Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

yallaɓai,ya kamata a rinƙa sallama dai"

"Ke fa ba'a razana ki,na manta"ya faɗa yana dungure mata kai"

"Akan me za'a razana ni?ka san dai na fika juriya ko?"ta faɗa tana murmushi gami da kashe ido ɗaya

Murmushi yayi yana faɗin"to anji"ya dauko hijabin ta da ke gefen ta ya fara ƙoƙarin saka mata,ta kalle shi don neman ƙarin bayani,ya raɗa mata a kunne"we have a visitor, very best friend"karɓar hijabin tayi ta ƙarasa sakawa,shi kuma ya fita ya shigo da baƙon

Mamaki ya kamata ganin Imran,wanda rabon ta da shi ma tun ranar da ta sauka ƙasar ita da su Aunty nusaiba,Amma bata nuna masa komai ba a fuska tayi masa sannu da zuwa,ya amsa da fara'a ya zauna suka gaisa a mutunce,yanayiwa Affan wasa

Deeja ta kawo musu soft drinks sannan ta samu waje ta zauna,Imran yayi ɗan murmushi yana faɗin"thanks"sannan ya zuba lemon a kofi ya fara sipping a hankali

Ya dubi Deeja cikin sanyin murya yace"Khadijah,zuwa nayi na musamman don neman afuwar inconveniences ɗin mu, I know we did alot to you that I'm sure you will never forget with it,can you find a place in your heart to forgive us please?I regret my evil act definitely and.......wasu abubuwan barin faɗar su inaga yafi amfani,ina roƙon ki yafe mana Ni da Umaima,duk da cewa zuwa yanzu Ni kaina ban san inda take ba"

"I can't get baka san in da umaima take ba"ta faɗa tana kallon shi

"Mun rabu ai"

"Na san da haka"shiru yayi yana kallon ta don bai gane abinda take nufi ba

Murmushi yayi tayi tace"duk abinda ya faru ya wuce, abinda baka son faɗa min ma na sani, kuskuren ka baka iya dogon nazari kafin ka aikata abu,da ace kana dogon nazari babu yadda za'a yi Najeeb ya rinƙa juya rayuwar ka har ma da ta matar ka,kuma na biyu,meyasa zaka kori Umaima?ina ce ta gaya maka bata da wajen zuwa? meyasa baka saurari uzurin ta ba,to ka sani duk wani hali da Umaima ta shiga bayan barin ta gidan ka kaine sila"

Mamaki mai tsanani ya ƙamar da Imran,kenan dama Deeja ta san Najeeb ke juya rayuwar su?ya akayi ta san cewa Umaima ba ƙanwar Najeeb bace,amma sai yace"babu abinda nayi Deeja,of course bana buƙatar ta a rayuwa ta anymore,tace zata koma garin su,na bata kuɗin da na tabbatar zai ishe ta kuɗin mota?idan ita marainiya ce bata da iyaye bata da family ne?idan har da gaske take why not ta koma wajen su?me zanyi mata after that? openly ta ci amana ta da aboki na, shiyasa naga gwara na bar masa ita, seems like bata shirya wa zaman aure ba,sai suje su cigaba da abinda sukeyi kawai"daga yadda yake maganar kaɗai ya isa a gane irin raɗaɗin da yake ji a zuciyar shi

Deeja tace"shine kuskuren da ka tafka Dr,baka san wacece umaima ba,baka san komai daga gare ta ba amma ɗauki zafi daita,ba sai na gaya maka ba,ka san na san yadda Umaima take mutuwar son ka,yadda take son ka haka take gudun ɓacin ranka,kasan da haka ko?"

Imran ya ɗan yi shiru in confusion yana kallon ta,shi dai Khalees kallon su kawai yakeyi,bayan wasu ƴan seconds yace"what are trying to say Khadija?"

Wayar ta ta ciro babu ɓata lokaci ta nemo wani hoto ta miƙa masa,ya amsa yana kallo,kallo ɗaya yayiwa hoton gaban shi ya faɗi,shima Khalees kallon babyn yakeyi,da ya kalle ta sai ya kalli Imran,tana zaune akayi mata hoton,sanye take da farar dogon riga mai adon pink flowers,kanta an sanya mata pink ɗin bandana,gashin ta irin na larabawa anyi masa style mai kyau da kayan kitso masu ɗaukar hankali,tana rike da abin wasa tana kallon wani wajen ta ɓangale baki haƙoran ta guda biyu sun fito, Imran ya tsurawa yarinyar idanu ko kiftawa baya yi, Khalees ya ɗago ya kalli Deeja yace"baby luv wannan babyn fa? resemblance ɗin su da Imran is too obvious"

Batare da ɓata lokaci ba tace"ƴar shi ce"a tare suka zaro idanu suna kallon ta a firgice, Deeja tace"yeah, Umaima ta tafi garin su da cikin ka kuma alhamdulillahi ta haihu lafiya,an samu yarinya ta saka mata suna na"ta ƙarashe tana murmushi,daga nan ta basu labarin Umaima,ta ƙara sa cewa"yanzu haka na ɗauko ta,tana nan gida na na Na'ibawa,yanzu zancen da nake ma ta koma makaranta,don na tabbatar da ace Najeeb a hanyar makaranta yaga tayi collapse da bai isa ya wulaƙanta rayuwar ta har haka ba,kuma duk da cewar Mima ta fara min takwara nafi jin na Umaima a raina"

Dukan su shiru sukayi na ƴan daƙiƙu cike da tausayin Umaima,Imran ne yayi gyara murya ya fara magana cikin sanyin murya"ban san komai dangane da rayuwar ta,bata taɓa bani labarin rayuwar ta ba,na ganta tana rayuwar ta comfortably,da farko nayi tsammanin Najeeb yayan ta ne,na shiga shock sosai lokacin da ya tura min hotunan su da videos ɗin su suna baɗalar su,har da ce min gudowa tayi daga garin su ta biyo shi,wai kuma lokacin da zata aure ni tayi masa alƙawarin duk runtsi bazata guje shi ba,amma babu komai,na yafe masa,don yanzu haka fama yake da kanshi,yanzu dai ina rokon ki ki taimaka ki shawo min kan Umaima,tunda kuka fara haka da ita mawuyaci ne ta dawo min, because Umaima is too stubborn"dariyar babu shiri ta ƙwacewa Deeja,tace"wallahi kuwa akwai ta da taurin kai na bala'i ma kuwa,batayiwa ƴan gidan su magana fa,ranar da muka taho fa don na matsa mata ta shiga tayi wa ƴan uwan ta sallama sai ta fashe min da kuka"

Imran yayi murmushi mai sauti yace"of course naji daɗin zama da umaima but ta cika kafiya da taurin kai, shiyasa lokacin da kika ɓace nace tasan in da kike,kuma na matsa mata ta fito dake"

Tunda dai ƴan adawar Umaima suka shirya daita nasan zasu shirya da likita bokan turai,ina nufin jidda da Juliet 😅

Proud of you commentors and likers🥰

#Nusy_bee

*****MATAR KHALEES*****

✍️Nusy bee

Post 38

Deeja tayi murmushi tace"zanyi maka ƙoƙari in Sha Allah,duk da stubbornness ɗin ta tana jin magana ta, a matsayi na na babbar yaya

Wani kallo sukayi mata duka su biyun, sannan suka fashe da dariya a tare,buɗa ido tayi sosai tana musu kallon ƙarin bayani, Khalees yana dariya yace"karo na farko a tsawon rayuwa ta da naga babbar yaya da auta sun haɗu waje ɗaya"kawar da kai tayi tana ɗan murmushi,ita fa a tsawon rayuwar ta dama ba wai tana ƙaunar sunan bane,amma bata taɓa jin sunan ya yarfa ta irin yau ba,amma saboda ƙi faɗi sai ta kalli Khalees tace"ai suna ne kawai,a family Mutum nawa na girma?ko baku san ina da ƙani ya rasu ba?idan Dr baka sani ba ai shi abban Affan ya sani"Khalees yana dariya yace"anyi haka,kin girmi mutane na manta,kamar yasmin,kin girmi fadila,kin girmi Mima,kin girmi Mubarak,kin......"

"Aa Ni fa ban ce na girme su ba,kunga a bar maganar kawai"ta faɗa tana shan mur

Imran yace"Hajiya Deeja kenan,ko bayan shekaru ɗari kaga mutum ka tambaye shi komai amma banda halin shi,ke kam Allah yayi miki arzikin son girma sai gashi kin zo a kalen hanji"

"Naji nace a bar maganar"ta faɗa tana zaro idanu"zanyi magana da umaima,zata dawo in Sha Allah"

"Kiyi mata barazanar yace idan bata amince ba zai amshi ƴar shi"a cewar Khalees yana murmushi,

Deeja tace"wa?umaiman?ita da tace na ɗauki yarinyar ta bar mini?amma idan baban ta yana so sai na bashi,tun ma lokacin ko zama batayi,"Imran yayi dariya yace"shiririta!baka san Umaima bane idan ta kafe akan abu,nayi mamakin yadda ta yarda ta biyo Deeja, gaskiya kinyi Sa'a,ko kuma yet she is feeling guilty na abubuwan da tayi miki ne"Deeja tace"whatever,sannan akwai abu ɗaya da nake roƙon ka Please"

Yace"ina jin ki"Deeja tace"ka koma Bauchi ka daidaita da mahaifin ka, it's already time,ko ba komai ka san abinda ya faru ba laifin shi bane,no matter what bazai taɓa juya maka baya ba,kuma for now ka bashi enough space, kusan six years,why not baza kayi letting komai ya wuce ba? I know yadda bai san Aunty Ramlah ba dole zaiyi kewar ka as the only son da ya mallaka"ta ƙarashe tana tsare shi da idanu

Da Imran da Khalees duk kallon ta sukeyi har ta ƙarasa bayani,a hankali Khalees ya mayar da kallon shi ga Imran da ya sunkuyar da kanshi yana tuna baya, Khalees ya dafa kafadar shi yace"all is well friend, Deeja tana da gaskiya, ba'a fushi da iyaye no matter what happen,I know you well friend,nasan ba fushi kayi ba but it's already time ka nemi sasanci da dady,You will never regret it in Sha Allah"Imran ya jinjina kanshi,a sanyaye yayiwa Deeja godiya sosai,yayi mata sallama suka fice shi da Khalees,ya ɗauki Affan da yake ta ƴan wasannin shi suka fita tare

Sati biyu tsakani Deeja, Afra,lubaisa da zakiyya suka ziyarci Umaima a motar Deeja,tana parlour ta goya little Deeja da ke jin rigima sai zaga parlourn takeyi,ta kunna suratul Nur a waya sai bi takeyi,ita kuma mama lami tana kitchen tana dafa musu abincin dare,sai jin sallamar su tayi

Da sauri ta leƙo,tana ganin Deeja ta tafi da gudu ta rungume ta tana dariya,duk da cewa kiyya ta san labarin komai amma tayi mamakin chanjin da ta gani a wajen umaiman,gashi yanzu asalin farin ta ya dawo,tayi fes da ita, dama umaima akwai gayu da iya kwalliya, yanzun ma tana sanye da English wears riga da wando pink colour,ta ɗauke gashin ta da baƙin ribbom. Afra tana kallon ta tace"lallai umaima!wato mu duk baki ganmu ba ko?"da sauri ta saki Deeja ta rungume su ɗaya bayan ɗaya tana murmushi,ta ja su suka shiga parlourn, kiyya ta amshi little Deeja tana kallon ta

Nan da nan ta kawo musu drinks da snacks tana faɗin"yau anyi surprising ɗina"lubaisa tace"sistern ki ce ta tattago mu"Umaima tayi murmushi ta kalli Deeja da take danna waya tana murmushi itama, kiyya tace"Ni kam ban ma san sanda aka tambayi abban su ba,sai ce min yayi wai khadija tace zamu fita"Afra tana dariya tace"ballantana kuma abban haneef,jira yakeyi auta tace ayi yace an gama"da tsokana ta faɗa tasan Deeja bata ƙaunar,ai kuwa ta ɗago ta zabga mata harara,duk suka kama dariya

Sun ɗan taɓa hira da raha, Deeja ta tambaye ta game da karatu,cikin zumuɗi take sanar mata da cigaban da ta samu,yanzu haka tayi wajen izu ashirin da biyar,ga litattafai na addini,game da institution kuwata fara lecture a MAAUN in da take karantar business administration,su kansu su Afra ba ƙaramin burge su Deeja tayi ba,a hankali Deeja ta shigo da maganar Imran

Ɗif umaima tayi bata sake magana ba,suka haɗu suna ta roƙon ta ta koma, Afra tana murmushi tace"nayi missing ɗinki sosai sister,gidanmu ma yayi missing ɗinki,kuma Dr ma yayi missing ɗinki sosai"Deeja tace"kuma ko ba don shi ba ki taimaka ki koma don takwara ta,she will be very happy ace ta tashi gaban iyayen ta duka biyun,sai ta fi jin dadin tarairayar da zaku mata"kiyya tace"seriously Umaima ko da nasan da Bama shiri ranar da Imran ya sake ki da abban su Aisar ya sanar min komai game da ke banyi bacci ba,I wish kin koma ɗakin ki,mu haɗa kanmu gaba ɗaya"ta ƙarashe tana murmushi, lubaisa ma tace"indai kika ƙi komawa Dr Imran to daga yau na daina yarda da love,indai naku ya mutu to I'm very sure namu Ni da ya abdallah yana mutuary"sukayi ƴar dariya,cikin sanyin murya Umaima tace"zan koma,ko don yarinya ta,i still remember Imran yayi min komai"shewa suka saka dukan su kamar ƙananan yara suna tafi

Baayi cikakken wata guda ba aka mayar da auren Umaima da Imran,har taura Imran yaje ya nemi auren ta,bayan sati uku kuma ya mayar da ita can ya sasanta tsakanin ta dasu,daga can suka wuce Bauchi

A Bauchi ya gamu da abin mamaki,don mahaifin shi kuka ya rinƙa yi yana neman yafiyar shi da mahaifiyar shi,ya sanar masa Zulfa'u ta haukace tun sanda aka samu ƙaramar ƴar ta da salma da ciki,ita kuma Ameera da cutar AIDS,shi kuma ya tattara yaran ya mayar da su wajen mahaifinsu ita kuma ya sake ta

Imran ya sha mamaki sosai,ya jinjina ikon Allah,ya gabatar da Umaima a matsayin ta na matar shi, Alhaji alƙasim ya sa musu albarka sosai

Imran ya bawa mahaifin shi labarin ƙanwar shi Ramla da mahaifiyar shi ta haifa,tayi aure itama a Abuja,har da yaran ta uku,dady yace"Allah sarki Aysha,don Allah ka nemar min yafiyar ta"

Kwanan su shida a Bauchi yau,sosai Umaima take girmama dady, kullum cikin yi masa hidima take,don sai taga kamar nata mahaifin

Deeja ce ta kira ta tace ta tambayi Imran zata je bikin ƙanwar Mima idan ya amince su tafi tare,tunda Deeja ta ambaci Mima gaban ta ya faɗi,don Allah shaida tana mugun tsoron Mima,gashi yanzu zata je gidan su,kuma bazata iya yiwa Deeja musu ba

Wajen ƙarfe biyar suka sauka gidan su Mima a azare,Mima bata wulaƙanta umaima ba,amma ko kaɗan bata sake mata ba,suna zaune a ɗakin miman suna hira, Mima na bawa Deeja labarin zuwan inna haleema takwarar ta gobe, wadda ta kasance ƙanwar mahaifin su ce

Mima tace"Allah ya kaimu goben,kice gobe da shafta,mama bilki fa?"

"Mama bilki maybe itama tazo goben, maybe kuma sai jibi"

"Allah ya kaimu"a cewar Deeja,suka cigaba da hirar su

Ita dai Umaima tana takure a gefen gado tana kallon yadda suke yin hira,sai su koma musu,sai su fara zagin juna sai su cigaba da shewa,a hankali ta goge hawayen ta tana jin kewar ƴan uwa,don ba wai sun saba da dangin ta bane har yanzu

Gashi tsoron maman su Mima ya kama ta ganin irin kallon da take bin ta dashi, shiyasa ma tunda ta rakuɓe a ɗaki bata fita ko'ina ba

Mima ta shiga ɗakin mahaifiyar su da sallama,mama sakina ta amsa, Mima ta samu waje ta zauna tace"gani mama"

Mama sakina tace"Mima wacece wannan wadda Deeja tazo tare da ita"

Mima ta taɓe baki tace"oho,kwashe kwashen auta ne,amma wai naji ance surukar ƙanwar Mamie babba ce"

"A ina take?"a cewar mama tana kallon ta

"Nace miki ban sani ba fa,ki tambayi Deeja"mama bata sake magana ba, Mima ta fice ya koma ɗakin ta

Bata samu Deeja a ɗakin ba sai Umaima da babyn ta take ta kuka,dama bata saka ran samun Deejan ba saboda zataje gidan Aunty Aziza,wadda itace immidiates ɗin Aunty Bintu,ko kallon Umaima da ke fama da little Deeja batayi ba,ta faɗa toilet don yin wanka

Umaima ta san matsalar little Deeja,bata bacci sai anyi mata wanka,gashi ita dai bazata iya tambayar ruwan wanka ba,dama dai Deeja tana nan ne,kuma mugun tsoron Mima takeji,haka ta miƙe tana ta jijjiga little Deeja da take sake mimmiƙewa tana tsala ihu

Sai da Mima ta gama shirya wa,ganin abin na little ba na ƙare bane ta kalli Umaima fuska babu yabo babu fallasa tace"ko bata da lafiya ne?"umaima ta girgiza kai,Mima tace"to lafiya take irin wannan kukan?"

"Ina ga ko wanka take buƙata"Umaima ta bata amsa

"Ko an saba mata wankan kafin tayi bacci?"Umaima ta gyaɗa kai

"Ikon Allah!shine bazakice a baki ruwa kiyi mata wanka ba?"bata jira cewar umaima ba ta fice daga ɗakin,bayan ƴan mintuna da dawo da baho da ruwan zafi,da kanta ta daidaita ruwan ,ta amshi little tayi mata wanka ta shirya ta,tun kafin ta gama little tayi bacci,ta kwantar da ita a hankali,tayi mata addu'a ta tofa mata,batare da ta kalli Umaima ba ta fice daga ɗakin, umaima sai bin ta takeyi da kallo,tana fita tayi murmushi ta koma kusa da ƴar ta ta kwanta itama

Sai wajen ƙarfe tara Deeja ta dawo,a parlour ta samu Mima tana yiwa Mee'ad kitso, ta sauke Affan da yake bacci ta kwantar da shi a kan kujera tana faɗin"wash Allah na"

"Gantali daɗi,sai yanzu?"a cewar Mima, Deeja ta harare ta tace "sai dai uwar gantali daɗi"Mima tace"seriously Baki da kirki Deejo,kin bar matar mutane kin tsallake kinyi tafiyar ki"

"Ayya!wallahi nayi mata tayin zuwa, tace a'a naje na dawo"Mima ta taɓe baki tace"ƴar ta sai kuka takeyi,wai ashe wanka take buƙata,tsabar sokwanci ta kasa tambayar ruwan wanka"Deeja ta kwashe da dariya tace"tsoron ki take ji ne, kullum kina haɗe mata rai kina mata tsawa,gashi don wulaƙanci kika je har gidan mijin ta a gaban mijin ta kika faffalla mata mari, leemo Allah ya shirya min ke"Mima tayi ɗan murmushi tana taɓe baki tace"ai kuwa ta haɗu da wahala"Deeja tayi dariya ta miƙe ta shige ɗakin da Umaima take

Washe gari ƴan biki suka fara halarta, kasancewar yau za'ayi event na Farko, Umaima dai ba don Deeja ba da tuni ta koma gida saboda har yanzu tana da tsoron shiga mutane,tana lafe a ɗakin Mima,daga ita sai wayar ta,don little ma Deeja ta amshe ta suna tsakar gida ana raha,bayan la'asar inna haleema da mama bilki suka iso kusan a tare,Mima sai raha da wasa da dariya sukeyi,bayan sun gaisa da mama sakina suka wuce ɗakin Mima inda Umaima ke zaune tana chatting da mijin ta

Sai da suka zauna sannan umaima ta gaishe su cikin girmamawa,bin ta sukayi da kallo suna amsawa,ɗauke kanta tayi ya cigaba da danna wayar ta,mama bilki ta kalli Mima tace"Mima ina kuka samo ƴar INNALE?"

Mima ta ɗago kanta cikin mamaki tace"wacce innale kike magana akai mama?kuma wacece ƴar tata?"daidai nan Deeja ta shigo da sallama

Inna halima tace"nima Ina ganin ta innale kawai na gani a tare da ita"

Mima ta kalli Umaima da tun ambaton innale na farko ɗago kanta a firgice tana kallon su inna haleema,mama bilki ta ciro wayar ta ta fito da hoton innale, wadda asalin sunan ta maimunatu ta miƙawa Mima

To pa 🥺me yake shirin faruwa ne?

#Nusy_bee

*****MATAR KHALEES*****

✍️Nusy bee

Page 39

Mima ta kalli hoton sannan ta kalli Umaima da ke kallon su idanu waje,tabbas basu da maraba, Deeja ma ta kalli hoton ta kalle ta,ta kalli su inna haleema tace"inna wacece innale?"

"Autar mu ce,asalin sunan ta maimunatu,ta rasu shekaru wajen ashirin baya, shiyasa baki santa ba,amma takwara ke zaki iya tuna ta ko?"Mima tace"sosai ma kuwa,kin manta na santa?mama tace Kafin auren ta tayi raino na sosai, lokacin da ta rasu ma da wayo na,na kai shekaru tara ma"

"Kin tuna lokacin da tazo zuwan ta na ƙarshe da ƴar yarinya ko?"a cewar mama bilki

Mima ta ɗan yi shiru,can tace"tabbas anyi haka,wai ma ni tunda ta rasu ban sake jin labarin yarinyar ba,gabanin rasuwar yadikko(kakar su)na taɓa tambayar ta ina ƴar innale amma bata bani wata gamshashshiyar amsa ba,Ni kuma tun daga sannan na watsar"

"Ai kuwa dai babu wanda ya sake bi ta kan yarinyar saboda wulaƙancin da mijin innalen yayi mana a lokacin da muka so amsar yarinyar"a cewar Inna haleema

Deeja da tun fara maganar su bin su take da kallo tace"inna a wane garin tayi aure ne?"

"Inna haleema tace"a jahar Jigawa ne,wani ƙauye taura"gaban Deeja ya buga,ta daure ta sake cewa"yaya sunan yarinyar ta ta?"

Inna haleema tayi ƴar dariya tace"nan fa ɗaya,wani sunan iyayi ta sa mata,duk sanda tazo ba wani iya faɗa mukeyi ba,Ni na manta sunan ma,sai dai ko yaya"Mima dai sai binsu da kallo take tana mamakin waɗannan tambayoyin na Deeja,don ta san halin ta kamar yadda ta san yunwar cikin ta,bata taɓa abu a banza

Mama Bilki tace "sunan dai gashi nan gashi nan dai,yana kama da hama,don Ni hama ma nake ce mata hankali na kwance"Deeja tace"ko dai UMAIMA?"mama Bilki tace"wallahi haka sunan yake? tabbas haka sunan yarinyar yake"

Deeja ta sunkuyar da kai tana jin wani iri,batayi aune ba ta ji hawaye ya ciko idanun ta,a sanyaye ta ɗago ta kalli Umaima wadda already hawaye ya fara zarya akan kuncin ta,kafin tace komai Umaima ta fara magana cikin kuka

"Amma baku kyauta min ba,wannan itace soyayyar da kuka nuna wa mahaifiya ta bayan babu ita a raye?kuka raye amma kuka bar ni rayuwa tana walagigi dani,na koma tamkar marainiyar da bata da asali?"saukowa tayi daga gefen gadon da take zaune,da rarrafe ta ƙarasa gaban su ta haɗe hannayen ta tana kuka mai sauti tana faɗin"meyasa?don Allah meyasa?a sanadin watsar da rayuwa ta abinci ya gagare ni, sutura ta gagare ni, ballantana ilmi na boko ko na addini,babu wanda zanyi shawara dashi,babu wanda zan kaiwa kuka na, azzalumai suka shiga rayuwa ta sukayi ya ƙwallo dani,don Allah laifin me nayi na cancanci wannan hukuncin daga gare ku? meyasa kuka rinjayar da ƙiyayyar mahaifi na akan soyayyar mahaifiya ta da kukeyi?"a haukace ta miƙe tana gunjin kuka tayi waje,ta bar su da bin ta da kallo, Mima tsabar shock bata san ma ta zauna ba,idan ta fahimta kenan ita da Umaima cousins ɗin juna ne

Deeja ce ta girgiza kai tana kallon su yadda suke bin umaima da idanu cike da mamaki,a takaice tayi musu bayanin rayuwar da umaima ta fuskanta har zuwa sanda ta ɗauko ta a garin su, Mima sai kallon Deeja takeyi ta kasa magana

Mama bilki da inna haleema kuwa fashewa sukayi da kuka,mama bilki ta miƙe batare da tayi magana ba ta zaro wayar ta ta soma neman babban yayan su wato abban Mima

Ita kam Umaima backyard ɗin gidan ta nufa ta zauna tana kuka mai motsa rai,babu abinda yafi mata ciwo kamar yadda taga suna rayuwar su cikin farin ciki da ƙaunar juna,amma ita sun banzatar da tata rayuwar da ta tunda har zina tayi da auren ta saboda rashin gata sai ta sake rushewa da kuka

Mima ta kalli Deeja cikin sanyin murya tace"abin mamakin deejo,wai ashe yarinyar nan cousin sister ɗi na ce?"ɗan murmushi Deeja tayi tace"ikon Allah kenan leemo"Mima ta juya tana kallon little Deeja da ke ta wasannin ta akan gado hankalin ta a kwance,sai ji tayi tausayin yarinyar ya kamata,ta matsa bakin gadon ta ɗauko ta tana kallon ta tana murmushi,ga ƙwalla a idanun ta,suna haɗa idanu yarinyar ta fara dariya, Mima ta rungume ta hawaye na zubo mata

A ranar mahaifin Mima ya dawo bayan maghriba,da sai gobe,amma dalilin issue ɗin Umaima ya bar abinda yake yazo,zuwa lokacin da ƙyar Mima da Deeja suka lallaɓa umaima ta taso daga backyard suka kai ta ɗakin amaryar da za'ayi bikin ta shukra suka kwantar da ita,don da kafewa tayi bazata koma gidan ba tafiya zatayi,tana shiga kuma ta nemi waje ta kwanta, sallah kawai ke tayar da ita, little kuwa tuni ta fita lamarin ta ko kallon ta batayi Allah ya sa yarinyar akwai haƙuri, Mima ta dama mata cerelac ta bata,da ta fara rigimar bacci kuma tayi mata wanka ta goya ta har tayi bacci,ta kwantar da ita

A lokacin ragowar yayyen Mima ma sun hallara,Aunty aziza, Aunty Na'ima,da Yaya mukhtar da shi ma baya ƙasar yana UK,sai Mima da amaryar da ke gidan ƙanwar yadikko Inna salame,sai ƙannen abban su Mima,banda inna haleema da mama bilki,akwai baffa Tahir,mama fati,sai autan su,wanda innale take bi,wato baffa mukhtar

Sai da suka kammala haɗuwa sannan Alhaji kabir wato abban su Mima yace a kira masa Umaima,Aunty aziza da Mama bilki ne suka shiga ɗakin shukra in da Deeja ke zaune a wajen ta,jikin ta ya rine da zazzaɓi,da ƙyar da suɗin goshi Deeja ta samu ta sha shayin da ta haɗa mata ta bata magani,da Imran ya kira Umaima a waya ita ta daga tayi masa bayanin abinda yake faruwa, kam yayi farin ciki sosai,yayi tayiwa Deeja godiyar ta silar ta duk wani cigaba yake ta samun su,ya ƙara da cewa shima zai shigo,ita dai Umaima tana jin su, kasancewar a speaker Deeja ta saka wayar,amma bata tanka ba

A wannan halin su Aunty aziza suka zo kiran umaima,tana ganin su ta sake fashewa da kuka, Cikin fusata Deeja tace"amma kinyi min alƙawarin bazaki sake kuka ba, wallahi sai in ƙyale ki in kama harkar gaba na"Umaima tayi saurin goge hawayen batare da tayi magana ba ta miƙe ta bi su zuwa parlourn

Da sallama suka shiga,ta gaishe su cikin girmamawa,suka amsa suna kallon ta,ita kuwa kanta a ƙasa ta kasa kallon kowa,har yanzu hawaye na ƙoƙarin zubo mata amma tana dannewa

Alhaji Kabir yayi gyaran murya ya bude taro da addu'a,bayan ya gama ya fara jawabi

"Kamar yadda muka sani shekaru ashirin baya mun rasa autar mu maimunatu,ko nace innale,mun so tilon ƴar ta ta dawo hannun mu amma mahaifin ta da dangin shi suka nuna sun fi mu iko da ƴar, dalilin haka muka bar musu ƴar su wanda shine mafi girman kuskuren mu

A yau ga yarinyar innale ta dawo gare mu amma kuma maimakon mu kasance cikin farin ciki sai akasin hakan dalilin irin rayuwar da ta samu kanta a ciki"a taƙaice ya basu labarin Umaima,da yawan su sai da sukayi kuka,wanda ya sanya Umaima fashewa da wani sabon kukan, Alhaji Kabir ya cigaba"don Allah muna roƙon ki Umaima,da kiyi haƙuri abinda ya faru ya faru,a irin soyayyar da mukayiwa autar

Please Login or Register in order to submit comment