Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ya mutu da ƙyar ya miƙe.

"Ba ya wuce rigimarta kin san yanzu kamar jaririyar goye take, in kika ga birgimar da ta yi sai kin yi mamaki." Ya ce tare da miƙa mata hannu da alamun ta zo, wanda ta noƙe.

"My dougher is crying I most go and check on her." Ta ce tare da gyara zaman rigarta.

Tsaki ya yi yana sakkowa daga kan gadon.

"A taƙaice ta hana mu samun lada?"

Gwalo mom ta yi masa ta fice tana dariya wanda ya biyo ta cikin kasala murmushi ɗauke a fuskarshi.

"Keeeeee! Ba na son iskanci, ina karatuna za ki sa uban ƙara sai ka ce wacce ka tsire, wallahi sai da na firgita. Uban mene ne?" Ba ta ko kalli Hajiya Baaba da take faɗin haka ba ta ci gaba da kukanta.

Dad da ya sauko ya kamata ya riƙe.
"What happen? Kin ci abinci wa ya taɓa mini ke?" Ya ce cikin tsigar rarrashi wanda ya sa Hajiya Baaba ta yi tsaye cikin baƙinciki ta na jin kamar ta kifa masa mari.

"No, I wanna go and take my food in the kicin, shi ne na zo wucewa Anty Nahlin ta mini dariya, kuma dama na ji suna mini dariyar za a aura mini tsoho."

Da sauri su Nahlin da Ummu suka zare idanunsu cikin tsananin mamakin jin sharrin da ta yi musu.

"To don ubanki da ta harare ki ciwo kika ji, ko ina hararar ta maƙale miki za ki haukata mutane da ƙarar ki kamar gyare?" Hajiya Baaba ta furta cikin ɓacin rai wanda ko kallon arziki ba ta samu ba ballantana ta yi tunanin za ta amsa mata.

Mom kuwa da dad kallon junansu suka yi suna baƙincikin ɓata musu yanayin da suke ciki.

"Tsoho, Ajmal ɗin ne tsoho? Ke Nahlin kika ce mata Ajmal tsoho?" Cewar mom cikin mamaki.

Nahlin da mamakin sharrin da ta yi mata ya cika ta sai tafa hannu take tana salati ta kasa cewa komai, domin ta daina shiga sabgarta tun jiya da ta kalleta ta zabga mata harara har da murguɗe ya sa ta kama kanta don ba ta son rashin kunya.

"Ƙarya ne ba tsohon bane? Mutumin da har ya yi aure da mata ai tsoho ne." Ta ce tana jan majina cikin zallar sanagarta.

"Ko da sanda yake tafiya da ita sai kin aure shi ja'irar banza kawai." Hajiya Baaba ta furta tare da tsakin tsaki ta koma kujera ta zauna.

"Ki yi shiru muje ki zauna zan yi mata faɗa." Mom ta ce tare da kama hannunta wanda ta wafce ta riƙe dad tana faɗin,

"Dad, am sterving." Kama hannunta ya yi yana faɗin,

"Ok, lets go and eat." Abincin ya zuba mata da kan shi ya ɗauko tana biye da shi a bayansa tamkar jela. Ya ije abincin akan dining tare da fara ba ta a baki tana ci tana danna wayarta duk wanda ya yi nasarar kallonta sai ta balla masa harara.

"Kai innalillahi wa inna ilahir raju'un! Ni kam ina ganin taɓara da sangarta. Wai shin arziki hauka ne da kuka mai da yarinyar nan kamar wata 'yar goye? Irin tarbiyar da na ba ki kenan Halimatuu? Wallahi da irin ta ne tuni Jabiru ya sake ki. Kun ɓata yarinya kun sagartata kun mayar da ita taɓararriya. Kun san Allah ku kiyaye ni domin in kuka ci gaba da haka, tsaf zan sheme ku har da Jannah."

Ta ja tsaki za ta shige ɗaki tana faɗin,"Adamuu, ka yafe mini domin na haɗaka da masifa da bala'i."

Mom da dad babu wanda ya yi magana sun san gaskiya ta faɗa, amma ba za ta gane ba ne, domin ita ce 'ya ɗaya tal wanda Allah ya mallaka musu in ba su kula da ita ba wa za su kula da shi.

Ɓata rai ta yi tana kallon ƙofar da Hajiya ta wuce bayan ta rakata da harara.

"Dad,"

"Do eat your food don't nagging." Ya ce da sauri tare da kai saka mata loma yana tunanin mood ɗin da ta ɓata mishi, sai ta ci gabada tauna abincin kamar an mata dole.

Washegari da safe mom ta shirya ta sauko ƙasa za ta wuce aiki ta tsaya turus tana kallon Hajiya Baaba da ta tsaye da jaka riƙe da kwankwaso.

"Lafiya Hajiya Baaba, na ɗauka tafiyar jibi ce?"

"Ban sani ba, yau na ga damar komawa gida." Ta ɓata masa cikin ɗaure fuskar da babu hanyar da za ta gani ta yi musu.

"Amma Hajiya Baaba, da kin bari sai gobe saboda jirginku na jibi na yi reserving."

"Kin san Allah? Yau in kika ga na ƙara kwana a gidan nan sai dai ba ni iya tafiya, amma ko a ƙafa sai na koma gida."

"Hakan ba zai taɓa fauruwa ba dole na san yadda zan yi." Ta ce tana ƙoƙarin kira a wayarta daidai lokacin da ta ce,

"Haka kawai, sai na zauna baƙinciki ya kashe ni. Ba ki da lokacin da za ki yi hira da mutane, sai dai wuni mutum ya yi ta kallon tibi, salon idanun su makance da wuri. Ga yar banzar yarinyarku da ku ka sangartata ba ta kallon kowa da gashi ta hana mutum saƙat da koke-koke. Gara na koma gidana zaman can yafi mini, in lokacin bikin ya yi kwazo ayi akai masa tsiyarsa."

Mom dai ba ta ce komai ba har aka ɗaga wayar da take kira ta yi magana sannan ta kashe.

"Ki ɗan jira zuwa rana sai ku wuce bari na sa a haɗa muku tsarabarki. Su Nahlin su bari sai an janye strike sai su dawo har da su Janna..."

"Jann me? Kin san Allah ko aljannah take karki sake ta dawo mini gida, domin ni da ita mun yi hannun riga mara mutunci kawai. Ai na yi muku tsawon shekarun da na yi tana gaza mini gyaɗa a hannu ya isa. Ku da kuka ɓatata can muku na gaji a sakin mini mara na yi fitsari."

"Ni ma ba dawowa zan yi ba, ni da gidan ki ko a ƙiyama in ana ziyara ba zan zo ba."

Jannah da ta fito da waya a hannunta ta ce ba tare da ta kalle ta ba ta wanda ita ba ba ta tanka mata ba domin ba ta da lokacinta.

Da misalin ƙarfe huɗu jirgin Hajiya Baaba ya ɗaga wanda Jannah tafi kowa murna a gidan domin gani take kamar babu wanda ya isa ya biyo ta har gida ya yi mata auren dole. Karatun ta ne kawai ta ke jin babu daɗi na transfer da za a yi mata saboda ƙawayenta da sabon da ta yi da su. Ummu kuwa dama ba wani harkanta take shiga sosai ba, tun da ta yi mafarkin ta yi mata dariya wai za ta riga ta aure ta ɗauke mata wuta.

Zaman na su sai ya yi babu daɗi ko kaɗan domin kowa harkar gaban shi yake yi. Su kansu su Ummun ba wani daɗin hutun suke yi ba duk da cewar ga komai nan sai dai cuci su sha su yi kallo, amma fa mom ba ta da lokacin su har gara dad ya kan yi ƙoƙari ya gansu kafin ya tafi aiki, da in ya dawo, amma mom sai ta yi kwanaki ba su sanya ta a idanunsu ba, domin da wuri take fita har gara Nahlin da take ɗan tashin wuri.

Su Bala da Mudi tuni suka kama kansu cikin murna suka tafi ganin yadda mom ta cika su fa abin arziki da jari mai nauyi, wanda suka yi matuƙar jin daɗi da alƙawarin wa kansu dawowa bayan wani lokacin, domin sun ga gurin zuwa.

Washegari da safe suna zaune a falo kowa na harkar gabanshi. Dukanninsu waya ce a hannunsu wani ni lokacin su duba wayarsu wani lokacin su yi kallo, amma babu mai ko tari a tsakaninsu.

Mom ce ta fito tana janye da troley cikin maroon ɗon abaya ta yi kyau sosai tamkar ka saceta ka gudu.

Murmushi ta yi lokacin da suka ji ƙarar saukkowarta suka kalli saman benen
"Nahlin, Ummu, Jannah, tafiya ta kamani zuwa cameroon kuma I think I will stay long, akwai komai da kuke buƙata duk abin da kuke so babu ku kira ni ko ku yi wa masu aiki magana. Da fatan za ku kula da kanku?" Ta yi musu tambayar yana nazarin fuskokinsu.

Ummu da Nahlin suka ɗaga kansu amma Jannah ko alamun da ita take magana ba ta yi ba ta ci gaba da danna wayarta.

"Jannah, I w.."

"Oh please mom! I heard you. If you like go to heaven I don't bloody care, since my dad is around." Ta ce cikin ɗaga murya ta ci gaba da abin da take yi.

Shiru ta yi tana kallonta sai kuma ta miƙe tana hamdala da ta riga shi tafiya domin ba ta san wainar da za a su toya ba, matuƙar ta ji zai yi tafiya kuma sai ya daɗe sosai donnsai gabda zaɓe zai dawo.

"To na tafi, Allah ya yi muku albarka."

"Amin." Ummu da Nahlin suka amsa ita kuwa miƙewa ta yi tana faɗin,
"This house is so boring." Ta haye sama kallon mamaki suka bi ta da shi.

"Wannan yarinyar fa ba ta da mutunci lokaci guda ta canza mini fuska, saboda mun zo gidansu. Na lura kallon banza take mana ba, wallahi zan mata mata ni ma ɗin ba kanwar lasa bane, kuma ta san gidan ubana ba abin rainawa bane." Cewar Ummu cikin ƙubula domin haushin shareta da ta yi take ji, tana ganin she didn't deserved that duba ga how very closely they are.

"Wallahi kuwa, ni kallon mamakin sharrin da ta yi mini nake kuma tai mursisi duk da na san kurace da fatar akuya ban yi tunanin ta kai haka ba.'

"Ƙyale mara mutuncin kawai! Ki barta maganinta zan yi. Ni Yaya nake tausayi yana zaman lafiya da matarsa za a kai masa fitina."

"Yayan za ki tausayawa ko ita? Ke ma kin san halin shi daidai yake da ita ba zai ƙyale ta ba, ƙaniyarta zai ci shi ma ba ƙyaleta zai yi ba. Kin san halin shi."

"Duka za ta ci kamar jaka wallahi ba ta da kunya ga kafiya da raina na gaba da ita, shi kuma zuciya da son girma."

"Humh, na ga yadda wannan aure da Hajiya Baaba ta haɗa zai yi wu kuma a zauna lafiya? Ita ma ta iya rigima."

"Ki barta sai sun kai ta lahira lokacinta bai yi ba, domin ta san ba alkhairi ta haɗa ba, dama ta ƙyale shi da matarshi mai hankali."

"To munafukai, duk na ji abin da kuka ce. Na ce kuna gulmata kun ƙaryata, yanzu mai za ku ce da na kama ku da kunnuwana."
Da sauri suka waiga suna mamakin ganinta a jingine da ƙarfen bene tana karkaɗa wayarta cikin isa da gadara.

"Ban sani ba, ai duk abin da muka faɗa haskiyane saboda mun zo gidanku kin gama raina mu har ki kalli idanun Anty Nahlin kice mata munafuka." Ummu ta ce.

"To malama kike so na kirata? Kuna ta wani gulma ba ku tausaya mini halin da nake ciki ba, ai duk na gane halinku kuma zan yi maganinku. Don kawai ina da wanda nake so ne da sai na yadda an yi auren kuga yadda zan wahalar da ɗan'uwanku na mai da shi tamkar almajirina na shishshuka masa rashin mutunci son raina sai na ga uban abin da za ku yi ku masu ɗan'uwa."

"Jannah, Anty Nahlin kike gaya ma haka?"

"Ki barta saman zan hauro na zane ta kuma ta san babu wanda zai ce mini komai."

"To mai ya hana ki ai gani a gabanki bismillah." Ta ce cikin tsiwa wanda ya tunzura ta ta fara hawa benen da sauri.

Ganin haka ta yi maza ta ruga ɗaki ta kulle ƙofa tana haki!




Labarin ya zo da wani irin salo da nishadi, karku baru a ba ku labari. Ku biyo ni domin it’s just like a little introduction part, and guess what? You will really enjoy it. Believe me, my dear readers. Your happiness is my concern. Follow me on Facebook, Whatsapp, Wattpad, Arewaboo, and Bakandamiya. Ta ku, Jamila Lawal Zango (Jamsy).

FOR WHATSAPP: 08144072423
CALL: 07072971093






KURA DA FATAR AKUYA



*RUBUTAWA:-*
*JAMILA LAWAL ZANGO*
(JAMSY)

*SADAUKARWA GA:-*

*BADAMASI (AUTA)*

FIRST CLASS WRITERS ASSOCIATION
(Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation?)






Ban yadda a juya mini labarina ta ko wace siga ko karantashi ba tare da izinina ba. Aikata hakan zai sa mutum ya fuskanci doka.





*PAGE 31-32*



*BOJUWA HERBAL'S*

*KAYAN CHAD ƘARSHE NE WAJEN GYARA MACE DOMIN ASALIN SAIWOWI NE NA ASALI WANDA BABU ALGUS KUMA BABU ILLAH GA LAFIYA*
*KI ZO KI GYARA, KI MAGANCE SANYIN DA YA BUSAR DA KE, KO YAKE SA KI FITAR DA ISKA TA GABA, KO RASHIN SON YIN MU'AMALAR AURE*
*GYARA GASKIYA NE SISTERS*
*KO KUNSAN DUKKAN MAGANIN DA YAKE SAUKAR DA NIIMA YA HADE MACE YAFI TASIRI IDAN AKA DAFA SHI?*
*KI TABBATAR KINA CIN KAZA, TATTABARU, DA AKE DAFAWA DA SAIWOWIN CHAD NA MUSAMMAN*
*A KARAN KANKI ZAKI JI SAUYI BARE KUMA...*😅

*080327733332*
*KU TUNTUBI SURAYYA DEE A WANNAN LAMBAR*.
*DAN SON ANNABI SAI KINSAN KIN SHIRYA ZA KI YI GYARA*.
*NA GODE*



*Contact*
*Bojuwa HERBAL'S*
*For all your kayan mata and maganin sanyi original for women of class*.
*08032773332 Whatsapp only.*



BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHEEM
Ganin haka ta yi maza ta ruga ɗaki ta kulle ƙofa tana haki." A tunaninki bari zan yi ki duke ni? Muguwa kawai." Ta ce cikin tsoro.

"Matsoraciya ai da kin tsaya ki ga yadda zan yi ƙasa-ƙasa dake." Cewar Nahlin cikin ɓacin rai.

"Ga rashin kunya sai shegen tsoron tsiya, ai ni addu'a zan yi Allah ya sa auren nan ya ƙullu, ko don ya koya mata hankali ta rinƙa girmama mom." Ummu ta ce suka ci gaba da kallo.

Tun da ta san tsiyar da ta shuka ba ta sakko ƙasa ba ko da ta ji yunwa frij ɗin dad ta buɗe ta yi ɓarnarta son ranta.

Tana kwance akan gadonsa gabakiɗaya ji take rayuwarta komai ya tsaya mata cak. Ko sallah ba ta tashi ta yi ba har sai da dad ya dawo sannan ta buɗe ƙofar ta faɗa jikinshi tana hawaye.

A tunaninsu wani ƙaryar za ta yi musu sai ta ba su mamaki don ba ta yi masa ƙorafin komai ba sai cewa da ta yi,
"Dad, I miss you." Ta furta tana riƙe da hannunta.

Ledar tsarabar da ya yi musu ya miƙawa kowa na ta sannan ya ije na Jannah yana ƙoƙarin buɗe mata robar ice cream.

Da kanshi ya fara ba ta sai kuma ya miƙa mata ya shige bayi don ya yi wanka.

Washegari da safe bai sakko ƙasa ba har sai sha ɗaya lokacin duk suna zaune a falo suna kallo.

Kwana biyu da tafiyar Hajiya Baaba, da mom duk sai gidan ya zama babu daɗi, domin tsoro yake ba su. Ko bacci za su yi sai tsoro ya kama su saboda girman gidan.

Zaman gidan sai ya yi musu babu daɗi domin shi kansa dad, sai dare yake dawowa, in bai fita da wuri bane ya fita takwas na safiya.

Ranar da ya cika sati ɗaya da tafiyar mom wanda ta gaya musu saura kwana tara ta dawo, suka cika da murna ganin an janye strike don haka suka fara shirin komawa Zariya cikin farinciki, ban da Jannah da take contemplating whether to stay or not, saboda ita kanta ba daɗin zaman gidan take yi ba.

Haka dai a ranar da aka yi call off ta wuni cikin tunanin ba tare da ta samu mafita ba, saboda hankalinta ya fi karkata da ta koma, amma in ta tuna auren sai ta ga gara zamanta a Abuja. In ta hanga a wata mahangar ta ga zaman kaɗaicin da take yi sai ta yanke shawarar gara ta koma Zariya duk abin da zai faru ya faru, saboda ko sun yi mata auren ita ce mai zaman ta ga yadda za a yi ta zauna.

Cikin wanann halin na tsaka mai wuya wanda take ganin rayuwarta yana gaba kura baya siyaki. Ta kwanta ba tare da ta samu mafita ba, tana ganin su Ummu suka haɗa kayansu cikin farinciki don har sun kira mom, sai dai rashin sa a wayarta ba ya shiga amma sun bar mata tsaƙon kar ta kwana na shirin tafiyarsu.

Cikin fargaba yake sakkowa da troley ɗinsa yana ja zuciyarsa cike da tsoron yadda zai tunkareta ya sanar masa da tafiyarsa.

Ilai kuwa ganinsa da jaka ya sa ta miƙe a zabure.
"Dad, traveling?" Ta ce tana kallon shi da idanunta har sun fara kawo ruwa.

Bai amsa mata ba har sai da ya sauko ƙasa ya riƙe hannunta suka zauna kan kujera.

"Eh Jannah, tafiya ta kama ni ban san da tafiyar ba, and I must go it is an important."

"No, you will no go anyway I know it is mom that send you."

"Haba Jannah, na gaya miki tafiya zan yi and I will stay a bit long." Ya ƙarashe maganar cikin tsawa domin ya san in ba haka ya yi mata ba zai sha fama da ita.

A maimakon ta saduda sai ta sanya kuka.
"Babu ind za ka dad, ita ba ta zauna ba kai ma ba ta barka ba, gabakiɗaya ta takurawa rayuwarka. Ga shi su Ummu za su koma Zariya sai a barni ni kaɗai a wannan ƙatoton gidan, ni wallahi ba zan iya zama ba, saboda yanzu I can't stay in loneliness, na saba za ma cikin mutane."

Dafe kansa ya yi cikin rashin dubara."So what do yo want Jannah? You know I must go cus na yi reserving flight ko so kike mom ta yi asara."

"Eh, Let her do. Ban damu ba in dai za ka kasance dani don ba zan iya zama daga ni sai masu aiki a wannan gidan ba."

"Am sorry but I have to go. nan da awaya ɗaya zai tashi I have to be hurry."

"I said you are not going anyway." Ta ce tare da riƙe rigarshi tana kuka.

Ransa ya ɓaci ya juyo ya kalli su Ummu da suka yi tsuru-tsuru suna kallonta.

"Nahlin, gobe za ku wuce ko? Mom told me that.I wished you safe trip and ku kula da karatu. Ga wannan mom ta ce a baku ku riƙe za ta yi booking flight na ku, sannan anjima direba zai kai ku shooping. Choose whatever you like it is on her."

"Ok, thanks dad, mun gode Allah ya ƙara buɗi."

Kallonta ya yi sai ya fisge rigarsa." Ba kya jin magana, karki manta ni mahaifinki ne, in na gaya miki magana you must obey haba you have to give me that respect I earned." Ya ƙarashe maganar cikin tsawar da ya firgita ta matsa gefe tana zare ido.

"Na gaya miki planning ɗina akan auren ki, amma you didn't agreed. Hajiya has power and authority that I can do anything than tha..."

"Leave me alone!" Ta ce tare da ƙara matsawa da fisge hannunta da ya yi.

"Na gane kai ma mom ta zuge ka da kuɗi, I understand that you were living in object puverty that's why mom manipulating you with money and make you like her errands boy. Your family are poor that is why you married mom to be rich. Saboda money sai ka kasa bani farinciki dad, ka na gani za a yi mini auren dole da wanda ba na so! Why did you marry mom becouse of money why dad?"

Sai ta fashe da kuka tare da durƙushewa.

"I love Huzaifah like crazy I want him to be my wedded husband, please do something."

"I'm sorry that I can't help, but you have to understand that my love to your mom is genuine."

"Isn't dad!"

"To shikenan, tun da ba kya jin magana you always do as you wish, sai ki je kiyi abin da za ki yi, kuma daga yau na cire hannuna akan maganar aurenki." Ya ce cikin fushi tare da ɗaukar jakarsa.

"Nahlin, ku gida gida zan kira in ji kun sauka lafiya." Ya kama hanya zai fita yana jin yadda kukanta ke ƙona masa zuciya.

"Ni ma zan bi su do the viser with me I can't stay alone." Ta ce cikin muryar kuka.

Jiyowa ya yi ya kalleta sai kuma ta ba shi tausayi ya kasa ce mata komai domin ya sani suna cutarta da yawa, ya yi tunanin dawowarsu zai ba ta farinciki, sai ga shi maganar aurenta ya taso wanda shi ne sanadin dagula komai, ba shi da zaɓi wanda ya fi ta koma gidan Aby ta amince da auren, domin zaman ta da rayuwarta acan sai ya fi mata fiye da nan da ba su da lokacinta.

"Shikenan, I will do the viser." Ya ce tare da ficewa ransa na ƙuna.

Nahlin da Ummu sai ta ba su tausayi sun sani duk wani abin da take yi da ɗaurin gindin iyayenta da suka yi sakaci da rayuwarta.

Kuka take sosai kamar ranta zai shiɗe tana ganin sam iyayenta ba su da buƙatar haihuwarta, wannan dalilin ya sanya da suka haifeta suka tsaida haihuwar gabakiɗaya,

Please Login or Register in order to submit comment