Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tare da tayi magana ba, doctor ne ya sunkuya a gabanta tare da kiran sunan ta.

" Jummo!!"

Shuru tayi tamkar bada ita yake ba, waro idanunsa yayi wannan fa shine tambaya ta farko da zai nuna tana hayyacinta, sau Uku ya kira sunanta bata amsa ba, yawu mai ɗaci ya haɗiye tare da nuna mata uniform ɗin jikinsa dake fari fat yace.

" Wannan baƙi ne ko fari.?"

Nan ma Jummo kau da kanta gefe tayi, jawo hannun Ya khalil yayi gabanta yace.

" Kinsan wannan."?

Sai yanzu ta ɗago kanta ta kalli Ya khalil a hankali tamkar mai koyon Magana tace.

" Yaya khalil!!! Ya Garkuwa ya mutu ko?"

Gabaki ɗayan su alhamdulillah suka furta, cikin dariya Ya khalil ya zauna gefenta tare da kamo hanunta ya girgiza mata kai.

" Bai mutu ba, yanzu ma zai shigo ki gansa, ya kike jin jikin naki."?

Kanta ta riƙe tace.

" Kaina yana min nauyi kamar dutse ya khalil sai dai nauyin da yake min bai dameni ba, kamar yadda zanso ganin Ya Garkuwa, Ya khalil dan Allah ka kaini wajen sa."

Doctor ɗago kai yayi ya kalleta cike da mamaki kusan maganarta ɗaya da wanda GARKUWA ya masa sanda ya farfaɗo, da alamu dai akwai wani abu tsakanin su, Ya Garkuwa kam murmushi yayi tare da miƙewa tsaye ya fita, room ɗin Garkuwa yayi tare da samunsa ya kifa kansa yayi shuru idanunsa sun cika da kwalla, kusa dashi Ya khalil ya zauna tare da dafa kafaɗarsa.

" Lafiya ɗan uwana, kake ƙoƙarin kuka, karfa ka manta cewa, baka da lafiya, kwanciyar hankali kake buƙata ba damuwa ba, just tell me pls what happening."

Karo na farko da Ya khalil ya fara tambayar ɗan uwansa damuwarsa, runtse idanunsa Ya Garkuwa yayi tare da jin wani sanyi, da Ya khalil ya tambaye sa maike damunsa, maimakon da da idan ya gansa a wannan halin sai dai yace, (Kai kuma a wannan ƙarnin mai zai maka zafi harka zauna sawa kanka damuwa a banza, just share koma meyene ka cigaba da rayuwarka) shima hanu yasa ya dafa kafaɗar Ya khalil, duk da a yanzu bazai iya sanar daahi damuwarsa ba, saboda akwai kunya yace Sadiya ta kira ta ci mutuncin sa, bare kuma ya faɗi abinda ke faruwa tsakanin su, juya Maganar yayi kan Jummo tare da cewa.

" Na gaji ne ina buƙatar ganinta sunƙi bani dama zuciyata kuma ƙuna take min, ganinta kawai zaisa naji sauƙi."

Murmushi Ya khalil yayi yana dukan kafaɗarsa yace.

" To mister romio tashi muje ka ganta, kaikam ma yau za'a sallameka mu koma gida, ita dai Jummo nata sallamar sunce ba yau ba."

Ɗan murmushi Ya Garkuwa yayi tare da miƙewa suka jera tare da Ya khalil, suna fitowa ya khalil ya doshi room ɗin dake kusa dana Ya Garkuwa, tsayawa Garkuwa yayi tare da cewa.

" Bros, me kuma zamuyi a wannan room ɗin."

" Wajen Mrs Love ɗin naka zamuje a nan take ba'a waje ba."

" Okay!!! Wayo kuka min kenan, kun maidani yaro, kaikam Bros bashi kaci kuma zan rama."

" Sai dai ka rame" cewar ya khalil yana shigewa room ɗin bayansa Garkuwa yabi, a zaune ta hangota tayi shuru, da sauri ya nufota, shi kuwa Ya khalil ya tare gabansa yana dariya, hanun Ya Garkuwa ya kama dana Jummo ya haɗa waje guda yana runtse idanunsa, har cikin zuciyarsa yaji zafi, sai dai duk da zafin da zuciyarsa ke masa hakan bai hana annuri bayyana a saman fuskarsa ba, cewa yayi.

" Ka kula da ita saboda kayi dace idan har ka samu aurenta duk rintsi duk wuya karka sake ko da wasa ka rabu da ita nasan akwai danja da ƙalubalen da zai fuskanto soyayyar ku, ka daure ka tsallake wannan siraɗin" Daddy Ya khalil ya kalla tare da cigaba da cewa.

" Daddy ga Jummo da Garko suna son junansu, sai dai ina da tabbacin zasu fuskanci matsala a cikin Soyayyar su, dan Allah Daddy ka zamo musu katangar da zata ƙetarar dasu siraɗin dake gabansu, idan ka samu a matsayin suruka, Daddy zakayi alfahari da ita."

Ya ƙarisa Maganar idanunsa yayi jajur tamkar garwashin wuta, Ya Garkuwa da kallo yabi Ya khalil bakinsa cike da tambayoyin ina khalil yasan akwai Soyayya tsakanin sa da Jummo, sannan menene ƙalubalen da yake tunkarar su cike da nauyin baki yace.

" Ƙalubale kuma Bros, wani irin ƙa............"

Hanu Ya khalil ya ɗaga masa tare da cewa.

" Daga kai har Daddy dan Allah karku min tambaya game da wannan ƙalubalen, lokaci shi zai baku amsar ku."

Daddy shuru yayi ba tare da yace komai ba, ya kalli doctor tare da cewa.

" Zaku iya bamu sallamar Garko, ita kuma sai ku taimaka ku bani takaddar transfer daga wannan asibitin zuwa medical center, saboda nan ɗin ya mana nisa sosai please help you Doctor."

Shuru doctor yayi yana tunani kafin daga baya yace.

" Okay ba damuwa ku biyoni office."

Da to Daddy ya amsa suka bi bayan doctor har Garko, Jummo jingina kanta tayi jikin gadon tare da yin shuru ta rufe idanunta, Mamma take hangowa "ko wani hali take" ta furta a fili.

Can kuwa DOCTOR ya basu sallama yayin da ya bawa Daddy takadda ya kai medical center, su kula da Jummo, haka kuwa sukayi daga sj gaɗam ɗin suka wuto medical, tare da yin duk wani cuku cuku daya dace aka basu room, Ya khalil ne ya bawa Jummo wayarta, wanda cikin ikon Allah babu abinda ya samu wayar, karɓa tayi suka barta da A'illo sannan suka koma gida, koda suka koma Momy da sauri ta rungume Garko tana dariya tace.

" Alhamdulillah!!! Allah mun gode maka, sannu Garko sannu."

Murmushi Garkuwa yayi yana ƙanƙame Momy cike da so da ƙauna, Ya khalil ne yace.

" Momy baki tambayi jikin Jummo ba."

Harara Momy ta watsa masa gudun bakin Daddy yasa ta cewa.

" Ya jikin nata."?

Murmushi Ya khalil yayi tare da cewa.

" Da sauƙi" yana shigewa room ɗin Mamma, tana nan kwance yanda take jikin babu wani sauƙi, sai Zarah dake zaune gefen INNO yayin da INNO ke haɗa wani ruwan magani, kallon khalil tayi tace.

" Kalilu ya jikin Jummo ta farfaɗo kuwa."?

" Ehh ta farfaɗo kuma Alhamdulillah ta dawo cikin hankalinta, INNO ya labarin jikin Mamma har yanzu babu wani sauyi."?

Shuru INNO ta yi cikin sanyin jiki, domin kuwa ita kanta rashin lafiyar Mamma ya fara bata tsoro.

" Kalilu gashi nan dai babu wani sauƙi, kullum jiya i yau, hmmm!!! Amma tabbas sihiri ne, sai dai na rasa gane ta ina zan fara karyasa, ni ba duba nake ba bare na duba taya abin ya faru addu'a kawai ya kamata mu dage dashi amma ciwon nata baya jin magani."

Shima ya khalil cikin sanyin jiki ya zauna tare da furta.

" Allah ya bata lafiya, sun juma sosai suna hira da INNO, a yanzu Aunty Zarah ta ɗan sauƙo daga gabar da take dashi.


✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨


Akwana a tashi babu wuya a wajen Ubangiji yau har satin Jummo Uku a asibiti ana kula da ita saboda suna tsoro matsalar ƙwaƙwalwa shiyasa suka riƙeta, sai yau suka bata sallama sosai Jummo tayi sauƙi tamkar bata samu matsala ba, haka suka dawo gida, baƙin cikin dawowar Jummo tamkar zai kashe Momy, ko sannu da jiki bata cewa Jummo ba, Aunty Zarah kuwa ta mata sannu tamkar babu abinda ya haɗa su.

Haka Rayuwa ta cigaba da garawa a cikin wannan gidan yayin da Mamma jiki kam babu sauƙi, Jummo kuwa da Momy ƴar tsama a tsakanin su sai ma ƙaruwa da yayi.


Ya Garkuwa dake zaune a cikin room ɗinsa ne yaji wayarsa ta ɗauki kuka, ganin Sadiya ke kira ya sashi ƙin ɗaukar wayar kusan 10 miss call ta masa bai ɗaga ba, shigowar text yaji wayar ya ɗauka tare da duba saƙon yaga abinda ta rubuta.

*_Shi dai butulu duk inda yake wallahi yayi asara, Garkuwa ka cuceni ka lalata min rayuwata kai kawar min da mutunci na, sannan ka gujeni, na baka duk wata Soyayyar gaskiya amma ka cutar dani ta hanyar amfani da Soyayyar da nake maka, bazan ce zan tona maka asiri ba, domin kaina zan tonawa, sai dai ka sani na barka da Allah insha Allah a cikin ƴaƴan da zaka haifa sai Allah ya saka min, daga yau bazan kuma shiga rayuwarka ba, kaje kai da Allah, Allah Ya isa tsakanina da kai mungu azzalumi._*


Runtse idanunsa ya Garkuwa yayi da ƙarfi yana jin ƙunar maganganun ta, bude idanun nasa yayi take har sunyi jajur, text ɗin ya goge cike da sanyin jiki, cikin zuciyarsa yana neman afuwar Ubangiji.

Sadiya kuwa bayan ta tura text ɗin ne ta fashe da kuka tare da Kwanciya ruf da ciki, duk da tasan tarayyar ta da ya Garkuwa kuskure ne, amma bata taɓa tunanin akwai ranar danasani ba a rayuwarta, ba mamaki wannan shine hukuncin zunubin da ta aikata, shin yanzu waye zata Aura ya ganni da mutunci, me zan cewa mijin da zai Aure ni, idan ya tambaye ni ina na kai budurcina mai zance mishi, tabbas na aikata kuskuren da bazai taɓa goguwa a idanun mijin da zan aura ba, Allah ya isa tsakanina da kai Garkuwa ka cutar da rayuwata.

Ta ƙarisa zancen zucin tana share hawayen dake gangaro mata tare da alƙawarin mantawa da Garkuwa a cikin rayuwarta.

Safreena sosai taji daɗin labarin da Zee ta kawo mata na cewa Garkuwa ya dawo hayyacinsa harma an sallamesa a asibiti ya dawo gida, hakan ba ƙaramin daɗi ya mata ba, a yanzu ƙiyayyarr da take yiwa Garkuwa yayi sauƙi sosai a cikin zuciyarta, a yanzu bata da burin daya wuce taga bayan Kawu Ibrahim, burinta ta ɗaukawa iyayenta fansa wannan shine kawai a ranta.

Yau tun safe Mamma take wani irin tari tun sanda INNO ta bata wani ruwan magani take wannan tarin, wani irin yalon kumfa ke fitowa daga bakinta, Jummo ke saka tisue ta goge wannan kumfa, INNO ta sani sarai tasirin gubar asirin da aka sawa Mamma ke fita daga jikinta, amma INNO tayi shuru taƙi faɗawa kowa gudun kar wanda yayi asirin yaje ya lalata mata shiri, su duk a zaton su jikin Mamma tsanani ya ƙara Jummo harda kuka, a yayin da a zahiri Mamma sauƙi takee samu Momy kuwa sosai take murna jikin Mamma ya ƙara tsanani.



*******************

Zaune Jummo take a falo tayi shuru cike da tunani, kusa da ita Ya Garkuwa ya zauna ba tare da ta lura da zamansa ba, taɓata yayi a hankali ta juyo tana kallon sa sai kuma ta ɗan saki murmushi.

" Ya Garkuwa yaushe kazo nan"?


Taɓe bakinsa yayi tare da cewa.

" Sanda kike duniyar tunani, meke damunki haka kikayi nisa cikin tunani."?

" Ya Garkuwa kasan ai tatsuniyar gizo bata wuce ta ƙoƙi, matsalar Mamma ke ɗaga min hankali tana sani cikin damuwa, ciwo kullum ba sauƙi sai ma gaba da ciwon ya ƙara ga INNO ma tazo amma har yanzu jiya i yau, yanzu haka zamu zubawa Mamma idanu a wannan halin."

Numfashi Ya Garkuwa ta saki yana dafe fuskarsa yace.

" Bazai yiwu a barta haka ba, idan INNO ta kasa ya zamo dole a nemo wani mai bada maganin, ki kwantar da hankalin ki, insha Allah duk inda ake nemo lafiya zamu nemowa Mamma bana son ganinki cikin damuwa."

" To shikenan Ya Garkuwa Allah yasa ya bata lafiya, ya Garkuwa ina labarin budurwar kane.?"

Cike da tsantsar mamaki yace.

Budurwata kuma, waye kuma budurwata bayan ke, kinga nifa gobe zan sanar da Daddy kawai aje Cilo a nemo min Aure ki, ayi kawai mu wuce wajen, na matsu na kasance da ke waje ɗaya Inuwa ɗaya kin san kuwa irin tsantsar Soyayyar da nake miki, ji nake tamkar na mai daki cikina tsabar so ina sonki Jummo."

Dariya Jummo tayi har haƙwaranta na bayyana cikin zolaya tace.

" A'a malam, aje Cilo da izinin waye, waya faɗa maka ina sonka, kaga fara sanar dani labarin Soyayyar ka da Sadiya kafin ka fara zancen Aure na, da alamu dai kun ɗan soye."

Dariya mai sauti ya Garkuwa yayi tare da cewa.

" Ehh mun soye harma mun kusa ƙonewa kwatsam ki shigo rayuwata kika ɓata tsakanin mu."

Wani irin bugawa zuciyar Jummo yayi take taji kishin Sadiya har kamar haushinta taji, tsumewa tayi tare da cewa.

" Oh nine ma na shiga tsakaninku ko, kuna son junanku na rabaku to meyasa yanzu bazan fita a rayuwar taka ba, idan yaso kuje ku babbake ma ba soyewa ba."

Tayi Maganar tana tura baki, hango kishi ƙarara yayi a idanun Jummo, dariya yayi sosai har dimple nasa yana loɓawa yace.

" Malama kece fa kika tambayeni ni kuma na faɗa miki gaskiya, to meye kuma na haɗa fuska, bayan kece mai tambayar, bari ma da kiji wato ni da Sadiya ko munsha.................."

Yatsanta Jummo tasa ta toshe kunnenta tare da cewa.

" Ni ya isheni haka bana son ji, dan Allah kayi shuru karka ƙarisa na roƙeka."

Dariya Ya Garkuwa yayi tare da cewa.

" Ashe dama haka kike sona sosai, duk wannan kishin wani kike mawa, alhamdulillah!!! Kwantar da hankalin ki farin ciki na, Sadiya dai mun ɗanyi Soyayya amma ba mai tsawo ba, asali ma babu zancen Aure tsakanina da ita, itace take ɗaukar Soyayyar da mukayi a matsayin zan aureta amma babu alƙawarin Aure tsakanina da ita, a yanzu haka albishir ɗin da nake son na miki, shine babu wata alaƙa tsakanina da Sadiya, mun raba Gari kowa ya kama gabansa."

Murmushi Jummo ta saki tare da juyowa ta fuskanci Ya Garkuwa tace.

" Dole nayi kishi a kanka karka manta da tun kafin nasan meye Soyayya zuciyata take ƙaunar ka, har zuwa yanzu da nasan darajar so, matsuguninka bai sauya a zuciyata ba, sai ma wajen zama ka ƙara samu a gareni, Ya Garkuwa daga yau sunanka ya sauya daga Ya Garkuwa zuwa Heartbeat wato bugun zuciya ta, kaine murmushi na kuma haske na, ban san Soyayyar wani namiji ba, bayan taka, ina sonka zan kuma kasance da kai a ko wani hali ka tsinci kanka a rayuwa bazan taɓa juya maka baya ba, zan tayaka mu rungumi dukkan wata ƙaddarar da tazo maka mai kyau ko marar kyau wannan alƙawari na ɗauka mutuwa ce kawai zata rabani da kai."

Tunda ta fara Maganar Ya Garkuwa ya lumshe idanunsa cike da jin daɗin zantukanta, ya sani itace kawai ke masa Soyayyar gaskiya har abada bazai samu mai sonsa da gaskiya irinta ba, sunanta ya furta a hankali.

" Jummo!!"

Ɗago idanunta tayi tare da amsawa tana murmushi kansa Ya Garkuwa ya kawar gefe tare da cewa.

" Karki ɗauki alƙawarin kasancewa dani ta ko wani hali domin kuwa ina tare da aibun da zaki iya tsanata kiji bazaki iya zama dani ba bare kuma Rayuwa ta har abada, a kullum ina son na sanar dake wannan aibun nawa kuma ina tsoron yanda zaki ɗauki zancen wata ƙila ma ki tsaneni ko ki gujeni, ni mai tarin zunubai ne Jummo, duk da tawa ƙaddarar ce tazo da haka, amma a yanzu na tuba nayi tuba ta haƙiƙa shin Jummo zaki iya kasancewa dani idan kikaji mungun halina, ina tsoron kiji ki rabu dani, rabuwa dake a wannan lokacin zai iya zamowa ƙarshen numfashi na.?"

Shuru Jummo tayi tana kallon ya Garkuwa cike da mamaki, mungun hali tarin zunubai da yake ambaton yana dashi, cike da ƙwarin gwiwwa tace.

" Ka faɗa koma menene ni zan tayaka mu rungumi ƙaddarar, tunda har kace ka tuba, shima kansa Allah ai gafurun rahim ne, bare kuma ni wata banza Jummo, ka faɗa min komai ba tare da tsoro ba, ni kuwa zan karɓi ko mai munin halinka a matsayin ƙaddarar rayuwata."

Ya Garkuwa sunkuyar da kansa ƙasa yayi ba tare daya kalli Jummo ba ya fara cewa......."




*UMMU NASMAH CE*


✨✨✨✨✨✨✨✨✨
[4/19, 9:51 PM] UMMU NASMAH❤️: *PAYMENT GROUP ONLY*




➰➰ *49 to 50*




" Rayuwata ta kasance ne cikin mungun saɓon Ubangiji wanda Allah ke fushi da mai aikata sa, na kasance mutum mai jarabar tsiya wanda sam bana iya riƙe buƙatata, ni mutum ne ma'abocin jarabar mace, akwai wata yarinya mai suna Safreena!! School ɗin mu ɗaya da ita munyi karatu da ita a Oxford University dake ƙasar Amurika, ita set ɗin ƙasan mune, a lokacin da idanuna suka sauƙa akanta naji zuciyata ta aminta da ita naji ina sonta, sai dai ita macece mai kamun da sanin darajar kanta, Asali ma ko ƙawa bata dashi a cikin school ɗin, bare kuma aboki namiji, a sanda naga Safreena na kuma ji ina sonta na fara tunanin ta yaya zan ƙulla alaƙa da ita wanda har zan samu ta saurareni, na kai sati Uku ina nazarin yanda zan fara tunkarar ta, kwatsam wata ranar monday, aka basu assignment Wanda Wannan assignment ɗin shine zai zamo S'A test ɗinsu assignment ne mai matukar wahalar gaske akan biological sciences wanda shi kansa lecturer ɗin daya basu wannan assignment idan aka ajiye sa ba lallai ya iya amsa dukkan waɗannan Quation ɗin ba, hankalin su ya tashi suka haɗa group domin ganin sun amsa wannan Quation amma suka gagara sun karaɗe dukkan school ɗin suna neman amsar amma basu samu ba, hmmm!!" Shuru yayi tare da kallon Jummo ya cigaba da cewa.

" kinsan meya faru a wannan lokacin?"

Girgiza kanta Jummo tayi alamun a'a cike da sanyin jiki da kuma jin kishin wacce ake bata labari a kanta, cigaba da Magana ya Garkuwa yayi.

" Abokina Shetima Ladan ne yazo yake sanar dani zancen assignment ɗin da aka bawa ƴan Cause ɗinsu kuma sun gagara samu, a wannan lokacin wani tunani ya faɗo min, me zai hana naje na ƙarɓo Quation ɗin da zumar zan amsa musu, duk da nasan bazan iya ba tunda ba Cause ɗina bane, amma na ɗauki wannan kasadar da wannan tunanin naje na tunkari Safreena, da farko da naje bata saurareni ba, sanda na nawa ƙawarta Zee bayanin abinda ya kawo ni sannan Zee ta sata saurarana dole, na karɓo assignment ɗin, tare da alƙawarin da safe zan kawo musu, room ɗin na koma na dafe kaina ina tunanin taya zan amsa abinda bani da ilimi a kansa, nakai 11 na dare ina nazari, kafin daga baya tunanin Bro khalil Cause ɗin da yayi kenan ya kuma zo first class, numfashi na sauƙe tare da kiran wayarsa nake sanar dashi halin da nake ciki sosai ya min dariya kafin daga bisani yace na turo masa Quation ɗin ta WhatsApp, haka kuwa akayi na tura masa cikin ikon Allah a 1 hours Bro khalil ya amsa dukkan tambayoyin ya aiko min dasu, cike da farin ciki washe gari na kai mata sosai taji daɗin abinda na musu, da wannan alaƙa Mai ƙarfi ta shiga tsakanina da Safreena, ya zamanto dukkan wani assignment idan aka bata bata gane ba, sai ta kawo min ni kuwa na bawa Bro khalil ya amsa mata, da haka muka shaƙu har Soyayya mai ƙarfi ta shiga tsakanin mu, sosai muka shaƙu da juna yayin da idan ɗaya baiga ɗaya ba hankalinsa baya kwanciya, muna tsaka da tsaftacacciyar Soyayya, na kammala karatuna, mukayi graduation, Sosai hankalina ya tashi ina tunanin ta yaya zan iya rabuwa da ita, itama hakanne a wajen ta harma ta zarta ni shiga cikin tashin hankali, ranar Sunday itace ranar walimar kammala karatun mu, a kuma ranar wani mummunan al'amari ya faru tsakanin mu da Safreena hmmm!!! Wannan baƙar rana ce a gareni wanda bazan taɓa mantawa da ita ba a rayuwata, Jummo Safreena tamin alƙawarin zuwa walimar kammala karatun mu, a wani holl da muka kama, a ranar dukkan abinda ya faru, nafi Safreena amma itace ta janyo hakan, Safreena ta shigo wannan holl ɗin da wani irin shiga wanda sam bai dace da shigar ɗan musulmi ba, ni kaina ban taɓa zaton Safreena zatayi irin wannan shigar ba, saboda kamun kanta, sai kuma aka samu akasi tayi wannan shigar wanda ita ba wai tayisa da nufin komai bane, rigace fara tas wacce ta kama jikinta sosai da wando jeans Wanda shima yayi mungun kamata tamkar zai fasa jikinta, komai na surar jikinta ya bayyana, gashi kuma ta saka ƙaramin gyale wanda ko ƙirjinta bai rufe ba, tunda na saka idanuna akanta a wannan daren, hankalina ya tashi sha'awa ta ta motsa na gagara control ɗin kaina, duk da haka nayi ƙoƙarin korar sheɗan daga zuciyata, amma banci nasarar korar sa ba, sai ma tunzurani daya yi, Jummo na taƙaice miki a wannan daren sanda nasan yanda nayi na sawa Safreena maganin kawar da hankali a ruwa tasha, na jata zuwa wani room, a wannan daren na lalatawa Safreena budurcinta........."

Wani razana Jummo tayi ta miƙe tsaye tare da dakatar da Ya Garkuwa ta hanyar furta.

" Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!!! What!!! Y..y...y...y... ya garrrrrkuwa!!! Kai ɗin ne kayi wannan mungun aikin.!!!"?

Jummo ta furta maganar cike da in'ina daƙyar Maganar ke fita tana nuna Ya Garkuwa Da yatsa.

Share hawayen daya wanke masa fuska Ya Garkuwa yayi tare da cewa.

" Kin firgita ko, baki taɓa tunanin zaki sameni da wannan mugun tabon ba, ko shiyasa na ce dole zaki tsan.........."

" Shittttttt!!!! Karka ƙarisa, ka cigaba da bani labarin kawai."

Tayi Maganar itama tana share hawayen ta.

Hankalina bai dawo jikina ba sai bayan na gama haye mata daga nan ne na fara jin takaicin abinda ya faru, ko da Safreena ta farfaɗo sosai hankalinta ya tashi ta shiga cikin damuwa da tashin hankali ta dinga kuka tamkar ranta zai fita, a wannan lokacin bani da bakin mata Magana saboda kunyarta, cike da haushina da tsanata Safreena ta miƙe taje tolet ta gyara jikinta ta mayar da kayan jikinta, tana ɗan ɗingishi ta bar holl ɗin gaba ɗaya, a ranar koni ba'a tashi walimar dani ba, hankalina ya tashi na shiga cikin damuwa sosai, na kasa hkr har sai da na sanar da abokina Shetima abinda yake faruwa shima sosai ransa ya ɓaci, yamin masifa tamkar zai dakeni, abun mamaki duk da abinda ya faru tsakanina da Safreena banji sonta ya ragu a cikin zuciyata ba, sai ma ƙaruwa da yayi, munje nida Shetima domin bawa Safreena hkr, amma taƙi ta haƙura ko sauraronmu batayi ba, sai ma Allah ya isa da take jamin, na shiga cikin ɗimuwa da ganin tsanata a idanun SAFREENA, haka dole muka barta ba dan naso ba, tun daga wannan Ranar Safreena ta fita daga rayuwata ta daina kulani, ni kuwa na shiga cikin damuwa, ga kuma zan koma gida, har ƴar wata rama nayi, haka na dinga yiwa Safreena naci ina bata hkr, komawa gidan ma na hkr dashi, ko da ban koma gida ba nasan babu mai tambayata meyasa ban dawo ba, saboda kowa rayuwarsa yake a gidan mu babu ruwan kowa da ɗan uwansa, muddun zamu shekara muna waya da gida bazasu tambaya meyasa na gama karatu ban dawo ba, hakanne ya bani damar zama har sai na samu Safreena ta haƙura, nayi iya yina Safreena taƙi saurarata, kuma ina da tabbacin Zee ke sake nisantani da ita ita a nata tunanin na ɓatawa aminiyarta rayuwa, an kai wajen Wata shida Safreena bata saurarata ko kallo na bata yi, ni kuwa Soyayyar ta tamin kamun da bazan iya hkrn rasata ba, daga nan ciwon ƙirji da tari ya fara sanɗata sakamakon damuwa da nake ciki, tun ina jin ciwon kaɗan har sai da ya yasar dani, ƙarshe har sai da na kwanta a asibiti, nasha rashin lafiya na ciwon ƙirji tamkar zan mutu, kafin Safreena ta dawo gareni, ganin ina ƙoƙarin rasa rayuwata saboda ita, daga nan ta kuma yarda dani a karo na biyu zuciyarta ta aminta son gaskiya nake mata"

Kallon Jummo yayi ya cigaba da cewa.

" Nayi mamaki da DOCTORn daya kula dani Asibitin Sj gaɗam bai gane ciwon zuciyar dake jikina tsohon ciwo bane, domin kuwa na samu wannan ciwon zuciyar ne ta sanadin Safreena, sakamakon rasata da na kusa yi, ban sanar

Please Login or Register in order to submit comment