Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ɗin ta tare da jawowa da sauri ya saka key a kofar Abdul ya ɗauka tare da ficewa daga gidan da sauri ya shiga mota rasa ina zaije yayi tsabar ya gigice, sosai hankalinsa yake tashe, Momy ya kamata yaje ya samu da Maganar sai dai bazai yiwu naje wajen Momy ba, tabbas ina cikin tashin hankali, Shetima ne ya faɗo masa a ransa, wayarsa yayi saurin ɗauka ya kira numbern Shetima, bayan ya ɗaga ne cike da tashin hankali Ya Garkuwa yace.

" Shetima kana ina?"

" Lafiya Garkuwa meke faruwa naji muryarka cikin tashin hankali."

" Bana cikin kwanciyar hankali, ina cikin tashin hankali Shetima kana ina ina buƙatar ganinka yanzu pls."

Numfashi Shetima ya saki tare da cewa.


" Ina gidan mu, kazo ka sameni."

Katse wayar Ya Garkuwa yayi tare da jan motar cikin tashin hankali mai gadi ya buɗe masa ya fice.

Ita kuwa Jummo sai buga ƙofar take cike da tashin hankali da ɓacin rai ga kanta dake mungun sara mata ji take idan ba ta bar gidan ba, bazata taɓa samun nutsuwa ba, tamkar mahaukaciya haka take dukar ƙofar, a birkice ta juya ta fara neman key a cikin ROOM ɗin ta buɗe kanta, komai na ROOM ɗin bincikarsa take tana watsarwa, idanunta ne suka sauƙa akan wani key dake cikin bedside drower da sauri ta kai hanu ta ɗauki key ɗin ta nufo ƙofar..........





*UMMU NASMAH CE*
[5/31, 12:40 PM] UMMU NASMAH❤️: *PAYMENT GROUP ONLY*







➰➰ *76 to 77*






Ƙarfe Uku dai-dai agogon Nigeria jirgin ya Garkuwa ya sauƙa a Birnin Egypt sanda fasinjan duk suka sauƙa ya yi settling ɗin jirgin kasancewar a ranar zai juyo, bayan ya samu hutu yaci abinci sannan ne ya kira numbern Safreena kusan ringin shida bata ɗaga wayar ba, dole tasa ya dakata da kiran, kafin zuwa can ya kuma kira, ai kuwa cikin Sa'a ta ɗaga wayar, numfashi ya sauƙe tare da sakin murmushi yace.

" Ina kika bar wayar ina ta kiranki shuru baki ɗaga ba, ina Egypt so nake mu haɗu da gaggawa domin jirgina zai tashi nan da awa Uku."

Shuru Safreena tayi zuciyarta sam bata ƙaunar haɗuwa da Garkuwa sai dai ta masa alƙawari kuma tasan girman alƙawari, cikin daƙilalliyar murya ta masa kwatancen inda take babu ɓata lokaci kuwa ya hau taxi a inda ta masa kwatancen ya tsaya tare da kiranta babu jumawa kuwa ta fito jikinta sanye da Kayan sanyi ta yane kanta da jan mayafi, sosai shigar ta mata kyau gefe dashi ta tsaya ba tare da ta kallesa ba tace.

" Ina jinka nima sauri nake ina da aiki."

Murmushi Ya Garkuwa yayi tare da cewa.


" Ko gaisuwar bazan samu ba, okay hakanma na gode, yanzu dai kafin mu shiga cikin maganar mu kai tsaye, ya labarin abinda ya kawoki ƙasar nan, kina samun Nasara kuwa akan Ibrahim ɗin."

Safreena cikin ƙunar rai tace.

" Har yanzu babu wata Nasara dana hango game da shirina akan kawu IBRAHIM, na ma kasa samun damar ganinsa, da alamu yayi ƙarfi sosai anan, hakanne ma yasa na yanke shawarar jibi zan dawo Nigeria na sake shiri kafin na komo."


Hanunsa ya Garkuwa ya zuba a aljihun sa tare da cewa.


" Dama ni na sani cutar da Ibrahim a wannan ƙasar zaiyi wahala, domin kuwa ganin sa ma zaki shekara baki gansa ba saboda done ne shi anan yayi ƙarfi yana kuma tare da manyan ƙasar nan, ni anawa shawaran naji labarin zaizo hutun ƙarshen shekara Nigeria, a Nigeria kuma na Tabbata zaki samu ganinsa cikin sauƙi mai zai hana bazaki hakura ba ki jira dawowarsa Nigeria, sai kiyi Amfani da wannan damar wajen cikar muradinki."

Kanta Safreena ta ɗaga cike da gamsuwa da Maganar Ya Garkuwa tace.


" Wannan shawarar tamin, ina ga nima hakan zaisa na samu sauƙin aikin, na gode da shawara, tell me meke tafe da kai."

Numfashi Ya Garkuwa ya saki tare da cewa.


" Harna fidda rai da samunki a rayuwata KULLUM ina miki addu'ar mamaci fatana dai Allah ya kai haske cikin kabarinki, dake KULLUM nake kwana nake tashi duk da ina ɗaukarki a matsayin matacciya, tunda na rabu dake ban kuma samun macen da zata maye mini gurbinki ba, sai Jummo, itace kaɗai nake kallo a matsayin ki, Safreena bazan ɓoye miki ba, ina son Jummo matuƙar so jigo ce ita a rayuwata, sai dai duk soyayyar da nake yiwa Jummo bata saka na manta dake a rayuwata ba, duk ke maƙiyi kika ɗaukeni ta fuskar zarginki, Safreena mahaifina ya amince na karɓi Abdul a matsayin ɗana, ya kuma umurceni dana aureki Saboda Rayuwar Abdul, kuma nima hakan take a zuciyata, ina sonki har gobe farin cikin rayuwata zai cika ya tumbatsa idan kika kasance dani, Safreena ina son muyi Aure."


Tunda ya soma Maganar Safreena take binsa da kallon mahaukaci, kafin ta dubesa ido cikin ido tace.



" Bazan aureka ba kuma bazan baka Abdul ba, ka sani rayuwata da ta ɗana zata inganta ko babu kowa a tare dani, ka sani babu Aure a gabana yanzu, kuma koda ina da niyyar Auren ma wallahi bazan aureka ba, zaifi maka sauƙi ka fita a rayuwata dani da ɗana, kaje ka riƙe matarka ta isheka rayuwa, sai kuma ka godewa Allah da bai jarrabeka da fitinanniyar mace ba, na zunuban daka aikata, matarka macece ta gari mai kima da mutunci mai Alkunya gami da kawaici samun irinta a yanzu yana matuƙar wahala koni nan ban Kaita ba, kawai kaje ka riƙe matarka ni ka rabu dani, ko sauraranka da nayi yanzu saboda alƙawarin dana ɗaukar maka ne, da ko inuwata bazan yarda mu haɗa ba, na barka lafiya."

Tayi Maganar tana barin wajen cikin sauri domin kuwa har cikin zuciyarta take jin bazata iya auren Garkuwa ba, shuru yayi cikin damuwa yana kallon ta, har sai da ta ɓace masa, idanunsa ya runtse yana jin insha Allah sai ya shawo kan Safreena ta amince dashi, juyawa ya bar wajen, ya koma airport ɗin, ƙarfe takwas na dare agogon Nigeria jirgin nasa ya tashi zuwa Nigeria.


Jummo ce zaune gaban Momy tana goge mata ƙafafunta tare da ɗan matsa mata, Momy sai bin Jummo take da kallo ba tare da tayi Magana ba, cikin zuciyarta ta fara jin son Jummo bata taɓa tsammanin wacce ta tsana a rayuwarta ba, zata jinyace ta, harta wanke mata kashi da fitsari, abinda ko ɗan uwanka ba kowa bane zai maka wannan aikin, Lallai duk yanda kaga Mutum karka rainasa a rayuwa domin kuwa baka san wacce irin rana zai maka ba a rayuwa zai yiwu shine wanda zai taimakeka a lokacin da kake neman mai taimako, lallai ta tafka kuskure na ƙin Jummo a rayuwarta, gashi ƴarta da ta haifa bata tsaya ta kula da rayuwarta ba harkokin gabanta kawai ta saka a gabanta amma ita Jummo gata da ciki ma amma haka take ɗawainiya da ita, numfashi ta sauƙe tare ɗago hanunta mai amfani da ƙyar ta ɗaura akan Jummo, Jummo ɗago kanta tayi ta kalli Momy, murmushi Momy ta mata, a hankali ta furta.

" Na gode Allah ya miki albarka"

Murmushi Jummo tayi cike da farin ciki tunda Momy ta kwanta jinya yaune kawai tayi Magana, Ya khalil ne ya shigo da Sallama, a gefen Momy ya zauna cikin sanyin jiki yace.

" Momy dan Allah kiyi hkr ki yafewa Garko ki cire damuwa a ranki Garko kuskure yayi ya kuma tuba, nasan bazai kuma ba Momy, Momy ubangiji ma fa muna masa laifi ya yafe mana, bare kuma mu ƴan adam, kiyi hkr Momy dan Allah lafiyarki muke nema yanzu."

Jummo ce ta ɗaura da cewa.


" Momy duk da nasan ba ƙaunata kike ba, amma zan nemi alfarma a gareki, ki yafe masa ke uwace fushinki garesa zai iya jawo masa wata masifar a rayuwa, Momy ya Garkuwa ya sanar dani dukkan abinda ya faru da rayuwarsa tun kafin ya Aure ni, harta wannan cikin da ya yiwa Safreena ya sanar dani cikin nadama kuma ya tuba tun tuni, wallahi Momy Ya Garkuwa mutumin kirki ne yanzu ƙaddara ce ta faɗa masa ki yafe masa dan Allah."

Momy hawayene ya zubo mata daga idanunta cikin ƙasa da murya irin na majinyaci tace.


" A irin tarin zunubai na, ai dole ubangiji ya jarrabeni, ni ba mutumiyar kirki bace, shiyasa rayuwa ta juya min baya, ku duba kuga yadda Allah ya mayar min da halitta ta lokaci ɗaya wai nice komai sai anmin, haka Rayuwa take muddun ba alkairi kake ƙullawa ba, to ka jira ranar tozartar ka, domin kuwa Allah bazai taɓa ƙyaleka ba, nayi sihiri iri iri a rayuwata, na raba tsakanin Uwa da ɗanta, Mamma tana cike da tsanata a zuciyarta, bana da kirki, to meyasa ma zanji haushin Garko saboda ya aikata wannan mungun aikin, me yiwuwa nubina ne ya biyo ta kansa, na yafe masa duniya da lahira, kema Jummo ki yafe min."

Cike da farin ciki Ya khalil da Jummo suke murmushi, wannan shine burin Jummo a rayuwarta, Momy ta gane gaskiya karta mutu cikin saɓon Ubangiji, cike da farin ciki Jummo ta sanar da Ya Garkuwa cewa Momy fa ta yafe masa sosai shima yayi farin ciki a ranar ya zo wajen Momy cikin farin ciki.




✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨


Rayuwa tana tafiya yayin da jikin Momy zaace alhamdulillah sai dai har yanzu ɓarin jikinta babu wani canji bakinta kam ya dawo dai-dai sai ɓarin jikinta har yanzu babu wani canji a yayin da cikin Jummo ke da wata bakwai ganin tayi nauyi yasa Ya khalil neman TRANSFER ya dawo Gombe shida Zarah, Jummo kuma ta koma gidanta Aunty Zarah ta cigaba da kula da Momy.



Suna zaune a falo suna hira Jummo ta dubi Ya Garkuwa tace.

" My love, gaskiya nifa idan na haihu Tulde zan koma wanka."

Zaro idanunsa yayi tare da tsuke fuska yace.


" Ban miki alƙawari ba, anan zakiyi wanka, karma ki saka a ranki."

Jummo zatayi Magana sukaji Bbc news na sanar da cewa jirgin daya taso daga Egypt zuwa Nigeria yayi hatsari ya faɗi, a yayin da jirgin ya ƙone ƙurmus, Ya Garkuwa a matuƙar razane ya miƙe tsaye wani irin gumi na keto masa hankalinsa yayi mungun tashi, Jummo miƙewa tayi tare da dafa kafaɗar sa tace.


" Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!!!! Safreena fa tana cikin jirgin nan innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!!!!!"








*UMMU NASMAH CE*
[6/2, 4:40 PM] UMMU NASMAH❤️: *PAYMENT GROUP ONLY*





➰➰ *78 to 79*





"Ta mutu kenan Ya Garkuwa.?"


"Jummo Safreena tana cikin jirgin nan domin kuwa Zee ta tabbatar min cewa Safreena ta taso yau, kenan tana cikin jirgin innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!!! Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!!! Allahumma ajirni fil musibati wa'akfilni kairan minha!!!! Bara nayi gaggawar zuwa airport ɗin mu, nasan suna can sashin bincike zan kuma nemi Zee naji ya ake ciki"

"Dan Allah idan kaje duk abinda ake ciki ka sanar dani dan hankalina bazai kwanta ba har sai naji halin da Safreena take ciki."

"Karki damu insha Allah zamuji alkairi."

Ya mata Maganar cikin sigar rarrashi domin kuwa ya tabbatar da cewa muddun Safreena tana cikin wannan jirgin sunanta gawa, saboda jirgi baya taɓa faɗuwa ƙasa wani ya rayu duk wanda suke ciki sai sun mutu, kanta Jummo ta ɗaga masa alamun to jikinta sai famar rawa yake.

Cike da tashin hankali shima yaje airport ɗin nasu sashen bincike ya nufa kusan dukkan ma'aikatan suna cikin wajen, a kusa da Shetima ya tsaya tare da cewa


"a wani ƙasa jirgin ya faɗi.?"

" Afghanistan anan jirgin ya faɗi kuma an tabbatar da cewa mutum 40 a ciki duka sun mutu harda Samuel drevern jirgin shima ya mutu."

Idanunsa ya Garkuwa ya runtse tare da zaro wayarsa ya kira numbern Zee ringin ɗaya kuwa ta ɗaga tana sakin kuka mai sauti, idanunsa ya kuma runtsewa kukan Zee ya tabbatar masa da cewa Safreena tana cikin jirgin kuma ta mutu, cikin raunin murya yace.

" Safreena tana ciki ko? Safreena ta mutu innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!!! Allahumma ajirni fil musibati!!! Kiyi haƙuri Zee mutuwa rigar kowace kowa dole sai ya saka wannan rigar babu wanda mutuwa zata bari, Ubangijin daya ɗauki Safreena ya fimu sonta, ita da ta tafi batayi sauri ba, mu kuma da muke raye ba muyi jinkiri ba, komai daren daɗewa sai munje mu tadda ta."

Ya ƙarisa Maganar hawaye na gudu a saman fuskarsa, Lallai yayi babban rashi, ya tsarawa rayuwa da farin ciki biyu Jummo da Safreena, hmmm sai dai ina Allah ya ƙaddara Safreena ba matarsa bane, katse kiran yayi yana durƙushewa a wajen ya saki kuka mai sauti Shetima ne ya sunkuya tare da dafa kafaɗarsa ya hau masa nasiha da bada baki, kafin ya samu yayi shuru, cikin sanyin jiki yabar airport ɗin bai doshi gidan sa ba, gidan su yayi a falo ya samu Momy zaune kan kenan da aka bata Daddy shima na zaune cikin kujera, kusa da Daddy ya zauna tare da sakin kuka yana cewa.


" Daddy Safreena ta mutu, hatsarin jirgin nan ya ritsa da ita Ta mutu Daddy Abdul ya rasa mahaifiya."

Ga baki daya falon salati ya ɗauka Daddy ne yace.


" Subahanallah!! Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!!! Allahu Akbar, oh rai baƙon duniya, Allah ya jiƙanta da rahama dama haka rayuwa ta gada, mutu tana sarƙe da kowa wanda kwanansa ya ƙare sai tafiya, Allah yasa idan tamu tazo mu cika da kyau da imani ita kuma Allah yasa ta huta, dama kuma jiya Zarah da Khalil sunzo sun roƙeni alfarmar cewa ka basu kyautar Abdul su riƙesa matsayin ɗansu na cikin su tunda su Allah bai azurtasu da haihuwa ba, Kuma na yanke shawarar cewa na basa, gobe in Allah ya kaimu zamuje mu yiwa Alh giɗaɗon ta'aziyya idan yaso in an kwana biyu sai naje da kaina na sameshi da zancen Abdul ɗin."


Kansa ya Garkuwa ya kaɗa tare da runtse idanunsa yana jin zafin mutuwar Safreena a zuciyarsa, ita kanta Momy ko da bata san Safreena ba, sai da taji mutuwar, ya juma sosai a gidan kafin ya shige gidan su Safreena suna zaune suma zugun zugun masu kuka nayi sosai ya tausayawa Zee yanda duk ta fita a hayyacinta tana maƙale da Abdul, Alh giɗaɗo ya gaisar tare da masa ta'aziyya ya juma a gidan har akayi sallar magaruba sannan ya koma gidan sa, ko da ya sanar da Jummo sosai hankalinta ya tashi, daƙyar cikin sigar rarrashi ya samu hankalin Jummo ya kwanta.


Washegari kuwa, aka iso da gawarwakin su Safreena Nigeria Birnin tarayya wato Abuja Alh giɗaɗo shida abokinsa Alh Kabeer, sai Ya Garkuwa sukaje babu wanda ya iya gane gawar ɗan uwansa domin kuwa duk sun babbake, haka dole aka haɗasu aka musu a can, aka binnesu, sunsha kuka sosai tare da baƙin cikin rashin gane gawar Safreena wannan yafi ci musu rai


Ranar da suka cika kwana uku da rasuwa Ya khalil da Daddy sukaje suka musu ta'aziyya, a nan ne Daddy yake sanar da Alh giɗaɗo zancen ɗaukar Abdul, haka babu musu ya amince musu, sanin cewa a duniya Abdul bashi da gatan daya wuce su dangin mahaifinsa, Zee Sosai taci kukan rashin Safreena da karɓe Abdul da akayi sai dai babu yanda ta iya dole ya zamo tayi hakuri Jummo ma taje ta yiwa Zee ta'aziyya tare da jajanta mata mutuwar Safreena, Jummo bata so aka raba Abdul da Zee ba.

Ko da Daddy suka dawo da Abdul gidan, Zarah sosai taji daɗi tare da amsarta zuciyarta tana sanar da ita itama yanzu ta samu yaro, Momy sanda taga Abdul sosai ya shiga ranta, babu ƙyama ta rungumesa, haka rayuwa ta tafi cikin jin daɗi a cikin wata ɗaya Abdul yayi mungun shaƙuwaa da Aunty Zarah da Ya khalil da kuma Momy, Zizah ne dai baya yadda da ita kasancewar bata cika masa wasa ko ɗaukarsa ba.


Misalin ƙarfe Uku na dare wani irin mungun ciwon ciki ya turniƙe Jummo Ga baya da mararta tamkar zai tsage, wani irin azaba takeji wanda tunda uwarta ta haifeta bata taɓa jin wannan azabar ba, ji take tamkar rayuwarta ne yazo ƙarshe, bakinta ta cije goshin ta ya tsattsafo da gumin azaba, Ya Garkuwa dake baccinsa hankali kwance ta riƙesa tana ambaton.

" La'iha'illahu Muhammadur Rasulullah!!!! Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!!!"

Sai kuma ta saki kuka jin kamar motsin mutum jikinsa ya saahi buɗe idanunsa a hankali, idanunsa ya zuba a kanta sai kuma ya miƙe a firgice yana rikota tare da cewa.

" Subahanallah!!! Jummo kaddai haihuwar ce?"

Ina itakam Jummo bata da bakin Magana saboda munguwar azabar da take ji, ga haihuwar tazo mata da ciwon baya, wanda yafi wahalar wa, ai kuwa babu shiri ya Garkuwa ya miƙe jallabiyarsa ya saka da sauri ya ɗauki key ɗin motar sa ya fito mai gadi ya samu tare da ce masa ya buɗe masa get, sannan ya koma ciki, Jummo ya kamo suka fito suka shiga mota, cikin gaggawa yake tuƙin Asibitin Doctor Sirajo suka je, cikin gaggawa aka shiga da Jummo ɗakin haihuwa tare da cewa Ya Garkuwa ya koma ya kawo musu kayan haihuwa da fallen zani, komawa cikin tashin hankali ya ɗauko ya kawo, tunda Jummo ta shiga cikin room ɗin hankalin Ya Garkuwa bai kwanta ba, har kiran sallar asuba ta farko Jummo bata haihu ba, sanda aka fito Sallah sannan ya kira Aunty Zarah yake sanar da ita yana asibiti Jummo zata haihu, Aunty Zarah tana idar da Sallah itama tazo ta, shuru shuru Jummo bata haihu ba sai da gari ya waye 7:30am Allah ya sauƙeta lafiya ta samu santalelen ɗanta fari tas kyakkyawa, koda aka sanar dasu ya Garkuwa haihuwar sosai sukayi farin ciki, Ya Garkuwa ne yace.


" Doctor ina mahaifiyar Yaron, tana lafiya dai ko DOCTOR."?

Murmushi doctor ya saki tare da cewa.


" Tana lafiya bata da wata matsala, taɗan samu ƙari kaɗan mun mata ɗinki, so tana ɗakin hutu ma da jaririn zaku iya shiga ku gansu."

Ai kuwa cikin farin ciki suka shiga room ɗin tana kwance tana bacci Babyn kuma an lulluɓesa da towel, Ya Garkuwa cike da farin ciki ya ɗago yaron numfashi ya sauƙe tare da mannasa a ƙirjinsa, kunnen sa ya kama ya masa kiran Sallah, tare da saka hanunsa a cikin aljihun sa, dabino ya tauna tare da sawa yaron a bakinsa, ya ɗiga masa zam zam, Aunty Zarah sai tsiya take masa, ganin suna cikin ƙoshin lafiya ya sashi komawa gida yayi wanka ya samu nutsuwa sannan yayi gidan Momy yake sanar da ita Jummo ta haihu murna Momy tayi tare da musu addu'a domin bata da ƙafar zuwa asibitin, cewa tayi yaje kitchen akwai ruwan zafi a plast da kayan shayi ya kai musu asibiti tare da ce masa idan an basu sallama su taho da Jummo nan Gidanta, cikin farin ciki ya amsa da to zuwa yayi ya ɗauka ya koma asibitin, ya samu jummo harta farka tana bawa jaririn nono, gefenta Ya zauna cikin murmushi yace.


" Oh yarinya ta girma."

Murmushi Jummo tayi tare da ɗago idanunta ta kalli Ya Garkuwa, cirewa Yaron nono tayi ta miƙa masa ya saka hanu ya karɓe sa, tace.


" Ka kira su INNO ne ka faɗa musu haihuwar."?


" Ban kirasu ba, na dai gwada numbern Baffa bata tafiya amma zuwa anjuma maybe ya tafi ko matsalar network ne."

Aunty Zarah ce tace.

" Ai kuwa ya kamata su sani likitan ma yace tunda bata da wata matsala za'a iya Sallamar mu zuwa anjuma."


" Okay Momy tace gida zaku koma idan an sallame ta."

Da to Aunty Zarah ta amsa, da yamma lis kuma aka sallamesu suka koma gidan Momy, Abdul sai murna yake yaga jariri, Daddy ma ya shigo ya duba jikan nasa, ko da Ya Garkuwa ya sanar da Baffa haihuwar Jummo, Sikayel da kanta tazo ta zauna mata.


Kwanan Jummo Uku da haihuwa yayin da jaririnta yayi kyau kamar yayi sati biyu, a ranar ne kuma aka kawo kuɗin Auren Zizah, wani ɗan Kano ne zai aureta wanda suka haɗu a facebook.


Meenat tun ranta suka sami saɓani da Momy bata kuma zuwa gidan ba, sai yau ta kira Jummo a waya kamar bazata ɗaga ba, sai kuma ta ɗaga muryar Jummo a daƙile ta amsa sallamar meenat, meenat daga can cikin sanyin murya tace.

" Ƙawata har yanzu fushi kike dani ne? Allah sarki Jummo kema kin sani abinda Momy tamin ba dai-dai bane, amma duk da haka ni ina mai baki hkr Allah ya huci zuciyarki, dan Allah kiyi hkr."

Cikin mutuwar jiki domin duk wanda ya maka laifi yace maka kayi hkr to Tabbas ya gama kashe maka jiki, numfashi ta sauƙe tare da cewa.

" Ba komai ya wuce amma dan Allah gaba karki kuma min irin haka, ana barin halak kodan kunya har yau Ya Garkuwa bai san abinda kika yiwa Momy ba, Kuma bana son ya sani Saboda yana ganin mutuncin ki."

" Hakane Jummo na gode sosai, kin sauƙa lafiya."?

" Lafiya Alhamdulillah!!! Amma dan Allah Meenat karki zoki gidan nan kin san ina gidan Momy kuma bazataji daɗi ba idan ta ganki gashi bata da lafiya ki bari sai na koma gidana sai kizo."

Da babu komai meenat ta amsa sun juma sosai suna hira kafin suka katse cikin farin ciki.



✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨




Ranar suna Ya raɗawa yaron sunan Baffa Wato Ahmad, sosai sunan yayi goshi, su INNO da Mamma duk sunzo yaro kuwa sosai ya samu kaya, babansa ma akwati Uku ya cika tam, dana yaron dana Uwar Momy ma tayi nata akwati biyu, shi kuwa Ya khalil, akwatin sa ɗaya yayi Aunty Zarah ma tayi nata turmin atamfa Uku da kayan Baby huɗu harda pampas, anyi taro lafiya an watse lafiya, da Ahmad ɗinsa suke kiransa Ya Garkuwa yace bai amince su sanja masa suna ba, a kirasa da sunan sa.



Haka rayuwa ta dinga gudu cikin farin ciki a yanzu Jummo bata da matsala da Momy tana sonta sosai sai dai har yanzu Momy gefen jikinta babu wani canji yana nan a yanda yake, ranar Jummo ta cika kwana arba'in washegari ranar Sikayel ta koma dama su INNO tun ranar da akayi suna washegari suka koma.

Itama Jummo washegari ta koma nata gidan ta, a wannan lokacin kuma aka saka ranar bikin Zizah.





*UMMU NASMAH CE*
[6/3, 12:02 PM] UMMU NASMAH❤️: *PAYMENT GROUP ONLY*



➰➰ *80 to 81*





Jingine yake jikin motar ya harɗe hanunsa, yana ƙarewa gidan kallo yanda mutane ke cike ƙofar gidan suna neman hanyar da zasu gansa , numfashi ya sauƙe tare da leƙa kansa cikin motar alamu yayi musu da idanu akan suzo suje, babu musu suka nufi ƙofar gidan, ɗan sandan dake gadi a ƙofar gidan Ya zaro kuɗi kimanin dubu hamsin ya miƙamasa yana neman abarsu su shiga gidan, aikuwa ganin wannan kuɗin yasa ɗan sandan barinsu a kunnensa ya raɗa masa cewa.

" Officer Mai gidan ya samu isowa ne."

Kansa ya ɗaga masa alamun a'a

" yana hanya dai tukunna jirgin su ya taso waɗannan mutane da kake gani ƴan jiransa suyi roƙo, amma ku kuwa me zakuyi a cikin gidan nan."?

Murmushi ya kuma sakewa tare da cewa.

" Akwai abinda muke nema, idan har zaka mana jagora zuwa lungu da saƙo dake cikin gidan nan to na maka alƙawarin Naira dubu ɗari bakwai da hamsin, cash."

Zaro idanunsa ɗan sandan yayi tare da furta.


" 7050 thausand serious.?"

" Yes serious"


" Baku da matsala muje kawai"

Yayi Maganar yana shigewa gaba suka rufa masa baya, tun daga babban falon daya ƙawatu da kayan more rayuwa suka fara bincike har zuwa room ɗinsa basu samu komai ba daga cikin abinda suke nema, duk iya bincike da zasuyi a gidan sunyi amma ina babu komai dole tasa suka haƙura suka fito sunzo dai-dai fita daga falon kamar wanda aka ce mata kalli nan, ta hango kamar ƙofar ROOM ta bayan drower, ai kuwa da sauri tayi wajen tana cewa.

" Kunga wata ƙofa, a bayan school drower."

Ai kuwa juyowa sukayi tare da rufo mata baya ƙofarce kuwa, drower suka ture gefe cike da mamaki, wani irin ƙura ne a ɗakin har bakan Gizo yayi saka sosai, wayarsa ya zaro tare da kunna haskenta suka hau bincike, dubanta ta kai ga hoton dake manne jikin bangon, hanu tasa ta karkaɗe sai

Please Login or Register in order to submit comment