Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

*PAGE 11-12*



BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHEEM
"I hate her. My mom is so selfishness. Za ta dawo Nigeria saboda she wants to be a politician? Or my God! I can't imagine this. Bayan ta ki dawowa saboda umurinin mijinta da ni. Allah ban taba ganin maiyar kuɗi ba irinta. So take ta kwashi kuɗin gwamna..."
"Haba Jannah, duk waɗannan mugayen kalamai ga mahaifiyaki kike furtawa. Wannan fa cigaban ahalinmu baki ɗaya ne, ke da za ki yi murna za ta dawo kusa dake."
"No, I won't go. Na fi son na zauna a gidan, amma babu inda za ni don ba ta da lokacina. So am happy here."
Hararar sakin mata tare da miƙewa" You know what? I can't deal with your shit right now, and is this attitude of you that annoyed me."
"You don't know everything. You don't know her shi ya sa kike faɗin haka.
"Then disclose it to me, kinga.."
"No I don't have that time, abin da kawai na sani ba ta sona." Ta ƙarashe maganar cikin kuka.
Hajiya Baaba ta fito daga ɗakinta ta balla mata harara,"Ke dai wallahi anyi 'yar baƙinciki. Ni ban taɓa ganin yar da take wa uwarta hassada ba sai ke. To ta Allah ba ta ki ba, mahaifin na ki da kike so ya fi ta ba haka Allah ya so ba, sai dai ki mutu.
Miƙewa ta yi ta tura baki tare da zabga mata harara kamar idanun za su faɗo ƙasa.
Ɗaki ta ruga tare da kulle ƙofa tana kuka sosai. Numbar dad ta kira wanda bugu ɗaya ya ɗauka,
"Helle dad, is it true that mom wants to come back to Nigeria because of politics?"
Shiru ya yi kamar ba zai amsa tambayar ba har sai da ta kara maimatawa cikin ƙaraji.
"Oh yes but understand her."
"Haba dad, supporting her all the time, you don't have right in your house. Na tabbata in har ta fara siyasa, sai kayi watanni ba ka ganta ba. Please ka rabu da ita ka dawo Nigeria ka yi aure mu yi zamanmu da matarka, ta haifa mini ƙanni, saboda ita mom neman kuɗi ya sa ta ƙi haihuwa. Ni ɗaya kawai ta haifa kamar mayya."
Wani irin abu ya daki kansa mai kama da guduma. Ko kaɗan bai taɓa tunanin za ta yi ƙorafi game da rashin haihuwar mom ba. Idanunsa ya rintse yana jin anya in ta ji shine sanadin hakan za ta yafe masa. Take zufa ya keto masa har yana ɗiga a jikinsa.
"Haba Jannah, ya kamata.."
Ɗif ta kashe wayar tare da jifa da ita."Na rasa wane irin so yake mata ba wanda ya kasa yin wani abu a gidansa. Anya ba asiri ta yi masa ba, don ta juya shi son ranta." Ta tambayi kanta cikin ruɗu.
Har ta danna numbarta za ta kira sai kuma ta ga rashin alfanun hakan, domin tunda ta ce za ta yi babu wanda ya isa ya hana ta.
"Rayuwarta ne ta je ta yi kowa yana da ikon zaɓa ma kansa abin da yake so. Kamar yadda take rayuwara son ranta ni ma ba ta isa ta ba ni umurni na bi ba." Ta faɗa a hasale

Don haka ta cire abin a ranta tunna shi kansa wanda yake da iko da ita ya kasa komai ballantana ita da ba ta bata mahimmanci a rayuwarta ba.

Jannah na kwance wayarta ta fara neman agaji. Ganin numbar mom ya sa ta yi tsaki ta koma ta kwanta.
Tunawa da motarta ya sa ta zabura daidai lokacin da wayar ta tsinke. Tana ƙoƙarin kira kiran ya ƙara shigowa.
"Hello Jannah, motarki ta iso. In sha Allahu gobe yayanki zai ɗauko miki ita." Ihun murna ta saki sosai tana tsalle.
Maganar mom ɗin da take yi yasa murnarta ta koma ciki."Haba mom, kan me za'a hana ni driving? Ni gaskiya ba zan yarda ba."
Sauke ajiyar zuciya ta yi tana faɗin,"Kafin ki gama sakandiri ne, amma da zarar kin gama za ki fara tuki, kin san Nigeria ba kamar London ba." Kashe wayar ta yi tana gunaguni.
Hajiya Baaba da take ƙoƙarin shiga ɗakinta ta ja ta tsaya jin tana ta magana ciki-ciki."To 'yar gidan fitsara, jikar marasa kunya. Uban wa kike zagi, in dai ba 'yata ba?" Harara ta banka mata ta miƙe ta shige cikin ɗakinta sai kawai ta sa kuka.
A mota Aby ke nuna w Ajmal motar da zai ɗauko wa Jannah a Abuja. Tsananin mamakin motar da kyauta da tsadarta yake yi.
"Yanzu Aby wancan ficiciyar yarinyar mom za ta siya wa mota, kuma ta yi driving da kanta?" Ya faɗa cikin tsantsar mamaki.
"Kar fa ka manta mahaifiyarta wace ce. Kuma ita kaɗai ta mallaka."
Jinjina kansa ya yi, bai ce komai ba, wanda ganin hakan Aby ya ci gaba da cewa,"Ka ji maganar an tsayar da ita takarar minister ko?" Kallonsa ya yi sai kuma ya mai da hankalinsa kan tuƙi.

"Eh na ji kuma ta amince?" Ya ƙarashe maganar da tambaya.
Abby ya ce,"Ta amince da ƙyar, amma dad bai bata goyon baga ba, sai dai ka san in har ta amince babu wanda ya isa ya canza mata. Cikin satinnan zan je India na wakilce ta kan kasuwancinta."
Ajmal ya kalle sa yana faɗin,"Tana burge ni mace ce kamar maza, samun ta a ahalinmu abin alkhairi ne. Sai dai 'yarta sam ba ta ɗauko ɗabi'unta ba. She doesn't have table manners and she is so cheeky. Ga shi hajiya ta ƙarashe sangarta ta."
Aby da ya ji an tsokano masa inda ke masa ƙaiƙaiyi ya gyara zama yana faɗin,
"Yauwa, dama na bari ka dawo ne. Ka san yarinyar nan, ta daina zuwa islamiya? Har makarantar ta je ta mari malamin don ya duke ta."
Shiru ya yi, a ransa ya ayyana da zata iya fiye da haka, amma a fili ya ce,"Kai Hajiya sai addu'a. To yanzu bata zuwa kenan?" Aby ya ce,
"Eh, ta dage sai dai a canza mata wata makarantar, ko a ɗauko mata malami a gida. Kuma wallahi mahaifiyarta ta roƙe ni akan na bata ilmin addini. Don Allah ka yi wani abu." Ya yi shiro ko zaice wani abu, amma sai ya ga bai ɗauki maganar da mahimmanci ba, sai bin karatun kur'anin da ya kunna yake yi, wanda ganin hakan ya ci gaba da cewa,
"Ba zai yiwu na zura mata idanu ba, mahaifiyarta amana ta ba ni. Don haka dole na kula da ilminta kamar yadda zan kula da naku, kuma ko Halimatu ba ta da rai ni me riƙe ta ne. Daga yau na ɗora maka kula da ita."
Da sauri ya kalle sa jin aikin da yake son ɗora masa."Ni fa sam bana son shiga lamarin su, kasan Hajiya, ni kaina ba ta barni ba, da na yi magata zata fara mini gori a gabanta salon ta raina ni."
"Ya za ka yi, hakanan zaka jure ka yi don Allah, ai wani lokacin tana shakkarka " Jinjina kansa ya yi, don ya san aiki ne a gabansa.
Kasancewar ranar Juma'a suka yi maganar, don har ya manta a ranar sati, sai da ya ga Nahlin ta fito da zubbulelen hijabinta za ta tafi hadda ya tuna, har ta wuce shi ya dawo da ita ta hanyar ƙwala mata kira.
"Na'am Yaya, barka da hutawa." Ta ce tana ƙoƙarin ƙarasawa inda yake.
"Ke Nahlin ma za ki ce wa Jannah ta fito kuje hadda." Ta ɗan yi jin sai kuma ta ce,
"To." Ta juya sashin Hajiya Baaba.
Ta same ta a ɗakinta ta kunna waƙa sai tiƙar rawa take yi.
"Ya Ajmal ya ce ki shirya muje hadda." Wani banzan kallo ta yi mata kamar ba da ita take yi ba. Tsawa ta daka mata wanda ya sa ta miƙe tare da tura baki.
"Haddar me? Babu inda zani." Ta ce cikin ƙunƙunai.
"Oho, ni dai tsaƙo aka aiko ni." Sai ta fara buga ƙafafunta tana faɗin,"Ni fa Allah ba zan koma islamiyar nan ba, wannan ai salon a raina ni ne, ina babban yarinya."
Mugun kallo ta yi mata sannan ta furta.
"Ki iya bakinki, wallahi Yaya ba sa'an yinki bane. Don haka ki natsu ki san wanda za ki yi wa, in ba haka ba sai ya canza miki halitta."
Ta turo baki."Tun da ga ubana ba." Jinjina kai kawai ta yi ta fice, tana mamakin tsaurin idanunta.
Tana isa gurin shi da yake ƙoƙarin shiga mota."Ya ta ce ba za ta je b.."
"What?" Ya katseta yana tambayarta da ƙarfi tare da daka mata tsawa wanda ya sa ta matsa cikin tsoro. Fitowa daga cikin motar ya yi ba tare da ya kashe ba."Lallai yrinyar nan ba ta da kunya zan koya mata hankali."
Buga ƙofar ya yi da ƙarfi ya shigo ga mamakinsa sai ya ganta a falo da remote a hannunta tana canza tasha, wanda ganinsa ta fara ƙunƙunai tana turo baki.
Ajmal ya tsaya cikin mamaki yana kallonta aransa ya ayyana da zaginsa take ganin yadda bakinta ke motsawa. Cikin fusata ya ce,
"Ke zagina kike yi don ubanki?" Mari ya kai mata a fuska tauu! Wanda ta ji shi har tsakiyar ƙwaƙwalwarta. Ta takura iya ƙarfinta ta canyara ƙara tare da kiran sunan Hajiya Baaba, wacce ta fito da gudu har tana tuntuɓe.
"Na shiga uku! Shalele, maciji ya sare ki, ko kunama?" Turus! Ta yi tana ƙarashe ɗaura zaninnta ganin wanda yake falon.
Da gudu ta koma bayanta ta ɓuya. "Hajiya Baaba, ya kashe ni mari hamsin ya yi mini. Wayyo na mutu! Dadddyyy."
Hajiya Baaba ita kanta ta san ƙarya take yi domin da haka ne wataƙila da wata maganar ake ba wannan ba, amma saboda rashin son gaskiya ta kurma salati da ihu tana faɗin,
"Kan uba, uban me ta yi maka da za ka fara dukanta kamar ka samu jaka?" Ta tamabaye sa cikin tsananin ɓacin rai tana girgiza.
"Gaya masa Hajiya Baaba, ko iyayena ba sa duka na ballantana wani ban.."
Ransa ne ya ɓace lokaci guda idanunsa suka canza zuwa wani kala, ganin tana shirin zaginsa a gaban Nahlin wacce ko magana yake ba ta iya kallon shi, sai kawai ya zare belt ɗinsa ya shiga zuba mata ta ko ina kuma iya ƙarfinsa.
Cikin azama Hajiya ta kai masa cakuma tana faɗin,"Ai ko yau sai na ga uban da ya tsaya maka da za ka duke ta."
Ture ta ya yi har ta buge da center table, amma ko kula ta bai yi ba, wanda ganin haka ya sa ta ɗora hannu aka ta yi tsakar gida tana ihu tare da faɗin,
"Na shiga uku, na lalace an kwaso mini dangin jaraba! Kai kan Muhammadu sam ba ka yi sa'ar zuriya ba. Jama'a ku kawo mini ɗauki."
Ammi da ta fito daga sashinta da makullin mota tana sauri domin ta yi latti ta ji abin da take faɗi wanda ya sa ta yarda makullin tare da rugawa sashin cikin tsanin tashin hankali.
Wasu irin zafafan mari ta sauke masa."Ashe ba ka da hankali 'yar'uwarka za ka kama da duka haka saboda ga jaka ko?" Ta ce cikin zafi.
"Ai ko yau za'a yi ta a gidanan, wallahi sai ka yi sana-sanin dukanta." Cewar Hajiya.
Wani irin ƙululu ya ji ya taso masa cikin tsananin ɓacin rai ya kalli Hajiya Baaba yana faɗin,
"Kin yi kuskuren fifitata da kika yi akanmu, ki sani in ban yi ajalinta ba to sai na naƙasata." Ya juya zai fice daidai lokacin da ta ce,
"Za ka iya, ai zuciyarka kamar ta fir'auna take."
Jannah da ta ji duka rungume ta ta yi."Na shiga uku! Don Allah ki kira mom ta yi mini viser na koma ma London, if not he gonna kill me."
"Babu inda za ki, sai dai mu bar musu gidan. Shakuruminki shalele." Ta ba ta masa tana shafa bayanta.
Aby da ya shigo cikin falon a lokacin da zai fice wanda hakan ya sa ya fasa yana ajiyar zuciya a kai a kai.
"Yauwa, ma za shigo, ai sai da na gaya maka ka ja mana layi a tsakaninmu kaƙi, ga shi yanzu zai kashe mini shalele. Dole mu bar gidan nan, daɗin abin mahaifiyarta za ta iya siya mana duk irin gidan da muke so mu zauna ko a ketare ne."
Lamarin sai ya rikita kansa ya rasa ta ina zai fara." Tashin hankalin da kake so ka ja mini kenan Ajmal da sunan gyara? Kana jin mahaifiyata za ta bar gidana saboda kai."
Takaici sun na shi magana juya wa ya yi ya fice daga falon ba tare da ya ce komai ba, domin matuƙar ya ci gaba da kallonta, ƙila nan da minti uku, sai dai ayi maganar kai jana'izar gawarta . Zuciyarsa ta ɓace tsananin tsanarta ya ƙara shiga ransa sosai.
"Tashin hankali na nawa? Ai aikin gama ya gama. Barin gida ya zamar mini dole, ko kwana ba zan ƙara yi ba a gidannan."
Jannnah da ta ji duka ƙwaƙwarar motsi wahla yake mata. Ta kwantar da kanta kafaɗar Hajiyan Baaba da ko zama ta kasa yi, sai famar jijjiga take yi.
"Ya zama dole ka ɗauki mataki in ba haka ba, watarana sai ya jawo mana tashin hankalinn da ba mu yi tsammann.."
"Rufe mana baki! Munafukar Allah. Ai duk tarbiyarki ce, da kika raini 'ya'yanki sakaka kamar kashi, ba kya iya tsawata musu. Ni da na isa da ɗana, kin ga ina ije kara ya tsallake? Ai ni an haɗa mana jini da jaraba." Ta ƙatse Ammy da take maganar.
"Ki yi haƙuri Hajiya maganar ba ta kai haka ba." Cewar Aby. Harara ta gallah masa."Ta ma wuce." Ta ba shi amsa.
Kamata ta yi suka nufi ɗaki tana faɗin,"Shakuruminki kin ji shalele, babu inda za ki. Sai na ga uban da ya isa ya kai ki islamiyar."
Ganin ta ɗauki waya tana neman numba ya yi saurin shan gabanta."Don Allah, kar ki kira Halima. Ni ma ina da iko a kanta, kar ki manta ciki ɗaya muka fito."
"Sai na bari ya kashe ta ina gani ko?" Ta tambaye shi cikin ɓacin rai tare da shigewa ciki ta banko ƙofar da ƙarfi.
Dafe kansa ya yi, yana dana-sanin gaya masa, domin gashi yanzu ya ɓata goma biyar ba ta gyaru ba. Juyawa ya yi ya fita ganin kowa ya tafi ya barshi shi kaɗai.
Ajmal yana shiga ɗakinsa ya shige bayi. Ba tare da tuɓe kayansa ba, ya buɗe ma kansa shower yana ƙoƙarin tuɓe kayan, ya yin da ransa yake zafi zuciyarsa ke tafarfasa kamar za ta yi tsalle ta fito waje.
A maimakom ya yi hushi ya ƙyaleta sai ya saka a ransa sai ya ƙuntata rayuwarta don ya baƙanta mata da Hajiya Baaba da ƙiri-ƙiri take fifita ta akansu. Idon don kuɗi ne, ko kuɗin da yake da shi ba na Aby ba ya isa ta daina yi musu gorin sun ci da arzikinta.
Yana fitowa ya saka milk colour na jallabiya tare da ƙarasawa frig ya rinƙa banka ma cikinsa ruwan sanyi ko ya ji salama, amma da ya tuna abin da ya faru sai ya ji komai ya zaman masa sabo.
Wayarsa dake ƙara tun da ya shiga wanka ya ɗauka cikin ɓacin rai."Kin dame ni." Ya furta tare da daka mata tsawa.
Da sauri ta kashe wayar saboda tsabar tsoro jikinta har rawa yake yi."Na shiga uku! Wa ya taɓa shi?" Ta furta cikin jimamin tsawar da ya daka mata.
"Allah ya ba ka haƙuri. Ba ni na kar zomon ba rataya aka ba ni." Ta ce tare da ije wayar ta ci gaba da kwaɓin cincin ɗin da take yi.
"Hello Halimatuu, kina jina?" Hajiya Baaba ta furta."Eh in jin ki, Allah ya sa lafiya? Don na ji muryarki ta canza." Ta ce kamar ba ta san abin da ya faru ba, don Aby ya yi mata text ɗin komai kafin ta kira wayar.
"Ina lafiya, an saci zanin mahaukaciya. Gida za ki canza mana ni da Janaatuu, wannan azzalimin yaron ya tashi..."
"Hajiya Baaba, na ce ki daina ce mini Jannatu. Kowa sai kin ɓata ɓasa suna?" Ta katseta cikin masifa cikin kaukausar murya.
Takaici ya kamata matsawa da wayar ta yi tana faɗin,"Ka ga mini ja'irar yarinya fitsarrariya! Ina neman miki mafita, amma sai kin nuna halinki, ai na gaya miki albarkacin 'yata kike ci da na bari ya miki dukan tsiya wallahi, na watsawa karnikan gidan ƙasusuwanki."
Murguɗa bakinta ta yi ta gyara kwanciyarta tare da ci gaba da kuka da ƙarfi da sheshsheƙa ta yadda mom za ta ji yo ta.
Mom da ke jin faɗan da suke yi sai ta shiga girgiza kanta a ranta tana tunanin za ta canza halinta na fitsara kuwa, ganin ko uwarta ba ta ragawa ba.
Tun lokacin da Aby ya sanar mata ta yi matuƙar murna da hamdala, domin ta fahimci tana buƙatar wanda zai gyara mata kuskuren da ta aikata, kasancewar ta gama raina su duka.
"Yauwa ki nema mana gida wanda zamu zauna daga ni sai ita."
Ajiyar zuciya ta saki tana jin yadda take shiga take fita da zage-zage da jawo masa jifa'i tamkar ba matsayinsu ɗaya ba a gurinta wanda hakan bai yi mata daɗi ba, don ko ita ta ji wani iri ina ga kuma shi da iyayensa.
"Kiyi haƙuri Hajiya, su ɗin duka matsayi ɗaya suke a gurinki, kar ki sanya tsana ko rabuwar zumuncin su. Zan yi magana da Aby sai..."
"Ban san ke shashasha ba ce Halimatuu! Anya kuwa nonona kika sha? 'Yarki ɗaya tal wacce Allah ya ba ki ake shirin kashewa shi ne sai kin yi shawara da ubansa? To shikenan, ki bari ya kashe ta, inya so kuɗin da kuɗin da kike tarawa, kinga sai ki bar ma duniya su..."
Fisge wayar ta yi daga kunninta don tana jin abin da take cewa.
"Na san ba kya ƙaunata. So I don't want you to prove it. You know? I'm not under age, and my dad has money so I can handle myself." Ta yanke kiran cikin ɓacin rai.
Baki ta buge mata."Ke kam ban san lokacin sa kika zama haka ba! Mahaifiyar taki kike wa tsawa tamkar 'yar cikinki?"
"Kyale ni, Hajiya ba ta sona ban taɓa yin abu na burgeta ba."




Labarin ya zo da wani irin salo da nishadi, karku baru a ba ku labari. Ku biyo ni domin it’s just like a little introduction part, and guess what? You will really enjoy it. Believe me, my dear readers. Your happiness is my concern. Follow me on Facebook, Whatsapp, Wattpad, Arewaboo, and Bakandamiya. Ta ku, Jamila Lawal Zango (Jamsy).

FOR WHATSAPP: 08144072423
CALL: 07072971093






Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/LQfVU1ABdFI14btWRhUB1K









KURA DA FATAR AKUYA



*RUBUTAWA:-*
*JAMILA LAWAL ZANGO*
(JAMSY)

*SADAUKARWA GA:-*

*BADAMASI (AUTA)*

FIRST CLASS WRITERS ASSOCIATION
(Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation?)






Ban yadda a juya mini labarina ta ko wace siga ko karantashi ba tare da izinina ba. Aikata hakan zai sa mutum ya fuskanci doka.





*PAGE 12-13*



BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHEEM




A can ɓangaren mom ajiyar zuciya ta yi cikin takaici."Yauwa, Alhamdulillahi! Allah ya kawo mini wanda zai kawo gyara a lamarinta."Dariya dad ya yi jin abin da ta ce.
"Lamarinta yana bani mamaki ko Hajiya ba raga ma wa ba ita kanta sonta ne ya rufe mata ido, amma ba ka ji yadda take daka mata tsawa ba. Gaskiya na yi sakaci a rayuwarta.
Wayarta ta ɗauka ta yi wa Ajmal transfer kuɗi naira dubu ɗari. Bayan ta tura mishi message akan ya sa kati.
"Mu yi mata addu'a watarana zata daina har da kuruciya. Ya faɗa daidai lokacin da kiranta ya shigo wayarsa.
"Ga kiran mutuniyar nan, ya shigo." Ya ce yana kallonta da murmushi a fuskarsa.
" Ka gaya mata yadda muka tsara." Jinjina mata kai ya yi.
"Hello dady, na ba ni na shiga uku! Wallahi dangin mom mugaye ne, ka mai da ni family ɗinku ko ka canza mini gida."
Murmushi ya yi jin abin da ta ce." Ba za ki iya zama a family ɗina ba, kiyi haƙuri har mu dawo kin ji."
"No" Ta ce da ƙarfi. " Ba zan zauna ba ana cin zalina sai dai ka kama mana haya ni da Hajiya Baaba." Ta ƙarashe maganar tare da sakin ƙara har sai da ya kauda wayar a kunninsa.
"Ok, sorry I will." Ya faɗa ba tare da shiri ba. Jin abin da ya ce ya sa ta yi shiru sai shan majina take yi.
" Ki bari zan nemi gida mai kyau ku

Please Login or Register in order to submit comment