Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Tarhanine nan ba mu san kowa ba,sannan yin auren mu shine kwanciyar hankalin mu baki ɗaya"Hawas ke faɗa shi kuwa AlGabid hararenta yayi yace "eh tunda yanzu kin bar sona ai doli ki faɗi haka,ina ce dai ke shaida ce iyayen ki ba ƙaunar auren mu suke ba" Hawas ta goge ƙwalla tace " AlGabid doli mu koma gida saboda ta hanyar ce kawai za mu samun cikar burin mu" ya katse da cewa "a'a ko ɗaya ki bar wannan maganar,in dai aure ne tuni na samu uwanda za su ɗaura mana shi yanzu haka zaman jiran su na ke"bai ko rufe bakin sa ba maluman suka yi sallama.



Abu kamar wasa sai ga shi an ɗaura auren su inda maluman suka gudanar da komi kan Shari'a, Hawas sosai tayi kuka saboda ko kaɗan ba haka ta tsaya bikin ta ba sai dai babu yadda za tayi alƙalamin ƙaddarar ta ne.
Jumma ta karɓi kuɗi ga AlGabid ta je kasuwa ta yo masu sayayyar abubuwan buƙata, ɓangaren guda kuma sai gyaran amarya ta ke dan ango ya nuna matarsa ya ke so.



_____________ GHANA ACCRA


Bayun Allah biyu zaune suke kusa da wata mata mai sana'ar sayar da dambu,tun zuwan su ta ke lura da su amman sai ta share.Ganin ba su da niyyar tashi ya saka ta tambaye su "dan Allah nace ko lafiya tun ɗazu kuke nan kuma kun ƙi sayen komi" Laminu ya kalleta yace "Mama ba mu san kowa a nan garin ba,mu ma wayar gari mu kayi mu ka gan mu a nan" Mama mai dambu ta waro ido tace "to ina ne gidan ku?" "Mu ma ba mu sani ba ,dan Allah su waye mu?" Wannan karon Adams ne yayi maganar.Fatima da ke kusa da mahaifiyarta dan ita ta ke taya ta sana'ar,bushewa tayi da dariya kafin tace "wai dan Allah miye sunan ka?" "Amadu " wata dariyar ta kuma yi kafin tace "sunan kuwa ya dace da kai,amman dan Allah wacce irin ƙwaya kuka sha?" Tsawar da Mama ta yi mata ne ya saka ta yin shiru shi kuwa Adams wani abu ne yaji ya caki zuciyar sa a kallon farko da ya yiwa Fatima.



Mama mai dambu Ƴa ce ga wani babban malami da ke can Maraɗi jamhuriyar Nijar ,aure ne ya kawota Ghana.
Ganin yanayin su Laminu kawai ya isa ya tabbatar ma mutum ba su cikin hayyacin su,dambu ta zuba masu suka ci kafin ta fara yi masu ƴan tambayoyi sai dai wasu su bata amsa wasu kuma su yi shiru.



A kwana a tashi suka yi sabo sosai,su Adams tuni sun fara sana'ar sayar da bola.Soyayya tsakanin shi da Fatima ta ƙullu wacce har yanzu da Amadu take kiran sa duk da ta san sunan sa na gaskiya Adams,Mama mai dambu ba ta da matsala don irin matan nan ne wanda dauɗar duniya ba ta dame su ba.



Sana'ar sayar da bola ta saka su Adams zagaya ƙasashe da dama ,tuni an yi auren Fatima da Adams yanzu haka sun bar garin Ghana su na Nijar a Maradi.Sosai Fatima ta ji daɗin ganinta kusan dangin mahaifiyar ta,a kullum kakanta sai ya aikowa da adams rubutu da ruwan addu'o'i a sannu sihirin jikinsa ya fara warwarewa ya samu kansa.
A nan ya ke baiwa Fatima dukan labarin sa,tayi kuka sosai tare da basa shawarar ya kamata ya tafi can AGADAS amman ya ƙi tafiya yace ba yanzu ba.Laminu ma a sannu ya dawo Nijar da zama,shi ma ya samu matar aurensa.
Sosai suke zumincinsu ta waya saboda ba'a gari guda suke ba,Fatima an samu ciki mai shegen laulayi da kwaɗayi a kullum cikin yiwa Adams liste ɗin abinda ta ke son ci ta ke.




Lokacin da cikin Fatima ya shiga wata na bakwai ta fara yin wata irin rashin lafiya ta tashin hankali,magani ake amman kamar ana ƙara mata cutar.Ganin na asibitin bai Baba Malam wanda ya kasance kakanta ya fara yi mata magani nan fa wani abun mamaki ya faru bayyanar aljana a jikinta,sai aka yi dagaske sannan ta rabu da ita.


Cikin Fatima na shiga watan haihuwa ta sunkuto Ɗan ta namiji,wanda ya ke chocolat ko irin hasken nan na jarirai bai yi ba.
Adams yayi masa huɗuba da sunan BASHEER,wato sunan mahaifinsa a ranar kuma ya zubda hawaye sosai saboda tuna ƙanwar sa Hawas wacce a kullum cikin rigima suke kowanensu na cewa shi zai yiwa Sarki takwara.

An yi biki daidai gwargwado, ɓangaren Adams Laminu ne kawai ya zo bikin sai matar sa tunda bai da wasu dangi.
A haka suka fara renon Basheer har ya fara yin tafiya,har izuwa wannan lokacin kuma Fatima ba ta bar yiwa Adams maganar zuwa AGADAS ba amsa guda ya ke bata da sauran lokaci.



Basheer na zaune ya na wasa haɗi da gwarancin sa,wani ƙadangare ya lalaɓo ya kama wata ƴar ƙaramar fara🦗 Basheer ya kama ƙadangaren ya cire farar daga bakinsa sai dariya ya ke.
Farar ta tashi sama,ta haye bisa igiyar shanya ta na mai ƙurawa Basheer ido........
[26/07 à 16:52] Chamsiya Laouali Rabo: *PAID PAGE🪶*




*LITTAFIN KUƊI NE ƳAR UWA KI BIYA 200 KACAL DOMIN KI KARANTA CIKIN KWANCIYAR HANKALI,DUK MAI BUƘATA TA TUNTUƁE NI TA WHATSAPP* +22795045822 DUK WACCE TA KARANTA MIN BOOK BA TARE DA TA BIYA TA SA A RAN TA INA BIYAR TA 200 KO GOBE.



*J*


Wani irin kuka Basheer ya fashe da shi kafin ya rairafa ɗaki gun mahaifiyar sa,ta ɗauke sa ta shiga rarrashinsa sai dai ya ƙi yin shiru.
Ta fito waje tayi masa wanka kafin ta goye sa a baya ta na ririga shi,an ɗauki lokaci kafin barci ya ɗauke sa sai ajiyar zuciya da ya ke.
Sai da barcin yayi nisa sosai sannan ta shimfiɗe sa,nan ta ci karo da birdina da jikinsa yayi da wani irin ja.Hankalinta ya tashi ta kira Adams wanda ya fara aiki a nan wata asibiti,murya na ɗan rawa tace "Basheer ne babu lafiya duk jikinsa yayi ja kuma kamar da zazzaɓi zai kama shi" "ok ki shigo adaidaita ki kawo sa asibiti" da "to"ta amsa kafin ta kimtsa ta nufi asibitin.




Bayan ya duba Ɗansa ya mashi allura kafin su dawo gida,ashe wasa farin girki dan kuwa tamkar an ƙara ciwon haka jikin Basheer ya daɗa yin ja.
Wunin ranar Fatima a sanyaye tayi shi,wani irin mugun son yaronta ta ke fiye da yadda kowa ke ƙaunar Ɗan farin.
Zuwa dare Adams ya dawo daga aiki,sosai yayi mamakin ƙaruwar ciwon."Miyasa ba ki gaya min ba duba ki ga yadda ya galabaita"cewar Adams ya na duban Basheer wanda duk yayi yaushi kukan ma yanzu ko yayi bai fita.
"Nace ko dai mu kai sa gun Baba Malam sai na ke ganin abun kamar ba na asibiti ba ne" Fatimah ta faɗa ta na shirin fashewa da kuka, Adams irin mutanen nan ne uwanda basu son canfi amman ganin hankalin Fatima ya tashi ya saka shi yarda suka tafi.



Baba malam ya ɗauki Basheer ya saka sa cikin wata ƙatuwar ƙwarya ya fara yi masa wanka,kuka ya shiga yi ya na halbe-halben ƙafa.
Baba Malam zufa ta kariye masa,cikin muryar sa ta tsoffi yace "baiwar Allah miye haɗin ki da jaririn nan ba ki tausayin shi kasancewar sa yaro?"
"Ya cece ni ne sai kuma ya matse min ciki ni kuma naji haushi na rama"muryar wata ƴar matashiyar yarinya ta faɗa tare da basa labarin yadda abun ya faru,malam ya shafi kan Basheer yace "ayya!ai shi yaro ne bai san yayi hakan ba ,ki fita daga jikin sa" "ba zan fita ba ina son zama cikin jikin sa ne"
"Miye sunan ki?"malam ya tambaya ta basa amsa da "Abrar ƴa ga sarki Nurein" jin furucin ta ya saka Baba Malam yin murmushi kafin ya fara karatu nan fa ABARAR ta fara kuka saboda jikinta da ya ke salewa sai kuka take ta na cewa ba za ta cutar da Basheer ba amman sam malam bai saurare ta ba har sai da ya cire ta.




Wani barcin wahala ya ɗauke Basheer,malam ya bada wani magani da za'a shafa masa sannan suka dawo gida.
Adams ya shafi fuskar Basheer yace "yarona ina so ka kasance babban malami kamar dai Baba malam,in shaa Allah zan saka ka makarantar Islamiyya da zarar ka iya magana Boko kuma ba sosai ba" Fatima tayi murmushi tace "Allah ya yarda nima zan so haka ko dan saboda wani babban dalili,ina yawan yin wani mafarki wanda na ke hango Basheer a wani babban matsayi na musamman" Adams ya kalleta yace "yauwa matata dan Allah ko bayan raina ki cika min wannan burin" Fatima ta ɓata fuska tace "mutuwa kuma?Ni dai dan Allah ka bar kira min ita saboda ba zan iya jurar rashin ka ba" ya laƙace mata hanci yace "nan da zarar na mutu da kin gama takaba za ki fara yin kitso da lalle na jawo hankalin jawaru"ta fara buga ƙafafu ta na mai masa dukan wasa a ƙirji tace "Allah kiyaye min har abadan abada ba zan taɓa yin kwanciya da wani namiji ba in ba kai ba"



Tamkar dirar mashi haka yaji saukar furucin ta a ƙawon zuciyarsa,ya janyota ya na kallonta cikin ido yace "kin tabbata?"ta gyaɗa kai yace "nima har abada ba zan yi maki kishiya ba" tayi dariya tace "Allah yasa wannan jarabar ta ka za ta iya barinka ka zauna da ni ɗaya tal" ya matse gefen cikinta yace "Na cika jaraba dagaske?"ta ɗan ture sa dan ta ga idonsa sun fara canza launi da sauri ya riƙo tare da cabkar bakinta.
Suka sauke ajiyar zuciya a tare,ya fara lalubarta ya na yawo da hannunsa ga dukan sassan jikinta.
A hankali yayi masu masauki kan gado kafin yayi sama da rigarta,manyan breast ɗinta da suka cika da madara ya fara tsotsa ya na wasa da gabanta ita kuwa sai wani mutsu-mutsu ta ke ."Dan Allah kar ka shanye masa madara Allah ban masa koko ba yau" Fatima ke faɗa ta na ɗan ture kan Adams amman ya ƙi sakin kan😆 can ya ɗago ya kalleta yace "to gyara min na shiga muhallina tunda an nuna wannan na Basheer ne"ta turo baki kafin ta tashi tayi position ɗin da ya fi so ,shi kuwa dariyarsa ya gumtse saboda ya san sarai ba ta fiya son goho ba.
Ta saki ƙara tace "dan Allah ka bari wlh har cikin hanjin cikina na ke jin ta"bai saurare ta ba ya cigaba da yin aikin sa.






_______________ZINDER

Ranar daren farkon su Hawas sai da Jumma ta toshe kunnuwanta saboda ihu da kukan Hawas ɓangaren guda kuma ta na jin irin yadda AlGabid ke sambatu haɗi da nishi.
Wata irin sha'awa lamarin ya saukar mata,ta lumshe ido ta tunanin Sarki yadda ya having sex da ita a ko wane lokaci in sun keɓe.Ita ɗin kwarkwarar sa ce tun asali, Hawas ce ta mayar da ita Jakadiyar ta sannan kuma uwar ɗakinta ba ta ɓoye ma Jumma komi dangane da rayuwar ta.
AlGabid yayi wani ihu wanda ya maido Jumma daga duniyar tunani, gémissement ɗinsa kawai da ta ke ji a yanzu ya tabbatar mata da shi ɗin jarumi ne sannan ya na son sex kamar yadda Hawas ke bata labari.
Shiru ne ya ratsa kafin can kamar mintin ashirin ta ji muryar Hawas na basa haƙuri ta na cewa ta gaji ko ina na jikinta ciwo ya ke yi mata.
Can kuma kukan Hawas ya yawaita yayinda AlGabid ya fara ihun sa,hakan ya tabbatar ma da Jumma sun koma 2coup ne.



Washegari
Dakyat Hawas ta iya zama duk da kuwa yadda Jumma ta gasa ta, AlGabid kuwa an shiga cikin gari.
Wani ƙaton gidan caca ya shiga,nan ya buga wasa ya canye kusan 50k hakan yasa ya dawo gida da murna.
Manyan kaji ya sawo Jumma tayi masu kalaci suka ci suka ƙoshi kafin ya janye Hawas ya kaita ƙurya ɗaki,da sauri Jumma ta bar masu gidan ta na Istigfar😂
"Ina dalili sai kace tantabaru kullum abu ɗaya,in shaa Allah ba zan sake wuni gidan nan ba na ga yaran nan so suke su jefa ni cikin wani hali ina zaman zamana mtws "ta ja tsuki kafin ta sayi gyaɗa ta zauna ƙarƙashin innuwar bishiya ta na ci.
Sai yamma lis sannan ta koma gidan,a falo ta tarar da su AlGabid ya rungume Hawas.Wani irin mugun so ya ke yi mata,a kan Hawas zai iya kashe kowa ba tare da shakka ba.Jumma ta wuce ɗaki ta na tunanin mafita dan gaskiya ba za ta iya cigaba da zama a nan ba,ta na son ganin Sarki a kusa da ita duk da dai ba kullum ya ke kusantar ta ba.




A kwana a tashi babu wuya gun Allah cikin Jumma ya tsufa haihuwa ko yau ko gobe, Hawas kullum burinta bai wuce ta samu ciki ba amman shiru.
Da kuɗin da AlGabid ya ke samowa gidan caca ya zuba mata kuɗin makaranta inda ta ke karantar comptabilité.Tuni ya sauya masu wani gida a yanzu ɓangaren Jumma daban ya ke,wajen yawon cacar AlGabid ya haɗu da wani frend wanda kusan shine AlGabid ɗin ke canye kuɗin da ya ɗora.Burin AlGabid na son yayi kuɗi ya saka frend ɗinsa jan ra'ayinsa,bai wani ɓata lokaci ba ya shiga ƙungiyar ASOMA wacce ta shimfiɗa masa doki ciki har da yin luwaɗi da yin zina.



Ya lafiyar kura balle an gama da bugu,shiga ƙungiyar ASOMA ta zame ma AlGabid tamkar wanda aka ba lasisin fasiƙanci.Rana guda Allah kawai ya san iya ƴan matan da ya ke keta haɗinsu,dayansu taimako suke zowa nema gun sa shi kuma ya shimfiɗa masu sharaɗin sai in sun yarda ya kwanta da su.Duk wacce ba ta amince ba sai dai aji an tsinci gawar ta,cikin wannan yanayi Jumma ta haifo Ɗan ta.Tun ya na jariri AlGabid ya ƙwallafa rai ga jinjirin.Sosai ya ke yi masa hidima ita kuwa Jumma ta ɗauka saboda har yanzu bai da Ɗan kansa ne.





Yadda aka fara saka ma AlGabid ido yasa shi barin Zinder ya dawo garin Maraɗi da zama,tuni dama ya gina ƙaton gidan sa.
Hawas kullum cikin kukan rashin haihuwa ta ke yi masa,a ƙarshe dai suka je asibiti aka ɗora ta bisa magani saboda taushin da mahaifarta da tayi.Cikin ikon Allah ta samu ciki sosai suka yi murna sai dai ya na kaiwa wata biyu ƙungiya ASOMA ta buƙace sa,kamar daga sama Hawas sai jini ta gani ya na mata zuba ana zuwa asibiti aka ce cikin ne ya zube.
AlGabid sosai shi ma yaji zafin sacrifice ɗin Ɗan cikinsa da ƙungiya ta ɗauka,amman babu yadda zai yi sai ya shiga baiwa Hawas ƙwarin gwuiwa a haka har aka ɗauki shekaru biyar.



Ahmad Ɗan Jumma tuni yayi wayo ya na kiran AlGabid da Daddy ita kuma Hawas Momy dan tuni riƙonsa ya dawo hannun Momy tun bayan da Jumma ta yaye sa.



*HOTEL HORIZON*

Banda gémissement babu abinda ke tashi ɗakin,Daddy ne kan ruwan cikin wata ƴar baby wacce ba za ta wuce 20years ba.Duk da vierge ba ce amman Daddy yayi ƙarfinta sosai nesa ba kusa ba,kuka kawai take ta na neman ya ƙyaleta amman ina Daddy bai jin kira sai sukuwa ya ke kan ta.Tsawon lokaci kafin ya sauka kanta ta na goge Dick ɗinsa da wani ƙyalle,yarinyar ta ware idonta ta dube sa garjejen ƙato da shi daga zuwa neman taimako ya murƙushe ta.
Muryarta ba ta fita sosai tace "duk abinda kayi da Ƴar wani kai ma sai an yi da Ƴar ka"wani naushi ya kai ma bakinta kafin ya fara tsafata kamar walƙiya yarinyar ta ɓace ɓat,wanda kuma démon ɗinsa ne suka ɗauketa daga ɗakin.
Tuƙi Daddy ya ke amman hankalin sa sam ya ƙi kwanciya bai san ko miyasa ba,ya na shiga gida Ahmad ya rugo ya rungume sa bai jin sa daidai hakan yasa bai ɗauke sa ba.
Momy ta ƙaraso da murna fal ranta tace "Tarhanine yau muna cikin farin ciki Ahmad zai samu ƙanwa ɗazu naje asibiti aka ce ina ɗauke da ciki kuma har scanning an yi min ashe mace ce zan haifa" zuciyar Daddy ta buga ya na mai jin furucin Ramlat yarinyar da yayi ma fyaɗe yanzu su na dawo masa a kai......
[27/07 à 12:50] Chamsiya Laouali Rabo: *PAID PAGE🪶*




*LITTAFIN KUƊI NE ƳAR UWA KI BIYA 200 KACAL DOMIN KI KARANTA CIKIN KWANCIYAR HANKALI,DUK MAI BUƘATA TA TUNTUƁE NI TA WHATSAPP* +22795045822 DUK WACCE TA KARANTA MIN BOOK BA TARE DA TA BIYA TA SA A RAN TA INA BIYAR TA 200 KO GOBE.


*K*



"Tarhanine yau ina cikin farin ciki" Momy ta faɗa ta na mai shigewa cikin jikinsa,ya rungume ta gam ya na jin son su ita da Ɗan cikin na ɓarka bango da tsokar tsakiyar ƙirjin sa.Damshin hawayenta suka jiƙa rigar sa har yaji ɗumin su,ya ɗan cire ta daga jikinsa ya na kallo kafin ya tambaye ta "minene Tarhani?"ta goge hawaye tace "na tuno da gida ne,mi zai hana mu je tunda yanzu mun samu ƙaruwa ina ga albarkacin sa za su yafe ma" fuskar Daddy tayi baƙi ransa ya ɓace cikin masifa yace "duk ranar da naji kin sake ambaton ko da garin Agadas ne sai na yi maki abinda ba ki taɓa zato ba "ƙuuu ya nufi ɗakinsa ya barta nan tsaye.
Jumma ta ƙaraso ta dafa ta tace "kiyi haƙuri amman jadawalin komawar mu Agadas ba ya nan kusa sai an ɗauki shekaru masu tsayi dan haka ki cire hakan daga zuciyar ki" ta goge ido tace "amman Jumma ai su ɗin iyayena ne,miyasa ba zan je na nemi albarkar su ba?" Jumma tayi wani murmushi wanda ita ɗaya ta san ma'anar sa kafin tace "Uwar ɗakina ke yarinya ce har yanzu ba ki san wa kike aure ba,zuwa AGADAS daidai ya ke da fitar ruhin ki dan haka in ki na son rayuwarki ki cire wannan a ran ki" "haba Jumma ya za ki ce haka?wannan sam bai dace ba"cewar Momy ta na mai yin tafiyarta ɗakin Daddy.
A zaune ta tarar da shi bakin bed ƙugunsa ɗaure da towel alamun ya fito daga wanka ne,ta zauna kusa da shi ta mai ɗora hannunta kan kafaɗar sa tace "Masoyi fushin ya isa haka,ka zo ka ci abinci yau ni na girka ma da kaina"ya sauke ajiyar zuciya ya dubeta wani irin sonta ya ke wanda baki ba zai iya furtawa ba.
Ya laƙace hancinta yace"Allah sa dai yayi daɗi dan an ce mata masu ciki sun fiya sangarta"tayi dariya ta ɗan kishingiɗa kan jikinsa tace "Allah Hubby yayi daɗi sosai ina ga yau sai kayi santi dayawa saboda girkin na daban ne" ya zagaye ƙugunta yace "kenan har kin fi Jumma iya girki?amman kam naji daɗi kice gobe in gayyato abokaina su ci girkin ki?" Ta ɗago da sauri tace "kenan kayi abokai?naji daɗi sosai mijina shi ma yanzu ya na da aboki ba ma ɗaya ba dayawa"



"Kin fiya surutu Tarhani zo ki shirya ni mu je mu ci abincin yau akwai wani meeting da za mu yi"cewar Daddy ya na mai tashi ya nufi drower,Mamy ta isa gun sa ta fara zaɓar masa kayan da zai sa maras nauyi.Tsaf ta shirya sa kafin su fita falo,Jumma na zaune ta baiwa Ahmad abinci a baki.Daddy yayi tsaye ya na kallon yadda Ahmad ke lashe hannun Jumma sai yaji wani kishi ya taso masa,duk ƙoƙarin hana kansa da yayi amman sai da ya tanka "Jumma yanzu abinci kike basa da hannu babu cokali ne?"ta ɗago ta kallesa sam yanzu ba ta iya karantar tunanin AlGabid balle ta ga abinda ke cikin zuciyarsa.
"Shi yace na basa wai nayi masa irin na Bébé "ta bashi amsa cike da ladabi da kuma tsoronsa,ya zo ya ɗauki Ahmad ya kaisa can table à manger kafin yace "daga yau nan za ka rinƙa zaunawa ka ci abinci kaji ko?" Ahmad ya gyaɗa kai yace "to Daddy"shi kuma ya saki murmushi kafin ya cewa Momy"zo kiyi servir ɗin mu " kamar jira take ta zuba masu abincin suka fara ci su biyu a plate ɗaya sai tambayoyi ya ke yiwa Ahmad game da makaranta.




Jumma ɗaki ta koma ta na jin haushin yadda ake nuna mata iko ita da Ɗanta,zuwa can kuma ta sauke ajiyar zuciya tuna yadda suke son Ahmad kamar su suka haife sa.
Kwanciya tayi kan gado,babu jimawa ta fara jin sanyi na ratsa ta kamar wacce aka sa cikin ƙanƙara.Macen nan wacce ta zama abokiyar hirar ta a cikin mafarki ita ta bayyana gare ta, Jumma ta ke dadaɓawa ta na yi mata raɗe a kunne.Tsawon lokaci kafin ta tafiyarta Jumma ta fara barcin ta mai kamar mutuwa,mafarkai barkatai ta ke yi uwanda tamkar alerte ne ake yi mata dangane da abinda zai faru cikin ƴan kwanakin nan.





Su na gama cin abincin Daddy ya ja Ahmad suka wuce ɗakinsa,ita kuwa Mamy kallon tv ta fara yi.
Wanka ya yi masa kafin shimfiɗe sa kan bed, Ahmad ya yiwa Daddy ƙuri can idonsa suka fara lumshewa Daddy ya sauke ajiyar zuciya yayinda kwanyar sa ta fara tambayar sa ya fara neman Ahmad tun yanzu koko sai ya ƙara wasu shekaru?
Ya shafi fuskar yaron kafin ya manna masa kiss a goshi,kaya ya canza ya fesa turare ya ɗauki makullin motar shi.




"Zan tafi sai na dawo in dare yayi sosai ku rufe ƙofar ɗakin" Daddy ya faɗa kafin ya fice,Mamy tayi masa fatan a dawo lafiya.Daddy ya yiwa mota key ya wuce can inda za su yi meeting ɗin,ƙaton hall ne duk wanda ka gani a nan to Ɗa ne ga ƙungiyar ASOMA.Dukkansu sun saka baƙaƙen kaya kamar yadda tsarin ya ke, Daddy na isa shi ma ya kama layi cikin ƴan uwansa ya suna jiran shugaban ya iso.


Bayan sun gama meeting Daddy ya koma gida,Mamy na barci taji ana shafar cikinta da sauri ta buɗe ido ta zube su kan Daddy.Haka kawai ta samu bakinta da yin addu'o'i,shi kuwa ya ɓata fuska ya na cewa "kamar kin ga wani mugu shine kike wani karanto min addu'o'i?"
Jikinsa ta faɗa ta na cewa "mafarki nayi za'a cire min Babyn,wlh in hakan ta faru kashe kaina zan na huta haba ina dalili tun ɗazu na ke jin wani abu kamar ana suivre ɗina" jikin Daddy yayi sanyi,shi kuwa bai shirya rasa matar shi ba amman ya san ya zai yi ya shawo lamarin.



Rarrashinta ya fara yi ya na kwantar mata da hankali a haka har barci ya ɗauke ta, Daddy ya fita ya shiga ɗakin sa.
Gaban madubi ya koma ya na yin suratai can sai wani haske ya bayyana tare da wani hayaƙi,fuskar Daddy a yamutse yace "ya mai girma Shugaba ayi haƙuri na canza Magaji na bayar da Ahmad a matsayin wanda zai gaje ni amman a ƙyale Ɗan cikin matata" ya na gama faɗa ya sunne kai,daga cikin mirror ɗin wata murya tace "amman kaji sarai abinda Demon suka ce, wannan cikin na matar ka barazana zai zama ga ƙungiyar ASOMA,sam babu alkhairi a tattare da shi.Amman babu damuwa za mu karɓi shi namijin matsayin magajin ka in ya kai shekaru goma sha biyu,sannan ka sani daga an haifi yaron cikin matar ka zai zamana cikin kulawar ƙungiya za mu tanadi aljannu wanda za su rinƙa gadin jinjirin har izuwa shekaru 25"
Daddy ya sauke ajiyar zuciya kafin yayi na'am da lamarin, wannan hayaƙin ya fito daga cikin madubi ya shiga jikin Ahmad wanda ke kwance ya na barci.





Bayan kwana biyu Daddy ya gayyato wani babban abokinsa na kasuwanci,sannan kuma ɓangare guda abokin tarayyar aikin jarida.
Sosai Mamy tayi masu girki mai daɗi,su na ci su na hirar jaridun da za su buga cikin satinan.Sai Daddy ya lura da irin kallon da abokin nasa ke bin Mamy da shi,ya gimtse fuska saboda akwai shi da kishi sosai.
"Abokina ka dace da mace mai kyau sai dai sam ba ta dace da kai ba,yadda kake mugu in ta sani na san barin ka za ta yi.Amm... nace wai mi ya jawo ra'ayin ka har ka shiga wannan tsarin na ga har Babyn cikin ta ma an ɗora masa matakan tsaro?" Ɗan Jarida Kader ya faɗa ya na kallon Daddy cikin ido wanda ya nuna sam bai gane abinda ya ke nufi ba,Kader ya murmusa yace "za ka iya ɓoye ma kowa ka na cikin ƙungiyar matsafa amman banda ni saboda tun ranar da mu ka fara ganin juna na ga hakan a goshin ka" Daddy ya miƙe yace "dan Allah ko za ka taso mu tafi wani gun"babu muso Kader ya miƙe bayan ya yiwa Mamy sallama Daddy ya ja sa zuwa wani daji.



Suka fito daga mota Daddy yace "na tsani

Please Login or Register in order to submit comment