Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

samu natsuwa da ana saura kwana goma su fara za a yi bikin Ajmal sai kuma aka ɗaga sakamakon mahaifin Mushiirat da ba shi da lafiya an fita da shi waje.
Cikin nasara suka gama zana jarrabawar wanda har sai da ta kwanta ciwo bayan exam ɗin sai hankalinsu ya koma kan bikin Ajmal da za a yi wanda aka ƙara wata biyar.
Tun kafin ya matso suke shiri da murna da tsare-tsaren shagalin da za su yi ranar auren.
"Na ɗauki nauyin haɗa paty da ƙawayenmu ranar auren don murnar zai bar mana gida muci karenmu babu babbaka. Wayyo Allah har na ga irin rayuwar da zan yi, ga shi lokacin mun shiga higher institution, kai akwai bidiri."
Jannah ta ce wa Ummu da take kwance a kan kujerar da Jannah take zaune.
"Habawa ke dai bari. Allah dai ya kai dare ga hawara, ko bai ci ba ya yi birgima.Kin san Allah in yaya ya bar gidan nan, akwai kankaro mutunci. Wani irin shiga zan rinƙa yi na mata masu class ina zuwa makaranta."
"Ki dai bari kawai! Duk na ƙosa Jamb ɗinmu ya fito. Dole mu hau mota masu kyau, kuɗin mom zai yi kuka."
Dariya suka kwashe da shi tare da tafawa sannan suka fice daga falon zuw ɗakinsu.
Suna zaune suna kallo Hajiya Baaba ta shigo da kwanon fura a hannunta ta ce,
"Ke Jannatu, maza ki kaiwa yayanki Adamuu hurar nan, yau isasshen ya tuna da hurata mai daɗi."
"Ni fa Hajiya kin san ban cika son aike ba, haka kawai ga 'yan aiki sai kin wahalar da ni, kuma kin san halin jarabben mutun nan so kike na je ya ce n yi masa wani abu..."
"Ta shi ma za kije, sai kin kai mishi banga damar aiken wani ba sai malalaciya kawai, ke Ummu ta ki rakata." Miƙewa ta yi tana zumɓura baki kamar za ta zubar ta fice.
"Ke kin san Allah ba zan raka ki ba, yau ikin da muka yi masa daban ne, ka wo wayarki ki same ni a sashinmu."Ta wuce ba tare da ta tsaya ta ni ƙorafin da take mata.
Da siririyar sallama ta shiga cikin falon amma ganin ya juya baya yana waya bai ji ta ba sai ta ja ta tsaya tare da maƙala kunninta sosai yadda za ta jiyo shi jin ya rage murya.
Cikin salo da jan hankali duk wata 'ya mace yake waya. Dariya ya saki mai sauti yan lumshe idanu, wnda ya ba ta matuƙar mamakin jin yana da irin muryar.
Hankalinsa gabaki ɗaya ya tattara akan wayar don har wani takun ƙasaita yake yi a hankali a tsakiyar falon.
Cikin wata irin murya ta ji ya ce,"Buɗe bakinki na yi miki kiss, kuma ki rufe ido."
Jin hakan ta hangame baki tana mamaki ta zare ido tare da haɗiyar miyau da ƙyar.
Wani irin zazzafar kis ya sakin mata har uku sannan ya ce,"Bye, ki kular mini da kanki."
Cikin tsananin razana ta saki kwanon furar domin saboda tsabar gulma kayansa ta ji ya ce ta kula da shi.
Ƙarar faɗuwar kwanon ya sanya ya juyo da sauri yana kallonta wacce ta zura a guje ganin aika-aikar da ta yi.
Sashin su Ummu ta same ta a falo tana waya da Huzaifah. Da sauri ta ja hannunta zuwa ɗakin Nahlin tana faɗin,"Humh zo na shafa miki labari, yau na ji abin da ya girmi kakata Hajiya Baaba.
"Mai ya faru sis, give me the gist."
"Sai da na gaya wa Anty Nahlin Ya Ajmal kura ne da fatar akuya, fakewa yake da addini yana cin karensa babu babbaka, wi shi a dole uztasu Ahlulu sunnah, amma ta shafawa idanunta toƙa ta ƙi yarda. Ga shi yanzu na gani da idanuna. Kun san me na ji yana faɗi wa budurwarsa?"
Anty Nahlin ta kasa magana sai kaɗa kanta take tana mata nuni da shi da yake tsaye a bayanta, amma gulma na cinta ba ta lura ba.
Ummu da ba ta ganshi ba ta ce," Do tell me now." Ta faɗa cikin zaƙuwa da son jin gulma.
"Kiss guda uku ya yi mata, kum har yana faɗin ta kula mishi da kayanshi. Oh ni Jannah ko wane kaya yake da shi a gurinta oho? Ashe ya Ajmal gogaggen ɗan duniy..."
Maganar ta maƙale mata a maƙoshi sakamon Ummu da ta yi mata alamun yana jin ta.
Wani irin tsalle ta yi sai ga ta a tsakiyar gado, domin ko kaɗan ba ta taɓa tunanin zai biyo ta ba.
Nahlin ta buɗe baki za ta yi magana ya daka mata tsawa,"Rufe mini baki shashashar banza kawai! Kin tsaya kina jin shirmenta."
"Yi haƙuri." Ta ce tare da bin bayan shi ta wuce wanda Ummu ta bita a guje domin tsuntsun da ya ja ruwa. A ranta addu'a take Allah ya taimake ta ganin yadda ransa ya ɓace.
"Yau zan yi maganinki, ba ke baki da tarbiya ba. A gidan uban wa kika ji na ce ta kular mini da kayana? Saboda kallon finafinai ya ɓata ki."
"Am very sorry. Wallahi ba haka na ce ba, please understand me."
Mari ya kai mata yana faɗin," I should understand what? Kin ɓata tarbiyarki kina son ki ɓata na ki, sannan ki sanya suna ganin mutuncina su raina ni. Wato dama you been spying on me?"
"No, wallahi I don't, I really respect you. It was mistake please forgive me."
Marin da ya ƙara kai mata ya sa ta canyara ƙara daidai lokacin da Ammy ta shigo.
"Kai Ajmal, so kake ka ƙara janyo wata rigimar? Ma za yarda bulalar nan." Ta faɗa cikin ɓacin rai. What has she done to you?"
"I really disappointed, having you as a sister." Ya ce tare da yarda bulalar ya fice ba tare da ya amsa tambayar Ammy ba.
"Ba kya jin maganar Jannah, kina ganin kowa a gidan nan, kaffa-kaffa yake kar ya shiga gonarsa amma ke kullum cikin takalarsa, bayan kin san abin da zai je ya dawo."
Wuri-wuri ta yi alamun rashin gaskiya sai jan majina take yi.
Ammy ta juya za ta fita daidai lokacin da Ummu ta shigo."Sory sis, I was signalling you, amma ba ki gani ba. Dukanki ya yi?"
Ture ta ta yi tana harararta." A, a albarka ya shi mini, tare da ba ni kyautar kuɗi. Ai wallahi na san matsayina da inda na aje ki, you left me in, wato ya kashe ni ba ki da asara." Ta faɗa tana harararta.
"Am deeply sorry. Kin san halinsa, ya zan yi? Amma ke ɗin tawa ce."
"In ban da neman rigima irin na ki, ina ruwanki da wayarsa ba matarsa ba to be ba ce? Kar ki manta it remains 26 days for their weeding."
Zuɓɓura baki ta yi ba ta ce komai ba sai ta kama hannu Ummu."Kin ji muje sashin Hajiya Baaba."
Shirye-shiryen biki ya kankama Ajmal babu zama duk da bikin gata ake masa amma shi kansa nuna bajinta yake yi. Kmar yadda mom ta yi alƙawari ita ta haɗa lefe na gani na faɗa wanda samun sa sai 'yar gata mai ƙashin arziki.
Events kala-kala aka shirya duk da angon yana nuna ustazu ne amma hakan bai hana tsara bikin yadda zai ƙayatar.
Amaryar ji take kamar ta yi tsuntsuwa ta kawo kanta gidanta ganin irin kayan alatun da ka shirya a ɗakin. Duk da iyyen amaryar sun yi bajinta, amma Ajmal sai da ya sanya kayan furnitures a bangarensa masu kyau.
A gefe ba a bar su Jannah ba da suke jin kamar an biya musu kujerar makka, ba ma kamar Jannah za ta huta da tashin asuba karatu. Don haka suka gayyaci 'yan makarantarsu da shirya shagali na musammman. Sun ɗinka kaya masu tsada da kyau.
Kowa ya yi tunanin mom za ta dawo kafin bikin amma sai dai ga mamakin su, ƙiri-ƙiri ta ƙi zuwa wanda hakan ba ƙaramin haushi ya bawa Hajiya Baaba. Ita ko Jannah ko a tsummar rigarta don ta san abu ne mai wuya tazo sai dai ra'yin kanta.
"Anya ba kurciya aka yi wa Halima ba? Lamarin nan akwai ruɗarwa. Tun yaushe take waƙar za ta dawo, amma shiru kake ji malam ya ci shirwa. Ƙila sai na tashi tsaye."




Labarin ya zo da wani irin salo da nishadi, karku baru a ba ku labari. Ku biyo ni domin it’s just like a little introduction part, and guess what? You will really enjoy it. Believe me, my dear readers. Your happiness is my concern. Follow me on Facebook, Whatsapp, Wattpad, Arewaboo, and Bakandamiya. Ta ku, Jamila Lawal Zango (Jamsy).

FOR WHATSAPP: 08144072423
CALL: 07072971093



KURA DA FATAR AKUYA



*RUBUTAWA:-*
*JAMILA LAWAL ZANGO*
(JAMSY)

*SADAUKARWA GA:-*

*BADAMASI (AUTA)*

FIRST CLASS WRITERS ASSOCIATION
(Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation?)






Ban yadda a juya mini labarina ta ko wace siga ko karantashi ba tare da izinina ba. Aikata hakan zai sa mutum ya fuskanci doka.





*PAGE 15-16*



BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHEEM







"A'a Hajiya, karki saka kanki ga bibiyan malamai da babu Allah a zuƙakansu. Halima za ta dawo, wani aiki ne ya taso mata. Kuma kin ga dole ta dawo ko dan takarar da ta tsaya. Lokaci ne kawai bai yi ba." Cewar Aby jin abin da ta faɗa.
Dinner da aka shirya suke shiri. Sun shirya cikin wani haɗaɗɗen less kalar milk kallo wanda ya karɓi jikinsu matuƙa don anko mom ta yi musu.
Ummu ta shigo da turare a hannunta tan fesawa sai kuma ta fara fesawa Jannah,
"Kiyi sauri kar mu yi latti, kuma su Huzaifah suna jira."
Ɗaga mata kanta ta yi sannan ta ɗauki agogonta ta ɗaura suka fita suna taku cikin yanga da kwarkwasa.
Da suka isa ƙofar gida inda Huzaifah yake sai ta tsinci kanta da jin kunyarsa, musamman gainin yadda ya kafe ta da ido.
Wow! You look gorgeous and marvelous. Kin zama tamkar wata tarwaɗa."
"You are a such Flatter and you are good in it" Cikin jin kunya ta faɗi haka.
Gaban motan ya buɗe mata yana faɗin,"No, gaskiya na faɗa." Ya kalli Ummu da ta tsaya tana murmushin sannan ya juya ya kalle ta da dake ƙoƙarin shiga mota ya ce,
"Ummu right?"
"Haba Huzaifah, nufin ka ba za ka gane ni ba?" Ummu ta amshi tambayar cikin nuna alamun damuwa.
"Sorry, na dai tambaya ne kawai, amma kin san hakan na iya faruwa saboda na tabbata ke din ce, kin san hoto ba zahiri bane, musamman da yanzu mata canza halittar su suke in za su yi hoto."
"Amm kuma mun sha yin video calls da kai, remember?" Ta faɗa tana kallonsa.
"Oh yes haka ne, am sorry." Ya ce tare da haɗa hannayensa.
"Kullum ba a barin kunnawana su samu natsuwa sai dai a cika su da labarinka. Yau dai na ganka kuma duk ka cancanci abin da take faɗa a game da kai."
Ta shiga bayan motar ta zauna tare da kulle motar sannan ta ci gaba da cewa,
" You know what? I have a ton of embarrassing story about Jannah, and it will be perfectly for marital blackmail."
"Ke he is my bud, as I said earlier on."
Jannah ta karɓe zancen tana faɗin haka da harararta wanda ya sa suka kwashe da dariya.
"Oh pardon me, I forgot, amma kin san soyayya ba ta ɓuya idanuwanku za su bamu amsa ko Mufid." Ta ƙarashe tambayar tana kallon Mufid da tun da suka gaisa bai ƙara tankawa.
"Exactly, a dai juri zuwa rafi watarana tulu zai fashe." Dariya ta yi jin abin da ya faɗa.
"Da gaske ina son 'yar'uwarki fiye da yadda nake son kaina, amma tunaninta ba shi a kaina, amatsayin aboki kawai ta ɗauke ni. Don Allah ki karkato mini da hankalinta gare ni, na yi miki alƙawarin kula da ita har ƙarshen rayuwa." Ya faɗa daidai lokacin da ya tashi motar ya fara tafiya kamar baya son tuƙi yayin da fuskarsa ta canza kalar tausayi.
"Kyaleta ta gama kauce-kauce da zagaye-zageye amma indai mutum ba makaho bane ko ya kalle ta ai ya sam abin da ke ranta. So exercised patient she has fallen in love with you."
Dariyar jin daɗin abin da ta ce ya yi, yana kallonta da ta ɗaure fuska ba ta ce komai ba.
Suna tafe suna hira har suka isa. Gurin ya cik ya batse babu masaka tsinke. Ango da amarya sun sha gayu da ƙyale-ƙyali, ba kamar amaryar da angon yake jin kamar ya sace ta ya gudu don ta yi kyau sosai. Sai murmushi mai tsada suke sakin ma junansu.
Bayan sun zauna Jannah ta kara kuninta a na Ummu,
"Ina ta tunanin matar da za ta aure shi da ƙaton ƙirjinsa, ashe ita ma yar lukuta ce, amma gaskiya ba yarinya bace na ganta da jiki."
Dariya Ummu ta yi jin abin da ta ce,"Wato ke a jiki ake gane girma ko? Ba yarinya bace, don ta gama degree har da masters aiki fa take yi."
"Oh kice guzuma ya aura kuma sun dace, ba ki ga ita ma bagidajiya ce irinsa ji fa wani shiga da ta yi na rashin wayewa on her weeding day sai ta sanya rigar da Ƙaramin hijabin da zai rufe mata duka jiki. Kai Allah ya kai mu nawa auren."
Duka ta kai mata."Ban son iskanci, and stop being dramatic you know they are compatible. Kuma Yayan kike kira bagidaje, don kawai yana ahlul sunnah."
"Ke dai bari, wallahi rayuwarshi babu wayewa. Kullum cikin jallabiyoyi da wando baya kai mishi ƙafa. Ji fa ko rawar sun kasa sai wani sunne kai suke."
"Ba ki da dama, Allah ya sa yaji kina ce msa bagidaje kin san halinsa. Duk wani events da aka yi ba, da yaƙi amincewa wai walima ya wadatar."
Tsaki ta yi cikin jin haushe ba ta ce komai ba ta koma ta zauna tana jin bikin babu wani armashi sosai, duba ga yadda take kallon a social media ana cashewa sosai.
"Allah ya kaimu nawa zai ga yadda za a yi hosting event differently, it will be a topic on social media."
"Allah ya kaimu. Ni ce amara ƙirjin biki.
Ganin an fara manna kuɗi suka tashi wanda dama jira suke su yi amfani da wannan damar.Rawa suka fara tiƙa suna musu manni, wanda ganin haka ya sa Huzaifah ya taso ya shiga zuba mata ruwan kuɗi tana tiƙar rawa.
Karab! Suka haɗa ido da Ajmal da ya tsaya cikin takaici da mamaki yana kallonsu yayin da baƙinci ya cika shi wai waɗanann ƙanninsa ne.
Ganin kallon da yake musu ya sa suka koma gurin zamansu.
"Kai Ya Ajmal bai yi ba, yanzu shikenan ya yi mana baƙin cikin tura shagalin bikinsa a social media. Gabaki ɗaya bikin nan babu daɗi. Ji yadda amaryar take motsa jikinta wai a dole rawa take yi."
A haka dai aka yi dinner aka tashi sam bata yi musu daɗi ba don haka suka ɗauki ƙudirin party da za su yi sai sun ƙayatar da shi.
Washegarin bikin sai shirye-shiryen paty suke yi. Sashin Hajiya Baaba cike yake da mutane haka Ammy don haka suka yanke shawarar su ƙayata gidan harabar gidan gonar Abby.
Duk wani hidima sa suka yi a aljihun mom ya fita wanda ta karɓa babu tausasa lafazi.
Ganin gidan a cike yake sai suka yanke shawarar yin party ɗinsu a bangaren gidan gonar Aby.
Gabaki ɗaya sun ƙure gidan da waƙar Umar m sharrif take tashi. Ba bu yadda Nahlin da Hajiya Baaba ba su yi ba kan su kashe, amma suka ƙi wanda ta yi fushinta ƙyale su.
Ajmal da ya shigo da abokansa su gaisa da Aby wanda suka zo masa daga waje. Hayaniyar mutane da kiɗan da suka sanya ya saukar masa da wani irin azababben ciwon kai.
"Yauwa Adamuu, gara da ka shigo waɗannan marasa jin maganar sun hana kunnuwana saƙat da kiɗa, don ko da na yi musu magana taƙadiriya Jannatu jawo ni ta yi cikin fage tana juya ni."
Tsaki ya yi ba tare da ya ce komai ba jin abin da ta faɗa. Matuƙar kunyar abokanansa suka kama shi.
"Albarkar auren nawa kuke son ku kwashe, saboda ga ku sheɗanu ko?!" Ya furta cikin ɓacin rai daidai lokacin da ya kashe kiɗan.
Jannah da ba ta lura da shigowarsa ba ta ibo shoki saura kaɗan ta faɗa jikinsa, Allah ya taimake ta ta ja ta tsaya tana mazurai tare da ɓata fuska.
"I just give you rest of two minutes, kowa ta ɓace daga nan kafin na yi ball da ku."
"Kai wallahi guy ɗin nan bai yi ba, ga shi dai a ido kamar wayayye." Cewar ƙawarsu Maryam tana ƙuta.
"You know what? Ku zo kawai muje mu kama waje, ai tun da muna da kuɗinmu bai isa ya hana mu wataya ba, dole na yi murnar aurensa za mu huta da takura." Cewar Jannah.
Haka kuwa aka suka kama guri suka sha rawa sai da su ka gaji don kansu sannan suka dawo gida, bayan sun ci sun sha.
Biki ya watse bayan an yi tarin shagulgula aka ɗauki amarya zuwa haɗaɗɗen gidanta tare da yin buɗar kai aka bar ta daga ita sai angonta.
Tana zaune akan doguwar kujera ta sha matuƙar kyai sai walwali take yayin da ɗakin yake ƙamshi mai daɗin shaƙa.
Sallama ya yi ya shigo fuskarsa ɗauke da annuri domin yana jin babu wanda ya kain shi farinciki.
Ya shigo shi kaɗai bai nemi rakiyar kowa daga abokanansa ba, domin tun daga get ya karɓi kayan da suka siyo ya nuna musu baya son rakiyar.
Tonan sa suka fara yi wanda ya ji ya shanye har suka gama suka ƙyale shi.
Da sauri cikin ladabi ta taso ta karɓi ledar bayan ta durƙusa a ƙasa.
Wani irin matuƙar farinciki ya kama shi domin yana ɗaya daga cikin abin da ke ƙara masa sonta tsananin biyaryarta.
"Barka da shigowa ranka ya daɗe abin alfaharina, barka da wannan rana da ba zamu taɓa manta wa da ita ba." Ta faɗa cikin murya mai sanyi da son jan hankalinsa.
Ajiyar zuciya ya yi mai ƙarfi har tana jin hushin numfashinsa a fuskarta duk da ta mayar da gyalenta ta rufe fuskarta.
"Ina matuƙar sonki haskena, ina fatan mu yi rayuwarmu cikin farinciki."
"In sha Allahu, za ka same ni mai tsananin biyayya tamkar Sarki da bayinsa. Domin zan yi koyi da matan Annabi Muhammad (S.A.W.). Suka ƙarashe tare sannan suka shafa.
Miƙewa ya yi yana faɗin,"Bari na shiga kicin na ɗauko plate na ciyar da sahibata."
"Kaicona!" Ta faɗi tare da riƙe hannunsa da sauri.
"Ni kuwa mene ne amfanin numfashina matuƙar zan bar zauji da aiki? Kenan babu amfanin hannuwana."
Tsananin mamakin abin da ta furta ya kama shi duk da ya san cewa ta iya kalamai na sace zuciya, amma sai ya ji ya ƙara darajata da kimanta ta, domin shi mutum ne mai matuƙar son a nuna mishi girma, don haka ya kama hannunta duka ya riƙe yana faɗin,
"Kar ki damu kar kiji komai, ki yi mini alfarmar yau na yi hidima da rayuwarki sai ki ɗora da ga gobe."
"To shikenan zauji, yadda kake so haka za a yi sam babu jayayya a tsakaninmu." Ta ce tare da komawa ta zauna zuciyarta fal tamkar gonar addu'a ganin yau Allah y mallaka musu junansu.
Bayan ya ɗauko ya juye musu banƙararrun kaji da drinks masu sanyi. Kaɗan suka ci sannan suka je bayi suka yi brush tare da canza kaya.
A wannan daren Ajmal ya nuna mata irin sonta da yake yi da dakon jiran ranar da ya yi, domin ya shayar da ita ƙauna mai tsuma zuciya ya sa ka manta komai, wanda ya sa ta farinciki ta san ta wuce zarra.
Sosai take ganin wautan 'yan matan da suke faɗin ba sa son auren ustazu domin auren riba biyu ne. Ga soyayya kuma ga sa mace kan tafarkin tsira.
Washe gari da safe bayan sun tashi sun yi sallah duk yadda ya

Please Login or Register in order to submit comment