Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

gashi nan har sai da ka jama kanka zaman guri ɗaya, da da ƙarar kwana ma yanzu wani labarin ake ba naka ba. Ni dai yanzu ga saƙo, Oga Mole da Oga Dagger sunce gobe zasu turo sabon driver ka turashi ga mutanen nan ya maye gurbin ka, zaɓi ya rage naka kayi koka kuskure kai ne zakai kuka, dan a yanzu ba kai za'a hara ba ƴaƴanka ne ko matarka”...
      Yana gama faɗa ya miƙa batare da ya saurari magiya da roƙon Baba Driver ba.....

★>><<<<★>>>><<★
        ★DUBAI★

   Ganin yanda Nabeeha ke faman haɗa kaya ya bama Ismat data kawo mata breakfast har ɗaki tsoro. Duk yanda taso daurewa saita kasa. Cikin damuwa ta ajiye tray ɗin da take ɗauke da shi ta nufeta. Hannunta ta riƙe cikin rauni da damuwa ta ce, “Aunty wai mi kike yi haka ne? Ina zaki kike haɗa kaya?”.
         Hannun nata ta fisge, kukan da take faman riƙewa tun daren jiya saboda taurin zuciya a karo na farko ta fashe da shi..........✍️


12

.........“Ismat zan koma ƙasata, wlhy na gaji da wannan rayuwar, bazan iya ɗaukar huɗubar Momy ba, gara na koma gidan mijina nai zaman jiran dawowarsa ko nan da shekara hamsin ne ma ba ashirin da biyar ba”.
       Ajiyar zuciya mai ƙarfi Ismat ta sauke, dan koba komai itama an taɓo mata inda ke mata ƙaiƙayi dama. Ta kama hannun Nabeeha suka koma bakin makeken gadon ɗakin da yaji shinfiɗu na alfarma, dan duk da haɗuwar gidan da komai na cikinsa ɗakinta na musamman ne. Gyara irin na ƴar gata Adeel yasa akai mata. Hannayenta duka a cikin na Ismat ta ce, “Aunty wlhy koni ina bayanki ki koma gidanki, dan ita Momy idannunta sun rufe da son kuɗi bata duba abinda muke so koya dace damu. Ita kawai tafi kallon abinda zata samu. Gamu dai a cikin ƙaton gida a kuma ƙasa irin ta Dubai da kowa ke buƙatar yazo, amma wlhy Aunty Jiddah ta fimu kwanciyar hankali, tana rayuwar auren ta ga yaranta abin sha'awa, shiyyasa wlhy nima na fara ji a raina zanyi na nata na koma gidan Abba na bashi haƙuri na samu miji nayi aure. Dan in har muka cigaba da rayuwa da Momy anan wataran sai mun lalace, dan waɗan nan shaggun mutanen babu abinda suka iya sai son mata kamar su babu matan a cikin nasu ƙabilar”.
       “Ismat wlhy ni duk bama wannan ba, babban abinda ke bani mamaki da Momy itafa kawai na kashe aurena saboda wannan mutum yace mata aurena yake son yi, haba miyasa ba zatai tunanin daya dace ba, dukiya irin ta mutumin nan, da nasaba ta gidan mulki, mulkin ma mai ƙarfin gaske ne zai zauna wani auren baƙar fata ƴar Africa saboda rainin hankali da ɗaukar mutane jakai. Kiga yanda suke wulaƙanta matan African fa kamar wasu dabbobi dan ko bayi na baya sun fi matan da ake kawo musu suna iskanci da su a yanzu mutunci da daraja. Wlhy Ismat ina son mijina, duk da ina jin takaicin auren shegiyar yarinyar nan har yanzu a zuciyata....”
       “Na sani Aunty, ki share wani batun yarinya kawai muyi tafiyar mu, dan uwarta mune zamu miki maganinta, da ƙafarta zata bar gidan batare da kowa ma ya sani ba ta koma ƙauyen su, idan tace ita ƴar hau ce mu ƴan hau-hau ne to”.
     Ajiyar zuciya mai ƙarfin gaske Nabeeha ta saki, tana mai jin nutsuwa da gamsuwa da zancen autar tasu. A gefe zuciyarta na jin matsanancin kewar mijinta da buƙatar son kasancewa da shi da akoda yaushe take yaƙi da kanta a kai, sauƙi-sauƙin ma da take samu kullum cikin mafarkinsa da yanda yake tafiyar da ita a shimfiɗa take, shiyyasa take samun sassauci da jinsa kamar a kusa da ita har yanzu.....

        Da baya-baya Hajiya Hasiba tabar bakin ƙofar ranta a matuƙar ɓace da tattaunawar yaran nata. Ƙayataccen ɗakinta ta shiga, ta zauna a bakin makeken nata gadon hannunta dafe da kanta. Jitake kan nata na wani mugun sara mata, sai dai abinda ke mata kai-kawo na takaicin yaran nata na son danne ciwon. Lallai lokaci yayi da zata nunama su Nabeeha ita ba sankaran uwa bace sha-sha-sha kamar yanda suke tunani. Taya zata bari ma Nasiru yaci nasara a kanta, bayan ya rabata da Jiddah ya rabata da Nabeeha da Ismat da suka rage mata kuma. Ta jima da fahimtar soyayyar da Ismat kema Ja'afar, sai dai bata damu ba ganin yanda shi Ja'afar ɗin yaƙi kulawa, amma yanzu ta fahimci Ismat na zuga Nabeeha ne su koma gidan ubansu saboda son da take ma Ja'afar, kenan da sunje sun kwantar ma da ubansu kai itama sai ya aura mata shi, shekenan ita kuma A'isha ta haifama ƴaƴa ko? To kuwa zasuci ubansu.
      Da wannan tunanin tai ƙwafa, tare da miƙewa zuwa gaban wadrobe ɗinta, ta ɗibo duk passport ɗinsu dake wurinta, cire na Nabeeha da Ismat tayi ta canja musu waje, daga haka ta hau shirin fita. Dan tana buƙatar ganawa da Adeel yanzu nan basai gobe ba.....

      
 §§§§§§§§§§§§§§§§
       ★EGYPT ★
      
             “Mammah muje ki huta yau kam kin gaji fiye da kullum. Ga su Yaya Ma'aruff nata kira nasan burunsu kawai suji yanda results ɗin suke ne. Aunty Ummi ma naga ta kira video call ta WhatsApp”.
Received      Murmushi Mammah tayi, cikin sauke ajiyar zuciya ta ce, “Ammar yarana duk sunyi kewata ne, nima ina tsananin jin kewarsu. Dan haka ni kam ba sai sati biyun nan ya cika ba zuwa jibi tunda sunce babu wata damuwa suna bamu maganin nan kawai mu koma gida”.
         “Duk yanda kike so haka za'ai Mammah”. Yay maganar yana ɗan rungumota ta gefe, dama kuma suna tafiyar ne hannunta riƙe a nashi. A yanda ya ɗan rungumetan yana dariya itama yana murmurshi da kai masa rankwashi a kai yasa basa kallon gabansu balle mai tahowa. Karaf kuwa sukaci karo da wani abun da ya saka Mammah faɗin, “Subahanallahi”. Shima sai Ammar ɗin ya sake ta yana waiwayawa da ambaton, “Ya salam”. A dai-dai lokacin shima wanda sukai karon ya ambaci, “Subahanallahi” ɗin yana kaiwa duƙe da son riƙo takardun hannunsa da suka tarwatse a ƙasa. Cikin sauri Ammar ya bishi shima yana ƙoƙarin taimaka masa da sake faɗin, “I'm sorry sir”.
       Fuskar mutum da murmurshi ya ce, “Karka damu ɗana, nima harda nawa laifin hankalina nakan takardun ne shiyysa ban lura da tahowarku ba. Mama kiyi haƙuri kem......”
    Ya kasa ƙarasawa saboda dai-dai ya ɗago ne zai kalla inda Mammah ɗin take sukai ido biyu. Dan itama ta miƙo masa takardar data ɗakko ne datai gefe zatai magana a lokacin, sai ta dakata cak tana kallonsa. Ko shekara dubu tayi bazata manta wannan fuskar ba a duniyarta, balle shekarun da basu wuce talatin ba. Jin sunyi shiru Ammar daya gama tattarowa shima ya juyo yana kallon su, Mammah ya fara kallo datai tsaye ƙyam baki buɗe tana kallon mutum, da sauri ya maida kallonsa kansa shima. Ai da sauri ya wani ja baya yana waro idanu waje da faɗin, “Ya rabbi! Mammah waye shi?”.
      Mammah da gaba ɗaya kanta yay wani dimmm ta gagara cewa komai, sai hannunta dake ƴar rawa har sai da Ammar ya matso ya riƙota jikinsa, sai dai har lokacin idanun nasa akan mutumin da alamu ya nuna shima dai yayi sumar tsugunne ne......
       
>>✿<<>>✿<<>>✿<<
       
           “Assalamu alaikum”.
    Aka kwaɗa sallama daga bakin ƙofar falon bayan anyi knocking har sau biyu. Ƙaramin tsaki Mu'azz dake zaune shi kaɗai a falon yana cin abinci yaja, ya tsani tashi yana cin abinci, dan yana tashin shike nan abincin ya fita a kansa kuma. Hanyar kitchen ya kalla inda yake jiyo surutun Nimrah da dariyar Biebah. Sai kawai ya ɗaga murya ya ce, “Ninah!”.
       Daga can ta ce, “Kai Yaya Mu'azz miye kuma dan ALLAH? Bana kawo maka harda ruwa ba”.
          “To uwar son jiki, dalla fito kiga waye ana knocking ne”.
      Baki a sama ta fito, tana sanye cikin shirt da riga na lass milk da furanni coffee. Tayi ƙyau sosai daka ganta kaga ƴammatan zamani masu shegen iyayi da rawar kai. Harta nufi ƙofa ya ce, “Haka zaki fita ba hijjab?”. Baki ta ƙara turawa gaba, ta dawo ta ɗauka hijjab da sukan ajiye a falon saboda irin haka, dan Mammah ta saba musu sakawa musamman idan akai baƙon ido ko suka saka ƙananun kaya, wani lokacin ma sai taga kamar anfi takura mata da sakawa fiye da Ruky da Aunty Biebah. Sai da ta saka ta zura hannayensa sannan ta nufi ƙofar da aka sake bugawar, sallamar maigadi ta amsa tana buɗe ƙofar. Ya ɗan ja baya yana gaisheta.
          “Baba ni dai ka daina rissina min dan ALLAH. Ina wuni?”.
    Murmurshi maigadin yayi da faɗin, “Ai girmanki ne Hajiya. Dama baƙone yazo yace kuma sabon driver ne Malam Buba tsohon Driver ya aikosa”.
     Ɗan jimm tayi sai kuma ta ce, “Okay to bari na sanarma Yaya Mu'azz, dan su Uncle's duk basa nan. Ammie da Ummie ma sun tafi gidan Mom (Aunty Mimi suke kira Mom) data haihu ɗazun”.
       Fuska ɗauke da murmushi ya ce, “ALLAH sarki ALLAH ya raya, ya albarkaci abinda aka samu”.
     “Amin ya rabbi”.
Ta faɗa tana rufe ƙofar ta juya ciki.
“Yaya wai sabon driver ne, kuma Baba Driver ya turoshi”.
     Ɗagowa Mu'azz yay yana kallonta, sai kuma ya maida kansa ga television yana faɗin, “Oh to sannunsa da zuwa. ALLAH ya iyakance min jigilarku kullum kuna damuna da surutun ku da fitina. Ki haɗa abinci ki kai masa dan abinci nake ci sai na kammala na fita mu gaisa”.
Received          Sai da ta cika baki da iska cikin ƙunƙuni ta nufi kitchen tana faɗin, “Ni wlhy yau ƙafafuna duk ciwo suke, dan anga Mammah bata nan sai wahala ake bani, yau tunda muka dawo school ban huta ba komai ni....”
     Fiiiffgg! Filon kukera da Mu'azz ya jiho ya sameta a baya. Tako dage ta ƙwalla ƙarar data saka Biebah fitowa daga kitchen da gudu tana tambayar lafiya da riƙo Nimrah ɗin. Kai Mu'azz ya girgiza cike da takaici yana nuna fillon daya jefeta da shi.
       “Small Mom fillo fa kawai na jefa mata dan tana min ƙunƙuni shine take wannan ihun. Wlhy Ninah kiji tsoron ALLAH. Wai uwar wa ma ya hanaki bin su Ammie ne kamar yanda Ruƙayya tayi?”.
        “ALLAH sai na gayaka da Uncle, kuma ai dai naji zafi. Tunda na dawo kaketa sani aiki, na maka gyaran ɗaki, kace na maka ɗan wake, duk baka gani ba sai da ka ci zalina”.
     “Oh gori kike min saboda kin min gyaran ɗaki da ɗan wake? Lallai ma Ninah ni ko”.
    Kai Biebah ta girgiza da jan ƙaramin tsaki ta koma ciki tana faɗin, “Kudai bazaku taɓa canjawa ba ALLAH ya shirye ku. Ba sai ku cinye kanku ba jarababbu. Wlhy na ƙagara Mammah ta dawo gidan dan kun isheni”..........✍️
    
15

........Shi ma'abocin ibada ne da ƙoƙarin ganin ya kiyaye dokokin UBANGIJI da kusantuwa da shi a lokacin da yake rayuwa kamar kowa. A yanzu daya ɓuya bisa faifan ƙaddararsa da jarabawa da makircin masu makirci hakan bai sauya komai ba. Sai himma da dagiya da hakan ya ƙara masa wajen sake kaɗaice UBANGIJI da bauta. Halin da yake ciki bai taɓa sakawa yaji kasawace ko tauyewa daga UBANGIJIN SA ba. Bai kuma taɓa jin nasara ce ga azzalumai ba. Bai taɓa mantawa da ƙasar da talakawan ƙasar ba. Yanda yakema kansa addu'a da zuri'arsa haka yake addu'a ga ƙasa baki ɗaya.
     Tabbas a siffa ta jikin ƙarfi da ALLAH ya bashi zuwa yanzu ya risina, sakamakon canjawar tsarin abincinsa zuwa zaɓin wanda ake ciyar da shi a yanzu. Shiyyasa ya zaɓi ɗaukar matakin yin azumi yau, gobe ya huta, azumi ibada ce mai girma, sannan kariya ce daga jarabawar ɗan adamtaka ta lafiya da halittun jiki da UBANGIJI ya ni'imata mu da su musamman akan abokan rayuwa. Nauyin jiki da raunanuwar ƙarfi bai sa ya gaza wajen ƙoƙarin cigaba da ƙarfafa ƙashi da tsoka da sauran ƙarfin daya rage masa ba, dan a cikin wannan nan dai tsukun ɗakin da yake ciki yakan gudanar da ibadarsa ya kuma motsa jiki da salo-salo irin nashi. Rashin ƙarfafa damuwa a zuciya, ya bashi kariya daga cututtukan zamani irin su hawan jini balle ciwon zuciyar da maƙiya ke fatar masa a kowane motsinsu. Ya riga ya amince UBANGIJI shine mai komai da kowa, idan kunga alkairi daga gareshi ne, saɓanin hakan daga shaiɗan ne ko halayenku ko jarabawar da zata sake ɗaukaka darajar ku zuwa wani mataki na duniya ko lahira. Yayi imani da hakan shiyyasa damuwa ta kasance abu na ƙarshe da zai iya cewa yana yi. A duk sanda ya tuna da ahalinsa musamman jajirtacciyar uwa irin Mammah, yakan mata addu'a da fatan samun nutsuwar zuciya daga shiga damuwar halin da yake a ciki. Hakama ƴan uwansa da suke masa kallon uban da matarsa daya tabbatar soyayyarsa mai ƙarfi ce a zuciyarta. Hatta ƴar amanarsa tana nan zaune daram a zuciyarsa, yana kuma mata addu'a da fatan rayuwa mai nasarori a yau da gobenta, sai dai daga ita har Nabeeha yana jiran wani lokaci ne da zai sawwaƙe musu suje suma su sake gina sabuwar rayuwar su.
       Bai yanke hukuncin fita a wannan wajen ba, dan bashi da wani tabbacin fitar. Sai dai yana fatan aikin daya ɓuya domin yinsa da hana Imran shiga cikin tarnaƙin su tabbata. Dan in har ALLAH ya bashi tsohon rayuwa a kurkukun nan, akwai matsayin da Imran zai kai a gidan soji da zai sa babu wanda ya isa hanashi zuwa ziyartarsa a-kai-a-kai. Idan kuma har UBANGIJI ya bashi damar cika shekarun da suka ɗiba masan ya tabbatar lokacin da zai fita koda bashi da ƙarfin jiki dana aiki, yana da zuciyar bin waɗan can azzaluman ɗaya bayan ɗaya ya hukunta su da hannunsa. Balle ma ko a yanzu ya gama shirya in har yay wasu shekaru a wajen nan sai ya nema hanyar dinga fita yana aiki yana dawowa koda a ƙarshe zai bayyana kansa a ƙarasa yanke masa hukuncin ɗaurin rai da rai koma kashe shi kai tsaye....
       Motsin buɗe ƙofar da akai ya saka tunaninsa katsewa, dan yana duk wannan tunanin ne tare da push-up daya sabama kansa yi sama da ɗaruruwa a kowane rana koda yana azumi. Dan haka har yanzu jikinsa a bubbuɗe yake sai dai raguwar ginanniyar tsoka da bata samun sinadarin da take buƙata kamar baya. Daga yanda yake push-up ɗin kawai ya ɗan ɗago idanunsa ya kalla yaran sojin guda biyu ya janye yana cigaba da abinsa.
     Suma sake nutsuwa duk sukayi, dan su sun san badan zaki na keji ba basu isa ziyartar ko gefen dajin da yake farauta ba. A tare suka ƙame tare da yin salute ɗinsa, kafin na gefen damarsa ya furta, “Sir kana da vistor ne”.
      Cak ya ɗan tsaya na sakan, sai kuma ya cigaba da abinda yake batare da yace da su komai ba. Fin mintuna uku, dan har sai da ya cika adadin da yake buƙata kafin ya tashi da ƙyau tamkar ba shi ya gama push-up ɗin ba yaja ƙaramin towel dake jikin ƙarfen gadon kusa da sallaya ya fara goge hannunsa zuwa wuyansa. Sanye yake cikin uniform ɗin prison ɗin, amma hakan bai hana su kasancewa fes ba alamar baya barinsu da datti, sai dai sun koɗe sosai alamar tsufa da gajiya.
A karo na farko ya furta, “Tsawon shekaru biyar kenan a tsarin jadawalin da doka ta sharɗanta a kaina No visitors, no communication. Miya canja hakan a yau daga dokar?”.
     Sake duƙar da kawuna sukai, kafin ɗayan yay magana cike da girmamawa. “Sir muma bamu sani ba. Umarni kawai aka bamu na zuwa da shi inda kake”.
      Idanu ya zuba musu sosai su duka biyun. Wani ɗan murmurshin gefen baki da shi kaɗai yasan yayi kayansa yayi. Ya ajiye towel ɗin a kan ƙarfen gadon ya taka a nutsensa cike kuma da tafiyar nan tasa ta nutsuwa, dattako zuwa gabansu bayan ya saka slippers a ƙafarsa.
       “Ku aikata aikin soja, Captains. Na fahimta.”
     A tare suka sara masa, zukatansu na sake jin rauni, ƙaunarsa da girmamawa.
    “Sir… I’m sorry.”
Suka sake faɗa a tare. Bai ce da su komai ba face miƙa musu hannayesa duk biyu. Dan doka ce fita da shi sai da handcuffs. Jikin sojan har ɗan rawa-rawa yake a ƙoƙarin ɗaura masa handcuffs ɗin, haka dai ya gama suka koma gefe suka bashi hanya. Shine ya fara fita sannan suka bi bayansa har ɗakin ganawar. Vistor ɗin nasa ya juya baya, dan haka bai fahimci ko wanene ba sai da ya zauna a kujerar da aka tanada domin shi.....
 
<<<>>><<<>>>
   ★EGYPT★

       “Mammah dan ALLAH ki daina kukan nan ya isa haka”.
    Ammar ya faɗa cikin tashin hankali muryarsa na rawa idanunsa shima cike da hawaye. Sai kuma ya dubi mutumin da shima ke sharar hawaye ya ce, “Bawan ALLAH ka min bayani dan ALLAH. Minene alaƙarka da Mammah ta? Ku taimaka ku sanar min kada zuciyata ta fashe, dan kukan Mammah ba ƙaramin azabtarwa bace mai ƙuna a zuciyata”.
        Hawaye mutumin ya sake sharewa da handkachiff harda ɗan fyatar majina. Kafin ya kalla Ammar cikin rawar muryar alamun tahowar wani sabon kukan ya ce, “Ɗana ka kwantar da hankalinka, duk da ban san wanne a cikin ƴaƴan nawa ba ina ji a raina ko Bilalu ko Abdul-rasheed (Ammar) ne kai. Dan kune dai ƙananu da zan iya gani a wannan shekarun ba Haysam ko su Ja'afar da Ma'aruff ba”.
    Kafin Ammar yay magana cikin zafi Mammah ta ce, “Har kana iya cigaba da riƙe zuri'ata a cikin ƙwaƙwalwarka amma ka gagara waiwayen inda nake Tasi'u....?”
        “Wlhy Adda A'isha kunya ce ta hanani, tsananin kunyarki nake ji da tsoro da nadamar son zuciyata. Ina ganin bazaki sake kallo na ba a rayuwarki, bazaki sake son ji koda daga wani ne kina da ɗan uwa irina ba. Adda A'isha ni azzalumi ne butulu da ban cancanci gafara daga gareki ba balle marigayi Yaya Abdul-rasheed, dan kuwa mun kasance butulu da ga ni har Bashir da danginsa......”
        “Bashir bai kasance butulu a gareni ba, dan kuwa na tabbatar idan shine a raye komai girman laifin da yake ganin ya min bazai ɓoyema ganina a tsaho waɗan nan shekarun ba. Haba Tasi'u, kun maida ni mara kowa a duniya, mara gata, mara dangi gaba ɗaya. Badan Yaya Nasiru ba da nace ban san daɗin zuri'a ba a duniya. Da ƴaƴan Kawu kamar sun waiwayemu munata zumunci har bikin su Haysam duk dasu a kayi suma yanzu sun sake ɗauke min wuta gaba ɗaya saboda ƙaddarar rayuwa da muka sake shiga. Shike nan kowa ya juya bayansa a garemu dangina dana Abdul-rasheed idan ka cire Jamilu da su Khadijah saboda kawai sune ciki ɗaya da Abdul-rasheed. Wlhy idan kowa zai barni banyi tunanin harda kai ba da muke ciki ɗaya Tasi'u, kada ka manta nice na fita a cikin Inna ka kwanta, sannan nice na gama sha daga jikinta ka amsa. Miyasa zaka gujeni tsawon shekaru ashirin da shida, a talatin kaɗan ne babu rabona da kai fa Tasi'u. Miyasa? Miyasa haka?”.
        “Wlhy kunya ce kamar yanda na sanar miki Adda, dan ALLAH ki yafeni ki gafarce ni na tuba”.
    Yay maganar yana sauka ƙasa ya durƙusa a gabanta tare da riƙe ƙafafunta duk da kuwa shekarun dattijantaka sun bayyana a gare shi shima. Bata hanashi ba, sai kuka da take itama. Ga Ammar dake rungume da ita shima tuni kukan yake, dan a duniya basa ƙaumar ganin hawaye Dada da Mammah na ɗiga. Tsohon lokaci suna a haka kafin Mammah ta fara tsagaita nata kukan ta kama dattijon tana miƙarwa da faɗin, “Shike nan ya isa. Na yafe maka  ka share hawayenka. ALLAH ya yafe mana gaba ɗaya. Ya jiƙan Inna da Baba da Abdul-rasheed da Bashir.
Amma dan ALLAH karka sake yin nesa da ni kaji”.
       Tashi yay ya koma kan kujerar yana share hawayen nasa da faɗin, “In sha ALLAHU har abada bazan sake nesa dake ba Adda, na baya ma kunya ce da nadama ta sakani dole. Amma wlhy a kullum cikin begen son ganinki nake keda zuri'arki”.
       “ALLAH ya rufa mana asiri”.
  Mammah ta faɗa tana shafa kan Ammar alamar lallashi. Ɗakin ya sake ɗaukar shiru na wasu mintuna kafin ta kallesa ta ce, “Mi kake yi a Egypt? Ko nan kake aiki?”.
        “A'a nazo ganin likita ne kawai. Yanzu ina Paris. Sai dai kusan shekara ma biyar kenan na koma ƙasarmu, kawai dai ina zaune a kudanci ne sakamakon tsoro da fargabar tunkarar ki.
     Murmurshi Mammah tayi mai ƙayatarwa da faɗin, “Ja'iri ashe kana shakkata?”.
         “Adda wlhy ina yi dan kece madadin Inna a wajena. Ya bayan rabuwa ya iyalai?”.
      “To sai godiyar ALLAH, Iyalai kuma duk gasu nan sun girma sun zama magidanta. Duk da dai Bilal da Ammar da Biebah basu kai da yin aure ba. Amma Alhamdullah duk komai ya dai-daita babu abinda zamuce da UBANGIJI sai godiya”.
        “Alhamdullahi naji daɗi sosai wlhy Adda. Kice yanzu gida ya cika da ƴan jikoki na”.
      “A ya cika kam. Dan a ƙalla yanzu kana da jika goma sha bakwai zuwa sha tara nan gaba kaɗan, dan yanzu haka yau ɗin nan Mimi ma ta sake haihuwa ta huɗu. Matan Ma'aruff da Ja'afar ma duk suna da ciki a yanzu haka na uku-uku duk da ƙarami ne.”
       “Kai Masha ALLAH lallai zuri'a ta haɗu. Ina yaron kirki Haysam?”.
    Shiru Mammah tayi na sakanni, sai kuma tai murmurshi gajere da faɗin..........✍️

16


..........“Yana lafiya shima Alhamdullah. Kai fa ina fatan dai ƙanwata ta koma ko ka sake sabon aure?”.
    Kansa ya ɗan shafa yana murmurshi, sai kuma ya ce, “Ta koma bayan taga na koma da kuɗin gidan nan, dan har mun sake haihuwar yara biyu ma. Amma ta rasu shekara kusan bakwai data wuce. Sai yaran yanzu kawai.” ya ƙare maganar idanunsa na tara ƙwalla. A take tausayinsa ya sake kamata. Ta shiga jajantawa da masa ta'aziyya. Shima Ammar yay masa ta'azziya. Dan har yanzu bai san ainahin wanene shi ba, tunda sanda wacan abun ya faru suna yara sosai musamman shi da Mimi ma da basu wuce shida zuwa bakwai ba maybe, sai dai ya fahimci ɗan uwan Mammah ne na jini koda kamanni da yanayin tattaunawar tasu.
     Cikin share sabbin hawaye Tasi'u yake amsa musu. Mammah dai ta babbashi haƙuri daga haka ta koma jansa da hira harya saki jiki shima yana jan Ammar a jikinsa......

%><%><%><%><%>

         Kwance take a madaidaicin gadon ɗakin daya kasance guda biyu iri ɗaya hannunta da waya tanata faman zabga murmushi, kai da gani kasan wani abu dake ƙayatar da ita take kallo. Dai-dai nan Ruky ta buɗe ƙofar bayinsu ta fito, ɗaure take da towel alamar wanka tayo, ganin yanda Nimrah ke zabga uban murmurshi bakinta har kunne yasa ta matsawa kusa da ita ta yarfa mata raɓar ruwankan dake ta bin farar fatarta.
       Ɗagowa Nimrahn tai da sauri irin na firgita, dan haka Ruky ta ƙyalƙyale da dariya. Cikin harara ta kai hannu ya goge ruwan data yarfo mata ɗin ta ce, “Ƴar wulaƙanci miye na yarfa min ruwa?”.
     Ruky na ƴar dariyarta har yanzu ta ce, “Gani nai kinata faman washe baki kamar ƴar tallar makilin, wai har yanzu hoton jaririyar kike faman kallo?”.
        “Humm bazaki gane ba Ruky ALLAH jarirai nada ƙyan kallo, ina son jariri sosai, shiyyasa kike ganin duk sanda su

Please Login or Register in order to submit comment