka fara sa ta yawon banxa, to in sha Allahu muna nan muna mata addu'ar Allah ya gafarta mata, ya yafe mata kurakuranta, ku kuma Allah kadai yasan yanda xai yi da ku, duk ku ne sanadin canxa halin Maryam" tuni Hajiya Sadiya da Balaraba suka fita daga parlon, kaka ta koma ta xauna tana matsar kwalla. Da yammacin ranan Khaleel ya xo gidan tare da Junaid, Kaka na parlor da Yakumbo sai Ta rasulu da wasu step sisters din Abba, Kaka ta amsa gaisuwarsu cikin sanyin murya tace "Tun da aka yi rasuwan sai yau ku ka xo min gaisuwa Junaidu?" Shi dai Khaleel bai ce komai ba, Junaid yace "A'a jiya mun maki gaisuwa kaka, kuma ko da safe ma mun xo har mun gaisa ma...." Kaka tace "Toh duk na rude, ai mutuwar maryam ya girgixa ni d'an nan, ga mutane kamar kiyashi, duk ana ta xuwa min gaisuwa gidan nan ba masaka tsinke, har daga Nijar, maiduguri da Taraba an xo min gaisuwa, kaga ai baxan lura da ku ba, to kun ma Amadun gaisuwa kuwa? Shi ma dai duk karfin hali yake, mutuwar mata ai babban tashin hankali ne, shekaransu talatin da tara tare, sai da suka yi aure da shekara shidda marigayiya ta haifi Shuraim d'an ta na fari" Junaid yyi kasa da kansa yace "Allah ya gafarta mata" Kaka ta goge kwallar idonta tace "Ameen dai, Allah ya yafe mata kurakuranta, mu ma kuma Allah ya kyautata namu karshen" Junaid yace "Ameen" Yakumbo dai sai satan kallon Khaleel take tana wuri wuri da 'yan idanuwanta, Junaid yace "Shuraim fa?" Da damuwa Kaka tace "Wa ma ya sani, ni dai nace da ma kukan yyi yanda duk muke yi ko xai ji dadi ya samu salama, rashin kukan ya fi cutarwa, daxu dai ya shigo da d'an uwan, ban san ko ya fita ba" Junaid ya sauke ajiyar xuciya yace "Allah ya kara hakuri da dangana" Kaka tace "Ameen, Rakiya na can parlon ku shiga ita ma ku kara mata gaisuwa, yau kwananta uku a nan gidan ita ma" Mikewa Junaid yyi ya nufi parlon da Kaka ta nuna masa Khaleel ya mike shi ma ya bi bayansa, Kaka ta bi sa da kallo kasa kasa tace "Yo ba sai ya sa6a xama cikin jama'ah xai sake ba, mutum dai kamar bass din shirin Indiya, ko murmushi bai yi, naga yanda Deedayah xata xauna da shi tunda tace ta ji ta gani, ba ruwanmu" Yakumbo tace "To ba dai ita da uban sun ji sun gani ba, har ynxu fa a dari dari yake da mutane, abin ka da wanda ya saba xaman daji" Mami na xaune parlon tare da su Hajiya Amina da Zuwaira, Heedayah ma na parlon da Farida da su Rabi'ah da su Zainab, Junaid ya xauna nan kasan carpet din parlon ya gaida su Mami, Khaleel ma ya xauna ya gaishesu kansa a kasa, Gaba daya 'yan matan parlon suka gaida su Junaid, Heedayah dai na kwance idonta rufe ta juya ba, Junaid na kallonta yace "Bacci Heedayah take" Mami ta ta6ata a hankali tace "Heedayah" da sauri ta bude ido ta juyo ta mike xaune ganinsu Junaid tace "Ina yini Yaya?" Yace "Lafiya lau bacci kike yi?" Tace "Uhm" Kallon Khaleel dake kallonta tayi a hankali tace "Ina yini?" Yace "Lafiya lau" Junaid yace "Ya karin hakuri?" Tace "Alhmdllh" Junaid yace "Allah ya gafarta mata" ta amsa da "Ameen" kallon Mami yyi yace "Shuraim na gidan kuwa?" Mami tace "Ehh yana dakinsa with Sudais, you check" Tashi yyi suka fita parlon tare da Khaleel. Washegari Mami suka koma gida gaba daya, gidan ya rage kaka da tawagarta da sisters din Abba, har su Rabi'ah Mami ta wuce da gidanta, sosai yaran ke bata tausayi hakan yasa ta sa su debi kayansu su koma can gidan nata tare, tunda suka dawo gida Heedayah gaba daya bata da walwala kai kace mahaifiyarta ce ta mutu, abinci sai tayi da gaske take ci, Suna kitchen tare da Farida da Maid din Mami suna serving ma kowa abinci a gidan, Farida ta mika mata plate din abinci da ta xuba ma Khaleel d'an kadan sanin haka yake ci tace "Ki kai ma Yayanmu" Heedayah ta jingina da cabinet tace "Ke dai ki kai masa, ba wanke wanke xan karasa ba" Farida tace "Ba ga Zainab na yi ba, meye kuma idan kin kai masa abinci" Heedayah dai bata ce komai ba, can ta amshi plate din ta dau wani plate ta rufe sanin ba a lkcn xai ci ba idan an kai masa ta juya ta fita kitchen din, sama ta wuce ta bude dakin junaid taga baya ciki, ta karasa last room dake wajen don yawanci nan yake xama yanxu, ta bude kofar amma ba gaba daya ba tayi sallama, sai da taji ya amsa snn ta shiga, xaune ta gansa yana danna laptop, ya daga kai yana kallonta shi ma, har ta karaso ta ajiye plate din tace "Ina yini" Yace "Have u finish mourning?" Ta d'an kallesa bata ce komai ba, yace "To Allah ya gafarta mata, naga kamar kun shaku da ita sosai ko?" Sake kallonsa tayi still taki cewa komai, Ya ci gaba da abinda yake a laptop, ta juya xata fita yace "Heedayah" juyowa tayi ya nuna mata kujera yace "Sit, let's talk" Ba musu ta dawo ta xauna tana kallonsa, ya d'an yi shiru kafin yace "Kamar naga baki son aure yanxu ko? Like... Karatu kike son ci gaba da" Ta kallesa, jin bata ce komai ba yace "Feel free talk to me" Tace "Why did you ask me that?" Yace "Because I have noticed ur changes in behavior" Ta hade rai tace "Wani irin changes?" Yace "Na baki son auren, may be u have other plans" Ta girgixa kai tace "I have no plans, kuma ni bance maka bana son auren ba" Ya d'an yi murmushi cikin sanyin murya yace "Don't worry Heedayah my heart have been broken so many times nasan damuwar ki kenan, na saba da heartbreak kar ki damu da haka... kawai dai naki will be different and may be more painful and difficult to endure, but all the same, ba a tilas a aure, I will help you tell ur parent su bari ki ci gaba da karatun ki...." Heedayah ta girgixa masa kai hawaye na sauka idonta tace "Ni ban ce haka ba, kai ma kuma kasan I so care about you bana son wani abu ya sameka, ni bance bana son auren ba.... just that ina son kada ka dinga kokarin hanani mu'amala da yayanni na, and you just have to trust me..... I will never betray you" Shiru yyi yana kallonta, ya mike ya isa gabanta yace "Baxan hanaki mu'amala da su ba, amma kuma ni ma kada ki hanani kishin ki" Ta sauke idonta kasa bata ce komai ba. Da daddaren ranan Heedayah ta fito daki xata kai cup din da ta sha shayi kitchen ta tadda Mami da Shuraim xaune downstairs, Kansa a kasa Mami na yi masa magana cikin kwantar da murya, shi dai bai ce komai ba, tun rasuwar mum dinsa wnn ne ganinsa na biyu da tayi, ta wuce kitchen ta ajiye cup din hannunta ta fito, bata karaso cikin parlon ba ta gaishesa cikin sanyin murya, ya daga kai ya kalleta ya amsa, Mami tace "Ki kawo masa abinci" Ya girgixa kai yace "Aa, I am full" Mami tace "Aa sai ka ci, you don't even look like someone that is eating" Shiru yyi bai ce komai ba, Heedayah ta juya a sanyaye ta koma kitchen din, Ko da ta fito da tray din abinci Mami ta riga ta bar parlon, ta karasa ta ajiye masa tray din gabansa tana kallonsa a hankali tace "Ya karin hakuri ya Shureen?" Yace "Alhmdllh, how are you?" Tace "I'm fine" Bai kuma ce mata komai ba, ta xauna nan kasa tace "Ya Shureen plss ka kwantar da hankalin ka, you don't look okay, don't get sick plss" Ya d'an mata murmushi yace "I am okay" Tace "Nooo gashi ka rame" Yace "Katuwa kike son in xama kamar ki?" D'an murmushin karfin hali tayi bata ce komai ba, yace "Ohk xauna, let's talk" Ba musu ta xauna nan kasa tana kallonsa, kamar baxai ce komai ba sai kuma yace "I want to ask for a favor Heedayah" Ta gyada masa kai tace "Sure, ina ji" ya sauke idonsa yace "Forgive my Mum Heedayah...." Ji tayi xuciyarta yyi rauni sosai, ta girgixa masa kai hawaye ya kawo idonta lkci daya, cike da karfin hali tace "Bata ta6a min komai ba ya Shureen" cikin sanyin murya yace "No Heedayah, I wished she had the privilege to ask for ur forgiveness before leaving, my mum was good, Just all of a sudden..... anyway just Forgive her for the sake of Allah and my father" ta goge idonta tace "I have done that already, Allah ya gafarta mata" Yace "Ameen, I appreciate, ya shirye shirye?" Tace "Na me?" Yace "Na bikin ki?" A hankali tace "Ba a fara ba tukun ai" Ya d'an yi shiru, ta daga kai ta kallesa, yace "Toh Allah ya kai mu lkcn lafiya, ki turo min su Rabi'ah" Tace "Toh" daga haka ta mike ta wuce sama. Mami da iyayen Heedayah sun so a dage bikin da ya rage saura sati uku yanxu sbda rasuwar Mumy amma Abba ya ki amincewa da hakan, wnn yasa aka bar bikin lkcn da aka yi fixing, bayan sati biyu da rasuwar Mumy kuma aka hau shirye shiryen bikin duk da ko kadan hakan bai ma iyayen Heedayah da ma Mami dadi ba, sai dai Abban Heedayah yace daurin aure kawai xa ayi sai walima bbu wani event.... Biki saura kwana goma Heedayah ta koma Kano ta private jet tare da su Farida da Rabi'ah.....




*Sick... Need ur prayers plss*


Heedayah isn't free, you read for free 🤷🏻‍♀️🤷🏻‍♀️


it's 300 via... Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah


Then you show ur evidence via WhatsApp 07087865788....






Heedayah na xaune daki tana kallonsu Farida dake fiddo ankonsu daga cikin akwatin da aka kawo har an dinka kayan wanda kala biyar biyar ne, kallonsu kawai take amma gaba daya hankalinta ba a kansu yake ba, tayi nisa tunanin da take aka kwankwasa kofar dakin, Farida ta mike ta nufi kofar ta bude don duba waye, Heedayah ta kalli agogo dake nuna tara saura na safe, ta koma ta kwanta a hankali saman gado, yau kwanansu biyu da dawowa kano, a kwanakin nan biyu a ko wani second cikin faduwar gaba take, duk ta rame abincin ma bata iya ci sosai sai tunani, babu wanda ke tambayarta don me a gidan da ya fara cika da jama'ah daga wajaje daban daban sai step mum dinta dake kokarin kwantar mata da hankali ko da yaushe sanin it's always like that for a new bride to be, Farida ta dawo dakin tana kallonta tace "Aunty na kiran ki Heedayah" Heedayah tayi shiru, kafin ta mike ta sa hijab dinta ta fita daga dakin ta tafi bangaren Mom Islam, Tsaye ta sameta dakinta ta fiddo da wasu tsadaddun atamfofi da laces da aka dinka kala goma daga wani sabon akwati, tana kallon Heedayah tace "An kawo kayan dinkin ki for the week" a hankali Heedayah tace "Toh" Mom islam tace "Me maki gyaran jiki tana jira a can bangaren Ammin ki, ki wuce can yanxu" A hankali Heedayah ta sake ce mata "Toh" Juyawa tayi xata fita, Mom Islam tace "Kin ci abincin kuwa" Heedayah tace "Na ci" Mom Islam tace "Okay anjima xa a kawo kayan lefen ki idan Allah ya yrda" Heedayah dai bata ce komai bata juyo ba kuma bata tafi ba, jin step mum dinta tayi shiru ita ma, ta juyo tana kallonta, Murmushi step mum din ta sakar mata tace "Haka kike son a kai ki duk a rame Heedayah, ba nace ki kwantar da hankalin ki ba?" Heedayah ta kasa ce mata komai, Step mum din ta nufeta tace "Tell me meye damuwar ki yanxu?" Lkci daya hawaye ya kawo idonta tace "Aunty kawai ni dai ina tsoro" Stepmum dinta tace "Ki kwantar da hankalin ki xaki daina, it's like that with some, yanxu ki fara tafiya kiyi ma Abbanki godiya kafin ya bar part dinsa..." Heedayah ta gyada mata kai snn ta nufi kofa ta fita, bangaren Abban nata ta tafi ta bude kofar babban parlonsa a hankali ta shiga, yana xaune parlon tare da Sudais da Shuraim, duk suka daga kai, ganinta Shuraim ya dauke kansa, karasawa parlon tayi a sanyaye ta xauna kasa ta gaishesu, suka amsa... snn ta kalli Abbanta tace "Abba Aunty ta bani kaya, I really appreciate it" Abba yace "U are wlcm Fatima" Sudais ya mike tare da Shuraim, yace "Mun gode ur Excellency Allah ya kara girma" Abba na murmushi yace "Ameen, yanxu xaka koma Kadunan?" Sudais yace "In sha Allah" Abba yace "Toh Allah ya tsare, Allah ya maku albarka...." Duk suka amsa da Ameen, suka nufi kofa... Abba da ya bi Shuraim da ido yace "Don't forget you meet me at office later Aliyu" Shuraim yace "In sha Allah" Daga haka suka fita da Sudais, Abba na kallon Heedayah yace "Hope no problem dear?" Ta girgixa kai tace "Aa babu" Abba yace "Toh Allah ya maki albarka" a hankali tace "Ameen" bayan few seconds tace "Abba me su Yaya suka xo yi?" Da mamaki yake kallonta yace "Me suka xo yi kuma?" Bata ce komai ba, yyi murmushi yace "Na ba Sudais appointment ne, shi kuma Shuraim dama a nan yake ai...." Heedayah ta ji dadin abinda Abbanta ya fada har xuciyarta, tace "Allah ya kara girma Abba, I am happy with that, I stayed with them from the beginning because of Ya Sudais, he didn't reject me even for a second, he supported my Abba and convinced everyone I stay.... Shine silar xamana tare da su" Abbanta ya girgixa kai yace "Kuma ban sani ba, I just saw his dad is nice also, shi ma naga yana da hankali" Heedayah ta gyada kai, Abba yace "Toh Allah ya saka masa da alkhairi, amma ya kamata yyi aure shi da Shuraim..." Murmushi Heedayah tayi tace "Toh ai shi ya kusa haka kaka tace mana" Abba ya girgixa kai yace "Aa we just talked about that now, yace his mum was against the marriage, bata son auren" Shiru Heedayah tayi mamaki ya cikata, can tace "Toh did you talk to Ya Shureen also?" Abba yace "Sure I did, yace min soon" Heedayah tace "Allah ya kai mu" Abba yace "Shi kuma Junaid his uncle called yesterday, yace jiya aka kai nasa gaisuwar Yola" Heedayah ta buda ido tace "I am happy for him" Abba ya gyada mata kai yace "Sure" A hankali tace "Toh Abba why didn't you give Ya Junaid appointment also?" Abba yace "He is working... Haka Mum dinku tace" Heedayah tace "Ya Shureen fa?" Abba yyi murmushi yace "He is now my assistant family doctor" Murmushi kawai ita ma tayi, Abba na kallonta yace "Baki tambayar ma Khaleel ba?" Sunkuyar da kanta tayi tana murmushi Abba yace "I appointed him first, after the wedding in sha Allah, he will report to work" A hankali Heedayah tace "Allah ya kai mu" daga haka ta mike ta sallami Abban nata ta bar parlon tunawa da tayi Mom Islam tace ana jiranta a bangaren Ammi. Sai da ta fara tafiya parlon baki ta tadda Shuraim and Sudais, Sudais na shan shayi shi kuma Shuraim na danna wayarsa, murmushi Sudais ya sakar mata yace "Amarya" ita dai bata ce komai ba ta karaso cikin parlon tace "Yaushe ku ka xo Yaya?" Yace "Yesterday, ya shirye shirye?" A hankali tace "Alhmdllh" kallon Shuraim dake ta danna wayarsa tayi tace "Welcome ya Shureen" ya d'an kalleta yace "Thanks, ya komai?" Tace "Fine ya karin hakuri" yace "Mun gode Allah" Tace "Kai baxa kayi breakfast din ba?" Yace "No I am okay" tace "Okay sai anjima" Yace "Alright" daga ma Sudais hannu tayi ya sakar mata murmushi ta bar parlon da sauri. Ammi na parlonta da frnds dinta da wasu mata uku that are wedding planners, Ammi na kallonta tace "Ki je spare room upstairs ana jiran ki" Heedayah tace "Toh" Da yammacin ranan motoci hudu suka xo daga garin gombe kawo lefen Heedayah government house, Aunts din Khaleel ne da matan uncles dinsa sun kusa su goma, aka masu tarba me kyau na mutunci da girmamawa, akwatuna set shidda sau biyu, sai set uku makil da tsadaddun kaya suka kawo matsayin lefen Heedayah, a cikin akwatin jewelries har da sarkan zinari da dankunne da rings, kowa ya6a kayan yake don ba karya sun yi, Yayar Ammi na kallon Ammi bayan duk an gama bude kayan tace "Daga gidan uwar rikon nata aka kawo wannan kayan?" Ammi tace "Aa daga dangin mahaifinsa ne" Hajiya Salamatu tace "Allah sarki, toh Allah ubangiji ya sa gidan xamanta ne, Allah ya basu xaman lafiya, ni ko angon ma ban gani ba har yanxu...." Ammi ta d'an yi murmushi tace "Ameen" Heedayah na bangaren Stepmum dinta da su Farida an gama mata gyaran jiki na ranan, wani kyau na musamman tayi skin dinta sai glowing da sheki yake kana ganinta kaga amarya, amaryar ma 'yar gata, tun da taji an kawo kayanta take kukan da bata san dalilinsa ba, babu irin lallashin da Farida da su Zainab basu yi mata ba amma kamar suna dada tunxurata, Stepmum dinta ta ja ta xuwa bedroom dinta tana mata wani kallo tace "Wani iskanci ne wnn kuma Heedayah, kukan meye haka kike yi ma mutane kamar warce aka doka? Kinsan idan bangaren Amminki kike sai ta 6ata maki rai ko?" Ta fashe da kuka sosai tace "Aunty kawai ni dai gabana faduwa yake, wllh tsoro nake ji" Mom Islam ta xauna gefenta cikin kwantar da murya tace "Toh kiyi ta addu'a, babu abinda xai faru my daughter, ko wacce amarya kan ji hakan ki kwantar da hankalin ki kin ji?" Heedayah ta gyada mata kai da kyar hawaye na sauka idonta, Mom Islam tace "Kun yi magana da Khaleel din?" Heedayah ta girgixa mata kai, Mom Islam tace "Toh ina wayar taki?" Cikin sanyin murya Heedayah tace "Yana can daki na" Mom Islam tace "Bari Farida ko Rabi'ah su dauko maki, kilan ma ya kira ki" daga haka ta juya ta fita, Heedayah ta koma ta kwanta hawaye na sauka idonta a hankali, ba a dau lkci ba Farida ta kawo mata wayarta ta amsa Farida ta fita dakin, miss call din Khaleel daya ta gani sai na Shuraim daya, a hankali tayi dialing number Khaleel, yana fara ring ya katse sai gashi ya kirata, cikin sanyin murya ta amsa sallaman da yyi mata tace "Ina yini?" Cikin cool voice dinsa yace "Alhmdllh Heedayah, how are you?" a hankali tace "I'm fine" yace "Noo, ur voice isn't, ko kuka kika yi?" ta turo baki tace "umm" yace "Why" mikewa xaune tayi tana goge idonta tace "I am just afraid" sai kuma ta sakar masa kuka, ya d'an yi shiru kafin yace "Afraid of what Heedayah?" Cikin rawar murya tace "Nima ban sani ba" Yace "Toh kiyi addu'a" tana hawaye tace "Ina yi" yace "Pls ki kwantar da hankalin ki, don't stress ur self much" Ta gyada masa kai kamar yana ganinta, yace "Kina cin abinci?" Tace "Bana iya ci" yace "Aa ki dinga ci, kina son ki kara ramewa ne? You are making me feel sick also" Ta girgixa masa kai bata iya ta ce komai ba, yace "Tell Farida to get you something to eat now idan kin gama ci sai ki kirani yanxu" Cikin sanyin muryarta tace "Toh" Daga haka ta katse wayar ta ajiye, mikewa tayi ta nufi kofa ta bude tana kallon su Farida dake parlon Mom Islam tace "I want a cup of tea plss" Murmushi kawai mom Islam tayi, Farida ta mike tace "Ohk dear" daga haka ta mike ta fita daga parlon Heedayah ta koma dakin ta xauna. Daukar wayarta tayi ta shiga kiran Shuraim da yyi mata miss call, har ya gama ring bai dauka ba ta ajiye wayar, Farida ta shigo dakin da cup of tea and pepper soup ta ajiye mata, saukowa Heedayah tayi kasa a hankali tace "Thank you" Murmushi Farida tayi mata tace "U are welcome Aunty Heedayah" Heedayah ta wani hade rai, da sauri Farida ta juya ta fita dakin tana dariya, Heedayah ta dau shayin ta fara sha a hankali, pepper soup din bata wani ci da yawa ba ta rufe snn ta tafi bandakin Auntynta ta wanke bakinta ta fito, daukar wayar tayi ta shiga kiran Khaleel, katsewa yyi ya kirata ta daga ta kai kunne, yace "Har kin ci abincin?" Ta gyada masa kai tace "Uhm" yace "Aa

Please Login or Register in order to submit comment