Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

da ka siyo ma Ummu duk abin da ka siyo mini, cus she is alot to me."


Sai ya yi dariya tare da miƙewa ya kama hannunta.


"Dad, ka ga yanzu tun da ka zo sai ka tsawatarwa Hajiya Baaba maganar auren da take mini I'm sick of it kullum maganarta kenan."


Gabansa ya faɗi sosai har sai da fuskarsa ta bayyana. Gyara zama ya yi sannan ya ce,

"Ki kwantar da hankali kin san Hajiya Baaba, suruka take a gareni, so I must speek to her politely kuma duka when I have arrived? At least I have to rest to tomorrow."


Ɓata fuska ta yi don ita ba haka ta so ba, saboda ta so daga zuwa ya zare mata ido da nuna iko akan dole ba za a yi auren ba. Miƙewa ta yi.


"Ok dad, amma ka san dole sai ka zare mata ido ka nuna isa a kaina, don wallahi ba ta da hali ta cika shiga hanci da ƙudundune. Haka kawai ina zaman zamana ta jawo mini bala'i da musifa."


Shiru ya yi ba tare da ya ce mata komai ba duk da cewar kallonta yake yana sauraronta, amma ba shi da abin da zai ce mata domin shi kansa tsoro take ba shi, musamman wani mugun kallo da ya gani kamar tana masa.


"Dad, you remember that you promised to me you will stand by my side?"



Ta tambaye shi cikin sauri ganin yadda ya canza fuskar tsoro, domin gabakiɗaya tun da ya ga Hajiya Baaba ya firgice, gani yake kamar za ta iya nasarar ra ba shi da Halima a karo na biyu.


"How could I forget. I had been counting the days, to come back and be by your side my girl."


Murmushi ta yi jin abin da ya faɗa." Amma dole ka nuna ba ka tsoronta wani lokaci.




Labarin ya zo da wani irin salo da nishadi, karku baru a ba ku labari. Ku biyo ni domin it’s just like a little introduction part, and guess what? You will really enjoy it. Believe me, my dear readers. Your happiness is my concern. Follow me on Facebook, Whatsapp, Wattpad, Arewaboo, and Bakandamiya. Ta ku, Jamila Lawal Zango (Jamsy).

FOR WHATSAPP: 08144072423
CALL: 07072971093


KURA DA FATAR AKUYA



*RUBUTAWA:-*
*JAMILA LAWAL ZANGO*
(JAMSY)

*SADAUKARWA GA:-*

*BADAMASI (AUTA)*

FIRST CLASS WRITERS ASSOCIATION
(Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation?)






Ban yadda a juya mini labarina ta ko wace siga ko karantashi ba tare da izinina ba. Aikata hakan zai sa mutum ya fuskanci doka.





*PAGE 24-25*



*BOJUWA HERBAL'S*

*KAYAN CHAD ƘARSHE NE WAJEN GYARA MACE DOMIN ASALIN SAIWOWI NE NA ASALI WANDA BABU ALGUS KUMA BABU ILLAH GA LAFIYA*
*KI ZO KI GYARA, KI MAGANCE SANYIN DA YA BUSAR DA KE, KO YAKE SA KI FITAR DA ISKA TA GABA, KO RASHIN SON YIN MU'AMALAR AURE*
*GYARA GASKIYA NE SISTERS*
*KO KUNSAN DUKKAN MAGANIN DA YAKE SAUKAR DA NIIMA YA HADE MACE YAFI TASIRI IDAN AKA DAFA SHI?*
*KI TABBATAR KINA CIN KAZA, TATTABARU, DA AKE DAFAWA DA SAIWOWIN CHAD NA MUSAMMAN*
*A KARAN KANKI ZAKI JI SAUYI BARE KUMA...*😅

*080327733332*
*KU TUNTUBI SURAYYA DEE A WANNAN LAMBAR*.
*DAN SON ANNABI SAI KINSAN KIN SHIRYA ZA KI YI GYARA*.
*NA GODE*



*Contact*
*Bojuwa HERBAL'S*
*For all your kayan mata and maganin sanyi original for women of class*.
*08032773332 Whatsapp only.*



BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHEEM

"How could I forget. I have been counting the days to come back and be by your side my girl."


Murmushi ta yi jin abin da ya faɗa." Amma dole ka nuna ba ka tsoronta wani lokacin she is so disgusting."

"Ok, I will Jannah, yanzu ya kamata ki je gurin mahaifiyarki ku yi hira domin ta yi kewarki sosai.


Miƙewa ta yi." I'm very exhausted I wanna rest, goodnight." Ta ce ba tare da ta ba shi amsar tambayar da ya yi ba.


Bin ta da kallo har sai da ta ɓace bayan ya ɗaga mata kansa yana murmushi. Mayar da kansa ya yi ya shiga duniyar tunani.



A falon Hajiya Baaba suna zaune suna hira bayan Aby ya yi musu sallama ya fice Hajiya Baaba ta kalli 'yarta cike da so da ƙauna.


"Ni kam Halimatu kin yi sakaci a rayuwarki, sam Jannah ba ta damu da ke ba. Tun da kuka zo take naniƙe da mahaifinta, amma kallon banza ba ki ishe ta ba."


Kanta ta shafa cikin tsananin baƙincikin hakan. Idanunta suka kawo ruwa sai ta yi maza ta goge da gefen hannunta.


"Na san cewa na yi kuskure a rayuwata na rashin kula da 'yar da na haifa, idan da ace ana maida hannun agogo baya ba zan barwa masu aiki alhakin kula da ita ba. Zan ware lokacina na kula da ita sai dai bakin alƙalami ya bushe, domin tamkar maƙiyarta haka ta ɗauke ni wanda hakan na mini ciwo kasancewa ita kaɗai na haifa."



"Daga baya kenan halimatu, wane irin jan kunne ne ban yi miki ba, amma ki ka ɗauki ɗabi'un yahudu kika ɗora wa kanki, ba ki da lokacin kanki ballantana na ta. Abin takaici kika gudu da ita duk akan banzan dalili na ƙi wanda kina da ikon kawo ƙarshen matsalar. Ai ni wallahi kin bani mamaki. Haihuwa sai dai kika ana yi ita ɗaya Allah ya ba ki, kuma kin ɓata rawarki da tsalle gurin tarbiyarta."


Hawaye ta share waɗanda suka zubo mata ba tare da ta sani ba."Na yi sakacin da babu gyara."


"Sakaci babba ma kuwa, domin Jannah ta buwayi kowa. Kin san yadda nake da iko a gidanan ba a isa na shata kara ba a tsallake, amma ina saka ɗauka take ta karya shi, ga shi nan yaran gidan gabaki ɗaya sun raina ni."


"Ki yi haƙuri hannunka bai ruɓewa ka yanke ka yar."


"Haƙuri ya zam dole amma kin san ko ku da kuke 'ya'yana kuka yi mini saina ɗau hukunci a kanku. Wannan dalilin ya sa zan haɗa aurenta da Adamuu domin shine kawai maganinta, sannan na rama abin da kuka yi mini na auren waɗanda ba na ra'ayi sai kuji zafi da raɗaɗin da na ji."


"Haba Hajiya, sau nawa za mu baki haƙuri akan haka? Don Allah ki manta komai ya wuce. Ina lura da kallon da kika yi wa Injiniya, gabaki ɗaya raina ya ɓace shi ɗin fa mijin.."


"Rufe mini baki.. Har yanzu kina nan kina wahalar da kanki a kansa duk abin da ya yi miki? Ke kam soyayya ba ta amfanar dake komai ba. Kin dai rako mata duniya wallahi."


Shiru ta yi tana girgiza kanta sao kuma ta buɗe ba ki za ta fara magana ta katseta.


"Ke ni ba wannan ba, maganar auren Jannah shine a gabana, ba na son a ja da nisa kafin ki tafi Abuja a sanya rana kawai."


"Hajiya Baaba, don Allah karki shiga cikin rayuwar Ajmal da matarsa. Suna rayuwarsu cikin farinciki don Allah karki tarwatsa hakan. Kuma Jannah ba ta son shi, tsarin rayuwar..."


"Kin san Allah Halimatuu, in kika ga ba ayi auren ba mutuwa na yi babu fashi, in kuma ba kwa so sai na sha guba na mutu ku huta."


"Subuhallahi! Ba ta kai nan ba Allah ya ba ki haƙuri."


"Haƙuri kayana ai sai an cuce ka ake ba ka shi."


Shiru ta yi ba ta ce komai ba sai Hajiya Baaba ta kalleta ta ce,"A cikin gidansa nake son ta zauna don karya je ya ije mini ita a wani guri can, so nake ta zamo mowa a zuciyarsa.


Kallonta ta yi tana mamakin ƙarfi hali irin na ta."Ba komai duk yadda kika ce za a yi. Shi Ajmal ɗin ya nuna yana so.."


"Adamun banza shi a suwa da zai ce ba ya so. Na ga lokacin da kuka yi auren ku ina so ne?"


Girgiza kanta ta shiga yi ba tare da ta ce komai ba domin lamarinta ya fi ƙarfinta.


"To kamar haka yadda kuka yi mini ƙarfa-ƙarfa zan yi musu."


"Allah ya sanya alkhairi ya kuma ba su zaman lafiya." Ta ce sai kuma ta gyara zama tana kallonta da ta amsa da amin cikin sauri tana harare-harare.


"Zan yi magana kan kayan ɗakin da duk abin da ya shafi biki." Ta faɗa cikin rashin karsashi.


"Mom, is what I heard coming from you? The you mean you support her?"


Ta ce cikin ƙara domin tun da suke maganar ta ke jinsu sakamakon ɓoyewa a bakin ƙofa da ta yi.


"Calm down, you need to understand m.."

"Understand what mom? No it shouldn't be happened da bakinki kike maganar aurena as my age. To bari kiji na rantse miki babu wanda ya isa ya yi mini auren dole we have passed that era."


"Aikin banza don ihu kike bayan hari aure sai dai ki ɗauki haƙuri da azaman yin biyayya don kin san kalar mijin ya jibge ki ba farau bane a garesa."


Ihu ta sa tana girgiza kanta." Kin ga Hajiya Baaba ba dake nake magana ba, domin tun da iyayena suka dawo babu ruwana dake."


"Au haka za ki ce, bayan na gama miki amfani ko?"


"Dad." Ta furta da ƙarfi tare da yin sashin da yake wanda har bacci ya fara kamasa.


"Muje ka gaya mata ba za ka amince da auren nan ba domin she is frustrating me da maganar."


Zare ido ya yi sai kuma ya kalli agogo."Please ki je ki kwanta za mu yi maganar sa safe.."



"No way." Ta katse shi tare da kama hannunsa tana ja.


"You must go and tell her, so that she will not be pestering me."


Jikinsa babu ƙwari ya bita har zuwa falon da murya Hajiya Baaba kawai ke ta shi.


Wani banzan kallo ta watsa mishi lokacin da ya shigo.


"Ai ni na ɗauka 'yan sanda za ki ɗauko mini sai kika tsaya anan, to sai ya ɗauko bulala ya zane ni."


"Ki yi haƙuri ba ta kai nan ba, amma don Allah ya kamata abi abun.."


"Ya kamata mene? Kai Jabiruu kake ko mene? Wallahi ka fita idona tun kafin na shuka maka rashin mutunci, domin ka san ina da cikinka na tsawon shekaru."
"Allah ya ba ki haƙuri."


"Oho, ko ma me za ka ce ka faɗi aure dai babu fashi, in kuma za ku nuna mini iyakata bismillah."



"Dad, ka na nufin kai ma ba ka isa da kanka ba sai abin da ta ce?" Ta yi mishi tambayar cikin tsananin mamaki.


"Ba ki san cewa ni dakali ba ne dole a zauna dani. Ai girman kenan tun da na haife su ai dole abi umurnina."


"Ina wallahi ba zan yadda ba ina ji ina gani ayi mini auren dole." Ta ce tare da kai wa tibin bangon falon duka, wanda nan take gilashin ya tarwatse hannunta ya fashe.


Sai kuma ta sanya kuka ta na jin yadda zafin raɗaɗin ciwon yake tasowa yana bin duk ilahirin jikinta.


"Wallahi ba na son shi. Ko a duniyar mafarkina ban taɓa tunanin auren mutum irin sa ba. I really hate him please dad do something if not I gonna die. How can I marry a such person like him?" Sosai take kuka ta faɗa kansa wanda hakan ya sa ya ji tausayinta ƙwarai to amma ya zai yi.


Kamota ya yi a hankali ya miƙar da ita ya zaunar da ita har zuwa lokacin ya rasa kalmar da zai rarrasheta da su, saboda sam baya ƙalubantar auren domin auren miji kamarsa ba ƙaramin tagomashi Allah ya yi mata ba.



"Hajiya Baaba, na san na saɓa miki arayuwarki kuma na yi butulci amma don Allah ki bari ta gama karatu kuma su fahimci juna, kin san suna da bambancin ra'ay.."


"Au wa'azi za ka fara ai ban sani ba, amma da ka je masallaci ka hau munbari domin an fi buƙatarka. Har kana da bakin da za ka yi wa wasu wa'azi?"


Sunkuyar da kanshi ya yi lokaci guda hawaye suka fara turereniya akan fuskarsa da take cike da haiba da kamala, yayin da yake nadamar abubuwan da suka faru a baya.


Cikin tsananin tashin hankali ta nufi inda Hajiya Baaba take tana girgiza da huci domin wani mugun haushinsa take yi kamar ta shaƙe shi in ta nuna irin abubuwanda ya aikata ya zama kura da fatar akuya..


"Ban san wane irin mutum ce ba kin takurawa kowa kin hana mu sukuni bayan kin ci lokacinki babu wanda ya takura miki, ba sai muna cikin rayuwarku za ku takura mana ba?"


Sai ta kama hannun dad ta riƙe cikin ɓacin rai ganin yadda yake zubar hawaye.



"Ka saki mom ka ƙara aure mu yi rayuwarmu cikin farinciki I hate them dad."


Gabkiɗayan su suk zaro ido har da su Aby da hayaniyar ya sanya suka shigo.



"What! Are you insane? Mahaifiyarki kike gaya wa mahaifinki ya sake ta? Cewar Nahlin kamar ta tsinka mata mari.


"Yes I do. Auren su babu abin da yake ƙara mini sai baƙinciki don haka rabuwarsu ya fi, kin ga sai na ga uban da ya isa ya yi mini auren dole."


Mom wacce tun da jannah ta ji ciwo take kuka sosai damuwarta jinin da yake zuba a hannunta.


Kau ta wanka mata mari."Ki iya bakinki in kika yi mini rashin kunya na ɗauka ba zan lamunta gareta ba." Ta faɗa cikin kaukausar murya.


Rintse idanunta ta yi."Ni dai wataƙila ba zan taɓa samun farinciki ba, ga shi na gudu don na yi farinciki amma kuma na dawo an ɗora daga inda aka tsaya."


Sai ta ƙara sakin kuka ta nufe ta."Mu tafi asibiti jini kika zubarwa."


"Fisge hannunta ta yi cikin kuka."Go away, I hate you." Ta ce tara da riƙe hannun dad.



"Taɓɗijan! Lallai kin yi sake Halimatuu. Auren ta da shi shine kawai maganinta domin ya ci mini ƙaniyarta in ya so ya kakkarya mini ita akawo ba su Binbo ƙasusuwa."



Wani mugun kallo ta yi mata tare da jan majina daidai lokacin da dad ya kamata hannunta suka fita daga falon.


"Kai Jannah an yi fitsarrariya." Cewar Hajiya ta galla wa mom harara ta shige ɗakinta.


Faɗawa jikin Aby ta yi ta fashe da kuka."Haƙiƙa Allah ka jarabce ni! 'Yata ɗaya tilo take sanar da mahaifinta ya sake ni ya auri wata? Ni kam mai na yi wa duniya take gara rayuwata kamar ƙwallo."


"Ki yi haƙuri Halimatuu, ka da ki yi saɓo." Ya furta tare da kama hannunta suka yi sashinsa.


A sashin Ajmal dad ya zaunar da ita cikin ɓacin rai ya kalle ta sai kuma ta ƙara ba shi tausayi, amma da ya tuna kalamanta zucigarsa ta ƙara tafarfasa.


"Haba Jannah, I really hate the way you talk to your mom honestly I dislike it you are so insolent to her."


Ya juya mata baya yana jin kamar ya mareta daidai lokacin da ta ƙara sakin kuka.



" So now, you gonna tell me you wanna side her? Tana jin munanen kalamai da mahaifiyarta take gaya maka amma she sat and looking her becouse ba ta ɗauke ka da mahimmaanci ba."



Kama hannunta ya yi ya riƙe yana ya rasa yadda zai yi ta fahimce shi domin ya na ganin aminta da auren shi zai daƙile bankaɗar da Hajiya Baaba take son mishi, wanda in har ta ji ya san daga ranar ba za ta ƙara kallonsa da daraja ba.


"I really don understand cus the whole situation is akward." Kuka sosai take yi sai kuma ta faɗa jikin shi ta ci gaba da cewa,


"Na tsane shi wallahi ba na sonsa ban taɓa hasashen rayuwa da shi ba, a kwai wanda nake so and we are compatible dad, please do something."
Idanunsa ya zaro cikin tsananin mamaki." So you mean you are dating someone without my awareness, how could you?"


Cikin jin kunyar abin da ya faɗa ta rufe fuskarta."Am deeply sorry dad, initially he was my best friend, but later I found him very valuable to my life and we fall in love. Mun haɗu ne a faling jirgi a ranar da na dawo Nigeria."


Sai ya yi shiru yana saurarenta da mamakin ɓoye masa da ya yi domin bai taɓa tunanin hakan ba.



"I said am sorry for hiding it, but ina son shi kuma he is well off haka iyayensa they are prosperous. In har ta nace na yi aure ta aura mini shi."


Sai ta yi matuƙar ba shi tausayi matuƙar gaske saboda yadda take maganar ya fahimci tana matuƙar son shi.


"But please stop talking to your mom in that manner, you shouldn't talked to her in that tongue."


Jin ta yi shiru ba ta ce komai ba ya fora da cewa,


"You have to go and sleep we will talk about it kin ji." Ya fada Yana shafa kanta.


Dukkan mutanen gidan ba su bacci cikin kwanciyar hankali ba sakamakon ko da abin da yake saƙawa a cikin ransu.


Washegari

Please Login or Register in order to submit comment