Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ɗansu meyasa ya aikata wannan kuskuren dole yana buƙatar neman gafarar Mamma, sai yanzu ya fahimci cewa bai samawa ƴaƴansa Uwa ta gari ba, domin kuwa shi kansa wani lokacin yana lura da yadda ake rayuwar da bata da ce ba a gidan sa, a wannan karon zai nunawa Momy matsayinta zai kuma hukunta ta, akan wannan shirmen, zai tsaya da ƙafafuwan sa wajen tabbatar da wannan Auren, domin farin cikin Mamma, nisawa yayi tare da cewa.

" Tabbas nayi kuskure nayi kuskure gareki Mamma a yau idanuna sun buɗe na fahimci hakan, dan Allah kiyi haƙuri Mamma ki yafe min insha Allah zan gyara tsakanina dake kuma zan tsaya da ƙafafuna domin tabbatar da Auren Garko, kuyi haƙuri."

Daddy yayi Maganar cikin sanyin jiki, shi dai Ya khalil ya gagara magana domin kuwa kalaman Momy sunyi mungun tsorata sa, bai taɓa tunanin cewa akwai Uwar da zatayi munanan kalamai akan ɗanta harta nema masa tashin hankali, Lallai ne Rayuwar Momy akwai gyara ita ko wacce suruka bata so, wannan wani irin ɗabia ce, duk da yaji zafin maganganun INNO da tayiwa Momy sai dai yasan koma me aka faɗa mata itace ta jawo, miƙewa tsaye yayi cikin sanyin jiki ba tare da yace komai ba ya juya zai bar wajen muryar Daddy yaji yana ce masa.

" Tunda aka fara wannan maganar baka ce komai, ka shirya gobe da safe zamuyi sammakon zuwa TULDEN FULANI."

Juyowa Ya khalil yayi tare da cewa.

" Allah ya kaimu Daddy"

Yayi Maganar a taƙaice tare da ficewa ya nufi garden, Shima ya Garkuwa tashi yayi yabi bayan sa, Daddy shima kasuwa ya tafi, Aunty Zarah cike da farin ciki ita da Zizah suka miƙe suka nufi bedroom ɗin Momy ita Aunty Zarah farin cikin ta shine, Momy ta shiga ƙunci domin kuwa Allah ya saka mata abinda ta mata, Momy tunda ta shiga room ɗinta ta kasa zama sai kaiwa da komowa take, ta goya hanunta a baya, sosai take cikin tashin hankali, Zizah ne da ta shigo ta doki mirror da ƙarfi cikin fusata tace.

" Why Momy!!! Why!!! Daddy zai ƙasƙantar dake a gaban waɗannan koɗaɗɗun tsofin, ba laifin kowa bane laifin Garko ne Domin kuwa shine baiji maganarki ba, waima meya gani jikin wannan jakar yarinyar, anya kuwa Momy ba asiri suka masa ba, na kasa gane meyake damun Rayuwar Ya Garko, shi a rayuwarsa abinda yaga dama shine yake yi, Ki barta ta shigo gidan Momy, Wallahi sai mun mayar mata dashi kurkuku."

Aunty Zarah ce ta taɓe bakinta tare da cewa.

" Tayani gani dai Zizah nima banga meya gani a jikinta ba, amma da shike kinsan a ruga suka fito, asiri zasu masa."

Girgiza kanta Momy tayi tare da cewa.

" Bazasu masa asiri ba, domin kuwa babu boka a gidan su gidan malamai ne, kissa ce kawai da iya munafurci yasa ta mallake min ɗa, ku barni da ita sai tayi danasanin shiga rayuwata, ku fita ku bani waje."

Ta ƙarisa Maganar tana zama tare da dafe kanta fita sukayi.


Ya khalil zama yayi tare da yin shuru ya rasa me yake masa daɗi maganganun Momy kawai suke masa yawo a kansa.

" Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!!!"

Ya furta tare da sakin numfashi kafaɗarsa Ya Garkuwa ya dafa tare da cewa.

" Ni kaina hankalina a tashe yake Momy tamin baki ta faɗa min mugayen maganganu, Momy tamin baki ina tsoro kar bakinta ya kamani, ya zanyi Bro meye mafita."

Ɗago idanunsa ya khalil ya yi ya dubesa tare da cewa.

" Babu yanda zakayi domin kuwa Daddy ya yanke hukunci, kuma ka sani Magana ɗaya yake yi, Baka da haƙƙin Momy insha Allah bakin ta bazai kamaka ba, kai dai ka cigaba da mata biyayya tamkar yadda kake karka fasa insha Allah komai zai shige Momy zata sauƙo zata gane gaskiya."

Shuru Ya Garkuwa yayi cikin tashin hankali, zama yayi shima yayi shuru dukkan su babu wanda ya kuma cewa ɗan uwansa wani abu.

Ita kuwa Jummo tafi kowa shiga cikin tashin hankali, bata taɓa tsammanin ƙiyayyar da Momy take mata yakai haka ba wannan wacce irin masifa ce, sai dai tasa a ranta zata dake da addu'a da sadaka insha Allah Allah zai karesu.


Yau Daddy da Abokinsa Alhaji Ahmed Sai Ya khalil suka nufi TULDEN FULANI, da niyar Tambayowa Garkuwa Auren Jummo.

MOMY sosai ranta yayi mungun ɓaci ganin da gaske fa wannan Auren zai tabbata, sai dai ta ɗauki alƙawarin bazata taɓa bari wannan Auren ya kasance ba.






*UMMU NASMAH CE*
[5/8, 10:29 PM] UMMU NASMAH❤️: *PAYMENT GROUP ONLY*



➰➰ *58 to 59*


"Wai ke Safreena me zakiyi da wannan aikin ne, just 30k ne fa kawai suke bawa ƙaramin ma'aikaci a wata, kuma ke kina da master's me zai hana bazaki je AA ƊAN DARMA ki nemi aiki ba, wannan ma'aikatar suna bada Salary mai tsoka, a babu suna bawa ƙaramin ma'aikaci 65k amma sai ki tsaya ki nemi aiki a wannan ƙaramin Companyn me 30k zata miki a wata."?

Ɗan murmushi Safreena tayi tare da cewa.

" AA ƊAN DARMA ba Companyn daya kamata nayi aiki a cikin sa bane Zee kema kin sani ko karima kanta da ta samu aiki a wajen ki duba kiga yanda take complain akansu basu da uzuri sannan basu ganin darajar ma'aikacin su, to me zakaje kayi a inda baza'a ga darajar ka ba, Su kuwa I D D BARAU NIG LTD company ne da suka san darajar ma'aikaci sukan bawa kowa mutuncin sa, ba kuma sa taɓa wulaƙanta ma'aikaci koda kuwa mai shara ne, ina son inda za'a mutuntani Zee, gara a bani kuɗi kaɗan aga mutuncina, ba wai a bani kuɗi mai yawa ba ana ɗaukata ƙasƙantacciya, Zee wannan 30k ɗin da zasu bani ta isheni nayi buƙatuna da kuma na Abdul saboda na rufa masa asiri yasa na nemi wannan aikin kuma kuɗin zasu isheni buƙatuna dana ɗana, bani burin ƙarya a cikin rayuwata ki gane haka mutunci yafi kuɗi."

Numfashi Zee ta saki tare da cewa.

" Hakane na fahimta, ɗazu kin fara bani labari, Baba ya shigo kikayi shuru, kikace kun haɗu da Garkuwa a wannan Companyn, ya ganki kuma."

Kanta Safreena ta kaɗa tare da sakin murmushi tace.

" A'a ban bari ya ganni ba, saboda bana son mu sake haɗa idanu dashi, a zuciyarsa na mutu, hakan nake so ya tabbata na mutu a cikin rayuwarsa, bazan taɓa yadda Garkuwa yasan ina raye ba, nasani har gobe ina zuciyarsa, fahimtar ina raye zai tono abubuwa masu yawa ciki harda barazana ga ɗana Abdul, dan haka na kashe Garkuwa a zuciyata bazan taɓa yadda mu haɗu ba."

" Safreena karkiyi haka dama ce yanzu a gareki na Garkuwa yasan kina raye, domin kuwa hakan shine zai fitar dake daga zargin ɗanki ma'ana dai ina nufin Garkuwa ya kamata ki aura domin rufin asirin ɗanki, ya kamata kiyi tunani akan maganata."

Murmushi safreena tayi tare da miƙewa tsaye tace.

" Bana buƙatar tunani akan wannan maganar taki babu ni babu Garkuwa har abada bazamu taɓa haɗuwa dashi ba ki ajiye wannan a ranki Aure tsakanina dashi abinda bazai taɓa yiwa bane."

" Amma Safreena ya kamata ki duba maganata kiyi tunani akan rayuwar ɗanki da kuma hanyar da kuka sameshi hakan zaisa ki fahimci gaskiya nake nuna miki."

" Zee bani da tunani akan Abdul muddun Baba yana raye na tabbata zai zamo gatansa bazai bari yayi kuka ba a rayuwarsa."

Dafe kanta Zee tayi ganin duk yadda taso Safreena ta fahimce ta abun yaci tura, har ga Allah ita tsakaninta da Allah take faɗawa Safreena gaskiya, duk gatan da Baba zai bawa Abdul koda kuwa kullum goyasa zai dinga yi, Wallahi wata rana sai tambayi waye ubansa da Safreena zata gane Garkuwa ya kamata ta aura tun Abdul yana yaro bai san komai ba ya taso a hanunsa hakan zai kauda hankalinsa ga tunanin shiba ɗan sunnah bane amma ta kasa fahimta, hmmm.

Zee taja numfashi tare da miƙewa tsaye tana cewa.

" Kinsan dai bazaki tabbata a rayuwarki babu Aure ba Safreena muddun kuwa Baba yana numfashi, idan mijin yazo me zaki ce masa kina da ɗan da kika haifa ba tare da aure ba, ko zaki ɓoye masa, ki sani koda kin ɓoye masa Baba bazai ɓoye ba domin kuwa anayin Aure ne bisa turbar gaskiya mai ɗaurewa dole ne a sanar dashi abinda ke faruwa domin samun ingantaccen aure mai ɗaurewa, a yayin da shima Abdul zai bincike ki waye mahaifinsa, domin kuwa akwai wannan ranar zata zota muddun baki ɗauki shawarata ba, kiyi tunanin wacce irin amsa zaki bayar a lokacin da aka miki wannan tambayar."?

Tana gama faɗin haka Zee ta fice daga ROOM tabar Safreena tsaye bakinta buɗe cikin nazari duban Abdul dake wasa tayi kyakkyawan yaro son kowa ƙin wanda ya rasa sai dai ƙaddara ta yiwa rayuwarsa mungun tabo shuru tayi tana nazarin maganganun Zee numfashi ta sauƙe ita kaɗai tasan hukuncin da ta yankewa kanta miƙewa tayi itama ta fita tare da ɗaukar Abdul sukayi ROOM ɗin Mama.



Ƙarfe biyu dai-dai na rana suka shiga cikin Tulde robon Daddy da garin tabbas ya juma da kallo yake bin garin abubuwa da yawa sun sauya kasancewar ya juma sosai rabonsa da wajen Ya khalil shine ya musu jagora har gidan su Jummo, a ƙofar gida suka samu Baffa yana cikin almajiransa, har abada Baffa bazai taɓa manta fuskar Garba ba, murmushi Baffa yayi tare da musu sannu tabirmar karamno aka kawo musu suka zauna Baffa da kansa ya shiga ya kawo musu ruwa bayan sunsha ne sukayi musabaha cike da mutunta juna, Baffa ne yayi murmushi tare da cewa.

" Garba kaine tafe garin namu, lallai anyi shekaru rabon da mu ganka, har mun fidda tsammanin zakazo, sannu ya Mamman take da INNO, da kuma iyalan naka, wannan kamar kalilu, ya jikin Mamman da ita Jummo."?

Ɗan murmushi Daddy yayi tare da cewa.

" Gaskiya na juma to ya muka iya abubuwa ne suka riƙemu bamu da isasshen lokaci, kuma kasan komai sai Allah ya nufa, Mamma jiki yayi sauƙi har Jummo, Ina Jauro yana nan kuwa da Garbati abokin faɗa, Baffa amma Jummo ƴar Garbati ne ko."?

Murmushi Baffa yayi tare da furta.

" Hakane komai sai Allah ya nufa amma idan aka saka niyya sai kuma Allah ya dafa, A'a ba ƴar Garbati bane ƴar Jauro ne, Garbati yana nan hayen tsallake shida matar sa da yaransa shi nasa yaran ai duka maza ne su Shida."

" Allah Sarki, Masha Allah, to Baffa so muke zamu koma gida da wuri, Kuma munzo wajenka ne da magana mai mahimmanci."

" Ayya to ina sauraronku."

Nisawa ALHAJI Ahmad yayi tare da sanar da Baffa abinda ke tafe dasu Daddy ya ɗaura da cewa.

" Allah yasa zaka bamu Auren Jummo, domin kuwa abun alfahari ne da farin ciki haɗa zuri'a daku idan akayi duba da tarbiyya da ilimin addini da kuke dashi."

Nisawa Baffa yayi yana hango tarbiyyar gidan su Momy da shi kansa Daddyn da yake shakku akan tasa tarbiyyar domin kuwa yayi watsi da mahaifiyarsa ya bi mace bai kuma wauwaice ta ba sai Itace ta nemesa Wannan ma babbar illace da zata hana a basu Aure a duba ta mahangar hankali, domin ana Auren mutum ma saboda nasabarsa, nasabar gidan su Momy ta tsubbu ce da suka maidashi SANA'AR da zasu ci su sha da ita, suka ɗauke ta ɗabiar jini da suke gada daga wajen iyayensu duk wanda yake zaune cikin ƙauyen Tulde yasan wannan asirin nasu, wanda suke gina kansu da haram, ga kuma fitsara da rashin kunya da suka ɗauke ta ɗabia, da hukuncin sa zai yanke tabbas bazai basu Aure ba, sai dai Idan ya hango Mamma baiwar Allah sai yaji bai cancanta ya bata kunya ba ta guje jininta saboda kuskuren ɗanta, numfashi ya sauƙe tare da cewa.

" Duk da ina da iko akan Jummo amma mahaifinta shine yake da haƙƙin ya bada Auren ƴarsa, da zaku min hkr ku ɗan dakata kaɗan sai na aika ayi kiransa a jeji muji ta bakinsa, amma bazan ɓoye maka ba Garba kaida matarka baku da hali na ƙwarai da za'a ɗauki yarinya a baku, saboda baku kyautawa rayuwarku ba, ka yi watsi da mahaifiyarka wanda a duniya baka da wanda zaka kyautatawa bayan ita ka samu albarka, domin kuwa uwa itace jigon rayuwar ɗa zata iya sadaukar da komai nata na rayuwa domin inganta rayuwar ɗanta ciki kuwa harda bada rayuwarta, a yayin da ko wani ɗa na ƙwarai yake kusantowa kusa da mahaifiyarsa domin samun albarka, kai kuma lokacin kake nisanta kanka da ita taya albarka da zaman lafiya zasu zamo mafakarka bayan ka juyawa wacce zaka samu albarka a wajenta ba, a yanzu kana da damar da zaka gyara kuskuren ka domin kuwa Mamma tana kusa da kai, kana da sauran lokaci har yanzu, ita kuma matarka kowa yasan asalin gidan su a wannan ƙauyen namu ba Mutane na kirki duk da ban sani ba ko ita zainabun Allah ya shiryeta ta gyara halinta."

Gabaki ɗayan su shuru sukayi cike da sanyin jiki suna sauraron Baffa yayin da jikin Daddy YAFI na kowa sanyi, idanunsa ne suka cika da hawaye tabbas ya sani gaskiya Baffa yake faɗa, hanu yasa ya share guntun hawayen yana ɗago kansa ya kalli Baffa tare da cewa.

" Koda baka bamu Auren Jummo ba, bazanji haushin ka ba Baffa, domin kuwa duk wanda ya sanni yasan abinda ka sani a kaina dole zai gujeni da haɗa zuri'a, na sani ban kyautatawa Mamma ba, tabbas nayi kuskure, amma a yanzu na gane kuskurena tun kafin na taho nan harma na nemi yafiyar Mamma kuma ta yafe min, na sani Allah ya na sona da shirya shiyasa yabar min Mamma har yanzu a raye domin na gyara laifuka na gareta, kuma a shirye nake ga hakan, zamu jiraka aje a kiran jauron."

Murmushi mai sauti Baffa yayi tare da furta.

" Masha Allah!!! Haka ake so Idan Mutum yayi laifi ya fahimci yayi kuma ya gyara, Allah ya muku albarka." Baffa yayi Maganar yana yana ƙwalawa Junguɗo kira almajirinsa, tare da basa umarnin yaje ya kirawo masa Jauro su taho dashi tare yanzu, da to Junguɗo Ya amsa tare da tafiya aiken Baffa, Ya khalil sosai hankalinsa ya tashi jin yanda babu mai faɗin alkairin iyayensa a cikin rugar musamman momy, numfashi ya sauƙe yana maida kansa ƙasa, basu wani juma ba kuwa Jauro suka taho tare da Junguɗo, cikin mutunci suka gaisa dasu Daddy, Baffa da kansa ya gabatarwa Jauro abinda Garba ke tafe dashi bayan doguwar tattaunawa a ƙarshe dai Jauro ya bawa Daddy Auren Jummo, harma suka saka rana cewa Auren bazai wuce nan da sati Uku ba, Alh Ahmad da kansa ya bawa Baffa sadakin Jummo Naira dubu hamsin 50k tare da sanar dasu cewa insha Allah a cikin satin da za'a shiga zasu aiko da kayan lefe, cikin mutunci da girmamawa suka rabu yayin da kafin Daddy yabar ƙauyen sai da ya bi ya zaga ƴan uwa, kowa sosai yayi mamakin ganin Daddy sai dai ya masu alkairi marar misaltawa har fadar lamiɗo sai da yaje, sannan suka bar ƙauyen, a cikin lokaci kaɗan labarin Auren Jummo da ɗan gidan Garban Mamma ya zagaye ƙauyen kowa yana mata son barka wasu kuwa suna cece kucen mai zaisa Baffa ya yarda ya haɗa iri da gidan su Zainabu, to dama dai shi Aure ya gaji haka duk sanda ya taso sai kaji ƙorafin kowa da mai faɗan alkairi da kuma mai faɗin sharri koma dai me sai dai muce Allah ya sanya alkairi.

A can kuwa Birni hankalin Momy yafi na kowa tashi jin da gaske Auren ya tabbata, gashi a yanzu bata da ikon yiwa Jummo asiri saboda tsoron INNO, Zizah kuwa sosai tasa Jummo a gaba da cakala da neman fitina, sai dai ina Jummo bata kulata mahaukaciya take maida ta har tayi ta gama Aunty Zarah kuwa murnar Auren taji domin kuwa hankalin Momy zai bar gareta zata daina takura mata ta maida hankalinta ga Jummo, shi kuwa Ya Garkuwa yayi farin ciki sosai sai dai hankalinsa yana tashi a duk sanda ya tuno cewa Momy bata son Wannan Auren sai dai babu yanda ya iya dole zaici gaba da hkr harta huce, ko Kayan Auren da Daddy yayi umarnin a haɗa Momy kin sauraran zancen tayi sai Aunty Zarah Daddy ya bawa kuɗi ta haɗa babu laifi ta saka mata kaya masa kyau zannuwa guda arba'in ta saka banda dogayen riguna da sleeping dress, kayan makeup turaruka masu tsada duk ta saka, akwati shida ta saya, koda ta kawo kayan Momy dai taƙi koda zuwa ta kallesu domin kuwa ji take tamkar makara suka kawo mata na kaita kabari, haka taƙi ta sanar da ƙawayenta da abokan mutunci zuwa makwafta suzo suga kayan, itama Aunty Zarah gudun fitina yasa bata faɗawa kowa ba, ko gidan su domin kuwa tasan muddun ta kira wani yazo yaga Kayan ta shiga Uku Wajen Momy, Wajen Mamma ta kai kayan sosai suka sawa kayan albarka hatta Jummo sai da aka kirata ta gani tare da ƙawarta Meenat shima Daddy ya shigo yaga kayan kuma ƙwarai ya yabawa siyayyar AUNTY Zarah, koda Daddy yaga kayan bai saurari Momy ba ya sanar da Hajiya Rabi matar abokinsa suzo su kai kayan ita da Zarah haka kuwa akayi washe gari da safe suka kama hanyar Tulde suka kai kayan cikin daraja da mutuntawa, wannan kenan.


Yau ta kama ranar asabar babu makaranta Jummo na zaune a harabar gidan cikin fararen kujerun roba tayi shuru, Garkuwa daya shigo da motar sa ne yayi parking ya nufo ta tare da zama a ɗaya daga cikin kujerun yana kallon ta harya zauna bata san ya zauna ba tana tunani, hanunsa ya tafa a fuskarta, da hanzari ta dawo daga duniyar tunanin da ta lula tana sakin ajiyar zuciya ganin Ya Garkuwa a gabanta, idanu ya zuba mata cike da tuhuma yace.

" Zaƙin Zuciyata, tunanin me kike haka.?"

Numfashi Jummo ta saki tare da maida hankalin ta ga Ya Garkuwa zuciyarta sam babu daɗi tace.

" Ina tunanin rayuwa ne My HeartBeat, Duniyar tana bani tsoro idan na dubi abubuwan da suke cikinta, hmmm!!! Momy bata sona bansan mena mata ba ta tsaneni haka, naso ace Momy ta ɗaukeni tamkar yar da ta haifa a cikin ta, ni kuma na mata biyayya kamar yadda zaka mata, sai dai ina hakan sam bai yiwu ba, taƙi ta sawa Auren mu albarka, meyasa Momy bazata amince da Auren mu ba muyi rayuwa cikin farin ciki, gashi jibi zamu koma Tulde da INNO tace lallai acan zaayi bikin."

Shima numfashi Ya Garkuwa ya sauƙe tare da cewa.

" Bani da amsar tambayar ki nima Jummo bansan wani dalili yasa Momy ƙinki ba, sai dai na san insha Allah komai yayi farko zaiyi ƙarshe, da yardar Allah ina ji a jikina wata rana Momy zata sauƙo ta soki tamkar yadda take sona ki daina ɗaga hankalinki akan wannan ke dai ki dage da addu'a Allah ya nuna mana ƙarshen wannan masifar, ga can Invitation card an buga, adress ɗin da aka saka can TULDEN ne tunda Baffa yace anan za'a ɗaura Auren, insha Allah gobe da safe zamuje ki buɗe account zan saka miki kuɗaɗen da zaki buƙata, ina ga yau saura 7 days ko, sai dai fa ni babu wani bidia da zanyi su dener su wani party ni duk bazanyi ba, walima kawai za'ayi kin gane."

Kanta Jummo ta ɗaga alamun eh, sun ɗan juma suna hira har akayi kiran sallah sannan suka tashi a wajen.


Sannu sannu bata hana zuwa sai dai a juma baaje ba, yau ta kama ranar Alhamis kuma itace ranar da Jummo zata koma Tulde, can harma sun fara hidimar bikin su tun kafin zuwan su Jummo, a yayin da cikin gidan su Ya Garkuwa kuwa babu wani bikin da aka fara domin kuwa babu wanda Momy ta bari yasan ana Aure a cikin gidan, INNO Mamma Jummo sai MeenatSune zasu kama hanyar Tulde, sam Jummo ta manta bata sanar da Safreena Auren nata ba sakamakon abubuwa da suka mata yawa ga kuma Auren sam babu armashi sakamakon rashin sakewar Momy, INNO da kanta ta bawa Jummo umarnin taje tayi sallama da Momy babu musu Jummo ta amsa tare da nufar room ɗin Momy, a rufe yake ta ciki, nocking tayi tare da tsayuwa tana jiran a buɗe ƙofar tafi minti goma tana tsaye kafin Zizah tazo ta buɗe ƙofar turus ta tsaya tana duban Jummo cike da mamakin me kuma ya kawo ta, wani irin kallon banza Zizah ta watsa mata tare da sakin tsaki tace.

" Mtsss!!! Ashema shara ce ke nocking ai ni nayi zaton mutane masu amfani ne suka zo, ashe Kuma jikar mayu ce mtss, marar zuciya."

Tayi Maganar tana taɓe bakinta tare da cigaba da zubawa Jummo mungun kallo, wani irin zafin maganganun Zizah Jummo tayi, sai dai a wannan lokacin tana buƙatar ta sarrafa zuciyarta saboda Ya Garkuwa, numfashi ta sauke tare da kauda kanta gefe tace.

" Naji na gode, Momy nake nema ba keba Zizah kina iya bani waje na shige."

Murmushi Zizah ta saki tare da furta.

" Heeee!!!! Na!wa!wo! Oh kaji wata banzar Magana a wajen wannan Yarinyar, to sai naga dama kiga Momyn, ko bokanki ne ya baki wani ƙullin ki sawa Momy, to kinyi ƙarya domin kuwa Momy tafi ƙarfin tuggunki kinji ballagaza.!"

Runtse idanunta Jummo tayi ranta na mungun ɓace tace.

" Ya isheki haka cin zarafin Zizah, da alamu kin rantse sai nayi faɗa dake, naso ace sanda nake jummon ƙauye ce na tabbata da sai nayi maganinki yanda gaba koda sunana aka kira sai kin tsorota, sai dai kinyi matuƙar Sa'a Jummo ta dawo ta ƙwarai ta barwa karnuka irinku faɗa,da zaki kwana dubu kina nemana da faɗa bazan taɓa biye miki muyi ba domin da alama ke jahilar karatun addini ne, dan Allah a koma makaranta ko za'a samu a zamo na ƙwarai, ni kuwa inama ni ina faɗa da karen Tailan karnukan hauka, ki matsa na shige ko ƙarfina yasa na shige."

Wani irin munduƙun baƙin ciki Zizah taji, Momy dake tsaye ta harɗe hanunta ne a ƙirji tana sauraron duk maganganun su sosai Momy taji zafin abinda Jummo ta yiwa Zizah a matuƙar hasale Momy ta nufar ƙofar idanunta na rufewa tsabar baƙin ciki, wallahi yau babu abinda zai hana bata yiwa Jummo shegen dukan da babu mai gane fuskarta.






*UMMU NASMAH CE*
[5/19, 12:33 PM] UMMU NASMAH❤️: *PAYMENT GROUP ONLY*





➰➰ *60 to 61*



Tas!!! Tas!!! Tas!!! Momy ta ɗauke Jummo da mari har Uku tana nuna mata hanya.

" Get out!!! I say get out!!!!"

Tayi Maganar cikin tsawa mai firgitarwa, cike da tsoro Jummo ta matsa baya tana riƙe fuskarta da tayi ja, shatin yatsun Momy ya bayyana a fuskar, runtse idanunta Jummo tayi tare da juyawa cike da ƙuncin Zuciya, tsuka Momy taja tare da cewa Zizah.

" Meyasa bazaki mata shegen duka ba, ki kwantar min da shegiya a sume, sai ki tsaya kina cacar baki da ita, na tsani wannan Yarinyar ta rusa min duk wani shirina harta tsarin tarbiyya ta cewa take ba dai-dai bane, bana son koda kallon fuskarta ne, abun baƙin ciki wacce na tsana a rayuwata wai itace take shirin zama surukata, tirrr tirrr!! Zan kalli wannan ƙaddara a matsayin baƙar ƙaddara "

Numfashi Zizah ta sauƙe tana zama bakin gadon Momy tare da taɓe bakinta tace.

" Momy ina ni ina saka hanu jikin wannan ƴar ƙauyen wacce taci tuwo ta ƙoshi ƙarfinmu ma ai bazai zo ɗaya ba, wallahi Momy baki kaini tsanarta ba, tunda ta mallake min room na fara jin tsanarta tazo kuma ta saki a gaba, hmmm!!! MOMY babu faɗan hanu tsakanina da ita amma wallahi Momy ko anyi wannan auren nine zan kashe wannan Auren bazan taɓa bari auren nan yayi lasting ba, da makirci da kirsa wallahi sai na kashe mata aure, naci wannan alwashin kuma sai na cika da, ki kwantar da hankalinki Momy zanyi maganinta

Please Login or Register in order to submit comment