Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

take shafa bayanta.
"Ina kike jikalleta farincikin rayuwata jikalle ɗaya tamkar da dubu ina kike zo rungume ni ki kwashe albarkan shekarun da kika rasa."
Hajiya Babaa ta fito daga cikin mota tana taku da takalminta mai tsini sosai, wanda yake barazanar kayar da ita.
Wani irin ihu ta ƙara saki tare da sakin Nahlin ta rungume ta tana ihu tana sakin mata kiss ta ko ina.
"Na yi kewarki hajjjajuta na yi kewarki sosai, ina matuƙar sonki ƴar tsohuwa mai ran ƙarfe." Ta furta cikin murna sai juyata take.
"Haba ai Halimatuu ni na haife ta, amma ban sa in da ta samo halinta ba, haka kawai ta nisanta ni dake akan wasu dalilanta mara ƙarfi, ina gaya miki yanzu kin dawo babu jirgawa ko ina, ko aure kika yi tare zamu je, don na san gidan ki ne kaɗai zani na huta." Ta ƙarashe maganar tana hararar Nahlin da take tsaya tana kyaɓe baki.
"Ai a ko sati ba za ki yi ba za'a koro ki sis, domin tsaf zata kashe miki aure, just imagined mijin ta na karyawa ki haɗa wannan kwacamalar ta ki, goro da lacasera. Oh my goodness. I will really pity him, how nausea and vomiting ɗin da zai yi. " Ta ƙarashe maganar tana yamutsa fuska kamar za ta yi amai.

"Wallahi yarinya ta zage ni. Uban baki mai haure zan ci. Kin sam ni ko uwarki ba ta ishe ni ba, balle ke da kike iƙirarin turancin ki da bai wuce rabin cokali ba. Kina zagina da turanci sai kin gaya wa aya sakin ta, don na ji kamar har da imanja kike fadi kome. Kin san ni da gidan ki har abada."
"Wo Hajiyata." Jannah ta ce, cikin rike baki duk da ta san hali, lokacin da ta zo za'a yi mata aiki a London an sha dirama, ga ba ido ga masifa.
"Wa ke gayyar ki a gidansa, ai never. " cewar Nahlin.
Babaa ta buga mata harara tana faɗin. "Allah ya kyauta wa rayuwa ni na je gidanki, domin na san yunwa sai ta kashe ni, an riga na gado baƙin hali.

Kama kumatunta tana dariya. "Mai hali baya fasa halinsa ko shekaru nawa za'a ɗauka. Kina nan dai da halin ki kamar yadda na sani. Tace cikin murmushi.
"Ya canza taɓ! Ai sai dai abin da ya ƙaru." Nahlin tace tana hararar ta. Nahlin ta kama hannunta tana faɗin. "Maza muje sis in dai Babaa ce sai ta kai mu dare a nan ba tare da mun je gida mun huta ba.
Babaa ta wafce hannunta da sauri. "Maza kar a ɓata mini jikalle da baƙin hali. Ma za muje kin ji ɗaya tamkar da dubu, ki huta kin shawo hanya." Ta ƙarashe maganar tare da jan hannunta suka fara tafiya.
Saboda dariyar yadda Hajiya Babaa take tafiya ya bawa Nahlin dariya, sosai har tana riƙe ciki. Rigima sosai ta yi kafin a sayo mata irin takalmar, domin Ammy sayo wa irin takalmar daga gani ta saka rigimar yana fifita matarsa, ganin irin takalmar ta kuma kafe akan dole sai ya siyo mata. Tun lokacin da aka siyo takalmar bata taɓa sawa ba, sai yau da zuwan Jannah domin takalmar hill ne, ko da za su shiga cikin motar a hannu ta riƙo su sai da suka ƙaraso filin jirgin ta saka.
Sai turguɗewa take yi amma ta nace dole sai ta yi tafiya da su, haka take tafiyar tana turguɗe, tana tafiya ta turguɗe sai gata tana shirin zubewa a ƙasa, ji ta yi wani saurayi ya riƙe ta yana faɗin,
"Kiyi a hankali Hajiya. Da sauri Hajiya Babaa ta juya tana kallon saurayin.
"Sannu ɗan saurayi Allah ya yi maka albarka." Ya amsa cikin natsuwa yana kallon Jannah da ta ƙaraso da sauri ta rungume ta. Nahlin ko me zata yi in ba dariya ba.
Tsabar haushin ta da Babaa take ji ko kallon ta ba ta yi, ta cire takalminta ta riƙe a hannun ta tare da jan hannunta suka fara tafiya zuwa motar su.
"Allah ya ƙara muki maganin ki da karambani kin ci lokacin ki kice sai kin ce na wani, in ban da rigima irin taki ina ke ina wani takalmi hill." Ta furta hakan a cikin ranta.
Buɗe ƙofar suka yi suka shiga yana tsaye yana kallonsa, duk da Jannah ta so ta yi masa magana, amma kunyar su Dad ya hana ta ko kallonsa.
Har sai da suka shiga cikin mota direba ya fara tafiya ta juyo ta kalle shi yana tsaye fuskarsa tamkar zai yi kuka duk sai ta ji bata ji daɗi ba, musammman da ta ga ya yi sororo yana nuna mata bata ba shi numbar wayarta ba.
Ajiyar zuciya ta yi mai ƙarfi tare da ji gina kanta saman kujera ta lumshe idanunta.
A lokacin da suka isa gida wanka ta shige ta rinka kwararawa kanta ruwan sanyi tana jin sanyin ruwan yana sauka har cikin zuciyarta.

Bayan ta ɗauki tsawon lokaci tana watsawa kanta ruwan sannnan ta fito daga cikin bayin ta sanya dogon riga kawai ba tare da ta shafa mai ba ta fito daga cikin ɗakin.
Kai tsaye kicin ta wuce in da take jin motsin Hajiya baaba tana kwarafniya da tukane.
"Yauwa shalelena kin fito? Yanzu nake son na shiga na yi miki magana jin kin daɗe a bayi. Ko ke ma kin ɗauki halin mahaifiyarki na watsa da ruwa lokacin wanka?"
Dariya ta yi mata Jin abin da ta fadi."Wai Hajiya har yanzu ba ki daina rigimar yi wa kanki girki ba?" Ta maida maganar tsigar tambaya.
"Ato ni hauka nake na rinƙa bari ina cin abincin da zai cutar da ni. Haka kawai ba za a ci abinci mai kwayu ba, sai kullum a rinka cin wata cimar da aka ɗauko daga wata Kabila can. Shi ya sa nake girki da kaina. Kin ga ma za je ki zauna yanzu zan kawo miki abinci, saboda ke na yi tuwon shinkafa miyar taushe, duk da na san ke ma ba'a iya miki."
Jannah ta yamutsa fuska jin abin tace mata."A haba Hajiya na yi duguwar tafiya sai ki rasa abin da za ki ba ni sai tuwon shinkafa. So kike cikina ya yi nauyi na kasa bacci?" Sai ta fice daga kicin din tana faɗin ni ba abinci zan ci ba tea kawai zan sha na kwanta bacci, sai bayan na tashi zan ci abinci, amma ba tuwo ba."
Hajiya ta biyo tana tana salati. " Haba Jannatuu so kike su yi mini dariya, tun da mahaifiyarki ta gaya mini za ki zo kwana na yi ban rintsa, don Allah kar ki watsa mini kasa a ido." Dariya kawai ta yi ta kwanta akan doguwar kujera daidai lokacin da Nahlin da mahaifiyarta suka shigo yayin da Nahlin take ɗauke da turen abinci, ganin haka Hajiya Baaba ta harari kwanon tare da ɗauke fuska bayan ta taɓe baki.
Murmushi kawai suka yi tare da shigowa. "Sannu da hutawa Hajiya." Mom ta furta da sauri ganin zata shige kicin.
"Ba aiki nake yi ba kamar yadda kike gani." Shiru ta yi ba tare da tace komai ba har ta shige kicin ɗin tana bambami.
Nahlin ta sauke tiren kwanon abincin tana bin bayanta da harara. Ba ta yi ninyar gaishe ta ba kamar kmar yadda tasan ba zata amsa ba.
Da sauri ta sauka daga kan kujera ta durƙusa." Mom barka da fatan na same ku lafiya?" Ta furta cikin jin kunya da girmamawa domin Allah ya sanya mata jin kunyar Ammy da ƙaunar ta.
Shafa kanta ta yi cikin so da ƙauna."Lafiya lau ya maihaifiyar ta ki."
"Daddy yana lafiya."Ta ce cikin basar da tambaya.
Murmushi ta yi kawai sannan ta miƙe tana faɗin."Bari na barki da Nahlin, in kika huta da fatan za ki shigo shashin nawa."
"Eh Amym ai a ɗakin Nahlin zan zauna." Ta furta domin ta ɗauki aniyar ba zata zauna a ɗakin Hajiya Baaba ba.
Akan me za za ki zauna a ɗakinta bayan tun kafin ki zo na sanya aka gyara mana ɗakinki." Ta ji muryar ta tana mata tambaya.
"Gaskiya ba zan zauna a ɗakin ki ba, kiyi ta damun mutane da surutu da labarin sa bai shafe ni ba, har da na matattu fisabilillahi ina wanda zai kwanta bacci za a bashi labarin mattatu salon na yi mafarkin fatalwa." Ta ƙarashe maganar cikin shagwaba.
"Jakar uban nan!" Ta furta ai kuwa in har ba za ki kwana a ɗakina kin ɗauko ruwan dafa kanki, domin magen da kike tsoro na ɗaura miki a jiki, jiya kasa bacci na yi ina murnar za ki zo, amma sai ki watsa mini kasa a ido, ai gara ki dawo hankalinki tun kafin ruwa ya kare wa ɗankada." Tana gama maganar ta wuce ɗakinta.

Dirama sosai aka yi akan inda za ta zauna ganin ta ki cinyewa da kanta ta zaɓi ta zauna a sashin Hajiya Babaa.
"Da dai kin hutar da kan ki. Haka kawai an mallake mini ɗana, kuma wanann 'yar gudaliyar za'a haɗa da ita. Ina wallahi uban kuturu ya yi kaɗan. "
Ita dai Ammy ba ta ce komai ba. Ajiyar zuciya ta saki, sannan ta fice daga ɗakin. Nahlin ta yi ƙunƙunai wanda ba za ka gane me take cewa ba zata fice daga ɗakin, wanda hakan ya kubular da Hajiya Baaba ta wawuri mafici ta jefa ta da shi. Nahlin ta ruga da gudu tana dariya.
Jannah ta yi shiru duk irin surutun da take ba ta da labarin yadda ta mallake mata ɗanta. Sam ba saurara take yi ba domin hankalinta ya yi nisan kiwon dan saurayin da ta ji ba ta kyauta masa ba, ya kamata ace sun yi exchanging contact if possible su rinƙa gaisawa.

"Magana na ke, kike kunnen uwar shegu da ni. Wato ga mahaukaciya ko? Kin ga wallahi zamu saka kafar wando daya dake, ba zan lamunci wannan isgilancin na ku da kuka gado ko a ina ba. " Sai kuma ta sausauta murya ganin halin ko-in-kula da ta yi mata.
"Kina ji na shalelensa jikata. Kin san ke kaɗai na fi so, duk cikin jikokina ko? Ya kamata ki tausaya mini, matar nan ta riƙe makogaron ɗana sam ba shi da wani kataɓus. Abynku ya zama mijin-ta-ce."
Wani irin takaici ne ya kamata sai ta ki ganin ba'a rabu da bakar bane aka haifi habu. Ita da take ganin za ta zo ta huta da damuwa, sai ga shi ko hutawa ba ta gama yi ba, an dauki mata wani damuwar, wannan dalilin ya sa ta so ta zauna a sashin Ammy, amma ta hana to ga shi ba'a je ko ina ba ta fara dana-sa-ni.
"To ni mai zan ce miki Hajiya Baaba? Kin san ni ban san komai ba game da rayuwar da kuke yi. Ki yi hakuri don Allah"
Tana gama faɗar haka ta shige cikin ɗakin da ta nuna mallakin ta don kar ta kara ce mata komai.
Ajmal bai shigo gidan ba, sai misalin goma da rabi na dare, don ya san a wanann lokacin yar rigimar ta yi bacci. Ko da Hamir ya so ya shigo da shi har ciki, amma sai ya bukaci ya yi parking a waje ya sauka.
Cikin sanɗa ya shigo zai ije mata hura da nonon da ya zame ƙa'ida kullum sai ta sha sai ka ce magani.
"Munafikin Allah! Ina za ka dawo ma za dawo na ce. Ai na ji karar bude get, labarai nake sauraro na yi ma za na kashe don na san haka zai faru. To dawo dan ubanka. "
Takaici da haushi suka cika shi, ji ya yi kamar ya wuya ya shake mata makogaro, domin ta saka shi a gaba. Ko iyayensa ba sa zagin sa, amma sai ita haka take tamkar jikar maguzawa.
Kamar ba zai juya ba sai kuma ya jiya ya watsa mata kallo yana ƙoƙarin barin wurin
"Ka dawo na ce Adamuuu ka na jima ko? Wallahi in ka tafi sai fushin nan ya shafi kowa, don gobe ba wanda zai karya ta daɗi. Ta shi zan yi tun asuba na fara masifa da bala'i. "
"Hajiya Babaa, na ce ki dena ce mini Adamuu! I really hate the way you pronounce it. Tun da kin ka sa kiran Ajmal please call me Adam."
Ya ƙarashe maganar cikin ƙunar rai da ɓacin rai.
"Umm, aikin bit in ji tusa. Da ba'a san asalin angulu ba, sai ta ce daga Ƙasar misrah ta ke. Inji uban ka da ga ƙauye ya fito ɗan kauye ne na gidi. Wallahi lokacin da ya fito birni komai bai iya ba. "Sai kuma ta sa kuka ta ci gaba da faɗin,
"Wallahi Allah ya isa tsakanina da ƙanina Hamisu. Haka kawai ka saka finitina ka gudo mini da yaya birni ga shi nan, zuriyana ba su da maraba da iyalan arna.
"Iyalan arna kika ce Babaa! "Ya tambaye cikin tsananin mamakin abin da ta furta.
"Ina maraban dabbe da faɗa? Bakiɗaya kun ɗauki ɗabi'ar yahudu da nasara kun ɗora ma kan ku. Ni wannan turancin ma da kuke yi shi ya fi ci mini tuwo a ƙwarya. Ƙiri-ƙiri ina gani ku zage ni ba ni da ta cewa. Ina ji ranar nan cewa ka yi ko myh God. Da ga ji zagi ne. Allah shi zai saka mini, don wallahi uwarka ka zaga na ni ba.
Takaici da dariya sun hana ya shi ce mata komai ganin ta yi shiru tana zare ido.
"Allah ya ba ki hakuri. Bar na je na kwanta bacci na ke ji. "Ya ce, tare da ƙoƙarin ficewa.
"Kan ka ake ji. Mahaukaci ya faɗa rijiya ya ce "Kan ku ake ji ni wankana nake yi. "
"Hmmm. Sai da safe." Ya ce yana ƙoƙarin ficewa.
Ƙunƙunai ta yi wanda bai ji me ta fadi ba, don haka ya fara ƙoƙarin ficewa a ransa yana addu'ar Allah ya sa kar ta ƙara ɗago wata maganar kamar yadda ta saba, gamakin sa sai ya ji ta mike da sauri ta nufo gurin sa da yake ƙoƙarin fita.
"Ai na manta ni jikar mantau. Dawo maza Adamuu. Zo ga yar'uwar bakuwar turai ma za shiga ku gaisa. "
Ajmal ya tsaya da takaicin abin da ta ce. "Haba da tsawon dare nan, zaki ce na gaisa da ita? Dare ya yi ki bari sai gobe. Ba ni da lokacin ta. "
"To sannu agogo sarkin ƙa'ida. Ai dama na san ba'a abin arzikin da kai. Yar gidan Anty ka Halimatuu ne fa. Kar ka manta duk da bazarta kuke rawa, shi kan shi uban na ka da wa yake taƙama in ba da ita. Arzikin ta ka ci na daina fadarda nake maka, tana hutun gajiya bana son na tashe ta." Ta dasa aya cikin murya mai raɗa kamar wacce ta shinfiɗar da jaririn goye.
Ajmal ya yi tsaye sororo. Tabbas ya saba da gorin Hajiya Baaba, amma na yau da ban ne. Yarinya ƙarama take son ya je ya gaisar? Haba wuce nan. Shine har da yi masa gorin ba. Take ya ji wani tsanar Jannah ya kama shi matuƙa.
"Ki san kalaman da za ki furta mini, kuma wallahi kika sa ta raina ni, karya ƙasusuwanta zan yi kin san ban ɗaukar raini." Yana fadin haka ya fice daga ɗakin har yana haɗawa da gudu, yana jin lokacin da take fadin,
"To sannu ubana ko mijina. Ai gidan nan duk wanda ya so zaman lafiya dole ya yi wa Jannatuu biyayya."
Komawa ta yi ta zauna tana bambamin ta tare da kunna rediyon.
"Su kuma waɗannan 'yan rashin mutuncin cigaba da labaren su ka yi ba su jira ni ba."Ta faɗi tare sa kallon agogo, inda ta ga sha ɗaya da rabi.
"Oh ni jikar maigishiri! Haka lokaci ya tafi wancan mara mutuncin ya tsare ni da surutu zai ja mini makara gobe, ga shi ina da tashin asuba na badawa shalele girki, koda yar gwadashin ba dole ta ci ba. Miƙewa ta yi tare da kashe wutan falon ta fara tofe-tofen addu'a wanda ya zame mata ƙa'ida.

Jannah na kwance cikin bargo tana sharan bacci ba tare da ta san wainar da ake toyawa a falo ba, kasancewar tun takwas da ta shiga yin sallah ta yi mata sallama bacci take ji.
Yanayi garin ya yi mata daɗi sosai kasancewar duk da babu room heater a ɗakin amma yanayin ya yi mata dadi don babu irin sanyin London.
Ba ta tashi ba sai da aka kira sallah. Shi ma karar ƙwanƙwasa ƙofar Hajiya Baaba ya tashe ta.
"Ta shi ki yi sallah. Malalaci shi ne ya ke barin jam'i ta wuce shi."Ta ce tana buga kofar ɗakin da karfi.
Miƙa ta yi da salati tare da kunna wayarta. Karar tsakon mom ya shigo da ga kunnawa, wanda dalilin kiran da ta dame ta da shi tun a jirgi ya sa ta kashe wayar.
"Na tashi Hajiya Baaba! "Ta furta cikin murya kaukausa ganin kiran sallar farko ne ta tashe ta.
"Ma za ki yi nafila ki roki Allah ya ba ki miji na gari. "
Tsuka kawai ta yi jin abin da ta faɗa. Ta koma ta kwanta duk da ta san ba lallai ba ne ta koma baccin.
"Akan miji kika tashe ni cikin tsakar daren nan, sai kace ba ni da buri da ya wuce na aure. Ko guda nawa nake da za ki yi mini maganar miji oho. "
Komawa ta yi ta kwanta sai da ta ji limami ta tada sallah san ta janye bargo ta shige bayi tare da sauro alwala, bayan ta bata lokaci gurin wanka, don a lokacin har an sallame sallah.
Tana idar da sallah ba ta yi azkar ba ta ta koma ta yi kwanciyarta, tare da saka earpiece a kunnin ta don kar ta dame ta. Season na Korean film take kallo mai dadi mai suna penthouse.
Hajiya Baaba ta yi kiran duniya da ƙwanƙwasa kofa akan ta so ta karya ta ƙi fitowa har sai da ƙarfe goma da rabi ya yi.
Ranta ya yi matuƙar ɓaci don ita ta ɗauka bacci take yi. Tun asuba ta gama dama mata koko, kosai kuwa bakwai dai-dai Talatu kai nika an soya, amma sai watsa mata kasa a ido ba ta fito ba yanzu.
Tana murɗa kofa ta fito ta kwashe da dariya ganin yadda ta zauna a kan kujera ga abin karya ta tasa a gaba tana kallo.
COMMENT,READ FOLLOW AND SHARE.






Labarin ya zo da wani irin salo da nishadi, karku baru a ba ku labari. Ku biyo ni domin it’s just like a little introduction part, and guess what? You will really enjoy it. Believe me, my dear readers. Your happiness is my concern. Follow me on Facebook, Whatsapp, Wattpad, Arewaboo, and Bakandamiya. Ta ku, Jamila Lawal Zango (Jamsy).

FOR WHATSAPP: 08144072423
CALL: 07072971093







Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/LQfVU1ABdFI14btWRhUB1K






*KURA DA FATAR AKUYA*



*RUBUTAWA:-*
*JAMILA LAWAL ZANGO*

*SADAUKARWA GA:-*

*BADAMASI (AUTA)*

FIRST CLASS WRITERS ASSOCIATION
(Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation?)






Ban yadda a juya mini labarina ta ko wace siga ko karantashi ba tare da izinina ba. Aikata hakan zai sa mutum ya fuskanci doka.





*PAGE 6-7*



BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHEEM




Tana murɗa kofa ta fito ta kwashe da dariya ganin yadda ta zauna a kan kujera ga abin karya a gabanta.
"Ungo nan! Na ce ugo Jannatu. Uwarki kika yi wa banza ba ni ba."
Ƙarasowa ta yi ta zauna kusa da ita tare da rungumeta. "Haba tawan ni kaɗai, kin san bamu faɗa. "
Murmushi ta saki tare da kama hannunta. "Ke kaɗai na damu dake, amma kika wulakanta ni. Kusan awa ɗaya ina buga kofarki. "
"Hajiya bacci na ke yi fa. "Ta faɗa a sangarce cikin muryar shagwaɓa jin abin da ta ce.
"Kai dai rashin zaman Halimatu ya sa ta yi sakaci da koya miki addini? "Ta faɗa cikin razana da mamaki.
Sai ta ɗora da cewar, "Ko karatun kur'ani ban ji kin yi ba, kamar yadda muka saba a gidan nan, sai kika koma bacci kika rinka shafa bacci kamar rago. "
Haɗe rai ta yi jin abin da tace. A ranta take tunanin ina mom take da lokacin ta ballantana ta koya mata karatu, gara ma dad shine ma yake dan ƙoƙari har ta ita haɗa baki a gurin sa.
"Aiko da sake. Yaran gidan nan duk sun sauke kur'ani da hadda ke kina nan. "Sai kuma ta kaɗa kanta tana faɗin,
"Halima Allah ya yi mace mai taurin kai, ni da ubanta sam bamu da wannan zuciyar ta rashin yafiya. Haka kawai

Please Login or Register in order to submit comment