Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

bokon da kuke yi ba son shi nake ba, domin da za a biye tawa duk aure zan muku."

Harararta suka fara,"Aiko da kin cuce mu Hajiya. Allah ya kyauta don ke an cuce ki am miki aure da wuri sai ki rama akanmu. Ta Allah ba taki ba."

"Dallah rufe mini baki.Auren nawa ai shi ya yi muku gata a duniya, don ya yi mini rana ban yi karatun na haifi minister."

Dariya Ummu ta yi ganin yadda take doro da ji da kai.

"Tab! An ce miki zama minister wasan yarane. Ki tsaya ki gane tun kafin zaɓe za ta sha ƙasa.. Aure ne dai sai na yi degree da master har da phd if possible na fara aiki."

"Baƙinki ya sari ɗanyen kashi ta Allah ba ta ki ba." Ta bata amsa tana kai mata dunduni.

"Wayyo Allahna! Hannunki kamar icce don Allah ki daina." Ta ce tare da gamtsarewa.

"Ba dole ya zama icce ba ya ga jiya ya ji yau."

Ummu ce ta karɓi zance da cewa,"Wai da gaske kike har sai kin taka wannan matsayin sannan za ki yi aure? Ni dai if pssible I wanna marry before finish degree don bani da wannnan ra'ayin ina samu wanda nake so zan yi aure, ba zan yadda na tsufa a gida ba, kum kina tunanin Huzaifah zai yarda?"

"Mai zai hana shi ma ba yanzu zai yi aure ba, don yanzu haka Maleshiya zai je ƙaro karatu."

"Ashe ko wani zai yi wuf da ke don wallahi ana bikin Hafsatuu zan tasa ku agaba. Ko mahafiyarki da ta samu ɗaukaka duk tana gidan aurenta ta samu." Cewar Hajiya.

" God forbit over my dead body ayi mini auren wuri, don babu wanda ya isa ya yi mini aure da wuri saboda komai na rayuwata a tsare yake ba zan iya haɗa aure da karatu ba."

"Shikenan, lokaci zai nuna ai domin aure lokaci ne. Ni bari na yi walha na gaji da suratun banza." Ta miƙe tare da shigewa ɗakinta.

Ranar Juma'a suka shirya da Huzaifah zai zo. Tun ranar Alhamis suka je aka yi musu kitson attach sannnan suka lalli mai kyau.

Washegarin ranar Juma'ar bayan an sauko masallaci. Jannah na gaban mirrow da soson hoda a hannunta tana gyara hoton da ta shafa. Ummu na zaune kan gado tana kallon tiktok.

"Sis Huzaifah zai zo amma bamu yi mishi komai ba don ni kam sai yanzu na tuna duk ni ma na shiririce. Ko iya drinks da snack za mu ba shi."

"Don't worry about that I have ordered food for him. They will bring the food before his arrival."

"Ok" Ta ce tare da ci gaba da kallonta, sai kuma ta juyo tana kallonta ta ce,

"Na so na ce miki mu yi wa matar ustazu magana ta yi mana girki mai rai da lafiya, amma sai na tuna muna zuwa za ta fara mana wa'azin mu koyi girki."

Dariya ta yi jin abin da ta ce,"I was thinking the same, but na so na yi mata maganar, amma na san ɓata mini mood ɗina za ta yi. So, it should be better na yi oder."

"Eh hakan yafi ai. Rashin kuɗi su ke janyo maka wulaƙanci. Akwai maƙociyarmu da take snacks ba ri na sanya ta turo mana da samosa ta ita sosai."

"Thanks." Ta ce ta zauna gefenta tana murmurshi.

Bayan an kawo abinci da samosa. Suka jera a dining ɗin Hajiya Baaba sannan suka sha gayu tare da turare gidan da turare .


Ta fito za ta shiga kicin ganin su a falo tamkar waɗanda za su fita. Ta kalli dining ɗinta da yasha kayan daɗi, sai ta juyo ta kalle su da suka ɗaure fuska, babu alamun son amsa tambayar da suka san dole sai ta yi.

Ga mamakin su sai suka ta basar tare da taɓe baki, ta shige kicin wanda 'yan mintina kaɗan ta fito za ta shige ɗakinta, sai kuma ta dawo da zauna tana faɗin,

"Ban gane ba, an yi yamma da kare. Munafunci da ƙus-ƙus da na ji kuna yi, na san da walaki goro a miya. Uban me kuke shiryawa.Ni da gidana mallakina ba za ku gaya mini Kon baƙi mata za ku yi? Don na lura yamzu kun iya kwashe-kwashe."

Kallon junansu suka yi tare da kwashewa da dariya."Gidan Abby dai." Cewar Jannah.

"Ai kai da kaya duk mallakar wuya ne." Ta bata amsa.

"Daɗina dake akwai son jin ƙwaƙwaf, wato tun ɗazu kin yi kamar ba ki san me muke faɗi ba, ashe kin baza kunne kina jinmu."

"Ah to za a hana ni ne da kunnina." Ta katse Jannah da faɗin haka..

"Abokin Jannah ne zai zo yau." Ummu ta ba ta amsa tana kallon Jannah da ta tsinci kanta da jin kunya ta rufe ido.

"Aboki ko? Munafukan banza. Kwa fito fili ku gayi gaskiya."

Dariya sunne kai da Jannah take yi ya bata mamaki.

"Eh, abokinta ne mana. Huzaifah ne, kuma ai kin san shi. Saurayin da ya ya riƙe ki a filin jirgi da za ki faɗi, wanda Ya Ajmal ya ce yazo bikinsa."

Sai ta faɗaɗa fara'arta tana kallon abincin da suka shirya a dining.

"Allah Sarki! Ce mini za ki yaron kirki, na gane shi. Kuma shi ne don son jiki da sangarta kuka kasa yi masa girki sai dai ku siyo masa? Ai da kun gaya mini da na yi masa girkina mai matuƙar daɗi na tsofaffinnda suka ga jiya suka ga yau akan girki."

"Dabbu, fate, tuwo, shishshika, ko caccaka ne sunan abicin ko me oh. Shi ne abinci da kika iya masu daɗi? Allah ya kyauta ya ci. Huzaifah namiji ne wayyayye ba irin Ya Ajmal ba. Sam ba ya cin abincin gargajiy..."

"Ai ko dai da yaji haushi kuma basir sai sun yi ajalinsa. Ai duk wanda ya bar gida, gida y barshi. Na fi gwara gurbin buduwar da yake so, wacce ko murhu ba ta iya haɗawa."

Ta yi shiru ko za ta ce komai amma sai ba ta ce komai ba sai dai harararta da ta yi domin hankalinta na kan wayarta da take tsammannin jiransa cikin sakannni don ya sanar mata sun iso 'yan mintina ya rage.

"Allah Sarki har na fara tausayinsa. Ga shi yaron kirki amma ya yi zaɓen tumun dare. Lallai ya haɗu da jarrabawa." Ta canza fuska zuwan kalar tausayi kamar za ta yi kuka.

Wani kallo ta watsa mata dai dai lokacin da ta juya zuwa kicin tan faɗin,

"Bari na je na yi masa tuwon shinkafa miyar kuka mai daɗin sai kunnensa ya kusa tsinkewa, na rama alkhairin da ya yi mini dama shi danƙo ne."

Da sauri ta kalli Ummu da ta yi zuru tana kallon Hajiya Baaba cikin takaici.

"Sis ya iso yana ƙofar gida." Ta ce tana kallon fuskar wayarta da ke ɗauke da numbarsa ɓaro-ɓaro.

"To sai ki bar girkin babu buƙata don sun ƙaraso suna ƙofar gida, kuma ko kin yi sai dai ya yi kwantai, kuma wallahi in kika kunyata ni kin san halina" Ta bata amsa da faɗin haka da ƙarfi don ta shige kicin sai ɓarin tukwane take yi.

Tabe baki ta yi ba ta ce komai ba ta karasa shigewa kamar ba da ita ta yi maganar ba.

Ummu ce ta bita kicin ɗin daidai lokacin da jannah ta buɗe ƙofa ta nufi harabar gidan.

"Hajiya Baaba don Allah in suka shigo kar kiyi wani abu da bai dace ba kin ga su ɗin baƙi.."

Kamar za ta cinyeta ɗanye ta taso mata."Dallah can shashasha rufe mini baki! Saboda gani ƙaramar yarinya, in suka zo zan je na sa hannu a abincinsu ko na yi rashin kunya ko?"

"Allah ya ba ki haƙuri ni ba haka nake nufi ba, kin san me nake nufi."

Harararta ta yi ta ɗora tukunya a kan gas ta ce,

Labarin ya zo da wani irin salo da nishadi, karku baru a ba ku labari. Ku biyo ni domin it’s just like a little introduction part, and guess what? You will really enjoy it. Believe me, my dear readers. Your happiness is my concern. Follow me on Facebook, Whatsapp, Wattpad, Arewaboo, and Bakandamiya. Ta ku, Jamila Lawal Zango (Jamsy).

FOR WHATSAPP: 08144072423
CALL: 07072971093






KURA DA FATAR AKUYA



*RUBUTAWA:-*
*JAMILA LAWAL ZANGO*
(JAMSY)

*SADAUKARWA GA:-*

*BADAMASI (AUTA)*

FIRST CLASS WRITERS ASSOCIATION
(Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation?)






Ban yadda a juya mini labarina ta ko wace siga ko karantashi ba tare da izinina ba. Aikata hakan zai sa mutum ya fuskanci doka.





*PAGE 18-19*



BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHEEM







Harararta ta yi ta ɗora tukunya a kan gas ta ce,

"Kun san kuna da abin faɗin ne ni dai ina gani ba zan yarda a cuci yaro ba don ba zan yarda na mayar masa da sharri akan alkhairin da ya yi mini."

Ba ta ce mata komai ba ta juya ta fita daga kicin ɗin amma zuciyarta sai faɗi take tana addu'ar Allah ya sa kar taba da su don sanin hali ya fi sanin kama.


Da murmushi mai tsada ta ƙarasa gurinsu wanda ya kashe mata ido tun da ta taho. Hure masa idon ta yi da ta isa gare shi. A jiyar zuciya ya saki mai ƙarfi.

"A koda yaushe muka haɗu gani nake kina ƙara kyau bab, kin kuwa ganki tamkar wata a cikin taurari.

Murmushi ta yi jin abin da ya faɗi."Ku shigo ciki Mufid ka ga abokinka sai zuba yake."

Dariya ya yi."Ai dole ya yi zuba kamar fanfo samun mace irin ki ai baiwa ne. Tabbas abokina ɗan baiwa ne."

Ƙara murmushi ta yi tare da nufar hanyar shiga cikin gidan wanda ganin haka suka bita.

"Ƙawarmu, aminiya, kuma 'yar uwarmu."Ya faɗa daidai lokacin da ya buɗe labulen falon bayan ya yi sallama.

"Barka da zuwa ku shigo. Huzaifah duk wannan matsayin ni kaɗai?"


"Ai kin wuce haka ko bab?" Ya yi maganar yana tambayar Jannah dake gefensa.

Ɗaga masa kai ta yi tana murmushi.

Bayan sun gaisa da tsokanar juna sai Ummu ta miƙe tana murmushin ta ce,
"Bari mu shiga ciki mu barku ku ci abinci."


"A don Allah ku tsaya na fi son ina kai loma ina cin abinci mai daɗi da my future wife ta girka. I know it will be very testing"


Hajiya Baaba da ta fito da hura da nono a hannunta tana faɗin,"Ina kuke 'yan son jiki? Sai ku karɓi wannan hurar ku dama masa, ko banza ya samu yaci abincin da ya fito daga gidanku tun da ƙila kafin in gama abincin sun tafi."


Turus ta yi tana kallonsu don ba ta ji shigowarsu ba saboda bayan fitar Ummu rediyo ta kunna.


"A lale marhabin da zaratan maza." Ta ce tana washe baki ta ƙarasa gurinsa.

Sai suka yi tsuru-tsuru don a tunainsu sun ji abin da ta faɗa.

Duƙawa suka yi suna gaishe ta. Guri ta samu ta zauna taci gaba da cewa,"Haba ku tashi ai kamar Adamuu na ɗauke ku. Ma za ku tashi 'ya'yan albarka."

Miƙewa suka yi suka koma mazauninsu suna shafa ƙeya.

"Sai na ji kamar ka ce za ka ci girkin Jannah ko?"

Ɗaga mata kai ya yi cikin kunya yana sosa kai tare da mamakin tambayar.

"Taɓ! Aiko ka bugo don wallahi ko ru.."

"Hajiya Baaba kamar kin ɗora abu a wuta kamar yana ƙonewa." Cewar Ummu tama kama hannunta ta miƙe.

"Ke dallah kyale ni na faɗi gaskiya ai ita ɗaci ne da ita." Ta ƙarashe maganar tana wafce hannunta da ta tsaya kamar mutum mutumi.

"In kana jin sangartacciya na bugawa a jaridan ita ce, ka ga duk wannnan abincin da suka shirya maka, wallahi duk siyo shi suka yi. Ni saboda takaici kasa magana na yi, amma na ce sai na gaya maka kar na cuce ka saboda alkhairin da ka yi mini."


"Haba Hajiya Baaba, gaskiya abin da kike yi bai dace ba, kum.."

"Kin san Allah in kika ƙara magana sai na kwaɗe ki da maficin nan. So kike na cuce shi? Ai gara na gaya masa idan aka yi auren da ni za a taho don ni zan rinƙa masa girkina mai daɗi da rainon yara. Maganar aure fa ake yi, kuma ai dole sai an faɗi naƙasun kowa."

Sai ta gyara zama tana kallon Jannah da takaici ya hana ta cewa komai sai hawaye da kin bin ƙuncinta domin ta ji a jikinta dole sai ta kunyata ta.

Harara ta banka mata tare da kallonsa ta saki dariya."Ka na jina ko yaron kirki? Da Ummu takan yi abin kirki amma zuwanta gidan komai ta daina, ba su da aiki sai kallo da hira a waya. Shi ya sa na ce ba zan ɓoye maka komai ba gara na sanar dakai fare zamu taho in an yi bikin."


Saboda dariya Mufid har tuntsira ya yi. Shi kuwa Huzaifah dariyar yake ƙoƙarin ɓoyewa, amma har sai da ta ci ƙarfinsa ya dara.


"Oh my God! Gaskiya you Grandma is so dramatic, I love her." Ya ƙarashe maganar yana kallon Jannah ta yi shaɓe-shaɓe da hawaye sai kuma ta share tana faɗin,


"Ai dama shi kansa ya san bai nemi aure inda matarsa za ta rinƙa masa kirki ba, in kin yi hakanne ki kunyata ni." Ta faɗa a tsiwace tana harararta.


"Au iyye a gabansa sai kin nuna halinki?" Ta ce tare da kama bakinta tana kallon ta. Sai ta juya kallonta garesa ta ci gaba da cewa,

"Ka gani ko? Allah na gode maka da ta nuna maka halinta. Yanzu da na ce maka fitsararriyace ba ta ganin kowa da gashi sai ka ji haushina, amma gara da ta nuna maka halinta ƙiri-ƙiri ka gani.Ita ɗin kura ce da fatar akuya. A waje kamar mutuniyar kirki."


"Oh common bab. Kin san ko wace irin mace kike ina sonki, saboda tsarinki da zubin ki duk sun yi mini." Ya ce mata bayan ya miƙa mata handkerchief ɗinsa, sannan ya juya yana kallon Hajiya Baaba da ta ɗaure fuska jin abin da ya ce don ita ba haka ta so ba, ta so ace ya nuna ba zai iya ba ko ta yi zuciya ta koyi aiki.

"Ba ki da matsala Hajiya Baaba, mu house is welcome to you at anytime you wish. Sosai kika burge ne Ina matuƙar son ki dawo gidana gabaki ɗaya da zama."

"Humh! Ka ji da gulman turancinka na bogi, ai ni ba na faɗa maka bane don na burge ka, na faɗa maka ne don na gaya maka gaskiya." Ta ce tare da juyawa za ta shiga kicin ganin haƙarta ba ta cimma ruwa ba.


Ajmal da ya yi sallama ya shigo don kawo mata maganin da tun safe ta addabe shi da kira ba ta da lafiya, amma ga mamakinsa tun daga ƙofar ɗakin ya fara jiyo muryarta tana zuba.

Idanu ya zuba musu bayan ya yi sallama ya shigo. Ba tare da ya ce komai ba ya juya ya fita musu magana ba duk da ganin yadda suka yi razana don sun ɗauka har su tafi ba zai shigo ba.

Da sauri Huzaifah miƙe zai bi bayansa amma sai Jannah ta hana shi,

"Lemme go and great Babban Yaya."

"No you don't have to do that."Ta ce tare da riƙe gefen rigarsa tana girgiza masa kai cikin rashin karsashi domin gabakiɗaya Hajiya Baaba ta ɓata mood ɗinta.

Sun daɗe suna hira har sai da suka gaji don kansu suka yi wa Hajiya Baaba sallama suk tafi bayan sun cika lalitarta da bugun Abuja wanda ta rinƙa shi masa albarka kamar a ta goya su.


"Wayyo Allah! Tun shigowa Ya Ajmal na rasa sukuni. Ni kam mun bani Allah ya sa karya gayawa Aby." Cewar Jannah tana dafe ƙirjinta ganin motar su ta ɓace daga gurin.

"Amin, ni wallahi har sai da cikina ya murɗa. I was thinking that he would embarrassing us in front of him, but thankfully he didn't."

"He never try that, cus i won't stay an watch it." Cewar Jannah cikin ɗaure fuska, sai kuma ta juya tana kallon hanyar da suka bi.

"Kin san Allah yau ni da Hajiya Baaba a gidan nan about what she did to me I was very devastated."

Dariya ta yi ta ce," To me za ki yi mata kamar ba ki santa ba, ki ƙyaleta kawai kar ki ja ma kanki. Allah I was expecting that, infact more than that from her. Kawai dai we don't have any options ne shi ya sa."


Ƙuta ta yi ba ta ce komai ba ta buɗe get ɗin suka shiga.

Washegari da safe ko breakfast ba su yi ba kiran dad ya riske su. Gwalalo idanu suka a tare.

"Kai anya kiran nan ba lafiya ba fa. Ni fa kallon da Ya Ajmal ya yi mana na san dole sai ya kai ƙararmu gurin Aby, don ya cika gulma kamar ba malami ba." Cewar Jannh da ta miƙe cikin tsoro.

Ita dai Ummu ba ta ce komai ba ta miƙe har ta murɗa ƙofa sai ta dawo ta kalleta,"Don Allah ki yi sauri kin tsaya sai kuma mun ƙara wani laifin."


Ta faɗa ranta a ɓace ganin ƙoƙarin zama take wanda ya sa ta miƙe suka fice da sauri.

Ganin Hajiya Baaba zaune a kan kujera tana ta girgiza da kaɗa ƙafa jikinsu ya ba su ba lafiya ba.

Da sauri suka durƙusa a tare."Ina kwana Aby."

"Rufe mini baki shashashun banza! Ina kallon ku masu hankali har na barku kuke zaman hostel ashe wawaye ne ku ban sani ba?"

Aby ya furta murya a zafafe," A'a Muhammadu ka san ba zan ɗauki hakan, wanda na san duk zugin wannan munafukin ne. Ai tun da na ga ya shigo ya ije maganin ba tare da ya ce komai ba na san sai ya haɗa munafunci. In ban da gulma tun yaushe na rinƙa kiransa ya siyo mini, amma da yake isashshe ne bai zo ba sai da gulmarsa ta kawo shi."


"Haba Hajiya Baaba, ya muna ƙoƙarin gyara za ki ɓata kuma." Sai ya juya gun su.

"Ke Jannah da gaske kun kawo saurayi gidanan?"Ya ƙarsa maganar cikin tsawa.

"To laifi ne hakan Muhammadu? Na ga shi mace ya aje a gidansa yana hutawarsa. Ko so yake mu rinƙa ado da su a ƙofar gida? In ban da gulma da sa ido waɗannan tiƙa-tiƙan da 'yan matan da ba bu abin da suke yi, sai warin balaga za a tsaya ana tambyarsu don sun kawo maza gida zance."

Zare ido suka yi suna kallonta,"Warin balaga?Kai amma Hajiya ta cuce mu duk irin ƙanshin da muke yi." Jannah ta ce tana hararar ta tare da shinshina jikinta.

"Ni fa ba aure zan yi ba kuma abokina ne. Bayan wannan babu abin da ke tsakaninmu." Ta furta cikin rashin shakku da tsoro.


"Gabakiɗaya ke kike ɓata yarannan Hajiya. Idan aure za su yi ai babu wanda zai hana su, amma sa bari su yi zurfi a karatunsu. Duka fa yanzu suka

Please Login or Register in order to submit comment