Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tashi, ta shiga banWaki ta duba, ta ga ta samu tsarki, ta yi wanka ta yi alwala ta fito. Ta kunna fitilar Wakin, haske ya gauraye Wakin, ba ya cikin Wakin. Duk da wasu lokutan idan ta kwanta bacci ba ta iya tantance mafarki ko kuma zahiri, amma ba ta tunanin da idonta ta taSa ganin ya kwana Wakin. Ko dai ya kwanta a farkon dare, tsakiyar dare ta neme shi ta rasa, ko farkon dare baya nan, cikin dare ta ganshi kafin asuba ta neme shi ta rasa.

Har ta doshi ofar Wakin, da niyyar ta Waga labule ta duba, ta gani ko yana waje, amma ta fasa da tuna abin da ta gani a wancan karon. Babu tsammani iska ta kaWa labulen, ta hango shi a kan benci a kwance ya takure, yana bacci.
Sai ta ji tausayin da ya kama ta.

Ta tayar da salla, ta yi nafila raka'a biyu, ta zauna ta din ga istigfari da salatin annabi Sallallahu alaihi Wasallam.
Bayan ta gama ta Waga hannayenta ta din ga tasbihi duk wanda ya zo bakinta yi take yi. La'ilahaillalahul azimul halim
La'ilahaillalahul jalilul jabbar
La'ilahaillalahul kabirul mut'al
La'ilahaillalahu muWWali'i sittar
La'ilahaillalahul khaliul laili wa nahar.
Allahu Allahu rabbi, la ushriku bi hi shai'an.
Ayshacool
Allahumma inni as'aluka bi anni, ashhadu annaka antal ahadussamadu lazi lam yalid wa lam yulad, wa lam yakun lahu kufwan ahad.
Sai da ta gama tasbihin kaf, sai kuma ta rasa abin da za ta roa. Ta sauke hannunta a hankali ta yi shiru, kawai daga bisani ta rufe da sayyidul istigfar, dai-dai lokacin an kira sallar asuba.

arar zubar ruwan famfo ta ji, ta dake ta je ta lea, ta hango shi a durushe yyana alwala. Ya idar ya zare sakatar gate ya fice.

"Abin mamaki, mutum mai taSin hankali ya san salla, ya san addini anma kuma a ce ba shi da lafiyar wawalwa anya kuwa?" Ta tambayi kanta.
"Zan ci gaba da tunzura ka, da oarin ure haurinka, har sai na tantance ainihin jinsin ka, sai na gano ko kai waye!" Ji ta yi an bushe da dariya mara daWin ji, gaba Waya Wakin ya Wauki sautin.

AYSHERCOOL
08081012143
Ayshacool
Page 33


oarin dai-daita nutsuwarta ta yi, ta tattara hankalinta guri guda.
Ta fara jin sanyi yana ratsa ta, ta din ga nanata Innalillahi wa innalillahi raji'un. Sai kuma Wif tamkar an yi ruwa an Wauke, ta daina jin sautin dariyar.
Ta tafi banWaki, ta sake yin alwala, ta zo ta yi raka'atanul fajari, sannan ta yi sallar asuba.

Ta zauna a kan daddumar, tana kallon wardrobe, tana son ta je ta Waukko Alqur'ani, amma ta kasa tashi.
Ta yi oarin yin karatun Alqur'anin da ka, ta karanta abin da ta sani, amma ta ji tamkar an tattare komai daga cikin kanta an kwashe bar mata fanko.

Ba ta san me ya ci gaba da wakana ba, ta ji an taSa hannunta. Ta buWe idonta ta Waga kanta ta kalle shi. Ta ganta zaune a kan daddumar, sai dai gari ya yi haske sosai, da alama takwas ma ta wuce.

Ya nuna mata ledar hannunsa ya ce "A zo a karya, ga abinci" amshin soyayyen osan ya daki hancin Nana yawunta ya tsinke. Duk son ta da osai ta girgiza masa kai.

Ya ce "Me yasa?"

"Azumi na Wauka"

"Da izinin wa?" da fari shirin tashi take yi, babu shiri ta koma ta zauna, tana bin sa da ido. Mamaki take yi har ya san sai da izninsa za ta yi azumi?.

Ya kamo hannunta, ya juyo cikin tafukan hannun ya ce "Kalli, kin zubar da jini sosai, ta ya ya za ki Wauki azumi? Ki ci abinci"

Ta noe kafaWarta ta ce "Ni ba zan karya ba, na riga na yi niyya, ka bari daga wannan idan zan kuma yi zan gaya maka in sha Allah"

A fuskarsa ta ga alamar ya ji haushi, saboda yadda y tsuke fuskar, kawai ya gyaWa kai ya ce "sai ki yi na gani" ya tashi daga gabanta. Ta bi bayansa da kallo, yana tashi ita ma ta tashi, ta haye katifarta saboda bacci kanta har wani nauyi ya yi mata.

*

Jamila fatar jikinta, ta warke, amma da yar take tafiya tamkar tsohuwa. Hatta banWaki sai an kai ta, komai a due take yin sa.

Babu shiri Mama ta Wauki Jamila, ta kira anwarta ta raka ta zuwa gurin wani mai magani, tana ta bala'in daga zuwa gidan Nana wannan masifar ta afka mata. Ta din ga faWan ba yadda ba ta yi da su ba, a kan kar su je gidan Nanan, tun da dai alkhairi babya bibiyar ta, amma suka nace su ka tafi.

Ko da suka je gurin mai maganin, ya are wa Jamila kallo ya ce "Gaskiya wannan ya fi arfina, sai dai na nemo Ibrahima wakilin rafi, ya duba ta. Idan da wani abu ma duk zai yi muku bayani"

Mama ta ce "Waye hakan? Kuma a ina yake?"

Ya ce "Kar ki damu, yanzu za ki gani, ba a nesa yake ba, yana nan kusa"

Mama ta ce "To madalla, mun gode sosai da sosai "

Mutumin ya tashi, ya din ga tattara shirgi a Wakin, da tsummokara ya cika gurin da su, kamar Wakin mahaukaci. Sannan ya buWe wasu manyan randuna a shae da ruwa, ya barbaWa wani magani a ciki. Ya buWa wata jaka, ya kwaso wasu tarkace, ya Waura wani guru a damtsensa, sannan ya saka yaronsa ya kawo masa, garwashi a cikin kasko, ya turare Wakin da wani irin hayai mai warin gaske, sannan ya nemi guri ya zauna a tsakiyar shirgin nan da ya baje.

Ya sunkuyar da kansa, ya din ga karanto wasu abubuwa da ba a iya gane me yake cewa, saboda ba yaren hausa ba ne, yana yi yana kaWa kansa.
Can bayan wani lokaci ya Wago kansa a hankali.

Gaba Waya kamaninsa sun sauya, fuskarsa duk ta wani tattare tamkar tsoho, jikinsa kuma sai karkarwa yake yi, kamaninsa sun canza.
Ba Mama ba hatta Jamila, a tsaroce suka ja da baya, su na rarraba ido.

Ya ure Jamila da ido sannan ya ce "Wannan ai wani aljani ne yake jinya a jikinta" Ba Jamila hatta Mama cikin bala'in kiWima da tashin hankali, ta kalli mai maganin ta ce "Aljani yake jinya a jikinta kuma, na shiga uku na lalace, ta yaya?"

"A'a ba ki shiga uku ba, uban duusa su ka yi wa laifi da alama, ya hukunta su ne, su duka daga ita har shi a haka"

Cikin rashin fahimta ta ce "Wa kenan?"

"Wani aljani ne shi ma"

Cikin damuwa ta ce "Ya za a yi Jamila ta ga aljani ta yi masa wani laifi?"

"To wannan kuma wani abu ne daban, ba na son dai yin doguwar magana, balle dogon jawabi, amma idan ta nutsa ita ta san ta yi laifin. Yanzu dai zan baku magani, na sha da shafawa, sai kuma wanda za ta din ga shea kafin ta kwanta bacci.
Ayshacool
Daga nan sai kuma a samu osai mai zafi, a yi sadakarsa bayan la'asar. Amma iya anan yara wanda ba su kai shekaru goma ba, su za a bawa. Za ta mie gaba Waya, ta warke. Sai kuma a nemi saurayin zakara, a yanka a fige shi a sulala, da almuru idan an gama rabawa yaran osan, a tona rami a binne zakaran. Zai bar jikinta ya yi jinya a wani guri. Wanda kuma su ka ba ta aikin. ta yi musu su za su Wauki ragamar ba wa uban duusa hauri. Ni ba ma shi nake ji ba, an riga an nakasta aljanin har abada. Ya one sosai daga feshin wutar da aka yi masa. Wata ila ya yafe mata gaba Waya, wataila kuma shi ma ya ce sai ya rama, duk da babu lallai ya samu damar hakan ungiya ba za ta ba shi wannan damar ba"

Cikin tashin hankali ta ce "Ni fa duk ban fahimta ba, ka na maganar ungiya, bayar da hauri, duk me ya kawo wannan zancen?"

Ya ce "Ki bar shi a haka kawai yadda na gaya miki "

Cikin damuwa "Ni dai malam ka taimake ni dan Allah, ka da yarinyar nan ta nakasa ita ma. Yayarta ta nan haka take ta fama da aljanun nan, da yar ta yi aure tamkar za ta haukace, daga zuwa gidanta ta gamu da wannan masifar"

"Kar ki damu, ba wani abu" Ya Waga hannunsa sama, ya dunule ya watsowa Mama wani ulli guda uku, ya ce "A je a yi mata wanka da shi, za ta ware, na baar takarda shi ne na shan, sai na shaar"

Bayan ya basu maganin ya sallame su.

****

HaWuwa da kuma asaitar Wakin, ya sanya Nana sakin baki tana arewa Wakin kallo, tare da tunanin yau kuma a ina take?.
Sai dai yanayin adon da aka yi wa Wakin, ba wai ado ne irin na wannan zamanin da muke ciki ba. Ta Waga kai ta kalli rufin Wakin, sai  
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~dai ga mamakinta, sai ta kasa tantance wani irin rufi ne, gini ne dogo mai matuar tsawon gaske. Sai da ta kalli wani sashi na jikin Wakin, sai ta ga ya yi kama da cikin dutse,, ba wai gini ne na bulo ko asa ba.
Wani irin amshi ya karaWe ilahirin Wakin, amma shi ma amshin sai ta ji bai dace da wannan zamanin ba.
A hankali ta kalli gadon da take kai a zane, ta shafa saman gadon, wani irin laushi na ban mamaki, bayanta ga fululluka a ajiye. Jin motsi ya sanya ta zabura ta waiwaya zuwa inda take jin motsin. Sai a yanzu ta hango wani sashi da ta sani a gurin. Gurin da ta gan ta jiya tana taje masa gashin kansa ne. Gadon ya tunkaro da kofin shayi a hannunsa yana takawa a hankali, jikinsa sanye da wata doguwar riga fara al.
Sai da ya zo gaban gadon sannan ya ajiye kofin a gefe, ya taka wani abu ya hawo gadon.
Kallonta yake yi yana wani irin murmushi mai ayatarwa, ya sumbaci bakinta ya ce "que se passe-t-il?"

"Ban iya ba" ta bashi amsa tana kallonsa ta asan idonta.

Ya yi dariya yana rungume ta a jikinsa ya ce "Me ya faru na ce" ya yi maganar yana shafa gefen fuskarta.

Ta Wan tura baki ta ce "Ni sanyi nake ji" ta yi maganar kamar za ta yi masa kuka.

Ya Wan girgiza kai ya ce "Ai ina kusa da ke, kwantar da hankalinki yanzu zan ba ki Wumin da ya dace da yanayin jikinki, wanda ba zai cutar mini da une ame(Soul/ruhinki ba). Ni ma ki bani wanda ya dace da ni, ni sanyin nake buata". Ya yi maganar yana rungumeta a jikinsa, cike da shaui.

Tamkar almara haka Nana take ganin abubuwan da suke faruwa a tsakanin ta da shi, Kasa saita kanta ta yi a dalilin yadda jikinta yake wata irin tsumar da tun da aka haife ta, ko a duniyarta ta zahiri ba ta taSa tsintar kanta a makamancin wannan yanayin ba. Ita duk yadda take tsintar kanta a mabanbantan yanayi, da gurare ba ta taSa mafarki makamancin wannan a rayuwarta ba. Ga shi ya fi kama da zahiri ba mafarki ba.
Amma duk da haka, ta bar wa zuciyarta mafarki ne, babu tunanin komai take biye masa, tamkar masoyan da suka shafe tsawon lokaci, cikin matsananciyar soyayya da aunar juna.
Bayan wani lokaci a hankali ya buWe idonsa, ya ura mata ido idanunta a lumshe. Ta buWe nata suka yi ido huWu.
Ta Wan zaro masa ido, tare da murguWa masa baki ta ce "Meye?"
Ayshacool
Ya yi murmushi ya ce "Komai ma, je suis heureux (Ina cikin farin ciki) na samu farin ciki amma ba cancan ba saura sex... Hannu ta saka ta toshe masa baki tana hararsa. "Kai ba ka jin kunya ne? Ka ke faWar irin wannan maganat?"
Dariya ya yi, yana oarin cizon hannun nata. Ya ce "Yanzu ma ai ba mu ji kunyar ba, tun da...
Ba ta bari ya arasa ba, ta yinura ta kama kafaWarsa, za ta cije shi, ya mirgina ta yana dariya.

"Haryanzu ka i ka gaya mini sunanka" ta yi maganar tana lumshe idonta

"asair" ya furta a taaice.

"aisar kuma?" Ta furta a zahiri bayan da ta buWe ido, ta ga yadda take aname da pillow.

Juyowa ya yi daga inda yake zaune, da wani Wan aramin littafi a hannunsa, suka yi ido huWu. Kawai ya yi wani irin murmushi yana Wan kaWa kai ya ci gaba da kallon Wan aramin littafin.

Ta tashi tana arewa kanta kallo, tana jin abin da ya faru a tsakanin su a jikinta, dan hatta amshin turaren da yake yi, shi take ji haryanzu.
Ita dai ba gwanar nannauyan bacci ba, balle ta ce ko abin ya faru a zahiri tana bacci. Ko da tana gurin aisar da an taSa ta take tashi. Wasu lokutan ko tsayuwa aka yi a kanta, sai ta farka.
Sai dai ba ta gama razana ba, sai da ta ji ta ba a daidai ba gaba Waya. Da sauri ta tashi ta tafi banWaki, cikin damuwa. Sai dai ko da ta duba, ta sha mamakin abin da ta tarar. Abin da ya faru a mafarki ta gan shi a zahiri, azumin ya karye Wungurungum, kamar yadda ya gaya mata.

Ta jingina da bangon banWakin, al'amuran sun fara ba ta tsoro, ta yaya mutum zai biyo ta cikin mafarki, har ya aiwatar da abin da ya ce? Yaya aka yi ta iya biye masa haka, babu kunya babu jin nauyin sa, duk al'amarin bai ne a gare ta, kuma ta farka sun haWa ido yana murmushi, kamar dai ya san abin da ya faru.
Maganganun aisar su na ta ara tabatta ba ta tunanin Wan Adam ne Buzun nan. Jiki a matuar sanyaye, ta yi wanka.

Ko da ta fito ba ya Wakin, ba ta ko yi yinurin gyaran Wakin ba, ta zauna zaman jiransa.

*

Mama ce take zaune a Waki, tana ba wa Suwaiba labarin yadda aka yi a gurin malamin nan.

"Ni anya ma kuwa Suwaiba, idan Jamila ta warke, ba gurinsa za mu koma ba, ya haWa muku maganin farin jini, tun da wannan karon na ga kamar maganin malam ayyabu bai yi ba".

Suwaiba ta ce "To mama, a bari dai a fara ganin yanayin jikin nata, amma na yi mamaki da aka ce wai aljani ta yi wa laifi. Ni na fara zargin Nana wallahi".

"Ai idan na faWa wasu lokutan haushi ku ke ji, a zo a sayo mini waken da zan soya a yi sadakar nan, anjima kaWan na je na sayo zakaran nan. Kar rana ta take an ce osan da zafinsa ake so a bayar"

Nasiru ya ce "Mama shi osan ne zai ba ta lafiya? Allah kawai za..

"Rufe mini baki kafin na ragargaje ka a gurin, dama yadda ka ke shishshige mata kafin ta tafi, duk ka ko yi miyagun halayen ta".

****
Nana ko karyawa ba ta yi ba, ba kuma ta da niyyar Wora komai, ta zauna zaman jiran dawowar sa.

Ba a yi mintuna talatin ba ya shigo, hannunsa rie da ledar buredi.

Ya ajiye mata a gabanta, bai yi magana ba zai juya, ta rio rigarsa ta tashi tsaye.

"Ina son na san waye kai? Me na aura? Na kasa fahimtar abubuwan da suke faruwa ka yi mini bayani" ta yi maganar numfashinta na fita sama-sama.

"Waye ni?" Ya yi maganar cike da mamaki, yana kallonta.

Ta ce "Eh shi nake son sani, ba na gane abubuwan da suke faruwa, ka yi mini bayanin waye kai? Daga ina ka ke? A ina danginka suke? Saboda na samu nutsuwar zuciya da kwanciyar hankali ka gaya mini"

"je ne sais pas (ban sani ba) ni ma haryanzu ban san waye ni ba"

Ta buWe baki za ta yi magana ya riga ta ta hanyar cewa "Ki yi mini magana cikin girmamawa, ki daina Waga mini murya"

"Ni ba ni da nufin Waga maka murya, amma ka yi mini bayani, ba na gane kan yadda al'amura suke faruwa, ta yaya za ka din ga bi na cikin mafarki kuma... Sai kuma ta yi shiru, ganin yana sauraren ta da mamaki a fuskar sa.

"Kuma me?"

"Ka din ga tsorata ni" ta arasa a sanyaye.

Ayshacool
"Ni kuma? Ta yaya zan bi ki mafarki? Mafarki ba gaske bane ai, kuma wani ba ya shiga baccin wani. Kuma me na yi na.." sai kuma ya yi shiru, ya kasa ci gaba maganganun da yake son yi, suka tsaya a iya irjinsa da maogwaronsa.

A oarin sa na ya yi maganar, kawai sai ya fara tari, ba tare da maganar ta fito ba. Sai kuma Nana ta rikice ta fara dana sanin abubuwan da ta gaya masa. A take aisar ya faWo mata. Ta san babu abin da ba zai iya aikatawa ba, duk domin ta amince da abin da yake so.

"Sannu, ko na baka ruwa?" Ya girgiza mata kai ya fita.

Kawai ta zauna ta tattara hannunta, ta zabga uban tagumi ta ma rasa mene ne abin yi, a tsakanin shi da aisar waye yake raina mata hankali.

Tun da take ta taso, ta fara ganin aisar a siffofi daban-daban, bai taSa yinurin yin makamanciyar wannan alaar da ita ba, ko a farke ko kuma a bacci. Ita hasalima idan ana irin wannan zantukan har mamaki take yi, ba ta taSa jin wani abu mai kama da feelings ba, sai da aka yi mata wannan auren, ta fara rayuwa inuwa Waya da wannan Buzun.
Sai dai yadda mafarkin nata ya kasance, tamkar zahiri ba mafarki ba, tun da har ta farka ta tarar sakamakon abin da ya kwana a zahiri.
Guntun tsaki ta ja, ta tashi da yar ta fara gyaran Wakin.

Da ta gama ta shirya cikin hijjabi ta fito harabar gidan ba ta gan shi ba, kawai ta yi shigewar ta cikin gidan.

A falon gidan ta tarar da matar, tana mopping, Nana ta gaisheta. Ta Wan saki fuska ta amsa ta ce "Kwana biyu ba ki shigo ba"

Nana ta ce "Ba ni da lafiya ne, kawo na yi miki"

"A'a ba komai, kar ki damu zan goge" Nana ta arasa ta karSa ta ce "Bani zan goge. Masu aikin naki ba su dawo bane?"

"Wallahi tsoron su nake ji ne, tun da suka yi mini sata ne, su ka gudu saroinmu na gold kaf suka sace. Shi yasa yanzu nake oarin mu yi komai da kanmu falon ma sai a yi sati ba shara, tun da ba yara"

Nana ta karSi mopping, ta goge Wakin tsaf, sai dai ta din ga jin jikinta wani iri babu daWi.

Har su Tv duk Nana ta karkaWe ta goge mata, bayan ta gama sai ga wani saurayi mai kama da matar ya shigo, da gayyar abokansa.

Bayan Nana ta gama da falon asan, matar ta ce "Dan Allah taimaka ki karkaWe mini falon saman ma"

Nana ta ce "Babu damuwa" ta hau saman benen, sai dai hawanta ke da wuya, ta ara jin jikinta babu daWi, kamar za ta fita hayyacinta. Sai ta fara sauri ta yi ta kammala, ta kammala kafin wani abin ya faru.

Ga mamakinta ta ga wata matashiyar budurwa, za ta Wan girme mata, ta fito daga wani sashi na Wakunan saman benen, tsiga-tsigal da siraran afafuwanta ta saka mini skirt sai vest a jikinta.

Nana ta kalle ta ta ce "Sannu ina kwana" Sai a lokacin ta kula da Nana ta ce "Yauwwa" ta nufi wata ofa.

"Siyama" matar ta kira sunanta. Cak ta tsaya ta waiwayo ta ce "Na'am"

"Wai Yusra ba za ta fito ta karya ba ne?"

Siyama ta Wan Wage kafaWa ta ce "I don't know"

Matar ta Wauki wayar ta, ta danna sannan ta kara a kunnenta.

"Ki fito falo, ina son ganin ki" ta ajiye wayar, tana mita asa-asa. Nana a ranta ta din ga mamakin, da mata kamar wannan a gida, amma a ce saboda babu mai aiki an yi sati ba a yi shara ba.

Nana ta nemi guri ta yi zamanta a kan carfet, tana kallon t.v. sai dai har ta shafe lokaci a zaune, ba ta ga wadda aka kira Win ta fito ba.

Aalla Nana ta kai awa biyu, tana kallon film a MBC2 na divergent. Sai da aka gama ta yinura ta tashi ta ce "Na tafi"

Matar ta ce "Har za ki tafi? Duba dining akwai ragowar bredi, ina ga har da sauran dankali ma ko za ku yi amfani da shi"

Nana ta yi murmushi ta ce "A'a Hajiya na gode sosai, idan na tafi da shi sai dai na ajiye, a oshe muke sai anjima" ba ta ma jira mai Hajiyar za ta ce ba, ta yi waje abin ta, tana jinjina rainin hankalin matar, dan wulaanci ma ita za a bawa ragowar buredi.

A harabar gidan ta hango shi yana ta kaiwa yana komowa, ita tun da ta samu kallo ma har ta manta da shi. Wani irin kallo ya yi mata da sai da ta Wan tsorata. A hankali take takawa tana satar kallonsa, har ta wuce bai kula ta ba, bai kuma bi ta Wakin ba.

*Ayshacool
Alhaji Fatuhu ne yake zaune yana kallo, ya Wan kalli matarsa Fadila ya ce "Kin an yi wa malamr su Muhsin aure kuwa?"

Ta ce "Haba dai?"

"arya na yi kenan?" Ta dafe bakinta da sauri ta ce "Afuwan"

Ya ce "Haka na ji a bakin Yaya Sa'a, ashe wai ta santa"

Fadila ta ce "Haka na ji ranar da ta zo gaisuwa, amma ba ta kyauta ba, abin babu gayyata"

"Ni tun kwanaki ta ce mini za ta yi auren ai, na ma zata tuni an yi fa, ashe sai kwanan nan aka yi, amma duk da haka zan bayar da wani abun a bata"

"Gaskiya yakamata, ni ma zan bayar, ina fatan Allah ya kawo rabo, ta yi yaronta takwara"

Ya Wan yi murmushi yana tuna yaron nasa.

Ta ce "Yauwwa Daddy, ya ciwon kan kuwa?"

Ya Wan Sata fuska ya ce "Ke dai a yi sha'ani kawai, daurewa nake yi amma duk da haka Alhamdilillah"

"To sannu Allah ya ara afuwa"

"Amin babyna" ta yi murmushi tana Wan yi masa fari da ido.

*
Yunwa ce ta ishi Nana, ita ba azumin ba, amma ba ta ci komai ba, ta Wora girki, sai dai fafur ya i shigowa Wakin.

Muryar Habu ta ji yana ta kwaWa sallama, ta saka hijjabi ta lea, ta ga Buzu ba ya gurin. Ta amsa sallamar ta ce ya shiga.

Ya shiga yana sake sallama, ta amsa masa ta ce "Ina ga ya Wan fita ne"

Cikin damuwa ya ce "Ya fita kuma, ina yaje?"

Nana ta ce "Nima ban sani ba, amma ai dama yana fita"

"Duk da haka, kar ya din ga nisa, ki din ga hana shi fitar, kin san ba shi da cikakkiyar lafiya"

Nana ta ce "Ta yaya zan hana shi fita, ni ka zo gaSar da nake son a zo. Ni fa mutumin nan tun da aka yi auren nan, ko sunansa ban sani ba, kullum na tambaye shi sai ya ce mini sunan shi Buzu. Yakamata na san waye shi, a ina ku ke a asar ku? Kuma yaushe za mu je na ga danginku. Tun da a haka tawa addarar ta zo."

Habu ya numfasa ya ce "Kin yi gaskiya Amarya, shi yasa na yi ta ce miki ki yi hauri, ki karSi addara, sai a yanzu na ara tabattar da wannan addarar ce ta haWo mu baki Waya.
Magana ta gaskiya, ban san waye Buzu ba, a sahara na tsince shi cikin mawuyacin hali, mai kama da gushewar hankali da Wimuwa. Yanayin kamaninsa ya sanya na san Wan uwa ne buzu, kuma buzyen ma kala-kala ne, na ji yana iya hausa ya kuma iya French, shi yasa na tabattar da Buzun Nijar ne. Na yi yinurin tafiya da shi Nijar, saboda idan na bar shi a saharar nan, zai iya rasa ransa, ban kuma san da wa zai haWu ba, dan haka na yi nufin tafiya da shi Nijar, domin neman ahalinsa. Sai dai da na yi yinurin nufin komawa Nijar da shi, sai guguwar sahara ta taso, ta rufe hanyar baki Waya. Dole na canza hanya na nufo Nigeria, jikina ya bani akwai wani abu, domin duk wata hanya da zan bi mu koma Nijar na kasa samun ta.
Ina da wasu abokai a Nigeria, su na kira suka karSe ni, da niyyar a taimaka mini, a samo masa magani. Saboda duk abin da na tambaye shi game da shi bai sani ba, sunansa, waye shi, daga ina yake, ina za shi duk bai sani ba. Wasu lokutan zai yi miki abu lafiya kalau na cikakken mai hankali, sai dai ba zai taSa iya ce miki waye shi ba. Wasu sai ya burkice, ba magana yana ma iya daina gane mutane gaba Waya. Ba ya son magana

Please Login or Register in order to submit comment