Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

"Ya zama dole ki yarda da abunda ƴan albarkar yarannan suka zo mana dashi. Da ba dan sunyi iliminba, da haka zaku zama ɗaya daga ke harsu, shin me ruwa uku kawai ( Sha_sha_sha) Zaliha kuyi abunda kuka saka a gaba. Allah yayi muku jagora, sai inda ƙarfina ya ƙare ni kuma" haka suka sani a gaba har saida na amince a maka su Audu a kotu ala tilas. Cikin kwana biyu, Zaliha ta dawo da takaddar sammaci. Ɗan lami, da Goggo Rakiya su suka tafi da sammacinnan har fada.
Ni kuwa koda muka dawo gida, jikina sam yaƙi daɗi, ga tunane tunane da suka addabi zuchiyata. Ga habaice_habaicen Hindu wanda ta matsa mun lamda dasu a kwanakinnan. Audu kuwa sai sabgogin gabanshi yake yi, shi da Shazili gani suke zasu ci banza. Ƙuta nayi nace.
Mu zuba, inda dane bani da ƙarfin ramawa, bani da muryar da za'a saurari kukana. Yanzu karana ya kai tseko"


Fada:
"Allah ya taimaki mai gari. Wannan takaddar sammacice daga kotun birni. Ta Audu ce mijin ƴarmu, da Shazili, da Hindu, Yaranshi ne suka doka shi a gaban kuliya, suna neman a ƙwato musu hakkinsu dana mahaifiyarsu. Tun daga lokacin da aka haifesu har zuwa girmansu. Domun baisan komai nasu ba. Kuma ya cuskuna ma uwarsu ainun. Dan haka suna neman hakkinsu a wajan Audu." Goggo Rakiya na kaiwa nan, fada ta ɗauki tafi da sowa. Saida mai gari ya dakatar dasu. Ya dubi Goggo Rakiya yace.
"Rakiya, ni ina ganin da anyi sulhu anan fada ta da zaifi. Duk da nasan dolen Audu da Shazili su amsa kiran kuliya. Amma ya yara zasu kai ƙarar mahaifinsu? Shifa tuwo ba'a sauya mishi suna.
Goggo Rakiya tace.
"Amma in ba'a sauyama tuwo suna, ai hannunka yana ruɓewa ka je asibiti a yanke maka ko? To da kabarshi mana kaga in baici gangar jikinba duka." Fada tayi shiru kowa saida ya kaɗu da wannan lamari. Aka saka su Zaliha a gaba akaita tattaunawa a kansu, cewar baza suyi albarka ba." Mai gari ya tashi fadawa biyu yasa suyi mishi kiran Audu."






Audu:
Yana zaune yana shan fura, Hindu kuma tana gefenshi sai sake zuga shi take yi akan lallai, ko a cikin gidanne tunda da samari, ya tursasa musu su auri su Shatu kowa ya huta."
"Damma baka zuwa sha'ani, da kaji yanda ake zagin Shamsiyya da ƙattin yaranta. Kuma abun takaicin, zagin har takan nawa yaran yake sakkowa. Yanzu Hannatu, mane minta cewa fa yayi in da gaske su Shatu yayyenta ne, bazai iya aurenta ba. Cikin dabara yanzu nake son tayi mun kiran yaron mu zauna mu tattauna" Audu yace.
"Shawararki mai kyauce sosai Hindu, ni kam nayi dacen samun mace mai hangen nesa. Aini ban tuno da samarin gidan ba, da bazan fita har dawa ina shelar masu aurensu ba." Sallamar Salame suka jiyo a ƙofar ɗakin. Hindu ta amsa mata."
"Baban Shatu, mai gari ne ya aiko ayi kiranka. Manzannin suna waje"
"To gani nan Salame" Miƙewa yayi, yasa babbar riga, ya kifa hularshi.
"E bari inje ɗin Hindu, ƙila an samu wanda ya daki ƙirji zaiyi jahaɗin auren ɗaya daga cikin yarannan ne" Yana kaiwa nan ya fita. Hindu ta sauke ajjiyar zuchiya na cin galaba akan raba Audu da yaran Musina data yi." Zainaba ce ta shigo cikin ɗakin hindu da kururuwar ihu, fuskarta duk a kumbure, da halama duka taci sosai."
"Ma'aikin Allah na madina ni Hindu. Haɗarin Bodi kuka yi ne Zainaba?" Cikin kuka tace.
" Fatsima ce tasa Tanimu ya rubuta mun takaddata saki uku. Kuma yace in tawo da yarana baya ƙaunar mu. Bayan tasa yayi mun mugun duka." Ɗiyar Zainaba ce ƙarama ta shigo mai sunan Hindu. Ga goyo ɗanye a bayan Zainaba."






MRS BUKHARI[08/04, 19:57] Mrs Bukhari: MRS BUKHARI
GAWURTATTU UKU


LAMBA TA ASHIRIN"




INA MIƘA ƊUNBUN GODIYATA S GAREKU MASOYA RUBUTUNA. HAƘIƘA WANNAN LABARIN YA KAINI WANI MATSAYI DA MATAKIN DA BAN TAƁA TUNANIN ZAI KAINI BA.
HAJIYA TURAI NAGA SAƘO INA GODIYA MAI TARIN YAWA.




YAWALE:
Ƙarema yarana kallo yake yi. Masha Allah ko wanne cikinsu ya ginu da tarbiyya, gasu da mugun haɗin kai da soyayyar junansu. Gashi kowa yana da abun hannunshi. Yaran mowa Kumatu kuwa, Saminun ne dama dama a cikinsu, amma du sauran basa sana'a sai yawon ɓel_ɓel da bin inuwa. Muttaƙa kuwa yayi nisa baya jin kira. Yanzu haka yana can a kulle a kurkukun bayan gari, mai gari yasa an kamoshi shi da abokan satar tashi, ya garƙamesu a mari. Babu irin bori da tumamin da Kumatu bata yi ba a tsakar gida."
"Musina nayi mamakin abunda kike shirin sa yarana suyi. Wata kam ba kya ƙaunar kiga muna zaune lafiya. Shin me Kumatu tayi miki da kika ƙi jinin yaranki su haɗe kansu da yaranta? Duk abinda yaranki suka kawo miki sai dai kici ke kaɗai. Kin nuna musu banda galihu a wajanki, kuma baki basu tarbiyyar su kula da Yadikkonsu Kumatu ba. Wai dam ɗiban albarka har Jamilu ya mallaki garjejen fili a ƙauyannan amman ni ubanshi banda labari Musina, ga gonakai daya mallaka da sa hannun mai gari amman ni ina nan hoto jibi yanda na dawo dan tsabar wahala komai nawa ya ƙare, dan baƙin hali yarana dana arziki amman kin hana su taimaka mun. Wallahi zan kafa dokoki a gidannan kuma dole abi, zaman zai sauya ko dan haɗin kan yaranmu. Ni dai bance uhm ba, bare um_um jira nake ya gama zazzago duk abinda yake cikinshi tukunna, su Jamilu sunyi tsuru_tsuru suna kallon mahaifinsu, ba'a taɓa yin zama irin wannan ba a gidannan sai yau.
"Daga yau duk abinda yaran wajanki suka siyo suka kawo miki, na ci, ko sutura, to dole su siyo da Yadikkonsu, in basu da halin yi muku duka, sai suyi haƙuri. Nan Alawiyya take wucewa da babban buhu shaƙe da kayan alatu, bushashahen kifi a miyarki kamar zaiyi magana, amman baki basu tarbiyyar su kula dani ba. To itama duk wata inya ƙare duk abinda ta siyo a raba da Kumatu. Jamilu da yake ɗiban hatsin da bai wuce rabin buhu ba ya bamu, shima na soke dole ya raba duk hatsin daya samu gida biyu, rabin a rumbunki, rabi a rumbun Kumatu bayan ya ware na siyarwa. Kema Kulu inajin labarin jar biya da kike kawo ma uwarki cike da zabi duk wata. Daga yau ko ki haɗa da Kumatu ko ki bari.Ita kanta Kattume ƴar gatan uwa da tana wajan zamannan wallahi saina bigeta ma, dan inajin hidin_dimun da take yi ita da mijinta a gidannan, amman dai_dai da hatsi baki taɓa bari ta auno bata Kumatu ba. Sannan Alawiyya da Zubaida duk su fitar da mijin Aure na gaji da ganinsu a gabana anayi mun ɗan kallo a gari. Wani iri numfashina yake yi, da ba dan yara ne a gabanmu ba, da yau Yawale yaga hau irin namu na masu haƙuri. Waigowa yayi wajan su Jamilu da suke jere da Saminu.
"Kai Jamilu na haɗaka da Zulai ƴar wajan Yayana Jamilu ka aureta, mun gama maganar da Yaya Jamilun, tuwona maina. Kai kuma Mustafa sai ka auri marka yarinyar Mudi duk a haɗe ayi auren dana Ƙasimu. Ke kuma Sauma'iyya mun gama magana da Zaidu zai aureki ya haɗaki da Harira zaki ci gaba da zama a cikin gidannan. Gida bai ƙoshi ba baza'a kaima dawa ba. Alawiyya, Zubaida, ku fidda mijin aure nanda mako guda in ba haka ba. Akwai samari fal gidannan zan tilasta musu su aureku, duk da baza su so auren fitsararru irinku ba. Ƙasimu ka samu Saminu zai yankar maka fili, kuma Jamilu ku sameshi a yanka muku." Kallon Yawale kawai nake yi, ko kunya baya ji sai hukunci yake zartarwa akan yarana dana gama wahala akansu. Har yake tunanin haɗa Jamiluna da Zulai yarinyar data zubar da ciki watan jiya, yawon bin maza take yi kwararo_kwararo. Ita kuma Marka ba ƙaramar fitsararriya bace, dan ko aiki,ko aike uwarta bata isa ta sanyata ba, sune za'a aura ma yarana, dan anga Allah ya tallafi rayuwarsu komai ya wuce rayuwa tayi mana shar. Su Jamilu sai kallona suke yi, kallo irinna kiyi mana rai. Ni dai Yawale da Kumatu nake kallo kawai, cike da maɗaukakin mamaki.
"Sannan Kumatu zanci gaba da muku rabon kwana ke da Musina, kuma duk nauyinta dake kaina zan sauke mata, fatana ku zauna lafiya.'
Kutumar bura ubanka, Yawale kaine kake faɗen haka da bakinka?" Bansan sanda bakina ya subce na narko wannan ashariya a gaban yara ba. Duk suka kalleni, nayi maza na sauke kaina. Yawake kuwa sai murmusawa yake yi, babu halamar fishi ko tunzura akan ashariyar dana narko mishi. Kallon su jamilu yayi yace.
"Ku tashi ku tafi, na sallameku Allah yayi muku albarka, ayi haƙuri kuma a yafi juna. Komai ya wuce yaran kirki" sai washe baki Yawale yake yi, nasan dukiyar hannunsu yake kallo kawai. Ina kallo yaran suka watse, ai fitarsu ke da wuya na miƙe.
Yawale bari kaji in faɗama, aure ni da kai ya ƙare daga yau, yau kaji kana son ka sake mayar dani matarka, sabida yarana sun samu arziki. Ni kuma ina baƙin ciki kaci dukiyarsu. Har hake cewa wai duk abinda suka kawo mun su ba Kumatu. Da kai da Kumatu Allah ya tsine muku albarka, ƴan iska, ƴan kutumar uba. Kuma wallahi babu ɗana guda ɗaya da zaiyi aure a zuriyarka. Yarona daya salwanta sanadiyyar sharrin da Kumatu tayi mishi. Bazan yafe ba, sai wutar Allah ta ciku." Da Yawale da Kumatun duk baki suka buɗe suna kallona. Dan na fusata ainun, shi kuma Yawale sai lallashina yake yi, sabida yana son cin banza. Kumatu tace.
"Musina Yawalen kike zagi haka? Wani mugun kallo na jefa mata nace.
"Dake dashi kun yayimi ƙwanyar bura ubanku, wakilin ɗaurin aurenku yaci uwatai. Haka na fice a ɗakin kamar kububuwa, ina huci dan jikina har kyarma yake yi mun, na koma nawa ɗakin. Duk yaran suna tsaitsaye sunyi cirko_cirko. Su kansu basu taɓa ganina a cikin irin wannan yanayin ba. Hakanne ya tilasta musu yin shiru, gudun karsu faɗi wani abun da zai kuma tunzurani. Kulu ta kasa tafiya gidanta, da dukkan halamu kwana zata yi, matan duk suka baibayeni"




Mrs Bukhari
[08/04, 19:57] Mrs Bukhari: GAWURTATTU UKU
Lamba ta Ashirin da ɗaya


BAKORI:


Laila:
Da idanu nabi Shehu ina karantar yanayinshi kawai.
"Laila tunda babu gaisuwa ina wuni" murmushi nayi mishi, na miƙa mishi Ɗahiru, yasa hannu ya karɓeshi yana kallonshi, take sai fuskarshi ta sauya, daga fara'a zuwa akasin hakan.
Ina Wuni Shehu, kazo lafiya?"
"Lafiya lau Laila. Kuma na fito jeji lafiyar Allah, harma an zaɓeni a matsayin wanda za'a bama kujerar sarkin mafarauta, har an saka rana. Sai dai ina fargabar abunda kaje kazo, sabida wannan yaron naki, zai iya kawo mun cikas a mulkina. Hakanne yasa zan ƙara aure Laila, harma an saka bikin namu, saura kwana goma cib." Banyi mamakin auren da Shehu yace zauyi ba, maganganunshi sunfi bani mamaki gaya. Auren mace sama da ɗaya haka addininmu yazo dashi, muddin in miji zai iya adalci a tsakani. Malam bahaushe yana girmama lamarin ƙarin aure sosai, musamman ga mu ƴan ƙauye, dan ɗan ƙauye iyakar jin daɗinshi ya ƙare a kwanciyar aure da mace ne, shi yasa suke girmama dare. Balle Shehu da yafi ƙarfina, dan nayi imani Shehu yafi ƙarfin mace biyu ma. Amma aurennan babu makawa zaiyi ne danya mayar dani bora, an gama canfani cewar ni mai farar ƙafa ce.
Allah ya sanya alkairi. Na taya ka murnar cin nasarar zama zakin mafarauta. Aure kuma Allah ya bamu zaman lafiya. Ina neman alfarma Shehu."
Jin ban ɗaga hankalina ba yasa Shehu ya sassauto.
"Ina jinki Laila" Nisawa nayi cikin ɗacin rai da ƙunan zuchiya nace.
Saura kwana goma muyi arba'in ina son ka ƙara mun kwana goma akai, sabida zanyi ziyare_ziyaren dangi na. Har can Dutsin ma nake son zuwa wajan Baba Kande." Kai ya sosa yace.
"Babu komai, zaki iya ƙara kwana goma akai ma, baki da matsala. Karɓeshi ki kwantar dashi, ni zan koma." Hawayen da nake dannewa ya zubo mun, ganin yanda yake nuna halin ko in kula akan Ɗahiru. Nasan ni da Ɗahiru cikin garari zamu yi rayuwa a hannun Shehu, ga aure zaiyi sabida ya samu kwanciyar hankali a wajan matar da zai aura. A tunaninshi ma na gama tashi a aiki, tunda ya gama buɗani, ya nakasa mun ƙafata, tawa ta ƙare ko? Hmm maza mutanen mu ( Allah ya gafartama Aisha Ɗan kano) Kallona yayi yace.
"Hmm Laila kenan, ashe ba zaki godemun ba dana zaɓi in ƙara aure ba tare dana sakeki ba? Kinsan irin iftila'in dazai shafeni a sanadiyyar wannan abun da kika haifa kuwa, baki da labarin yanzu haka a gida, amma daina sayen kayan siyarwan da su Baba suke sayarwa, sabida baza'a iya aiko yara ba, shine har kina da idanun kuka dan zan ƙara aure, me yasa mata baku da adalcine ku, baza ku tausaya ma maza ba?" A al'adance laifine babba in ɗago in kalli Shehu ma a yayin da yake cikin fishi, in kuwa na mayar mishi da martani, tamkar na aikata wani zunubine mai girma. Dole na haɗiye maganganun da Shehu ya dinga yaɓa mini, a wajen ya fita ya barni, Ɗahiru na rungume a hannuna. Ina jiyo Shehu na gaisawa da Malam daya shigo yanzu.


Shehu:
"A Shehu kaine a tafe da rana haka?" Cewar malam. Shehu cikin girma da ladabi ya gaishe da malam, yake kuma labarta mishi batun zaiyi aure nan da kwana goma. Su Daddo suna tsakar gidan suna jiyo su. Malam yace.
"Naji labarin a wajan Buba, dan jiya na shiga Dutsin ma ɗin naje cin kasuwa. Kuma ya labarta mun komai. Fatanmu yarannan Allah ya basu zaman lafiya a tsakaninsu kawai. Ina taya ka murna Sarkin mafarauta" Dariya da Shehu da malam suka saka, yayi musu sallama ya fita.


Ta Asibi:
"Malam ni na kasa gane wannan zarwancen da kuke yi da Shehu fa" Murmushi Malam yayi, tare da nufosu. A gefensu ya samu waje yaima kanshi mazauni.
"Auren da Shehu Zaiyi ba kowa zai Aura ba, sai Asiya ƴar Kande ƙanwarki Ta Asibi. Malam Buba mahaifin Asiyan ya shaida mun, wai sunfi shekara guda suna nema. Shehun ya auri Laila da kaɗan suka soma nema. Abunda Allah ya nufa, Annabi sai ceto. Daddo tace.
"Asiya dai ɗiyar ƙanwar Yaya uwa ɗaya uba ɗaya, ita Shehu zai aura Malam? Ai ana barin halas dan kunya, duk matan da suke a gari, baiga wacce tayi mishi ba sai Asiya, yarinyar da taje birni ta gama buɗe idanunta a gidan aiki da aka kaita. Ta Asibi tama rasa tacewa, ta rasa dalilin da yasa ƴar uwarta bata ƙaunar farin cikinta, gashi su biyu rak iyayensu suka haifa. Taso ta Auri malam Zangina dan taso ta ribaceshi ya jiya ma Ta Asibi baya. Amma da yake yafi sha'awar mace mai alkunya ne yasa yaima Kande tawaye. Da bata samu hakan ba saita ƙulla zazzafar gaba da ƙiyayya a tsakaninta da ƴar uwar tata. Ta Asibi kasancewar itace babba, sai taita yin haƙuri da halayyar Kande, taci gaba da janta a jika, taci gaba da ziyartarta tana kuma yi mata alkairi. Shine daga baya ta saki jikinta, ashe ta ciki na ciki. Baƙin ciki Ta Asibi ta dinga haɗiya. Malam yace.
"Ta Asibi naga kin ƙume, abinda nake so dake shine. Kuyi haƙuri ku duka, kuma ku taushi zuchiyar Laila ta daure tayi ma Shehu biyayya akan auren ƴar uwarta da zaiyi. Taci girma ta kame kanta a matsayinta na babba. Kuma, ku daure karku nuna ma Kande wani abu na sosuwar rai, gudun lalacewar zumuncinku, da Laila da Asiya duk naki ne. Abinda Shehu yayi ba laifi bane, tunda ba Allah ya saɓa ma ba. Sai dai yin hakan ya kaucewa al'adar malam bahaushe mu da aka sani da yakana da alƙunya. Kande zata zo yau haka Malam Buban ya faɗa mun." Yana kai aya ya kurkure bakinshi da ruwan buta yaja langar abincinshi, ya soma cin gwaɗon zogale. Bai idasa gama cin zogalennanba saiga sallamar Kande da ɗan buhun kayanta a ƙunshe, Asiya na biye da'ita. Ta Asibi ta kallesu dukkansu tana jin wani zafi da zugin Kande. Malam Zangina ne yai mata ido, saita ɗan saki fuskarta.
"Kande kune tafe a kwanɗeɗiyar ranar nan? Maraba lale, sannunku da zuwa Asiya" Cewar Daddo kenan dan Ta Asibi ta kasa iya sarrafa harshenta balle tayi musu sannu da zuwa. Kande ta ya da buhun kayanta, tana faɗin.
"Wash Allah makashin kakata Rakiya. Malam Zangina yau baka fita kasuwar bane?" Cikin girma yace.
"Nafita. Abinci dai nadawo inci, sai in koma Jafaru shima saiya je yaci. Sannunku da Hanya." Gaggaisawa akayi dukka. Malam Zangina ya wanke hannunshi, yai musu sallama ya fice."


Laila:
Ina tsaye ina share hawayena, na jiyo shigowar Inna Kande, kasancewar tana da ƙarfin murya. Da sauri nashare hawayena. Na shinfiɗe Ɗahiru na fita.
Inna kune a tafe? Asiya hmm ai nayi fishi wallahi kuwa" Kusa da Inna Kande naje na zauna,muka gaggaisa. Baki ɗaya saina kasa gane ma Asiya dan ko fara'a taƙi yi mun. Saɓanin da, da in muka haɗu tamkar zamu cinye junanmu, hira kuwa sai mun raba dare munayi. Saita tunomun zance da take rakani wajan Shehu in yazo, muita wasa da dariya. Maganar Inna Kande ce ta katse mun tunanina.
"Laila ashe mata maza kuma muka samu? Kaik abun baiyi daɗi ba. Dan samuwar yaronnan zai iya taɓa duniyarki, an riga an canfa irin haihuwarsu." Dam gabana ya faɗi har nake jin hawaye na shirin subce mun. Daddo tace.
"Wannan duk canfinmu ne Kande na malam bahaushe. Ba wani abunda zai samu Laila sanadin haihuwar yaronnan sai alkhairi. Ke Laila shiga ɗaki jikinki ɗanye ne. Yanzu ma zanzo muyi wanka. Kici gaba da kwanciya a gadon ƙasannan." Jikina a saɓule na miƙe, kobi ta kan Asiya ban sake bi ba.


Ta Asibi:
"Sai muka ji biki Malam yana shaida mana, ashe Asiya Shehun Laila zata aura? Shehunma bai jima da tafiya ba. Allah ya sa gidan zamanta ne" Cewar Ta Asibi kenan. Kande duk rashin kunyarta sai taji nauyi ya rufeta, nan ta shiga kame_kame dasokiburutsun zance"
"To ya zanyi. Buba ne ya ɗaure mata gindi. Har duka nayi mata, amman ta kafe sai shi. Wai tun lokacin bikin Lailan suka soma maganar aure. Yaya Abinda Allah ya nufa saiya faru. Masu iya magana sukance matar mutum. Shine na tawo da'ita zan kaita wajan Laraba ta zauna a can, ta dinga yi mata ƙunzugun lalle. In yaso in bikin ya rage kwanaki, saiki tawo da'ita Yaya" Da Daddo da Ta Asibi sun sha ruwan mamaki. Amman haka suka kanne, Kande ta kwana washe gari ta juya. Ta Asibi ta ɗauki Asiya ta kaita gidan Laraba. Kwananta bakwai a gidan Laraba, ana takwas ne Ta Asibi dasu Nazeefa suka ɗunguma zuwa Dutsen ma dan gudanar da biki. Laila tana nan gaho bata san wa Asiya zata aura ba. Har sai bayan da aka kammala biki Amarya ta tare a ɗakin angonta. Sannan suka zaunar da Laila dan faiyace mata halin da ake ciki.




Laila


Mrs Bukhari




[27/01, 11:04 am] BADI'T IBRAHIM: *_🔥GAWURTATTU UKU🤟2023_*


*_TALLAH TALLAH TALLA🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️_*


_A HAYYEH SAMAH MATAH💃💃💃💃💃🏻💃🏻_
*Ku shiga wannan link ɗin don zaɓar kaya masu rahusa👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻*
https://chat.whatsapp.com/G6BmHCxso0rDZyWVQGgYYj
----------
No
07067964894


*_INA KUKE MATAN KWARAI MATAN DA SUKA AMSA SUNAN SU NA MATA A DUNIYA KU GARZAYO KUZO M A C DON ZABEN NA KWARAI KI DAURA ASAN KIN DAURA SAI ATAMFA DA LACE DA SHADDA, MATERIAL WITH SHOE'S AND BAG WITH JEWELRIES DAGA MAMAN ANNUR COLLECTION._*
*_ANAN KWALIYA ZATA MAIDA KUDINTA GAREKI, KIFITO ASAN KIN FITO KIN FASA TARO SAI M.A.C AKAN FARASHI MAI RAHUSA SAYEN NAGARI MAIDA KUDI GIDA IYA KUDIN KI IYA SHAGALINKI🤝_*
*_TANA KANO TANA AIKAWA KO INA DA IKON ALLAH A CIKIN AMINCIN DA YARDAN UBANGIJI_*
*_YAN UWA INA MASU SON SUYI SANA,A BASU DA JARI TOH GA DAMA TA SAMU, INJI MAMAN ANUR DON ZAKU IYA DAUKAN KAYAN MU KU TALLATA KU DORA NAKU RIBAN SAMA ZAMU AIKA MAKU KAYA GA MAISHI DA SUNAN KU A DUK INDA CUSTOMER DIN KU YAKE BA TARE DA MUYI SAVING NO BASHI BA KUMA BA ZAISAN BA DAGA WURIN KI KAYAN YA FITO BA TAKEN MU GASKIYA DA AMANA, MUM ANNUR COLLECTION DA KARAMAR RIBA MUKA DOGARA SABODA NEMAN ALBARKA SAI KUN ZO 👏👏👏👏👏_*
[27/01, 11:04 am] BADI'T IBRAHIM: Gawurtattu uku,zasu buɗe aji na musamman da azumi,don koyar da girke girke na musamman na azumi don kun san mu mata ƴan adone,wajen yin girki in akace baki iya girki ba to tabbas mijinki fa kullum yana kan hanyar yawon restuarent, sannan idanuwansa suna kan ƴammata saboda ya samu sarauniyar girki, kada ki bari a barki a baya don gwangwaje me gidanki.


Domin nema ƙarin bayani,sai ku tuntuɓi waɗannan numbobin👇🏻👇🏻


07068606171
08104335144
08179523215


💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻


*🤟GAWURTATTU UKU A SABUWAR SHEKARA TA 2023🤟*
*_Ina kuke masoyan gawurtattu uku ga su ssun dawo muku da wasu sabbin labaransu a wannan sabuwar shekarar, wannan karon salon gawurtacce ne, ku hanzarto kar ku sake ayi babu ku._*
_Sun shirya tsaf a wannan karon don kawo muku labaran da zakuyi fahari da su, tafiyar mai zafi ce sannan ta musamman._


*_Haziƙai kuma gawurtattu ukun sun shirya ne domin kawo muku gwarazan labaran da zaku yi alfahari da su._*


*MATA IYAYEN GIJI*
_Mrs Bukhari_




*INDA BA ƘASA..!*
_Ummu Maheer_




*KARO ƊAYA...!*
_Ummu Affan_




_LITATTAFAN GABAƊAYA AKAN FARASHI MAI SAUƘI DA RAHUSA 1K_




1 500
2 700
3 1000


_Kai tsaye zaku tura kuɗinku ta wannan account number ɗin._
2212328303
RABIATU BASHIR
Zenith bank


_Don Allah wannan karon ba ma buƙatar katin waya, idan baka da account to kaje POS ka bada 50 kob 100 a cikin kuɗin a turo ta account number please._




_Ƴan ƙasar Niger kai tsaye zaku turo ta nan._ 0706 860 6171


*DOMIN NEMAN ƘARIN BAYANI A TUNTUƁI ƊAYA DAGA CIKIN LAMBOBIN NAN.*


0810 433 4144
0817 952 3215
0706 860 6171




*MUN GODE DA KASANCEWA DA GAWURTATTU UKU A SABUWAR SHEKARAR 2023 SABON SALO SABON TAKU.*


[08/04, 19:57] Mrs Bukhari: MRS BUKHARI
GAWURTATTU UKU


LAMBA TA ASHIRIN DA BIYU


LAILA:
"Laila ki buɗe kunnanki da kyau kiji me Daddonki zata faɗa miki. Kuma kiyi haƙuri da dukkannin abunda zaki ji." Innata tana kaiwa nan saita fice. Ni kuma jikina har rawa yake yi tsabaragen kaɗuwa, dama a daren jiya da aka ɗaura auren Shehu banko iya runtsawaba. Yanzu na gane dalilin matan da suka kasa tawakkali dan mijinsu ya ƙara aure, suyi hauka. Zafi da ciwon kishi, iyayen gida ne kaɗai ka iya ɗanɗana harsu gane abunda

Please Login or Register in order to submit comment