Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

yake yi yake. Ƙananan kaya ne a jikinsa, yanda rigar ya kamashi sosai gashi ƙaramin hannu yasa kallo ɗaya datai masa bata sake gigin yin na biyu ba.
Sai kuma ta tafi tunani mara dalili daya sakata shagala a wajen ta kasa ƙarasawa ta ajiye abincin..
         “Idan kikai ɓarin abincin nan sai kin cinye shi”.
     A bazata furicinsa ya shiga kunnenta. Da sauri ta dawo hayyacinta. Saman table ɗin gaban sofa taje ta ajiye tray ɗin. Dan shi yana a study chair ne zaune. Desktop ɗin sa a kunne gefe yana rubuce-rubuce. Ta bayansa kaɗan ta risina ta ce, “Dada ina kwana”.
        “Haɗa min abincin”.
    Ya faɗa batare daya amsa gaisuwarta ba. Baki ta zumɓura dan taji haushin ƙin amsa matan da yayi.........✍️

75


..........Harta gama zuba komai dai-dai misali ta zuba shayin lemon tsami da na'a-na'a dake ta ƙamshi bakinta na a sama. Inda yake ta nufo, ya matsar da takardunsa kafin ta kife masa abincin a kansu. Shiru bata ajiye ba, hakan ya sashi ɗagowa dole ya kalleta. Suna haɗa ido ta risinar da nata, shima sai ya kauda kansa ya cigaba da aikinsa. Kusan sakan biyar sannan ya furta,
        “Fishin mi kike yi?”.
    Bakin ta ƙara turawa taƙi magana.
Yay ɗan jimm na mamaki, sai kuma ya ɗago ya sake kallonta.
       “Abincin naku ne baƙya son naci?”.
      Yanzu ma kai ta girgiza.
  Ya dai sake daurewa ya ce, “Idon ne?”.
       Sai kawai ta sakar masa kuka. Mamakin duniya ya gama mamaye shi, kaji yarinya fa dan ALLAH kamar wata mai aljanu. Bai sake magana ba ya zuba mata idanu kawai. Ganin kukan ma daɗi yake mata sai ya amshi abincinsa da kansa ya ajiye. Kafin ya furta, “Tunda bazaki  yi magana ba wuce ki tafi”.
         Gurin tai ƙoƙarin bari tana sake fashewa da kukan da ita kanta bata san dalilin yinsa ba, kawai jitai tana son yi masa kukan ko a cikin drama ɗinta ne, duk da da gaske taji haushin bai amsa gaisuwar datai masa ba. Jiyay bazai iya barinta ta tafi tana kukan ba, ko wani abu akai mata. Sai ya riƙo hannunta ya dawo da ita inda take da. Bai saki mata hannun ba ya cigaba da kallonta har kusan mintuna biyu.
          “Kina son na zane ki?”.
    Kanta ta girgiza masa.
Cikin sake tsuke fuska ya ce, “Bana son wannan kukan. Faɗa min mike damun ki? Wani ne ya miki wani abu?”.
     Hawayen ta fara sharewa da faɗin, “A'a. Kai ne”.
       “Kiddo ni kuma?”.
    Kanta ta jinjina tana tura baki.
“Ikon rabbu, to mi nayi?”.
“Na gaishe ka baka amsa ba. Sai naga kamar kana fushi da ni”.
         Sagale kawai yay yana kallon ta, mamakin duniya ya gama mamaye shi. A ransa yace (Ƙuruci dangin hauka. Kaji yarinya fa) a fili kam baima san ya furta, “Ni kuma yau a hannun ƴan sari na tashi kenan!. To sake gaisheni sai na amsa ba shike nan ba”.
       “To ba fushi kake ba?”.
    Tai maganar cikin yanayin ɗan waro masa idanu. Sai kawai ya girgiza mata kansa yana ƙoƙarin danne murmushin dake neman bayyana a tsukakkiyar fuskarsa. Ajiyar zuciya kuwa ta saki, sannan ta sake gaishe shi. Ɓoyayyar ajiyar zuciya shima ya saki ya amsa yanda take son, harda ɗorawa da, “Yaya idon ki?”.
         “Da sauƙi, amma yana zafi kaɗan”.
      “Tunda kina kukan da babu dalili ba dole yay zafi ba. Ɗauka min leda gashi can a mirror na sa miki magani”.
        Ya kai ƙarshen maganar yana sakar mata hannu. Inda ya aiketan ta tafi, ya bita da kallo yana girgiza kai kawai. Tabbas yana da son yara, bai sani ba kodan baida su. Duk da Nimrah da Ruƙayya sun girma a yanzu, ganinsu yake ƴan 7years ɗin nan daya tafi ya bari... Dawowarta da ledar ya saka tunaninsa katsewa. Amsa yay ya buɗe, ya ciro maganin sannan ya kalleta, kamar ta fahimci mi yake nufi ta tsugunna kawai tana mai dafa hannun kujerar. Kanta ya dafa da hannu ɗaya, tare da buɗe idon sosai da babban yatsansa ya zuba mata maganin.....
         “Wayyo Dada zafiiiiii”.
     “Shiiiii!”.
  Ya faɗa yana riƙe da kan nata, dan ya hanata ɗagowa kar maganin ya fita. Sai da ya tabbatar ya shiga sannan ya barta. Har zata miƙe ya ce, “Ɗauka wannan abinci ko canja ya huce. Kije ki kira min Ruƙayya itama”.
       Cike da tsantseni ta amsa, dan duk wannan biye matan da yake shakkarsa na nan damar a zuciyarta. Musamman da fuskar na tsukenta ne babu ko murmurshi. Sai dai son cikar burinta da shirinta a kansa yasa take danne zuciyarta da bama kanta ƙwarin gwiwa. Alhamdullahi kuma taga tasirin hanyar data biyo masa. Bayan ta ajiye wani sabon abincin dan ALLAH yaso ba plate ɗaya Kulu ta saka ba, haka ma kofi. Tana kammalawa ta fita a ɗakin.
     A ƙasan ransa ya furta (Kiddo kina bani ciwon kai)...
     Babu jimawa suka dawo ita da Ruƙayyan, dan ta iske ta tashi barcin. Yanda yay ma Nimrah tambayoyi jiya cikin wayo da dabara akan makarantarsu haka ya dinga musu a tare yau, suka dinga bashi labarai kala-kala, har kansa ya fara ciwo sai da ya gaji ya korosu.
Oho ko'a jikinsu, dan daɗi ma suka dinga ji Dada yayi hira da su, koda suka dawo wajen Mammah sai suka dinga yi ma Mu'azz wulaƙanci. Har sai da yaji haushi ya haura saman yace shima ya tafi ɗakin Dadan. Mammah dai murmurshi take kawai da jinjina shiriritarsu. Sauran Uncles ɗin nasu ma duk wanda ya shigo sai an bashi labari yau sunyi hira da Dada. Congratulations suka dinga ce musu suna dariya..

      Wannan hira ta bama Dada haske sosai akan makarantar su Ruky. Koda suka tattauna da Daddy Imran yayi mamakin wayon yaran. Dan abune ma da shi kam bai taɓa kawoma ransa ba...

))))★(((((★))))))★((((

           A bangaren Hajiya Hasiba kamar yanda First Lady tace tayi hakan tayi, ta buɗe su Nabeeha. Ta kira likitanta ya fara duba su saboda damuwar da suka sakama kansu duk sun rame. Ya tabbatar mata da basa tare da wata matsala sai damuwar kawai. Amma ya basu shawarwari sosai da suka fahimcesa. Bayan tafiyarsa itama ta zauna da su. Ta nuna musu ta haƙura, amma su kiyaye gaba. Sannan tace Nabeeha ta fara shirin komawa gidan mijinta.
      Ba Nabeeha ba hatta Ismat ta shiga matsanancin mamaki. Dan har sai da ta furta, “Momy da gaske kike yi?”.
       “Oh na saba miki ƙarya ne Ismat?”.
    “A'a Momy kiyi haƙuri. Wlhy mamaki ne kawai abin ya bani”.
      “Humm to sai ya daina baki. Kawai shawara likitan nan ya bani akan na barta ta koma kada ta kamu da wani ciwo. Dan haka na amince ta koma. Kema kuma na baki nan da wata uku ki kawo mijin aure, idan ba haka ba ni inada wanda zan bama ke. Masu gyaran jiki zasu zo gobe idan ALLAH ya kaimu sai ki shirya”.
    Tai maganar ƙarshe tana kallon Nabeeha. Kai kawai Nabeeha ta jinjina mata, dan al'amarin Momyn tasu a wannan gaɓar ya razanata fiye da ko yaushe. Tana sonta sosai, amma maganar gaskiya ta fara jin tsoron ta mai girma.
        Tun daga ranar suka fara ganin canjin abinci masu ƙyau, saɓanin wanda ake basu a kwanakin nan da suke a kulle. Sannan ta dawo musu da wayoyinsu. An kuma dawo da network ɗin gidan. Sukan fita falo su zauna, har ma tayi hira da su. Ƴar Kamaru tazo ta fara aikinta na gyaran jiki wa Nabeeha. Dan maƙudan kuɗaɗe First Lady ta biya kamar bata san ciwon kuɗi ba. Koda yake bata san ciwon nasu ba tunda an tara musu, ta yanda ko jikokinsu bazasu yi talauci ba idan ba wata jarabawar UBANGIJI ba kuma....

    <•••><••••><••••><•••>

         A lokacin da can ake gyara Nabeeha anan Dada da Imran sun matuƙar maida hankali wajen haɗa runduna ne akan aikin da zasu fara. Dan kamar yanda shugaban ƙasa ya bama Dada damar samar da masu taya shi aiki cikin kowanne jami'an tsaro dama farar hula haka yaketa tattarasu. Sai dai fa dukansu kowa bai san da zama ɗan uwansa ba. Hasali ma su Dabo aka saka suke yi basu san waye shugaban tawagar ba.
       Har yanzu suma su Dabo basu ga Dada da idanunsu ba, sai dai su duka yayi waya da su ta hannun Imran. Duk abinda zasuyi Faro ke basu umarni. Sai yau ne ma yake tunanin zama da su. Dan akwai tsofaffin bayanan da yake so a hannunsu. Sannan yana son jin bayani akan duk wanda suka ɗakko a cikin tafiyar dan tantance ko zai iya aiki da shi ko bazai iya ba.
          Kwanaki biyar kenan da haihuwar Shariffa, tunda kuma akai haihuwar kullum su Aunty Ummi na gidan nan. Hakama ɓangaren dangin su Imran tunda abu ne duk na gida. Shiyyasa sam Dada baya zaman gidan. Bama zai iya cewa yasan wace waina ake toyawa ba. Suma sun maida hankalinsu akan wancan gidan da suke shirin maidawa na sirri. 
Tabbas, wannan gida a zahiri Dada da Imran sun maida shi tamkar gida na yau da kullum, amma a gaskiya UNIT ZERO ne, cibiyar sirri da aka gina domin yaƙin da ba a sakawa suna ba a fili. An sauya duk wani abu mai ƙarancin tsaro zuwa mafi girman matakan tsaro. Tun daga ƙofar shiga, komai ya sauya. Ba ƙofa ce da ake buɗewa da hannu kawai ba. Ana amfani da multi-layer authentication: lambar sirri, na’urar biometric, da kuma time-based access. Ko su da kansu, idan lokacin bai dace ba, ƙofar ba za ta buɗe ba.
       Tagogi kuwa an maida su bullet-resistant glass harbi ba zai iya ratsa su ba. An saka ɓoyayyun cameras ko’ina. An kuma tanadi ɗaki guda na musamman domin ajiye ayyukan sirri, ɗakin da Dada shi kaɗai ke shiga, sai Imran da Faro. Smart perimeter sensors sun zagaye gidan gaba ɗaya ba wai don mutane kawai ba, har da motsin iska, ƙasa, ko duk wani abu da bai dace ba. Akwai silent alarm system: babu ƙara, babu haske, amma UNIT ZERO ya riga ya zama ido da kunne na komai. Thermal cameras suna iya gano mutum ko da cikin duhu ko ta bayan bango. Ƙofofi kuwa EMP-resistant ne ko an katse wuta, ko an yi hacking, ba za su buɗe musu ba..........✍️



76


.........Cameras marasa gani da ido, ba su da haske, ba su da amo. Wasu an saka su a cikin bango, wasu ma a cikin furanni. An tanadi blind-spot tracking a inda babu camera, akwai sensor. Duk motsi ana adana shi ne a local encrypted server, ba tare da haɗin internet ba. A wasu sassa ma babu wata waya da ke kama signal, musamman a EMI shielded rooms.
      Hatta talabijin da ke nuna dukkan motsin gidan ta hanyar cameras suna cikin ɗakin kula da tsaro. Akwai na'urorin aiki na musamman da shugaban ƙasa ya samar, irin waɗanda manyan ƙasashe ke amfani da su a duniya. Manyan monitors suna nuna duk motsin gidan, sarrafa cameras, da ajiye bayanan sirri. Babu waya, babu recorder, babu wani motsi da zai faru ba tare da sun sani ba, ko da basa cikin gidan. Abin da aka faɗa a nan, ya mutu a nan. Ko hoto ma ba ya ɗaukuwa a gidan, balle a ɗakin sirri.
       A tsararren ɗakin sirri, dukkan takardu suna cikin classified physical files da aka kulle da code da fingerprint. Wasu bayanai ba su da suna, sai lambobi kawai. Wasu hotuna da bayanai ana ajiye su ne a dead vault, ba a buɗewa sai an cika sharaɗi guda uku. Ana amfani da dead-drop system wajen musayar bayanai, ba tare da haɗuwa kai tsaye ba.
      Akwai makamai iri-iri makaman da ba a rubuta su a kowanne rijista ba. Na'urorin sauraro, bin sawu, da ɓoye fuska. Haka kuma akwai kayan fitar gaggawa idan aka kai hari, da wuraren ɓoye ainihin jami'an sirri masu kai ɗauki. Da zarar ka shiga wannan ɗakin, zaka fahimci cewa an shirya yaƙi ne yaƙi na gaske, ba wasan yara ba.
     Ba kayan aiki kaɗai aka tsaya ba. An tanadi hanyoyin fitar sirri ta ƙasa, waɗanda kai tsaye ke haɗuwa da manyan magudanan ruwan unguwar. Hanyoyin ƙasa da aka ɓoye cikin tsarin gine-gine. Ba hanya ɗaya ba fiye da uku. Wasu suna kaiwa wurare daban-daban a unguwar, wuraren da ba za ka taɓa tunanin suna da alaƙa da gidan ba.
          Tabbas shugaban ƙasa yayi ƙoƙari wajen zuba kuɗi akan wannan aiki, duk da dai ba'a fitar da su daga asusun gwamnati kai tsaye da wannan manufar ba, an laɓe bayan wani aiki ne da aka bada kwangilarsa kai tsaye, a bayan fage kuma akai wannan aikin. Kowa da zaiyi aiki da UNIT ZERO bai san ainihin shugaban tawagar ba. Umarnin aiki zai dinga zuwa ne ta code name. Idan aka kama mutum, babu abin da zai iya faɗa da zai rushe tsarin gaba ɗaya. UNIT ZERO ba gida ba ne kamar na shirin Film kawai, babbar FADAR YAƘI ce a ƙarƙashin umarnin ZAK-SHADOW. Wani gawurtaccen station blinding ne da zai ruguza duk wani mai tsautsayi da zai iya shiga tarkon ZAKI. Dan duk wani shiri an kammala shi yanzu kam hatta filin saka mazare rawa da sarƙa a kafa. Shi kansa uban gayyar ya furta “YANZU NE AIKIN ƘARSHE ZAI FARA. A kashe ko ya kashe, wannan shine ƙarshen BURI......”

        “Alhamdullahi komai ya kamala, lokacin fara aiki yayi. Yanzu minene shiri na farko?”.
        Iska Dada ya ɗan furzar yana ajiye takardun hannunsa ya gyara zama da kallon Imran mai maganar. Cikin sake maimaita godiyar ga UBANGIJIN shima ya bashi amsa da, “Inaga zan gana da su dabo a daren yau. Kai ma lokaci yayi da zaka koma aiki sosai kafin su fara tsarguwa da rashin zamanka office.”
      “Nima nayi wannan tunanin. In sha ALLAHU kuma zan koma wannan Monday ɗin. Yaya batun karatun yaranka, ya kamata su koma makaranta fa. Dan in ka biye musu su wannan zaman shiriritar daɗi yake musu, musamman daya zam babu islamiyya. Ammien su tace a zaman jegon nan babu abinda suke sai rashin ji, kawai dan baka yini gida ne kai ma. Dan jiya ALLAH ya kiyaye suda yarinyar nan Hanoon da anyi babu daɗi.”
         Murmushi kawai Dada yayi. Daddy Imran ya hararesa. “Kace mune ke ɗaure musu ƙugu, amma ka fimu. Nazata dawowarka zata saka su nutsu amma shirun da kake musu yayi yawa, ya kamata ko sau ɗaya kaci ƙaniyarsu.”
      “Basuyi abinda zanci ƙaniyar tasu bane shiyyasa. Makaranta kuma zasu koma. Dan baza'a canja musu ba akwai shirin da nakeyi kafin su koma ɗin, da kaina zan maida su”.
      “Hakan yayi ALLAH ya kaimu. Sai mutuminka ya dameni akan batun Auta. Wai kunyarka yake ji shiyyasa ya kasa magana. Kar kaga kamar yayi gaggawa.”
    Nan ma murmushi Dada yayi da faɗin, “Ai yayi ƙoƙari, ya kamata ka duba masa. Sai ka haɗa da Bilal da Ammar. Dan suma bana son zamansu haka. Ya kamata duk su ajiye iyali”.
        “Eh wannan shawara ce mai ƙyau. Amma ban taɓa ganin Ammar da budurwa ba. Gara Bilal”.
     “Na tambaye shi nima yanata min ƙunshe-ƙunshe. Shine nace masa yaje ya tura min saƙo to. Sai jiya yake tura min wai ai bata girma ba, kuma tana a gidan tare damu. Amma bai taɓa nuna mata ba sai ta kammala Secondary”.
        “Tofa ji ja'iri, wacece haka?”.
     “Bai faɗa ba, amma ni na fahimci Ruƙayya yake nufi”.
   “Kai amma Ammar mashiririci ne. Yarasa mata sai wannan kayan shirme da shiriritar. Kuma a haka kake cewa a haɗa da shi, ciwon kai kawai ka nemar masa”.
        “Ko?”.
    Dada ya faɗa yana ɗan ɗage gira sama. Baki Daddy Imran ya taɓe. “Kaima ka san yarinyar nan taka sai a hankali”.
       “Ba komai zata bari wataran. Ai dama na gaya maka aure zan mata”.
     “To ALLAH ya taimaka. Sai kai kuma uban gayyar. Dan ALLAH kayi haƙiri muje bikon Nabeeha. Dan ina cikin mamakin yanda har yanzu bataji ko labarin dawowarka ba. Ko har yanzu tana fushi ne”.
      “Dawa zaka je ɗin?”.
   “A! Dakai mana. Zakina dan ALLAH ka rage taurin kan nan. Sufa mata ba'ai musu haka. Lallaɓasu ake, a riritasu. Ayi haƙuri da halayensu marasa ƙyau. Tunda har akace mana tun daga tushe a karkace suke, tsaurin mu bazai sa su miƙe ba fa. Idan ma muka tsananta zasu karye ne.”
         “Ni babu inda zanje, ƙafarta data fiddata idan ta gaji da zaman ta dawo da ita”.
      “Kai kuma halin da kake ciki fa?”.
   “Ni na gaya maka ina cikin wani hali ne?”.
    “Kasan na sanka fiye da kowa. Ai ba sai ka faɗa min ba. Koda kake ganin dama can kana azumin ka ai na yanzu yasha banban. Sannan yanzu fa kake faɗar su Bilal su ajiye iyali saboda shine cikar kamala. Amma kai kana bijirewa. Kai ne fa uba, ko Mammah na tabbatar ta maka shiru ne taga iya gudun ruwanka. Idan kai bazaka je ba, ni ka barni naje to”.
      “Wlhy bazaka ba”.
   “Harda rantsuwa? To shike nan Nimrah ta tare”.
    “Amma baka da hankali”.
  Dariya Imran yayi sosai, ya ce, “Naji banda shi. Miye a ciki to. Naga yaran ƙauye ana musu aure ƙasa da shekarunta. Balle su suna cin abinci mai ƙyau kuma ALLAH ya kawo girman da wuri. Kadai duba al'amarin nan. Bar ganinsu haka sun san abubuwa da yawa tunda suna zuwa islamiyya. Idan ba hakaba kana nan wasu zasu fara koya mata abinda kai kake ganin bata sanshi ba. Dan kwanaki sai da naci ƙaniyar wani malamin islamiyyar su wai shi Kamal. Daga baya ma na bincika wai yabar makarantar, amma da ya dage shi son Nimrah yake yi. Har ya fara zuwa gidan fa”.
       Wani mugun kallo Dada kema Imran kai kace shine Kamal ɗin. Aiko mi Imran zai yi inba dariya ba. Sai kawai Dada ya miƙe abinsa daga nan hirar ta watse ma. Har ya kawo shi gida bai sake kulashi ba. Haka ya sauke shi shima ya kama hanyar gida yana kwasar dariya. Dan shi kaɗai yaga bala'in daya hango a idanun zakinsa. Ai ko a fagen fama albarka.
      Ƙasa daurewa yay sai da ya bama Ammie labari. Itama taita dariya. Daga ƙarshe tace, “Ni kaina nayi tunanin fara shiri sai naga bakuce komai ba, amma share masa ɗaki a sashen Mammah. Amma magana ta gaskiya bana son Nabeeha ta dawo gidan nan Yarinyata bata tare ɗakinta ba.”
         “Ai kunji matsalarsu iyayen zamani, zaku fara koya mata kishin banza ko”.
     “Ba wani koya kishi Daddyn Khalifa magana ce ta gaskiya. Tunda ita bata da hankali dan mijin ya ƙara aure kin ɗauki ƙafa kin tafi gida. Ya shiga wani hali ki dawo ɗakin ki ki zauna kuyi jimami, kuyi kuka tare da ƴan uwansa da Mahaifiyarsa amma kin biyema taki uwar sai yawon gantali. Yanzu duk randa yasan wannan zaman Dubai ɗin da taje tayi mi kake tunani dan ALLAH. Zargi ma bazai shigo ciki ba”.
        “Ai babu ma wanda zai gaya masa. Yanzu dai mubar maganar, gyara kuma kiyi tayi, sai ki haɗa da Biebah da Asma'u harma da Ruƙayya”.
     Idanu sosai ta waro na mamaki. “Ruƙayya fa?”.
        “Eh, ubanta yace aure zai mata, yama mata miji. Gara ma yayi hakan, dan zanfi samun dama a kansa nima game da tarewar Nimrah ɗin”.
      Ammie da abin ma ya bata dariya ta ce, “To ALLAH ya sanya alkairi, yasa ayi damu, amma dai wannan miji zai kwasa.”
       Dariya Daddy Imran yayi itama tana taya shi. Ya ce, “Kamar kina wajen abinda na faɗa kenan nima. Amma tunda mai abu da abunsa sai ka tayashi da sambarka.”
       “Haka ne kam, ALLAH yasa ayi da rammu to”.
     “Amin ya rabbi”.........✍️



77


........Ana gobe suna su Gwaggon Alawiyya suka iso. Ai fa gida ya kacame. Su Nimrah amarori. Dan ma ita damuwa ta raba mata hankali biyu, dan ta gama shirya a cikin rarumar sunan nan zata haɗu da Dagger. Shiyyasa ma tai luff abinta a kwanakin da suka gabata kamar komai baya damunta. Amma da yake ita Ruƙayya na tare da ita tsaff ta gane damuwar kwanaki tana neman dawo mata. Koda ta dameta da tambaya sai tace rashin zuwa makarantar su ne ke damunta. Har tana bada shawarar idan anyi suna su sami Dada da maganar, dan gani suke kamar Mammah ce bata son su koma tana tsoron a musu wani abu. Ruƙayya ta gamsu da hakan shiyyasa ta saki maganar. Itama kuma Nimrah sai ta sake canja takunta. Dan yarinya ce mai shegen wayo da iya rikiɗa kamar hawainiya.
    Cikar gidan kuma ta sake maidata busy, dan ranar su aunty Ummi ma duk anan suka kwana. Dada ne dai basu gashi a gidan ba kwata-kwata tun safe. Babu ma wanda zaice ga sanda ya fita.....

<>%<>%<>%<>

A ɓangaren Malam Buba jinsa yake sharr, dan kuwa shugabannin ƙungiya sun sake zama na biyu da shi. A cikin satin nan ma akwai babban aikin da zasu fitar. Ya samu cikar burinsa an bashi shugabanci harda yara a ƙarƙashin sa, sai dai ba yaran Dagger aka raba aka bashi ba kamar yanda yaso. Sabbin yara ne waɗan nan da baima san dasu ba. An basu horo mai suna horo. Sai yaji ya sake tsoro da shakkar al'amarin ƙungiyar duhu. Dan hatsabibancinsu na gaske ne ƙwarai da gaske. Sannan sun wuce dukkan inda ake zato da tsammani. Duk iya hasashenka baka isa iya ƙare musu gudu ba. Suna da ɓoyayyun abubuwa da sai UBANGIJI ne kawai ya sansu sai su.
     Abinda dai ya tayar masa da hankali shine sun tabbatar masa dole ne yabar gidann su Nimrah. Dan zamansa bazai yiwu ba dan yau da gobe zata iya kwaɓewa kasancewar sun san waye Zak-Shadow, sun karanceshi sun kumayi imani da mutumin ne mai shegen wayo. Na biyu ɓoye fuskarsa da nisantar Nimrah zai bashi damar cimma burin dawo da ita cikin rayuwarsa. Duk kuma randa zata san shi waye a gareta zata ji martaba da girmansa matsayin uba.
      Ya gamsu, duk da hakan ya saka shi a damuwa. Amma sun bashi shawarar ziyartar gidan lokaci-lokaci koda da nufin gaisuwa ne, hakan zai sa ya dinga ganin nata...

    Na biyu Sanda. Sanda har yanzu yana wasan ɓuya da Dada, bai taɓa bari Dada ya ganshi ba. Yaƙi kuma sanarma maigadin komai. Tun yana tambayarsa harma ya daina. Nimrah kuwa dakan ari wayarsa bai taɓa hanata ba. Gashi Sarkin wayon data gama take goge number ɗin. Sai dai yana nan ya shirya. Dan yana son yasan abinda take ɓoyewar. Tunda duk da akwai camaras a gidan ta iya kaucewa hakan ta ɓuya a inda babu tayi wayarta. Ya saka mata ido sosai batare data sani ba. Dan ita tana ɗaukarsa ne a garan ƙauye da baya gane komai....

      ••••••••••••••
            ••••••••••••••

       RANAR SUNA.....

RANAR DA ABUBUWA UKU MASU MUHIMMANCI SUKA FARU A CIKINTA.

  NA FARKO....

      Yau take suna a gidan Mammah, tun daga sallar asuba aka raɗa sunan yaro da yaci Uncle Nasiru. Wato Naseer. Dada ne kuma ya zaɓa masa wannan suna bai kuma sanarma kowa ba sai a yau ɗin. Kowa yayi farin ciki da abinda yayi, musamman Mammah dake ta saka musu albarka. Tun kafin tara tayi su Nimrah suka cika gidan da hayaniya.
         Dan party suka shirya ita da Ruky, Bintu, Feedo. Babu wanda

Please Login or Register in order to submit comment