Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

irin shekara ɗayan nan ba ta bata. Sai Auta namiji, shi kam zasu iya dai-dai da Mu'azz. Kai da ka gansu kasan rainon ƴan gayu ne, sai dai kuma da ganin inda suka zo ɗin yama fi gidansu komai suka kama kansu. Ga Mammah ta musu tarba ta mutuntawa da soyayya kamar zata haɗiyesu. Su Aunty Mimi ne ma dai sama-sama suka amshesu dan ma gargaɗin Yaya Imran ne. A haka su Nimrah suka dawo gidan suka samu baƙi, duk da dama a kwanakin nan kullum gidan bai rabo da baƙin. A gidan nan babu wanda yakai Nimrah da Ruky wulaƙanci idan mutum bai musu ba.
       Sun gaida Uncle Tasi'u da girmamawa matsayinsa na uba. Amma ƴaƴansa kallo ɗaya sukai musu suka watsar da su kamar sun ga kashi. Sun kuma yi musu haka ne saboda ganin yanda suketa wani jijji da kansu su a dole ga rainon turai. Kota kansu kuwa basu sake bi ba suka shige ɗakinsu, bakuma su sake fitowa ba ko abinci sakawa sukai masu aiki suka kai musu dan yau alhamis ne babu Islamiyya. Sai da Mu'azz ne ma ya dawo gidan yazo ya jajibesu suka haura sama ganin ɗakin da aka zubama kaya. Anan suka lalace sunata santi da hotuna da wayar Mu'azz ɗin. Dan ɗakin yayi ƙyau matuƙa. Haka suka fito suna damun Mammah da tambayar wazai zauna a ɗakin. Tace bata sani ba itama Daddynsu ne kawai yace a gyara....

★RANA BATA ƘARYA......★

  Tabbas wannan batu haka yake. Dan kuwa washe garin juma'a kamar jiya yau ma Daddy Imran ya kira Mammah a waya yace su shirya za'azo a ɗaukesu bayan sallar juma'a zuwa wani waje. Kan Mammah ya fara ɗaurewa, amma sai nan ma bata tambaya ba saboda halin girma da dattako irin nata tace kawai to. Su Bilal ne ma data sanar mawa suka fara shan jinin jikinsu. Jiya an gyara ɗaki, yau ance su shirya anya kuwa?..
     Kasancewar baƙin ido a gidan yasa basu ja maganar da nisa ba. Bayan sunyi shirin massalaci sun fita harda ƴaƴan Uncle Tasi'u Dayyan da Afeef, suma su Mammah dake gida suka hau shiri. Sai ga su Aunty Ummi sun fara isowa da tasu tawagar suma. Dan yaran basu sami sukunin zuwa gidan ba sai yau saboda makaranta. Shiyyasa yau juma'a kowa da ɗansa yazo.
Nan fa aka sake kacamewa har wani baya jin zancen wani.
         Banda yara za'ai fitar, dan haka su Nimrah a gida akai shirin barinsu da yara amma suka shiga magiya da roƙon Mammah dole tace su shirya. Kasancewar harda Aunty Biebah da su Aunty Lailah su Nimrah sune ƙanana. Su yaran ma murna sukai da tafiyar tasu, dan a sanin da sukai musu basa ɗaukar raini, idan aka barsu da su dole su daku. Dan kaɗan daga aikin Damisa da Zakanya yaro yaci duka kafin uwarsa ta dawo....
      Ba ƙaramin ƙyau sukai ba kuwa da kwalliyar tasu. Nimrah skirt da riga ne na atamfa da tai mugun zama mata a jiki, sanin ba barinta ake fita da ƙaramin gyale ba idan ta saka irin waɗan nan kayan yasa ta ɗora after dress a sama, ba ƙaramin ƙyau tayi ba ga fuska tsaff da kwalliya mai nutsuwa. Hakama aminiyar tata tana sanye da irin kayan nata sai dai ita kam gyale ta saka. Suka kawo turarrukan SHUWA INCENSE AND MORE +234 704 229 3387. suka saka, gashi dama sunyi kabasa da shi a kaya..
     Suna fitowa Ya Mu'azz ya fara tsokanarsu wai kamar ranar auren su. Ba raga masa suke ba, dan haka suka shiga ramawa ana dariya. Daga haka suka fito harabar gidan kowa ya shiga mota. Ninah da Ruky na tare da Mammah, Uncle Bilal ke tuƙi sai Mu'azz a gefensa. Ana buɗe gate suka fito motocin sojoji biyu dake jiransu suka take musu baya. Ɗaya a gaba ɗaya a baya. Wannan matakan tsaro na ba kowa mamaki a cikinsu, dan ko yanzu su Nimrah sai da sukai magana. Dan har a makaranta ma yanzu tare suke zuwa da sojojin da a yanzu suka zamewa kowa dogari a gidan batare da sun san dalilin yin hakan ba. Abinda kawai sojojin suka sanar musu tun a ranar farko da aka kawosu shine umarni suma kawai suke bi........✍️
KIƊA A RUWA 2

51

.........★AIRPORT★

Ba ƙaramin mamaki su Mammah sukai da ganin inda aka kawosu ba. Airport fa, sukam wa garesu da zai dawo daga wata ƙasa. Imran ne kawai yay tafiya, basa jin kuma dan zai dawo zai musu irin wannan tattarowar iya su kaɗai. Kowa da magana a bakinsa sai dai sunyi dauriyar dannewa.
Ba a kai su Mammah da iyalanta cikin waiting hall na jama’a ba. Sai ma wani mamakin da aka sake basu, dan kuwa Jami’an tsaro masu bakaken kaya suka sake tarbarsu anan ɗin sannan suka jagorance su zuwa wani ɓangare na musamman a airport ɗin da zasu iya rantsuwar basu taɓa sanin akwai shi ba. (VIP lounge) wurine da ya sha bamban da hayaniyar waiting hall. Ga tsaro ko’ina. Iska mai sanyi ga ƙamshi mai saka nutsuwa. Ga kujeru masu taushi da ƙawa kai kace wani shiryayyen falon hutawar shugaban ƙasa ne. Koda yake ko ba'a faɗa ba kai kasan wannan wajen sai dai tanadin zaman shugaban ƙasar.
Sai da Mammah ta zauna sannan kowa ya zauna ana kallon kallo. Su Nimrah kam kasa haƙuri sukai cikin raɗa-raɗa sukace Ya Mu'azz dake kusa da su yay musu hoto. Bai ko yi musu ba ya fara ɗaukarsu, daga ƙarshe ya koma yima kowa video sai da Mammah ta masa daƙuwa.
Cikin dariya ya ce, “Mammah yi haƙuri, ALLAH wajen ne ya haɗu. Idan bamuyi hoto ba ai ansha damu. Wai dama a waiting hall na airport akwai vip room irin wannan?”.
Kowa murmurshi yake da zancen Mu'azz. Uncle Ja'afar ya bashi amsa da, “Ai dole ne ya zama akwai irin wannan ɗin Mu'azz kodan shugabanni ko”.
Cikin gamsuwa Mu'azz ya ce, “Haka ne kuma Uncle. Tunda dama kasarmu komai yana da banbanci dana talaka dana masu mulkin”.
Basuyi ko zama mintun goma ba jirgin da ake tsumayen zai sauka ya sauka ɗin. Sai dai da yake a ɓangaren ɗaya suke na masu jira basu san wainar da ake toyawa ba har matafiyan da suka fito a jirgin suka fara fitowa. Tun suna tsumayen ganin fuskar wanda suka sani ya shigo vip lounge ɗin har suka haƙura. Dan kusan sai da sukai zaman fin mintuna talatin zuwa lokacin har ruwa an kawo musu da lemo, bayan nan kusan wasu mintina uku security ɗin dake ƙofar ta waje ya buɗeta. Duk ƙofar kuwa suka zubama idanu dan a ƙage suke su kam.
A bazata Daddy Imran dake gaba ya bayyana a idanunsu. Kusan a tare duk suka miƙe, idan ka cire Mammah da bata motsa ba ta dai zuba masa idannunta na girma kawai. Yayinda zuciyarta ke wani irin bugawa da bugu mai girman gaske a cikin ƙirjinta. Hakama Nimrah dake kwance a jikinta tana game da wayarta, kasancewar hankalinta na kan game ɗin bata san mike faruwa ba ita kam.
“Oh kona koma ne?”.
Daddy Imran ya faɗa yana ɗan wara idanunsa akan su Ammar dake tsaye kawai sun zuba masa idanu abubuwa na musu yawo a zuciya da ƙwaƙwalwa. Murmurshi suka saki a tare, kafin su ɗaga ƙafafunsu da sukai musu nauyi na rashin dalili su nufesa a jere, zaratan mazajen Mammah kenan guda huɗu, masu kamanni ɗaya, dan su duka huɗu da mahaifinsu suke kama, Dada ne kawai ya ɗakko hasken fatarta amma shima kamaninsa irin nasu ne.
Dai-dai lokacin itama Nimrah ta ɗago saboda zaburar Ruky da uhununta na ambaton Daddy!... Sai dai ta yunƙura zata tashi itama ta tsaya cak, kamar yanda suma Uncle's nasu suka tsaya ɗin. Dan takunsu bai gaza biyar ba suka iso inda Imran ya ke, sai dai kamar jira yake su iso ɗin suna ajiye ƙafafunsu a takun ƙarshe shi kuma ya matsa gefe tamkar mai shirin basu hanyar wucewa, hannunsa ɗaya riƙe dana Ruƙayya, ɗaya kuma ya nuna musu ƙofa. Dai-dai nan ƙofar wajen da suka zubama idanu su duka ta shiga buɗewa, buɗewar data kasance tamkar tare da zukatansu dake rufe ne tsawon shekaru takwas da wata shida....
Ɗasss! Ɗassss! Ɗasss!! Sautin takunsa ya fara bayyana a cikin shirun su mai nauyin gaske, dan a wannan gaɓar ko numfashi mai ƙarfi babu mai yi idan ka cire Imran da fuskarsa ke cike da wani irin murmushi mai nauyi da armashin gaske. Kafin bayyanarsa cikin kwarjini da kamalar masu natsuwa ta wanzu cikin idanunsu. Shi ɗin ne dai, shi ɗin da suke zaman jira tsahon shekaru da hawaye da bugawar zukata a kowace daƙiƙa ta kwanakin da suka shuɗe da abubuwan da bazasu lissafu ba.

Duk da basa ganin ainahin fuskarsa, sannan ba wasu kaya bane na alfarma a jikinsa. Hasalima sanye yake da ƙananun kaya da suka kasance baƙaƙe daga sama har ƙasa. Baƙin wando da riga t-shirt mai gajeren hannu data bayyana murɗaɗen damtsen hannunsa duk da kuwa jikinsa bai gama dawowa ba kamar da, sai dai ya ciko fiye da sanda ya fita a prison. Fuskarsa da norse mask daya ɓoye bakinsa da hanci, sai ƙwayoyin birkitattun idanunsa da ko yana a cikin kwanciyar hankali basa zama tas-tas, daga sama da hula p-cap itama baƙa. Hannunsa ɗaya a aljihu, ɗaya rataye da jacket ɗinsa da itama ta kasance baƙa. Sassanyan ƙamshin turarensa da duk suka sanshi da shi kuwa ya cika wajen...
Kamar yanda suka tsaya cak suna kallonsa haka shima ya tsaya cak yana musu kallo mai matuƙar nauyi da tsawa a zuciya. Dan kuwa Imran ya matuƙar yi masa bazata. Sam bai sanar masa da zuwansu tarbarshi ba, kasancewar dama saukar tasu sauka ce ta sirri kamar yanda ya buƙata. Da wani irin slow motion ya janye idanunsa daga kallonsu ya maida su kan Mammah dake zaune a inda take, sai dai kamar wadda ta suma dan babu inda ke motsi a jikinta sai idanunta dake tsaye a kansa cak... Nimrah kwance a kafaɗarta itama dai ta zuba masa ido ne kamar yanda kowa ke kallon nasa. A bazata idanunsa daya janye slowly daga kan Mammah suka shige cikin nata. Shigewar data saka mummunar faɗuwar gaba riskarta. Dan ji tai tamkar an matse zuciyarta da hannu ne har sai da ta kumburo kamar zata fashe sannan aka saki. Kasa jurewa tayi, a hankali ta fara lumshe idanun nata dake cika da hawaye na rashin dalili. Hakan kuma yay dai-dai da cigaba da takowar Dada inda suke kai tsaye dan burinsa kawai ya iso gaban Mammah...
Karo na biya ya fara motsawa a hankali, yanda ɗakin yay musu shiru tamkar an tsaida duk wani motsi na ƙasar da mutanen cikinta yasa sautin takalmin nasa cigaba da bada sauti kamar ɗazun. Sautin daya cigaba da bugawa da bugun zukatansu har ya ƙarasa inda Mammah da Nimrah suke ya tsaya cak. Kafin a hankali ya tura ƙafarsa ɗaya baya, ya sauke gwiwar ɗayar ƙafar itama a ƙasa tamkar mai shirin bama budurwa zoben baiko. Hannunsa ya kai ya zare p-cap ɗin ya ajiye a ƙasa, ya sake maidawa ya zare norse mask ɗin shima. Duk dai Mammah na kallonsa tamkar sumammiya, dan idannunta ne kawai dake yawo a kansa ke motsawa...
A ɓangaren su Ja'afar da su Aunty Ummi, Lailah, Mimi, Mommy, Shariffa da Biebah kam idan akace maka suma sun suma ɗin ne tamkar Mammah kada ka musa. Dan yanda duk suka kasance a tsaye ƙyam babu motsi babu ƙyafta ido ya isa shaida ga mai kallonsu. Dai-dai yana gama sauke norse mask ɗin cikin tamkar fisgar numfashi Mimi ta furta kalma mai nauyi da girgiza zuciya a karo na farko, kalmar data zama tamkar ta yayyafa musu ruwan sanyi ne daya farkar da su a suman nasu...
“D..a...da!!”.
Sai kawai ta tafi luuuu zata zube ƙasa saboda yanda jikinta ya ɗauki rawa. Da sauri suka zabura kanta dan taro ta, sai dai kuma hankalinsu ya rabu biyu. Dan a dai-dai wannan lokacin itama Mammah da sunan Dadan ya daketa sakamakon fitarsa a bakin Mimi jikinta ya hau rawar, duk da ƙoƙarin da take na riƙe kanta hakan ya gagara. Hannunta ta motsa a hankali tare da kai shi kan fuskar da ta shafa kumatunsa dake ɗauke da kwantaccen gashin saje mai adon farin gashi tsilli-tsilli. Da wani irin gudu hawayen da take riƙewa suka zubo a saman fuskarta, lips ɗinta dake rawa suka motsa a hankali ta furta,
“Muhammad!”.
Sai kawai ta tafi itama luuuuu ɗin kamar Mimi, sai dai ita da alama suna ma tayi. Ƙarar firgita Nimrah ta fasa tana cukuykuye Mammah jikinta na rawa, hakan yasa shi kuma Dada tarosu su biyun duka a jikinsa ya rungume....
Ƙarar Nimrah ce ta kasance tamkar zaburarwa garesu duka. A tare sukai kansu suma. Wata irin runguma Ammar daya fara isowa yay ma Dada tare da fashewa da kuka mai matuƙar dukan zuciya, dan a wannan gaɓar wlhy ya manta da kansa a matsayin namiji. Tamkar yanda Ammar yayi suma su Ma'aruff rungumesan kawai sukai suna hawaye..
A hankali Dada ya lumshe idanunsa da suka juye lokaci guda, cikin wani kalar sanyin jiki da tsinkewar jini ya shiga ƙoƙarin shanye hawayen da yake jin tamkar suna neman ciko masa idanu shima. Da ƙyar Imran daya ƙaraso inda suke da ruwa a hannu ya shiga ɗagasu ɗaya bayan ɗaya. Nimrah dake jikin Dada male-male batare data fahimta ba ya fara kallo, janyewa yay kawai yana murmurshi a zuciyarsa da ƙoƙarin shafama Mammah dake jikinsu su biyun ruwa. Cikin sa'a kuwa ta kawo nannauyan numfashi.......✍️
KIƊA A RUWA 2

52

........“Mammah are alright?”.
Nimrah ta faɗa tana shafa fuskarta ga hawaye na gudu suna ɗiga har kan fuskar Mammah ɗin. Mammah ta buɗe idanu a hankali tana kallonta, sai kuma tai ƙaramin murmushi da kai nata hannun kan fuskar Nimrah ta shafa da jinjina kai. Sake lumshe su tai kafin ta sake buɗewa kai tsaye akan Dada. Shima dai ita yake kallo, cikin wani irin yanayi mai zafi da kamilalliyar fuskarsa ta kasa iya shanyewa. Dan in mai kallonsa bai ƙarya ba ma ƙyallin hawaye idanun nasa keyi. Mammah kam ta kasa jarumtar riƙe nata hawayen tamkar shi, a take ta sake su suka fara kwarara tamkar an buɗe fanfon ruwa. Hannun nata dai data shafa fuskar Nimrah shima takai kan fuskarsa ta sake shafa fuskar a karo na biyu, ɗayan hannun kuma takai kan Imran. “ALLAH yay muku albarka”. Ta faɗa hawaye na sake zubo mata.
A tare suka amsa da amin. Imran da a wannan gaɓar zuciyarsa ta matuƙar raunana da tausayin wannan ahali ya haɗiye abinda ya toshe masa maƙoshi da ƙyar, dan baima san kuka yake ba shima sai da yaji saukar ɗumin hawaye akan tashi fuskar. Da ƙyar ya iya dauriyar dai-daita kansa ya fara lallashinsu.
Sai lokacin Nimrah ta farga da jikin wanda take. Mutumin da ko gama tantance wanene shi batai ba. Sai suna biyu da taji Mammah da Mamy sun ambace sa da shi kacal a yanzu. (Dada! da Muhammad). Yanda take mutsu-mutsu yasa shi shima farga da abinda ke faruwa. ALLAH ya soshi dai-dai Mammah na ƙoƙarin tashi ne, Daddy Imran ya kamata ya zaunar da ƙyau. Har neman faɗuwa Nimrah take wajen barin jikinsa, sai da Aunty Ummi ta riƙeta. Shima Dada sai ya basar kawai tare da maida hankalinsa kansu Mimi, hannu ya miƙa musu, da sauri kuwa suma suka nufoshi suka rungume sa suna kuka. Hannunsa ya ɗaura a bayan Biebah da Mu'azz yana ɗan bugawa alamar lallashi, sannan ya shafa kan Ruƙayya itama. Kafin a hankali ya furta, “It's okay”.
A tare suka shiga jinjina kawuna suna ɗagowa da share hawayensu. Yayinda su Bilal suka kasa daina kallonsa, dan bayyanar fuskar tasa a garesu ta ƙara zama wani abu mai girma da kimantawa. Dadan ne dai da suka sani, sai dai sajen dake kan fuskarsa da basu taɓa gani a baya ba ya canja shi kaɗan. Shima ganin yanda suka zuba masa idanun gaba ɗaya ga falon yayi shiru tamkar an musu tsawa sai ya motsa tausasan laɓɓansa kaɗan ya furta,
“Kallon fa?”.
Cikin yanayin ɗage gira kaɗan akan su Ma'aruff. Tamkar waɗanda ya farkar a barci duk sai su Ja'afar suka fara sakin murmushi, kafin su Ammar su sake rungumesa kamar wanda suka ji kunya. Ya ɗan murmusa kaɗan shima a karo na farko, yana shafa bayansu. Cikin golden voice ɗin nan tasa data iya shanye abubuwa da yawa ya sake furta, “Shi dai wannan kukan bazai ƙare ba halan. Imran kama ƙannenka magana su daina min kuka”.
Murmurshi Imran yayi yana kallonsu, yayinda su Bilal da suka ɗago a jikinsa ke goge hawayen suna murmushi. Cike da lallashi Daddy Imran ya ce, “Gaskiya Haysam ya faɗa, yanzu ba lokacin kuka bane lokacin farin ciki ne. UBANGIJI ya nuna mana wannan ranar batare da mun biyasa ko sisi ba, hasalima ba muyi zato ko tsammani ba. Dan haka a maimakon kuka sai muyita jera masa godiya da kirari zaifi mana alkairi da ƙarin farin ciki a zukata”.
Cikin gamsuwa suka shiga jinjina masa kai suna ƙara share hawayensu. Dai-dai nan cikin kasa haƙuri Ruky ta rage murya da faɗin, “Mammah dan ALLAH waye?..”
Mammah da idanunta ke jajur na kukan da tasha ta ɗaga tana kallon Dada dake zaune a kujerar kusa da ita hannunsa riƙe da nata, murmushi tayi mai cike da abubuwa da yawa, kafin ta janye ta maida kansu dan Nimrah da Rukyn na zaune ne ɗayan gefenta, sai dai daga ƙasan carpet ganin haka su Biebah sukayi, duk sun ƙagu ta basu amsa... Zatai magana caraf Uncle Bilal ya ce, “Mammah karki faɗa dan ALLAH, sai sun bada goron albishir sannan”.
Murmurshi Mammah ta sake saki mai faɗi tana share hawayen da suka sake silalo mata. Yayinda shima Bilal ɗin hawaye yake sharewa tamkar su Biebah da nasu suka gagara tsayawa. Sanyi jikin su Nimrah ya sake yi, tamkar zasu saki kuka suma suka sake maida kallonsu ga Daddy Imran.
Hannu ya ɗaga musu alamar shima babu ruwansa, dan haka akai ƴar dariya mai zuwa batare da an shirya mata ba. Dan shi kansa Dadan sai da ya ɗan yi gajeren murmushi yana kallonsu su duka biyun ƙasa-ƙasa. Sai kuma karo na farko ya miƙa musu hannu alamar su zo garesa...
Ruƙayya dai babu musu ta rarrafa inda yake, Nimrah kam ɗan shiru tayi kamar mai tunani, sai da Mammah ta kamo hannunta tare da mata nunin taje da ido sannan. Itama matsawar tai, amma sai ta zauna kusa da Ruky idannunta a ƙasa dan gaba ɗaya jinta take kamar a cikin matsa-tsi, ba kamar sanda suka shigo ba da take sakayau. Ba ta san dalilin rawar jikinta ba. Ba ta san dalilin bugun zuciyarta ba. Ta san sunan Dada kawai, sunan da take ji a bakin kowa na gidan, suna mai nauyi da daraja a cikin gidansu, sunan da ake furtawa da girmamawa da bege. A karo na farko hoton bidiyon nan ya ratsa cikin tunaninta. Sunansa na ainahi yay mata amsa kuwwa acan ƙasan ƙirji matsayin wanda akace ya kashe mata Ummanta, (Aka ce ko kika gani da idon ki) wani sashe na zuciyarta ya tuna mata, samun kanta tai da matse yatsun hannunta cikin juna, ta sake sunkuyar da kai, dan ji take tunaninta na neman hargitsewa da rabuwa kashi-kashi a kwakwalwar ta.
A lokacin suma su Shariffa suka ƙaraso. Cike da matuƙar girmamawa suka shiga gaisheshi. Idanunsa dake karantar yanayin Nimrah da babu wanda zai iya fahimta ya ɗauke. Kallo ɗaya yay musu suma ya janye idanunsa, su ɗin ƙanne suke a garesa koba auren ƴan uwansa a kansu, sai kuma ga alaƙar auren ya ƙarama matsayin ƙarfi. Cikin kamewarsa da cikar kamala ta uba kuma babban wa ya shiga amsa musu, tare da musu fatan alkairi a cikin aurensu. Sosai suka sake shiga cikin yanayin kunya, girmansa ya sake mamaye musu waje ko kallonsa sun gagara yi, dan koba shekaru shi ne uba ga mazajensu, sannan shi ne garkuwa, shi ne ginshiƙi. Babu wacce ta iya amsawa a cikinsu sai ma sake sunkiyar da kawuna da sukayi. Sai su Mammah ne suka amsa addu'ar tasa da amin.
Sai da suka miƙe suka koma wajen zamansu sannan Ruky da Nimrah suka fara gaishe shi. Suma ya amsa musu da tambayarsu karatu. Suka amsa da Alhamdullah har yanzu kan Nimrah a ƙasa tana cuɗa yatsunta cikin juna. Yatsun nata ya ɗan sake zubama idanu a fakaice tare da janyewa duk a lokaci ɗaya dan cikin sakanni harya gama karantar akwai abinda ke damunta bayan kasancewarsa baƙon ido a cikin waɗanda ta sani, sai dai babu wanda zai ce kallon nata yake, sai ma maida hankalinsa da yay kan Mammah can ƙasan ransa kam mamakin girmansu yake ita da Ruky da Mu'azz fiye da kowa. Ƙasa-ƙasa yay maganar da babu wanda zaice ya ji abinda ya faɗa mata. Sai murmushin ta kawai da kowa ya gani a bayyane....
Shigowar Daddy Imran daya fita ta katse Mammah daga maganar datai niyyar yi, ya dubi su Ma'aruff yana faɗin Su tashi suje gida kafin mutane su farga da abinda ke faruwa. Dan tabbas ana gama sanin Zak-Shadow ne a airport ɗin ba ƴan media da jama'ar gari ba hatta munafukai bazasu barshi ba, dan dama ce mai sauƙi a garesu duk da zagaye suke da jami'an tsaro da suka fara fargar da mutane akwai wani babba dake airport ɗin, saboda a fitar nan tashi ya fahimci hakan ta hanyar ƙananun maganar da ya fara jin na tashi, da ƙyar su Ma'aruff suka miƙe, dan sun san gaskiya Yaya Imran ɗin ya faɗa. Dada ne ƙarshen miƙewa riƙe da Mammah da har yanzu hawaye sun gagara barinta. Ya kuma maida facemask ɗinsa.
A yanda suka fito cikin tsari da nutsuwa duk da kuwa ta hanyar sirri ce yaja hankalin tsirarun mutane dake ta wajen kansu. Dan tamkar ƙyaftawar ido sojojin da suka zo da su da jami'an tsaron da suka tarar na farin kaya a airport ɗin suka zagaye su, suma an ajiye su ne a sirrance batare da sanin su Imran ɗin ba. Wannan kuma duk aikin shugaban ƙasa ne. Mutane da son ɗauke-ɗauke a waya kam har sun fara batare da sun farga da sanin su wanene ba. Sai dai yanda jami'an tsaro sukama mutanen zobe yasa kowa fahimtar koma su waye su lallai masu muhimmanci ne a ƙasar.
A haka suka shiga motoci babu ɓata lokaci aka bar wajen. Sai dai mi, kafin ma su isa gida guntayen videos ɗin da wasu suka ɗauka da ƙananun magana da ake a airport ɗin har ya fara yawo a media, sai dai anata canki-in-canka ne na rashin sanin wanene. Mike faruwa?. Yayinda ƴan bin ƙwaf nacan sun fara bibiyar al'amarin dan sunyi ma kansu alƙawarin kafin dare sai sun gano su wanene ɗin.........✍️


53


.........3:21pm

     Jerarrun motocin masu baƙin gilashi suka

Please Login or Register in order to submit comment