Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

sai mu san abin yi." Bai ce komai ba, ta yi wa mai chemist magana, ya shigo ya gwada jininsa.
Ya gwada ya kalli Nana ya ce "Jininsa bai wani hau sosai ba, 140/90 ne" Ajiyar zuciya Nana ta yi. Ta ce "A ganinka wannan hawan zai iya sanya masa shanyewar hannu?.
Ya girgiza kai ya ce "Gaskiya ba na tunanin haka, amma ban tabattar ba tun da ni ba likita ba ne ba. Amma a shekarunaa bana tunanin jinin 140 zai shanye masa wata gaSa a jikinsa, amma dai ku je Asibiti a ara bincikawa"
Nana ta ba shi kuWin sa, ta yi tai masa godiya. Ta koma Waki ta zauna ta yi shiru, tana tunanin ko Uwani za ta tambaya, idan akwai wani mai magani, ta raka su, sai dai ta fasa saboda akwai sauran SurSushin jahilci a tattare su, ba ta son surutu kuma tana tsoron a kai su gurin da ba shikenan ba.

****

Alhaji Fatuhu kuwa kamar yadda ya matsa, sai da aka sallame shi ya koma gida. Gidan nasa ma wani abokin kasuwancinsa ne ya saya, ya bar shi a ciki ya zauna ya bar masa aro.

Sagir yana kwance a kan gadonsa, yana kaWa afa ya ura wa screen Win wayarsa ido. Yusra ce zaune sanye da doguwar rigar material, kanta ko Wan kwali babu, dogon gashin kanta ya sha gyara. Tana ta zuba masa surutu.
Har mamaki yake yi, yadda Yusra ta zama mai Wan karen surutun tsiya, wanda da ba haka take ba.

"Ya ka yi shiru ne?" Ya wani lumshe ido ya ce "Ina jin ki ai".

"So talk, ka yi magana mana" ta yi maganar tana cika bakinta da guggurun hannunta.

"Ina ga zan shigo Abuja mu haWu very soon in sha Allah" wata irin zabura ta yi ta ce "Are You serious, dan Allah da gaske?"

"Da gaske nake, zan zo na ganki, amma ki na ganin babu matsala a zuwan nawa? Kar a yi miki faWa fa, ba zan ji daWi hakan ba"
Ayshacool
Yusra ta ce "Babu wata matsala, ba za a yi mini faWa ba, ai ba na tare da su Mami, ina gidan Anty Sumayya. Dan Allah ka zo"

Sagir ya yi murmushi ya ce "Kin yi missing Wina ne?"

Ta gyaWa masa kai tana murmushi.

"Shikenan, i miss you too, ban taSa tunanin ma za ki neme ni ba, na za ta ki na jin haushina haryanzu, amma in sha Allah zan shigo, zan sanar miki lokacin da zan shigo na zo na ganki" ya yi maganar yana kashe mata ido.

Shukura ce ta turo ofar Wakin ta shigo, a burkice ya kif wayar yana kallon ta. arara yanayinsa ya nuna alamun rashin gaskiya, amma ta share shi, ta haye kan gadon ta ja bargo ta lulluSe jikinta.
Ya matsa kusa da ita yana Wan shafa ta ya ce "Sweetheart, ya na gan ki kamar a fusace ne? Lafiya dai ko?"

"Lafiya alau" ta amsa a taaice. an shiru ya yi yana tunanin ko dai ji wayar da yake yi ne? Amma a yadda ya santa da azababben kishi, da zargi da ta ji sai ta yi masa magana. Sai dai ya bar abin a haka bai matsa mata da tambayoyi ba gudun kar su yi faWa.

Tana ankare da take-taken Sagir, na rashin gaskiya. Sai dai ita yanzu ba wannan ne a gabanta ba, bin diddigin mutuwar Wanta take son yi. Dan haryanzu zuciyarta ta kasa amincewa da natural mutuwa ya yi. Domin haryanzu tana mafarke-mafarke marasa daWi da mahaifinta da kuma Doctor Sharif.

****
Aka shiga sati na biyu, Sayyid yana cikin wannan yanayi na rashin lafiya, kuma hannunsa bai saki ba, yana nan a maale.
Ga hauka da yake yi tuburan wasu lokutan, wasu lokutan idan ya burkice sai ya shae ta, ko ya hankaWe ta asa, sai dai ta yi oarin kare cikinta. Ko kuma Ya ya ta watsi da duk abin da ya ci karo da shi, a Waki ko a tsakar gida. Wasu lokutan ma katangar Wakin yake duka da kansa. Ya i cin abinci ya i shan magani, ba salla, komai sai dai ta yi masa cikin rarrashi da ban hauri. Tun tana jin tsoron ya yi mata wani abin, har ta daina ji, ta zuba wa sarautar Allah ido.
Sannu a hankali ta rage yawan amai, sai dai zazzaSi da rashin son cin abinci da take yi, hakan ya sanya ta tabattar da cikin jikinta bai fita ba haryanzu. Sai dai ba ma ta cikin nutsuwar da za ta nemi inda Asibiti yake ta je, ta tabattar da halin da suke ciki ita da jaririn saboda tashin hankalin da take ciki.
Yanayin yadda uwani ta lura kamar Nana na Soye wani abu, ya sanya ta daina zuwa gidan,ta rage aika yara ma. Sai dai lokaci lokaci, ta kan aika mata da Abinci.
Haka sauran 'yan uwansu na garin ma, su kan aiko mata da sha tara ta arziki saboda su na tausayin Nana, sun san mijinta a kwance yake babu lafiya.
Yawon roro a gona kuwa yanzu Nana ta ware, ranar kasuwa ta je ta sayar da abin ta.
Kasancewar ranar Asbar kasuwar garin take ci, sai ta tashi ta yi fanke da sassafe, jikan Uwani Haladu, ya kai mata kasuwa. Ko ta dafa masa zoSo ta uula ya tafi da shi.
Idan ta gama komai kuma, ta bi yara gona roro.

Dare ya tsala, amma Nana tana zaune tunkurkur, wuni Sayyid ya yi yana wani irin nishi, ga wannan azababben zafin jiki da yake fama da dhi.
Tana zaune tana tunani, tana jin yadda mararta take motsi, cikin jikinta yake motsawa.
Ba ta da sauran wanda za ta kai kukanta bayan Ubangiji. Ta fara tunanin oarin tara musu kuWin mota, su tafi Nijar, neman danginsa, sai dai idan sun je Nijar Win ina za su nufa? Babu tsammani ta ji Sayyid Win ya laluba cinyarta, ya kwantar da kansa.
Ta shafa gashinsa ta ce "Sayyid" bai amsa ba, sai dai ya rie hannunta. Hakan ya tabattar mata da ya dawo hayyacinsa ne. Haka ta tashi a cikin daren ta tsiyayo ruwan zafi, ta ba shi shayi ta yi masa wanka suka kwanta, ta lulluSe su da bargo.
Sheshshear kukansa ta ji, duk da yadda ta san ya daWe yana dauriya, da son Soye gazawarsa, sai dai ta ga hakan a idanunsa.

"Sayyid idan ka na kuka, ni kuma ya zan yi kenan? Dan Allah ka daina" ta yi maganar muryarta na rawa. Ta din ga shafa bayansa a hankali, har ya yi shiru, bacci ya Wauke shi.
Ayshacool
Sai dai tun daga wannan, haka aka sake shafe kwanaki biyu, bai sha ko ruwa ba. Dama rashin maganarsa ya daina damunta.
Ga shi yau abin ya tashi sosai, haukan yake yi da gaske. Ta rufe shi a gidan, ta je ta samo gasara a gidan Uwani, ta dawo ta dama masa kunu. Ta nufi Wakin cike da fargaba tare da fatan ya samu ya sha ko kaWan ne.

Sai dai ta ji wata irin guguwa ta taso mai arfi.

Jin yadda guguwar ta taso da arfinta, take fatali da duk abin da ta ci karo da shi a tsakar gida, ya sanya ta tashi da azama, ta fara oarin rufe ofar katakon da take Wakin. Sai dai tana danna ofar guguwar ma na danno ofar.

A take ta fara karanto "A'uzubillah, Allahumma inni as'aluka khairiha wa a'uzubika min sharriha. Allahumma inni as'aluka khairiha wa khairi ma fihi, wa khairi ma ursulat bihi, wa a'uzubika min sharriha wa sharri ma fiha, wa sharri ma urisilat biha" take ta ji nauyin da ofar ta yi ya ragu, ta samu ta rufe ta, ta juya da sauri ta nufin gurin da yake.

Da fari yana zaune a guri Waya ne, amma yanzu Jifa yake da kayan Wakin da hannu Waya, da sauri ta fara bi tana tattarewa, cike da damuwa.
Cikin siriryar muryarta ta ce "Sayyid za ka ji wa kan ka ciwo, ka saurara ka saurari muryar matarka, ni ce a gare ka, ni ce fa, Husnan ka ce fa" Ta arasa maganar a raunane, duk yadda take oarin tare shi ta kasa, domin ta gama firgita da lamarinsa. Tun safe take fama da shi, ya i cin komai, kuma ta kasa sarrafa shi duk rarrashin da ta yi a banza.
Cikin matsananciyar damuwa, hawaye na bin kuncinta ta ce "Ubangiji ka dubi mijin Nana, ka cire masa zafi da raWaWin da yake ji, ka saita masa tunani da wawalwarsa, ya yi rayuwa mai cike da nutsuwa da farin ciki irin na sauran mutane" sai kuma ya tsaya cak, ya juyo yana kallonta.
Ta arasa gurinsa, ba tare da fargaba ba ta rio hannunsa cikin nata jikinsa zafi sosai. Ta kalli cikin idanunsa sai taga yana birkice mata yana rikiWewa kamar ba Sayyid Win ta ba, idanunsa har wani hayai yake fitarwa, gaba Waya kaminsa sun sauya.
Ta lallaSa ta zaunar da shi, Ta yunura zata tashi, domin ta Waukko kununsa ta sake jarraba ba shi, ta ji ya cafko ta yana wani irin sambatu bakinsa na kumfa da dalalar da yawu, da alama magana yake son ya yi mata. Rashin arfin jiki ya sanya ta faWa jikinsa. Ya aname ta sosai, saboda zafin da yake ji, ita kuma jikinta sanyi alau. Ita ma jikinta ya Wauki rawa, ta lafe a jikinsa ta kwantar da kanta a irjinsa tsawon mintuna, jin ya Wan nutsu jikinsa ya rage zafin ya sanya ta zare jikinta a hankali.

Ta Waukko kofin kunun da cokali, sai wani Wan aramin tsumma, ta zauna a gabansa ta Webo kunun a cokali ta kai bakinsa, sai dai ya tsaya yana bin ta da ido, kamar ya ga bauwar halitta, ta buWe nata bakin, ya kalleta shi ma ya buWe nasa.
Ta fara zuba kunun a bakinta ta haWiye, sannan ta zuba masa a bakinsa shi ma. Ya haWiye sai dai wani na biyo gefen bakinsa, bai haWiye duka ba. Tana bashi tana goge masa wanda yake zubowa. Sai da ta tabattar ya oshi, sannan ta goge masa bakinsa. Ta Wauki kofin ta nufi ofa ta buWe a hankali ta ga an daina iskar, ta fita da kofin ta ajiye, ta tattara abin da guguwar ta watsa sannan ta dawo Wakin.

Jiki a sanyaye, ta zauna a gabansa tana are wa kyakyawar fuskarsa kallo. Da yar yake jan numfashi yana saukewa. Ta sanya hannayenta biyu, ta gyara masa gashinsa, da ya rufe masa gefen idonsa, ta saka idonta a cikin nasa, cikin rauni da karaya, idanunta na zubar da hawaye ta motsa bakinta, ta fara magana

"Sayyid, dan Allah ka yi magana ko na ji daWi, wannan karon ka daWe ba ka ce mini komai ba. Da na sanya ran ka fara samun lafiya, amma kullum lamarin nan gaba yake yi. Ka gaya mini wane ne kai? Daga ina ka ke? Ina zan samu danginka da 'yan uwanka, wataila kai naka dangin ba za su guje mu ba, za su karSe mu, tare da sarar da ta haWa addarorinmu wuri guda, duk da ban kasance Waya daga cikinku ba, ni fatana a nema maka magani ka samu lafiya, ba na son ganin ka cikin wannan mummunan yanayin, idan na ci gaba da ganain ka a haka, zuciyata za ta iya bugawa. Dan Allah ka yi magana" Ta yi maganar wasu hawayen na zirarowa daga cikin idanunta.
Ya haWiye wani irin yawu, da yake yi masa zafi a irjinsa, yayi oarin Wago hannunsa na dama, sai ya tuna ya riga ya shanye, ba ya iya komai da shi. Ya buWe baki da nufin ya kira sunanta, saboda tasiri da kuma ciwon da kukanta yake yi masa a zuciyarsa, amma ya gaza bakin ya karkace yawu ya fara zubowa daga bakin nasa, maimakon kiran sunanta da ya yi yinurin yi.
Tana kuka, ta sanya tsumman da tayi amfani da shi wurin ba shi abinci, ta goge masa bakinsa. Ba shi da zaSin da ya wuce, ba wa hawayen da yake maale a cikin idanunsa damar zubowa, ko shi ma ya samu sassauci abin da yake ji.
A hankali ya hura mata iskar bakinsa a fuskarta, a take ta silale ta faWi a jikinsa.
Ya sanya hannunsa mai lafiya, ya rungume ta, ya ci gaba da kuka. Jikinta gaba Waya ya saki.

aisar ta gani a gurin haWe-haWen magungunan sa, yana ta haWa wani abu a cikin kwalba. Zuciyarta ce take ta azalzalarta, da oarin ingizata, sai dai ba ta yi magana ba.

Babu tsammanni, ta ji ya fara magana "ZaSi Waya ya rage miki, a halin yanzu, ko dai ki yadda da abin da na zo miki da shi, ki rungumi addararki, ko ki na kallo Buzun nan zai mutu, domin ba zai taSa tuna waye shi ba har abada, muddin Giyaz yana tare da shi. Dan ba na tunanin akwai wanda zai iya raba shi da shi. Idan har bai iya tuna waye shi ba, shikenan kin ga ba ki da wata makoma. Abu Waya zai sanya a wannan karon na bar miki abin da yake cikinki, duk da ba ni da tabbacin zai zama mai cikakkiyar lafiya ko akasin haka, Giyaz da muarrabansa sun riga sun fara taSa shi a cikin ki. Kin san meyasa ban arasa lalata wannan cikin ba?" Bai jira ta ba shi amsa ba ya ce "Saboda zan so na ga yadda za ki yi, a lokacin da Wan zai amsa sunan shege, kuma ba za ki iya hanawa ba, domin ba ki da hujjar kare kanki. Idan Buzun nan ya rayu bai san waye shi ba, ga kuma nakasa. Idan kuma ya mutu suwaye dangin baban Wan ki? Daga ina yake? Suwaye ahalinsa? Kin san ku a jinsinku na bil'adam da uba ake ado ba riga ba. Babu wanda zai damu da wacece ta haifi mutum, amma za a damu da waye ubansa meye nasabarsa? Tun da ki ka zo garin nan, zuriyarmu suke alwashin yadda fansar su za ta kasance a kan ki. Kafin zuwa wannan adamin babu abin da ban gaya miki ba, na gargaWi. Dan haka dabara ta rage ga mai shiga rijiya"

Cikin kuka Nana ta hau girgiza kai ta ce "Ba zan yi bori ba aisar, ba zan yi shirka da Allah ba. Babu tsanani ko wahalar da za ta sanya na rabu da imanina. Amma na rasa gaba na rasa baya, ba dan ina neman taimakon ka ba, ko ka kawo mini Wauki ba. Na san Ubangiji Allah shi zai taimake ni.
Amma dan zatin Allah idan ka na da hannu a ciwon Sayyid, ka yi mini rai ka rabu da shi, shi ne kaWai duniyata. Ina matuar tausayin sa, ban damu da jinya da nake yi ba, wahalar da yake sha ta isa haka. Idan kuma laifikan zuriyarmu ne suke shafar sa, dan Allah ku yi hauri ki yale shi haka"

Cikin sautin muryarsa mai ban tsoro, da ya kan yi amfani da ita, idan ya so razana ta, ko yi mata magana mai muhimmanci ya ce "Na sha gaya miki na maimaita miki, daga lokacin da ki ka fara bani umarni, kin yadda kin amince da buata ta ne. Ba ni da hannu a ciwon mijinki, kuma bai ya cikin zuriyar ku, sai dai addara mai arfin gaske, ta haWa ku tarayya guri guda. Amma muddin ki na son ya warke daga wannan rashin lafiya, ba ma iya haka ba, ya tuna waye shi, sai kin karSi addararki.".

Nana ta sake marairaicewa ta ce "Ba zan iya shirka ba, ba zan iya zama 'yar bori ba. Zan jure jarrabawata komai zafinta amma ba zan yadda rasa imanina ba"

aisar ya ce "A cikin biyu dole abu Waya ya faru, tunda kakaninki su suka yanyashi wannan matsalar. Na yi iya oarina gurin dakatar da ita a wancan lokacin, amma ta sake tasowa a wannan karon. Dole a cikinku Waya zai warke ya rayu Waya ya mutu a haka, dan babu alamar Giyaz zai sassauta wannan mummunan udirin nasa a kan zuriyar ku. Gefe ga aikin da ya karSa yake yi a akan mijinki, ko dai ki ci gaba da rayuwa da shi, laifukan ku na shafar sa, ko kuma ki yarda ki karSe ni a matsayin hadiminki ki yi abin da nake so, ni kuma na san yadda zan yi da Giyaz, na baki maganin da mijinki zai warke"
"Ta yaya? Me yasa sai ni? Me yasa ni zan biya zunubin da lokacin da aka aikata shi ba na nan, zunubin da zamanin da aka aikata shi, ya yi nisa da nawa zamanin? Me ya sa kakannina suka zaSi zama 'yan bori? Suka gada mini wahala da masifa take ta bibiyar rayuwata. Na zama mujiya a cikin mutane, duk inda na tsuguna sai wata masifa ta afku, da za a jefa mini zargi, kasantuwata ni ba mutum ba ni ba wani jinsi daban ba? Me yasa zan girbe baar shukar da ban san a lokacin da aka dasa ta ba? Ina son mijina duk da daga ni har shi, ba mu san waye shi ba.
Duk da Nijar ba Waki Waya bane ba, ba kuma aramar alarya ba ce ba, asa guda ce, na gwammace zagaye ta neman ahalinsa na dama shi a gare su, da na ci gaba da zama da shi, mummunar addarata tana shafarsa, ko kuma na zama 'yar bori na ci gaba da gadar da wahala da masifa ga zuriyarmu, gara ko ma mene ne ya are a kaina." Ta arasa maganar cikin araji, tana kuka mai bayyanar da tsantsar bain cikin da yake binne a cikin zuciyarta.

*

A hankali yake driving cikin nutsuwa, yana sauraren Jamila, da ke bin waar da ke tashi a cikin motar asa-asa, sai kuma ta yi shiru.

"Ya ki ka yi shiru kuma?" Ta ce "Au wai ka na ji na?"
Abba ya ce "Eh mana, har kin fi masu waar ma iyawa" Dariya ta yi ta ce "Ka ji ziga, muryar ta su da aka tace, aka goge tawa kuma a haka, ka ke cewa na fi su iyawa"

"Au ba ki yarda ba? To shikenan ni dai na san kin fi iyawa" ya yi maganar yana parking Win motar a harabar gurin shan ice-cream Win. Abba bai taSa soyayya ba, duk wannan abubuwan da yake yi wa Jamila, bai taSa furta mata cewar yana sonta ba. Sai dai ita sarai ta gane sonta yake yi, so kuma ba na wasa ba. Sai dai tana mamakin yadda duk wannan abin da yake yi mata, ba ya iya nuna wa a gaban Hajiya Sa'a, hakan ya sanya ta fara tunanin ko dai yana da wata manufa a kanta ne.
Sai dai ta lura halaye da Wabi'unsa, sun sha banban da na Hajiya Sa'a, shi Abba akwai tsantseni, da gudun saSa wa Allah. Dan duk da son da yake yi mata, sai da ya yi mata faWa a kan shigar banza da ta kan yi wasu lokutan.

Ice cream su ka sha, yana ba ta labarin yadda ya yi karatu, da irin alubalen da ya fuskanta na rayuwa. Su ka gama ya Wauke ta ya mayar da ita gida.

Bayan ta shiga gida, Mama ta ce "Yauwwa ke nake jira dama, gas ya are na kira wayar ki kuma ba ki Waga ba"

"Ina hanya ne, ga ATM Wina, a bawa Nasiru ya je ya Wuro. Har za ta shiga Waki sai ta fasa ta ce "Ni kuwa jama'a ina Nana ne? Wayarta ba ta shiga, shekaranjiya waccan ma na biya gidan da mijinta yake gadi, na ga kamar babu kowa a gidan"

Mama ta taSe baki ta ce "Au ke ba ki san abin da yake faruwa ba dama?"

Ta tsaya tana kallon Mama ta ce "Mene ne yake faruwar?"

"Ai tuni aka kore su daga wannan gida. Ke ba zama ki ke yi ba ne shi yasa, suka koma unguwar su Ummi, to kin santa duk inda ta zauna bala'i ne yake bibiyar gurin, hatsaniya ta haWa ta da matan gidan da suke, suka ce mayya ce aka tashe su. Ai nan Babanku ya je aka yi ta fafatawa, da ta kwaso jiki ta taho nan, wai za ta dawo mijinta babu lafiya, na ce bani da gurin jinya a gidan nan. Allah ya raba ni da masifa, ba za ta dawo mini ba, to arshe dai wai yanzu tana auye, can gurin Uwani a can take jinyar mijin nata"

Jamila ta yi sak, ta ce "Mama Nana tana auye fa ki ka ce?"

"Eh mana, to idan ba auyen ba ina za ta je? Tana can"

"To waye yake ba ta Abinci?"

Mama ta ce "Oho ina na sani?"

"Amma ya aka yi tsawon wannan lokacin ban sani ba? Yanzu ba kamar da ba ne, ban ji daWin abin da ki ka yi ba Mama, bai kamata a kore ta ba a ce ta koma auye da zama ba. Da ina nan ko na sani, da na kama musu wani gidan, gaskiya sai ta baro auye"

"To ke ina ruwanki? Mene ne naki a ciki uwar Iya? Kina kallon irin baar azabar da na sha, a kan zamana da ita a gidan nan. Na meye za ki kuma jajubo mana ita. Gara ki bani kuWin da za ki k 
ama mata hayar na bawa WanLadi, Wan autanmu ya tafi kasuwa da zaman banzae da yake yi, na yi masa aure tun da Allah ya sanya kuttun arziki ya fashe mana, ba ki kai kuWi inda babu amfani ba"
Jamila ta dubi Mama ta ce "Wannan Wan uwanki ne, sai ki nemi kuWinki ki yi masa, nima 'yar uwata nake tunani. Haba Mama, ko wani Nana ta kashe miki iyayyar ta isa haka ai. Ai yakamata a tausaya mata, miji babu lafiya ga zaman auye, ita Uwanin za ta Wauki nauyin Abincinsu ne? Tun da muka tashi a wahala muke a gidan nan, amma ita nata ya fi na kowa ma" Jamila ta arasa maganar cikin damuwa, ta shige Waki, ta bar Mama da buWaWWen baki.

*
Kallonsa Nana take yi, suna zaune sun yi juguum daga ita har shi. Bayan ta gama yi masa kitson zanen hannu guda takwas, ta yanke masa faratansa na hannu da na afa.
Kamar wadda aka mintsina ta tashi tsaye, ta kalle shi ta ce "Sayyid, bari na je na dawo" ya bi bayanta da kallo har ta fice.

Sai dai a alla ta kai awanni biyu kafin ta dawo, ko da ta dawo ta tarar da shi ya haWe fuska, ta yi shiru ba ta kula shi ba, ta koma tsakar gida.
Ta laluba kayanta, ta Waukko wata takarda mai Wauke da ayoyin ruiyya da na karya sihiri, sannan ta hura wuta a cikin murhu.
Ta dawo tsakar gida ta zauna, ta fara da Bismillah da karanta Suratul fatiha, sai Suratul falai da nasi. Ta karanta ayoyi biyar Win farko na Suratul Baara, ta fara karanta Suratul mulk, a hankali sai ta fara gani dishi-dishi, ta fara daina ganewa. Ta busa ayoyin a cikin ruwan, Sai ta ajiye takardar. Ta Wauki wata leda da ta zo da ita, ta fito da man habbatussauda da jan Almiski.
Saboda wauta sai ta buWe miskin, ta kai hancinta, da sauri ta dungurar da shi a gurin, ta ja da baya, dan tuni ta ji jikinta ya fara tsuma.
Sai da ta Wan samu nutsuwa, sannan ta zazzaga tazargaWe a cikin bokitin, ta kawo ganyen magarya guda bakwai, ta saka a leda ta Wan bubbuga musu muciya, ta haWa a cikin ruwan. Ta yi shiru tana tunani a ranta ta ce "Allah ya sa ba mai magani na zama ba, aisar bai mayar da ni 'yar bori mai bayar da magani ba, larurar Sayyid ta saka na fara koyi da magungunan sarkin baka."
"Amma ai ayoyin Alkur'ani ki ka karanta, shi ma kuma Sarkin Bakar yana amfani da Alkur'ani" wata zuciyar ta tunatar da ita. Haka dai ta ci gaba da wasi-wasi.
Can yamma, bayan ta tabbatar da ganyen magarya da tazargaden sun tsumu, ta Wumama ruwa ta tsiyayi ruwan tofin ta tace ta haWa da ruwan Wumin, ta kawo man habbatussauda ta tsiyaya a ciki, ta kawo jan miskin nan da ta saka kwalbar a ruwan Wumi, ya narke ta tsiyaya a ciki, ta Webo garwashi a kasko ta shiga Wakin. Yana ganin Nana ya tashi zaune yana kallon ta, ya ga ta samu yalle ta Waure hancinta da bakinta.
Ta nufo shi ya ga ta hau tuSe masa kaya, ya din ga bin ta da ido, ta bar shi daga shi sai gajeren wando. Hannunsa da yake maale take kallo cikin damuwa, ta shafa hannun.
Sai kuma ta

Please Login or Register in order to submit comment