Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

suna masa congratulations yana gyaɗa musu kai da ɗaukar waya dan bakinsa ma ji yay ya masa nauyi. Kai tsaye layin janar ya kira duk da baida tabbacin samu, dan yasan a yanzu duk wani masoyinsa abinda yake ƙoƙarin yi kenan...

Tabbas hasashen Daddy Imran akan Janar haka ne, dan wayoyine keta rige-rigen shigowa wayar sa a dai-dai wannan lokacin, sai dai ta yayansa kawai ya ɗaga sai ga ta Imran ma. Sunan da ya gani yasa zuciyarsa ta tsaya na ɗan daƙiƙai. (Imran....) Sai yaga sunan na koma masa bibbiyu tamkar haɗe da sunan Haysam. Sai da ya lumshe idanu ya sake buɗewa sannan ya ɗaga yana kaiwa kunnensa. Daga sallama abu na biyu da Daddy Imran ya furta shine,
“Sir… mun yi nasara Alhamdullah. Subahanal-lah. Allahu-akbar. ALLAH ya tabbatar da alkairi, mulki jarabawa ce mai girma, ina roƙon UBANGIJI ya dubi tsarkin zuciyarka, da ƙyaƙyƙyawan fatanmu da ƙyaƙyƙyawan zaton da muke maka yay riƙo da hannayenka wajen baka damar sauke nauyin al'ummar wannan ƙasa gwargwadon iko. Duk wanda zai kasance da kai a cikin wannan sha'anin mulkin in har bazarana ne shi ga sauke hakkokin mutane koda wanene ALLAH ya tauyeshi ta inda zai rasa ƙarfin iya yin komai. UBANGIJI ya zama gatanka, bangon jinginarka, mafakarka, damu baki ɗaya. Once again, Congratulations, Sir.”
“Thanks you Imran. Amin ya rabbi Jazakallahu khairan. Imran ka san wannan nasara ba tawa ba ce. Tawa da taka ce. Ta Haysam ce. Ta gaskiya ce.”
Hawaye ne suka cika idanun Daddy Imran daga can, muryarsa na rawa ya ce, “Na gode, Sir… na gode da bama wannan YAƘIN daraja da kake yi.”
“Yaƙin Haysam yaƙinmu ne ƙasa gaba ɗaya, wanda bai sani bane ko bai fahimta bane kawai keja da baya. Ka shirya, dan tun gobe idan ALLAH ya kaimu nake so ka fara haɗa min duk bayanan shari’ar Haysam tun daga farkon ranar da aka fara har ƙarshe. Ba zan shiga gidan gwamnati ba tare da na duba gaskiya ba. Lokaci ya yi da za mu dawo masa da mutuncinsa tare da namu muma Imran. Dan haka kwana ɗaya kawai zanyi da shiga gidan gwamnati Haysam ya fito in sha ALLAHU”.
Daddy Imran ya gyaɗa kai, hawayen da yake ta riƙewa tun ɗazun na sauka masa. Muryarsa ta shaƙe a cikin maƙoshinsa dake kai-kawo da nauyin shekaru takwas na zafi ya furta, “Sir! Sai nake jin kamar ina mafarki ne irin wanda na sabayi. Dan ALLAH idan barci nake kada ku tada ni”.
“Ba barci kake ba Imrana. Gaskiya bata da lokacin jira. Dole tun a yau mu tunawa kammu akwai wani mutum da ba zamu bari ya cigaba da kwana cikin duhu ba bayan ALLAH ya bamu wannan AMANAR, maza kaje, jeka ka fara shirin fitowar gwarzon haziƙin jarumin soja mai gaskiya da kwatanta gaskiya akan kowace gaskiya duk ƙarfinta.”
“Thanks you Sir! Thanks yo...”
Daddy Imran ya kasa ƙarasawa saboda yanayin da yake ciki misaltashi sai UBANGIJI. Ji yake tamkar zai faɗi sai da ma Ammie ta riƙeshi suka zauna ta miƙa mashi ruwa. Dama ta kora su Asma'u suje suci abincin dan kaf ɗinsu yau babu wani abincin kirki a cikinsu saboda uban gayya bai ci ba hankalinsa nakan television yini guda.
Tambayar da Ammie ta jefa masa a karo na farko game da al'amarin yasa Daddy Imran kallonta cikin ido. Wani sassanyan murmushi ya sakar mata, batare da ya buɗe mata ba a dunƙule ya furta, “Akwai wani mutum guda dake bina bashi Hafsat, bashin adalci, bashin ƙauna, bashin zuminci.
Kuma lokaci ya yi da zan biyashi koda da kwatantawa ne.”
“ALLAH ya cika maka wannan buri Daddyn Khalifa”.
“UBANGIJINA ya cika min sai dai tabbatarwa”. Ya faɗa cikin salon raɗa da rungumeta a jikinsa.....

=============
★PRISON★

A kwanakin farko na kawo television ɗin ɗakinsa bai maida hankali akan zaman kallonta ba, dan lissafinsa nakan haɗa kalaman vistor ɗinsa da musu fashin baƙi a farashin mutane masu hangen nesa da basu raina bincike irinsa. Abu uku kawai da aka turke tvn da ita ne ya fara tasirin jan hankalinsa gareta dole. Sun saka mata security ta yanda bata kasuwa, bai iya rage volum, bai canja tasha daga ukun nan kacal duk da kuwa akwai remote. Duk da basu sakata da ƙara mai takura ba kasancewar sa mutum mara san damuwa da hayaniya sai da ta fakurashi a kwanakin farkon. Sai daga baya daya fahimci an kawota ne garesa dan tai masa irin wannan takurar ai sai ya dake ya ajiye komai gefe har a kwana na huɗu ya maida hankali a kallon fashin baƙin masana akan taron campaign ɗin da aka rufe, a bazata yaci karo da na Janar Yusuf Shu'aibu Tafida ne a gaba. Duk da bawai akan Janar ɗin masu fashin baƙin ke tattaunawar ba, suna tattaunawa ne akan mabiyan ɗan takara, inda daga ƙarshe suke faɗin alƙaluma na sake nuna tsohon Janar dake gaba wajen tara masoya a duk jahar da yaje. Wannan shine karo na farko daya fara bama tvn hankalinsa, daga ranar kuma ya cigaba da bibiyar komai daki-daki, har hakan ya bashi damar fara tantance kowace fuska dake tare da Janar Yusuf dama sauran ƴan takara tun daga na shugaban ƙasa har zuwa shugabannin jihohi. A haka aka gangaro har ranar zaɓe, duk yanda abubuwan ke gudana nan ma yana biye, sai ta kai har ƙirga ƙuri'u ya bibiya. Sai dai a yau da aka tashi da jiran faɗar sakamako ya yini da ciwon kai saboda matsawa kansa da ayyukan ƙwaƙwalwa da yay a cikin satin nan gaba ɗaya. Dan haka bai wani maida hankali ba sosai ga television ɗin, bayan ma ya idar da sallar isha'i yay zaman fara karatun Alkur'ani ne, kasancewar tvn ba kasuwa take ba, ba rage ƙara take ba a bazata bayanin shigaban hukumar zaɓe ya shiga cikin kunnensa.
Cak harshensa ya tsaya dai-dai da bugun zuciya na sakanni, kafin ya iya ɗago manyan idanunsa zuwa kan tvn ya saukesu akan fuskar ɗan jaridar dake maimaita kalmar.........✍️

KIƊA A RUWA 2

29

..........“Wow! Congratulations, Her Excellency General Yusuf Tafida.”
Dada bai motsa ba. Bai yi murmushi ba. Bai yi mamaki ba.
Sai dai zuciyarsa ta furta abu guda ɗaya dai-dai da lumshewar idanunsa a hankali (Wata rana gaskiya za ta dawo da kanta. In dai har zuciya bata manta da UBANGIJI da masu gaskiyar ba) sai kuma a hankali ya ajiye Alkur'anin ya zame zuwa sujuda. Ya jima kafin ya ɗago ya sake ɗaga hannu yana ambaton, “Subahanal-lah! Allahu-akbar!”. Akan tausasan laɓɓansa
Bai ce ya damu da samuwar shugabancin Janar Tafida domin ya fita anan ba, amma tabbas ya damu da addu'ar ƙasar nan tasamu mai kishin ƙasa kamar Janar da yakema ƙyaƙyƙyawan fata akowane motsinsa, ta samu shugaba mafi alkairi, yana ji kuma a ransa ogansa kuma yaya koma uba shine zaɓin ALLAHn da suke fata da roƙa in sha ALLAHU. Sake juyawa yay yana kallon tvn a karo na biyu, dan duk da sanarwar dare ce wasu wajajen har al'umma sun fara bikin murna, sauke numfashi mai nauyi yayi, zuciyarsa tana ƙonewa irin ƙonawar da MAZAN FAMA kawai ke iya fuskanta a lokacin da suke iya hango HASKEN MASU GASKIYA......

÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷
★ONE WEEK LATER★

Sati guda kenan da bayyana sakamakon zaɓe. Janar da ubannin gidansa dama talakawan ƙasa da suka zaɓesa sun sha shagulgulan biki tako wane ɓangare. Idan ka cire sauran mabiya sauran jam'iyyu dake cikin takaici da baƙin cikin rashin samun nasara. Sai dai abinda mu talakawa da muke a wannan yanayin basu fahimta ba. Su waɗan can manyan da suke so tuni sun ƙulle da Janar ɗin anata farin cikin samun nasara. Sai a kafafen media ne kawai suke suka da nuna rashin jin daɗi. Duk da kuwa da yawansu har cikin zuciyarsu suna jin rashin daɗin, amma suna shanyewa saboda a hakan ma dai da ai dasu za'aci gwamnatin tunda dama duk tafiyar ɗaya ce a baɗini, a zahiri ne ake daban-daban.
A lokacin da nan ake faman bidirin farin ciki ga sabon shugaban ƙasa janar Yusuf ba haka bane ba. Duk da bai kai ga tarewa a gidan Gwamnati ba aikin suke ta ƙarƙashin ƙasa shi da Daddy Imran da Haydar Galadima (Faro).
Dan a yanzu haka a yau Janar Tafida ya gama ganawa da kwamitin miƙa mulki da sukai zaman meeting da tunda aka ci zaɓen nan shi suketa zamanyi saboda tsare-tsare musamman ƴan jam'iyya da kowa ke ganin lokacin fanshe wahalarsa tayi za'a bashi muƙamin da yake buƙata. Suna fitowa daga meeting ɗin aka ɗaukeshi zuwa gida. Tun ma kan ya ƙarasa shigewa falon sashensa ta baya kasancewar gidan bashi cike yake da dangi sati guda kenan ya ciro wayarsa a aljihu ya fara neman layin Daddy Imran.
Bugu biyu Imran ya ɗaga, dan a lokacin shima suna tare da Faro ne a wani guesthouse ɗinsa da in har zasuyi magana akan Dada can suke zuwa.
A nutse Daddy Imran yay sallama tare da gaishe da Janar. Daga nan ya amsa masa sai dai Daddy Imran baya jinsa sosai sakamakon matsalar rashin network da kowa ya sani ƙasar na fuskanta. Hakan ne yasa Janar ɗin faɗin, “Ka na ji Imran?”.
“I’m here, Sir.”
“Yauwa ina fatan kun kammala dukkan abinda muke buƙata?”.
“Yes sir! Yanzu haka ma ina tare da Haydar anan guesthouse ɗina. Ga komai daya dace a hannunmu ko abu guda bana tunanin mun bari yayi saura. Hatta da sabbin bayanai akan Ojo Dabo ya zo da su a daren jiya, sune kawai nake ganin zanyi ƙoƙarin tabbatarwa dan nima akwai wasu a hannuna”.
“Babu lokaci Imran, inaga ku ajiye sabbin bayanan Ojo yanzu a hannunku, muyi amfani da tsoffin dake wajenka zasu wadatar. Dan wannan aikin shine farko da nake son na gabatar a ƙarƙashin mulkina a ranar dana taka ƙafata a gidan gwamnati in sha ALLAHU washe gari sake nazarin shari’ar Haysam Abdul-rasheed Shehu zai tabbata. Babu wani aiki da zan gabatar na tabbatar da godiyata ga ALLAH sai in fara da wannan. Dan haka ku kasance cikin shiri kawai”.
Daga can Daddy Imran ya runtse ido yana sakin wani wadataccen murmushi mai faɗi da armashi, dan yana jin kamar an buɗe wata ƙofa da ta rufe a zuciyarsa da ƙwaƙwalwa a shekaru takwas da suka gabata, ƙofar dawowa, ƙofar adalci, ƙofar fansa.
Cike da wata irin muryar shauƙi ya furta, “Sir! Umarninka kawai muke jira a wannan gaɓar”.
Murmushi mai faɗi shima Janar ya saki, tare da faɗin, “Imran… ka shirya abinda na tambaye ka?”.
“Na shirya Ranka ya daɗe. Na dawo da kowace takarda, kowace sanarwa, kwafe-kwafen shari’a, rahotanni, bincike, duk wani abu na shekaru takwas ya kammala a cikin kundi guda ɗaya. Kundin da saka hannunka kawai yake buƙata da umarni yayewar baƙin labulen daya rufe min gani da jin Zak-Shadow. KIƊA A RUWA MAI TADA HANKALIN DODONNI.”
“Good Imran. Lokaci ya yi da zan sa hannu wajen dawo da gaskiya. Lokaci yayi da The two shadows zasu sake bayyana a inuwa ɗaya. Amma…” ya ɗan yi shiru, sai kuma ya cigaba da faɗin “......ba za mu je tare da kararrawa ba.”
Daddy Imran ya fahimta. Aikin da aka basu ba na kan titi ba ne. Yana cikin inuwa, cikin sirri kamar yadda azzalumai ke yin wasan su. Tamkar yana a gaban Janar ya ƙame jikinsa waje guda irin aƙidar sojoji da girmamawarsu, sannan ya sara masa da Salute na girmamawa mai harsuna da yawa har Janar na iya jin ƙarar bugawar ƙafafunsu shi da Faro da shima ya miƙe ya ƙame. A tare suka furta, “Yes, Sir. I'll handle it quietly”.
Daga can shima Salute ɗinsu Janar yayi yana wani shegen murmushi mai matuƙar bayyana tsantsar makamancin farin cikin da yake a cikin zuciyarsa. Daga haka ya yanke wayar. Ba ajiyeta yayi ba, sake lalubo wata number yayi. Lambobi ne da ba kowa ke da su ba, lambobin da suka tsaya tsayin shekaru biyu babu wanda ya kira shi da su. Badan bai isa ba, sai dan shiri irin na masu makirci dake da dama a hannu. Sai dai yau shi zai kira, kiran da dole a ɗauka masa kuma a risina masa, dan wannan kiran ya zama dole ga masu amsawar..
A bazata kiran tsohon Janar ya shiga wayar babban hafsan tsaro da zai hau aiki tare da shi a sabuwar gwamnatinsa. Kiran daya saka General a ƙaulani, firgici, ruɗani duk da bai san takamaiman dalilin sa ba. Amma shi ya san jiya ba yau bace, ko giyar waye yasha bai isa hana kansa amsa wannan kiran ba a yanzu. Cike da rawar jiki kuwa ya amsa, cike da girmamawa da risinawa da ƙanƙan da murya ya fara gaishe da tsohon Janar ogansa a gun aiki, sabon shugaban kasar sa mai jiran gado kuma a yanzu.
Janar Yusuf Shu'aibu Tafida yay wani murmushi mai ma'anoni da yawa yana mai jinjina kai. Lallai ƙasa ta lalace, lalacewar da mutane sun koma girmama kujerun iko sama da girman daraja da kimar ɗan adamtaka da UBANGIJI yayi ma bayinsa. Bai ja tunaninsa da nisa ba ya fara magana ba daɗi, ba sirri mai nauyi, amma da umarni.
“Ina bukatar sashin ku ya fara nazarin batun jami’in SOJA da aka jefa cikin gidan maza shekaru takwas da suka wuce. Ba tare da hayaniya ba.”
Cikin matuƙar bugawar zuciya Genaral ya furta, “Sir! Zak-Shadow?”.
“Eh. Na san akwai ɗan hazo. Ina so ku share min hanyar ganin shi cikin sirri kafin na shiga ofis.”
Yawu mai matuƙar kauri Genaral ya haɗiya jininsa na tsitstsinkewa, a take zufa ta jiƙe jikinsa sharaf. Ya kasa magana har sai da Janar Yusuf yay gyaran murya irin ta manyan da umarni kawai suke badawa sau ɗaya tak.
Kamar wanda aka farkar a suma General ya amsa da sauri har harshensa na sarƙewa. “Za’a yi, Ranka ya daɗe. Amma wannan… zai bugi wasu mutane.”
“Ai dama so nake ya buge sun da bulala mai zafi da dafi. Dan lokaci yayi da zasu ji su kuma sani. Gaskiya ba ta tsorata da MAKIRCI ko ƘARFIN IKO. Gaskiya ce take tsoron TUGGU koda MAKIRCI yayi nasarar ƁOYETA.”
General ya kaɗa kai kamar tsohon ƙadangare dan ya kasa magana ma. Sai sake wanke masa jiki zufa take dan tabbas a wannan gaɓar yana a tsaka mai wuya ne.....

<<%>>★<<%>>
PRISON

*8:30pm* aka samu baƙuncin jami’an tsaro na musamman, dole a kirasu jami'an dana musamman, domin ko sun iso ba tare da hayaniya ba balle yanayin rububi. A nutsensu suke cikin Uniform. Kai tsaye kuma sun nema ganin shugaban prison ɗin ne ta hanyar bama securitys ɗin dake kula da shiga da fitar kowa takarda.
KIƊA A RUWA 2

30

.........Isowarsu ɓangaren da Dada yake ya tabbatar min da lallai ba wannan jami'an bane ainahin vistors ɗin, dan a ƙofar wajen suka samu wanda akaima rakkiyar. Bayan sun ƙame tare da salute ɗinsa ɗaya ya matsa yana sanar da ogan nasu cikin magana ƙasa-ƙasa. Kansa kawai ya jinjina batare da yin magana ba, kuma ba'a ganin fuskarsa dan ya saka norse mask ga eyeglass, sannan kansa da hula p-cap data sake ɓoye ainahinsa. Yana sanye cikin ƙananun kaya daga sama har ƙasa baƙaƙe.
Har cikin ainahin ɗakin ganawar securitys ɗin sukai masa rakkiya, dan shi kaɗai ya shiga banda jami'an sa. Koda suka nuna masa kujerar zama bai zauna ba, yana daga tsaye kawai a cikin dakin yana jiran shigowar wanda zuciyarsa ke bugawa saboda tsoron abin da zai gani, tsawon shekaru biyar har da wattani huɗu a kai bai ga Zak-Shadow koda daga nesa ba. Mintina kaɗan da suka kasance masu nauyi na cika wanda yake begen gani da ƙagauta ya iso.
Cak numfashinsa yaso tsayawa sakamakon bayyanar mazan fama, sosai ya rame fiye da wancan ganin da yay masa na shekarun baya. Duk da lokaci-lokaci ana masa aski hakan bai hana gashin saje taruwa a farar fuskarsa ba da kansa. Fata kam tayi haske da kwanciya saboda zaman waje guda. Sai dai baza'ace akwai laushi na jin daɗi ba. Yanda yake kallonsa haka shima Dada ke kallon nasa, dan duk da ya rufe fuska a kallo ɗaya ya gane wanene, dan ko cikin rububi manta wannan halittar ta gabansa sai dai ɗimuwa a lokacin magagin mutuwa amma ba a cikin hayyaci ba.
A karo na farko baƙon ya ɗan murmusa da ƙoƙarin danne abinda ke yunƙuro masa. Sai kuma ya kai hannu a hankali ya zare glasses ɗin idanunsa. A tare idanuwa nasu suka haɗu a cikin na juna. Imran ya kasa motsi. Haka shima Dadan bai motsa ba, dan kai tsaye zuciyarsa yake kallo a zahiri.
Fin sakan talatin suna a haka kafin Dada ya saki wani ɗan murmushi da lumshe idanu ya buɗesu a lokaci guda, a hankali ya cigaba da takowa har inda Imran yake. Har yanzu nutsatstsiyar fuskar nan tasa da murmushin nan nashi na ƙasaita, ya motsa lips kamar mai son raɗa ya furta, “Ranka ya daɗe, soja… har yanzu baka daina kuka da ido ba?”.
Kauda kai Daddy Imran yayi yana haɗiye hawayen da basu ƙaraso cikin idanunsa ba, amma da yake Zak-Shadow ɗin nasa Zak-Shadow ne shi har ya karantosu daga ƙirjinsa.
Wata ƴar ƙaramar dariya Dada ya saki da kaiwa zaune, ƙafarsa ɗaya kan ɗaya hannayensa da yau babu handcuffs harɗe a ƙirjinsa ya sake faɗin, “Sit mana my Boss”.
Yanzu kam shima murmushi Daddy Imran yayi, sai kuma ya gyara kujera ya zauna irin zaman Dadan suna kallon juna tamkar wani saurayi da budurwa.
“Na yi missing naka sosai, Zak...” kalma mafi nauyi da girma dake riƙe da zuciyar Imran ta fito daga bakinsa. Sai kuma hawaye suka cika masa idanu.
“Idan ka cigaba da wannan kukan, how many missions za ka gama?. Kalleni da ƙyau ina raye, kuma ina cikin ƙoshin lafiya mi kake buƙata bayan hakan daga UBANGIJI? Ko sai na tashi mun gwada ƙarfi ne?”.
Dariya sosai Daddy Imran keyi cikin hawaye, dan ya fahimci yau raha Zak.. ɗinsa ke ji. Kai tsaye ya ce, “Kai dai ba zaka canza ba.”
“Zama da kai ne Imran, kwana biyu sai nake jin matsanancin kewar ka. Ashe kana gab da ni ne shiyyasa.”
“Duk randa muka zama a nesa da juna lallai ƙasa ta bizne idanun wani a cikinmu ne ko mu duka. Sai dai ni nafi fatan fara tafiya na barka dan nasan bazan iya ɗauka ba idan kai ne ka barni”.
Idanu sosai Dada ya zuba masa. Dan haka shiru ya biyo baya, irin shirun nan mai cike da abubuwan da bazasu faɗu ba. Tsohon lokaci kafin Daddy Imran ya katse yanayin nasu ta hanyar miƙa masa briefcase daya shigo da ita.
“New President Yusuf Tafida… ya buƙaci nazarin shari’arka tun daga farko har ƙarshe. Sai dai ba yau za mu faɗi komai ba. Amma daga yau ɗin game ya fara dawowa.”
Cak numfashin Dada ya tsaya ba ƴan sakanni, ya kuma zuba ma Imran ido tamkar zai haɗiyo shi da su, “Sabon shugaban ƙasa, zai iya zama yana da alaƙar huɗɗa da waɗanda suka karyar da ni fa Imran, sai dai maybe shima bai sani ba.”
“Miyasa kai wannan tunanin? Dama ce fa tazo mana daga UBANGIJI. Kafa san wanene Janar”.
“Tabbas nasan Janar, sani na nagarta da mazantaka. Ba kuma bana farin ciki da damar bane, ina ganin kamar yazo da gaggawa ne, gaggawar da zasu iya kaishi ƙasa da ita a kaina, dan yazo musu da bazatar abinda ba shi suke hasashe ba a kansa. Dole ya zama mai zaɓi biyu a lokacin da ya bayyana musu ainahin fuskarsa a kaina. Saboda a tsarinsu babu wani shugaban ƙasa da zai kasance baya abota da su. Koda sun ɓoye masa waccan fuskar tasu a yanzu inada tabbacin zasu bayyana masa ita ya sansu ya san aikinsu. Matsalar kuma idan har yana son gaskiya, to sai ya tabbatar min da hakan da aikin shi. Ba da kalamai ba. Dan kar ya kasance na amince na fita ya zama yana cikinsu bazan ƙyalesa ba koda shine Abdul-rasheed Shehu Isa Kobi”.
Daddy Imran ya fahimci hangen Dada, dan haka ya sauke numfashi mai nauyi yana jinjina kansa da faɗin, “Haysam na yarda da ku kai da Janar da Faro. In sha ALLAHU Janar bazai bamu kunya ba, yanda muka fara da shi zamu ƙare a tare koda sai bayan babu ran mu ne NASARA zata bayyana. Na tabbatar shima kamar mu ya ke, idan gaskiya tana gona, zai haƙo ƙasa ya nemota da kansa.”
Dada yayi murmushin mai zafi fiye da bala’in da yake hangowa da ƙurar da zata tashi. “Shike nan Imran! ka gaya masa, idan yana neman gaskiya, kada ya zo da haske. Duk wanda yake neman ƙasar nan, sai dai ya biyo duhun dare. Ni zan fara jiranku daga yau. Ku dinga tuna kuma zan dawo da gudunmawata. Game on.... again.” yay furucin ƙarshe da wani salo yana kashema Imran ido ɗaya da yin alamar harba bindiga da yatsu biyu.
Dariya Imran ya kece da ita, irin dariyar da shi kansa yasan ya jima baiyi ta ba. Kai koda kwatance baya kawota a zuciyarsa balle ma fuskarsa. Shima Dadan kallonsa yake yana wani shegen murmushi mai bayyana haƙwara, kai daka gansu kasan ƙara'in farin ciki ne na tsahon shekaru ke fidda kansa tun daga ƙasan zuciya har zuwa fuskokinsu. Sai dai Imran yasan minene ma'anar murmushi irin wannan a fuskar Zak-Shadow ɗinsa. Ya tabbatar zafin daya jure cikin wannan duhu na tsawon shekaru takwas da wata huɗu, sakamakon wannan murmushin idan ya fito ƙasa za ta sake girgiza......

<%><%><%><%>

“Malam Almu maganar ciwo ai ta wuce wasa, kuma ta kori komai a rayuwa. Dan haka babu batun neman alfarma zuwa gida daga garemu. Ka shirya kawai abinka ga kuɗin mota. Wannan kuma sai kai amfani da shi wajen kaita asibiti, ALLAH ya bata lafiya yasa kaffara ne. Zaka wuce yau ne ko sai zuwa gobe? Dan muma zamuje airport ne ɗaukar Bilal yau zai dawo”.
“Kai kai Masha ALLAH. Yau Alhaji Bilal zai dawo ashe? To bari na jira ya dawo tukkuna ai kamar zai fi”.
Kai tsaye Mammah dake saurarensu ta ce “A'a Malama Almu ban goya bayan haka ba, kaje dai tunda zaka dawo ai. Itama Innarka na buƙatar ka, kuma tana

Please Login or Register in order to submit comment