Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ganin Mami sai da akayi bincike Sosai Falonta datake ganin bak'i aka kaishi. Jin Yasir neh yasa batad'au wani lokaci bah ta shigo falon tana fara'a


"Idonka knan Yasir, tun bayan election ban k'ara ganinka bah"

Duk'ar dakai yayi fuskanshi bah Annuri, ganin haka yasa Mami ta zauna a sanyaye

"Yasir meke faruwa?"

Labarta mata duk yanda sukai da Masroor yayi cikeda damuwa. Mami ta girgiza kai rai bace

"Lallai Masroor ka kyalleshi ai dai ba'achan zai xauna kwatakwata bah koh? Zai dawo ya sameni"

D'agowa Yasir yayi

"Mami Masroor nasan yarinyan nan sosai, ni ina tunanin tsabar k'iyaiya ce kawai da Mahaifinta yake mata yasa yace haka"

Jim Mami tai alamar tunani Sannan tace

"Nima ina tunanin haka saidai bah yanzu zamu tunkari Alhaji da maganan bah dan yanzu yayi fushi"

Yasir ya gyada kai ya mik'e tsaye tareda mik'a mata keyn motan Masroor. Amsa tai tamai godiya yabar gidan...

Kuka sosai Sulthana take tana gudu batareda tasan inda zata bah, gashi gari ya fara duhu dan anata kiraye kirayen Sallan Magriba. Bata farga bah Ruwa ya tsuge kamar da bakin kwarya sam bata lura da hadari bah. Cigaba tai da gudun lokaci lokaci tanasa bayan hannunta na hagu tana share hawayen Fuskanta. Hasken Fitilan motane ya haskata ko kamin tai wani yunkuri tuni motar tai ciki da ita ta fadi k'asa sumammiya...

Ummy Abduol✍🏻

💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐

By *Ummy Abduol*


*DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION*

_Mak'i Gani Ya Kauda Idonsa_

*Page 156 to 160*

Dedicated dis page to *Hadiza Ya'u* best fan.. Allah ya bar zumunci


Hasken fitilan motane ya haskata ko kamin tai wani yunk'uro tuni tayi ciki da ita ta fadi K'asa sumammiya. Dasauri ya fito daga motan hankalinshi tashe, Ganin wanda ke wajan yayi baya da sauri da Alamar mamaki. Nunata ya soma y bakinshi na rawa yace

"Su..Sulthana"

A hankali ya k'arasa inda take kwance ya d'auketa yasata a mota ya figi motan xuwa babban Asibiti dake cikin garin Kano inda yake aiki. Shi da kanshi ya shiga bata taimakon gaggawa duk da yanayi jikinshi na rawa zuciyarshi na bugawa, saida numfashinta ya daidaita sannan ya fita zuwa gidanshi kamin ta farka lokacin wuraren k'arfe goma na dare..

Sallah yayi Sannan yayi wanka duk hankalinshi na wajan Sulthana, wayanshi ya jawo ya soma neman layin Sa'ood yakoyi Sa'a yana fara ringing ya d'aga

"Aboki ya Akaine?" cewar Sa'ood

Murmushi Dr Fareed yayi suka gaisa sannan ya zaiyanamai abinda ke faruwa. Shiru Sa'ood yayi nad'an wani lokaci Sannan yace

"Yanzu abinda za'ayi gobe mu hadu a asibitin da safe lokacin ta farka sai mu tattauna"

Tho Fareed yace tareda mai godiya ya kashe kiran. Keyn motanshi ya d'auka ya rufe gidan ya koma asibiti, har yanzu bacci take. kujera yaja ya zauna kusada gadon datake kwance. K'allanta yake yana murmushi, hannunta na dama ya saka cikin mashi yana murzawa a hankali, a haka barci ya d'aukeshi ya d'aura kanshi gefen gadon..

Masroor na Sauka Lagos Airport, taxi ya shiga ya kaishi hotel dinda zai kwana. Yini yayi bah walwala koh abinci ya k'asa ci. Zuciyarshi Sunan Sulthana kawai take kira, Wayanshi ya janyo ya kunna sannan yasata a Fight mode dan baisan a nemeshi. Pictures d'in wayanshi ya shiga, hoton Sulthana ya dubo wanda ita batamasan an d'auka bah tana xaune tana murmushi da alama Gyada akazo siya

Shafa hotan ya soma yi hawaye cike a idonshi

"I love uh my beauty, meyasa kikamin k'arya"

Hawayen dake mak'alle a idonshi suka gangaro ya share tareda mik'ewa ya shiga toilet don watsa ruwa..

Sulthana bata farka bah sao wuraren k'arfe bakwai da rabi na safe. Firgigita ta mik'e zaune, bin dakin da Kallo ta soma yi cikeda mamaki. Ganin kan mutum kusa da ita yasata kwace hannunta tareda sakin ihu, tana k'okarin sauka daga kan gadon..

Farkawa Fareed yayi ya mik'e yana k'allanta da Murmushi

"Meya faru? Y are you shouting"

Drip din hannunta take kici kicin Cirewa tana k'allanshi a tsorace, rik'e hannunta yayi dasauri ganin tana kokarin jima kanta ciwo

"Me kike kokarin yi, ki kwanta bakida lapia neh"

Girgiza mai kai tayo hawaye na fita a idonta dak'yar da budi baki tace

"Ni ka ciremin wannan abin na tafi, ina neh nan? Waya kawoni"

Jin tashin Magana yasa Wata nurse ta shigo dak'in ganin dr Fareed yasa ta koma dasauri tana cewa

"Sorry sir"

Baice komai bah ya maida dubanshi ga Sulthana dake kuka a hankali

"Jiya da Daddare na bigeki a mota shine na kawoki asibiti, ina zaki da daddaren nan Sulthana"

Sai a Sannan ta tuna koran da Baffa ya mata, wani sabon kukane yazo mata, ta kauda kai gefe tana kuka kamar ranta zai fita. Runtse idonshi yayi ya naushi Iska ya fice daga Dak'in, Nurse dinda ta leko yama magana akan karta bari ta fita Sannan ya fita zuwa haraban asibitin. Motarshi ya hau ya figeta yabar Asibitin

Gidanshi ya nufa saida yayi wanka sannan ya k'arya duk abinda yakeyi jikinshi a mace yake. Wayan Sa'ood ya kira yace su hadu k'arfe tara a asibiti. Yana gama wayan yad'au keyn motarshi ya fice. Gidansu ya nufa batareda dogon bincikeba saboda securitys din sun sanshi aka barshi ya shiga gidan..

Mottoci ya gani kusan guda biyar a haraban gidan cikin shiri, da wasu mata dake gefe da Alama Umma suk'e jira. Side din Umman ya nufa kai tsaye dan yasan yanzu Abba ya fita zuwa Office, Bai sameta ta falo bah sai ma'aikata daketa gyara Falon. Benen dake falon ya hau a nan suk'ai kicibus da ita cikin shiri da Alama fita zatayi

"Good Morning Umma" yace kanshi a k'asa

Tsayawa tai chak sannan tace

"Morning"

Jin tayi shiru yasa yad'an dago suka hada ido

"Fareed Meke damunka?"

Wayancewa yayi

"Babu komai me kika gani"

Hannunshi ta kama suka sauko k'asa. Ma'aikatan na ganin haka sukabar falon dasauri, zaunar dashi tai kan 1seater itama ta zauna ana kusa dashi

"Fadamin meke damunka? Bah haka ka saba zuwa bah"

D'an murmushi yayi

"Bbu komai Ummah i'm fine bah abinda ke damuna."

Bayaso ta cigaba da tambayatan shi dan haka yace

"Ummah inace ke ake jira a waje"

Mik'ewa tai dasauri

"Eh wallahi, zamuje mu hadu da Matar governor zamuje wani meeting neh"

Kai ya gyada yana y'ar murmushi

"Allah ya tsare, kice ina nan zuwa na gaidata"

Hararanshi tai cikin sigan wasa

"Ni y'ar aikenka ce?"

Dariya yayi k'asa kasa yana shafa sumar kanshi
Sallama tamai ta fita. Shima mik'ewa yayi shima yabar gidan.

Saida ya tsaya yasai mata abinci mai rai da lafiya sannan ya koma asibitin. Patient ya gani burjik sunata jiranshi, saida ya tsaya suka gaggaisa sannan ya nufi dakin da Sulthana take kai tsaye.

Zaune ya sameta kan gado ta hada kai da guiwa tayi shiru. A hankali ya k'arasa kusada gadon yaja kujera ya zauna, zabura tai ta d'ago idanunta da suka runne tana k'allanshi. Harta bud'e baki zatai magana kuka yazo mata ta k'auda kai gefe tana kukan a hankali..

Runtse ido yayi ya bud'e tareda aje mata abincin a kusada ita

"Kici abinci sai kisha magani barin duba patients"

Bai jira mai zatace bah ya bar office din. Kamar yanda suk'ai da Sa'ood k'arfe tara ya k'araso Asibitin lokacin ya gama duba patients dinshi. Fareed ne yama Sa'ood jagora zuwa dak'in, yanda ya barta haka ya dawo ya sameta bata taba abincin bah. Nunama Sa'ood kujera yayi ya zauna shi kuma ya tsaya a tsaye.

Sa'ood ya nisa yace

"Sulthana!"

Kai ta d'ago ta kalleshi shi kuma ya cigaba da cewa

"Ki kwantar da hankalinki bazamu cutar dake bah"

Fareed ya nuna da hannu yana cewa

"Nasan kinsan wannan, ki fadamin meya fito dake jiya da daddare har ya bigeki da mota"

Hawaye ya cika mata ido ta k'auda kai gefe murya chan k'asa tace

"Bah komai"

Murmushin takaici Fareed yayi tana girgiza kai. Sa'ood ya cigaba da cewa

"Karki boyemana komai Sulthana, munsan halin da kike ciki keda Baffanki so ki fada mana meke faruwa? dukanki yayi ko meh?"

D'agowa tai ta kalleshi da mamaki. Murmushi Sa'ood yayi dan ya gane k'allan datake mai

"Kina mamakin y'anda akai muka sani koh?"

Kuka ta saki tana cewa

"Baffa ne ya koreni daga gida yace bashine babana bah wai banida..."

Kukane yaci k'arfinta. Sakin baki su Fareed sukai da mamaki

"Bashi ya haifeki bah?" cewar Fareed

Kai ta gyada kanta a k'asa tana cigaba da kuka. Lallashinta Sa'ood ya soma yi dakyar tai shiru, ya mik'e ya kama hannun Fareed suka bar dakin. Wata nurse Sa'ood ya samu budurwa wacce bazata wuce shekara ashirin bah da gani y'ar practical ce yasa hannu a aljihu ya ciro kudi masu tsoka ya mik'a mata

"Inaso ki kulamin da patient din dake dakin chan"

Ya nuna dakin da Sulthana ke ciki sannan ya cigaba da cewa

"Tak'i cin abinci neh inaso kisata taci abinci pls and banaso tana kuka"

Kudin ta amsa tana washe baki

"Bbu damuwa sir za'ayi kamar yanda kace"

Office din Fareed ya shiga ya sameshi zaune yayi tagumi. Sun dad'e suna tattaunawa Sannan Sa'ood ya mik'e tareda mai Sallama yabar Office din.


Saida Sulthana tai kwana hudu a Asibiti kullum tana tareda Nurse dinda Sa'ood ya barma amanarta, Sun saba sosai dan Sulthana batada wuyan sabo har tad'an saki ranta.

Kayan sawa kala kala Fareed ya saima Sulthana, sister Aisha ita ta koya mata yanda ake saka kaya da sauransu. Randa ta cik'a kwana shidda aka sallamesu a nan neh hankalin Fareed ya tashi dan baisan inda zai nufa da Itabah..

*wai ina labarin Masroor neh?*

Ummy Abduol✍🏻

💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐

By *Ummy Abduol*


*DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION*

_Mak'i Gani Ya Kauda Idonsa_

*Page 161 to 165*

Randa ta cika kwana shidda aka sallamesu a nan neh hankalin Fareed ya tashi dan baisan inda zai nufa da itabah. Yanke shawara kawai yayi ya kaita gidanshi dan haka ya juya akalan motarshi zuwa gidanshi...

A bangaren Masroor kuwa kwanashi Biyu a Lagos sannan jirginsu ta d'aga zuwa k'asar turkey. Karatunshi ya cigaba dukda har yanzu san Sulthana na nan mak'ale a zuciyarshi. Mami da Daddy sun kirashi sun mai fada sosai akan rashin Sallamasu da baiyi bah, kullum yakan zauna yayita tunanin Sulthana gani yake kamar bai mata adalci bah daya taho ya barta batareda ya mata Sallama bah.

Yau ya kama sunday yana zaune a gidanshi bayan ya dawo daga supermarket. Waya ya d'auka ya soma neman layin Yasir, bugu d'aya ya dauka suka gaisa. Shiru Masroor yayi nad'an seconds sannan yace

"Alfarma nake nema Yasir"

Batareda bata lokaci bah Yasir yace

"Ok babu damuwa"

Ajiyan zuciya Masroor yayi sannan yace

"Dan Allah Yasir inaso neh kaje min wajan Sulthana, she's always on my mind. Kullum zuciyana bugawa yake gani nake kamar wani abu ya faru da ita"

Saurin katseshi Yasir yayi da cewa

"No stop saying that, babu komai insha Allah"

Runtse ido Masroor yayi sannan ya bud'e, Yasir ya wuce aboki a wajanshi ya wuce Amini ya zama hamimi. Bah abinda zai iya boye mai, zaiyana mai duk yanda Sukai da Fareed yayi hankalinshi tashe..

Yasir yayi murmushi yana cewa

"Oh friend wani tabbaci kake dashi akan cewa Sulthana ce"

"Naji a jikina itace Yasir, idan har Fareed santa yakeyi bansan yanda zanyi bah I cn't live witout Beauty"

"Ka kauda wannan tunanin a ranka pls"

Kai Masroor ya gyada kamar yana ganinshi

"Shiknan sai na jika"

Sallama sukai tareda kashe kiran..

A kauye kuwa Mama na fita Ameenatu ta bita a guje tana kuka bako hijabi, hannun Mama ta rik'e

"Dan Allah Mama karki tafi, idan kika tafi dawa zamu zauna"

Kuka itama Maman keyi

"Ameenatu bazan zauna bah, duba fah abinda Mallan yayi yanzu kina kallo, wannan wanne irin k'iyaiya neh?"

Ameenatu ta share hawayen idonta da bayan hannu

"Kiyi haquri Mama karki tafi dan Allah, nasan Sulthana batai nisa bah zan dubota nidai ki koma gida"

Hannunta ta kama suka koma cikin gidan, dakinsu ta shiga ta samu hafsatu zaune kan gado tana nunke kaya

"Hafsatu komenene ya faru Sulthana K'anwarmu ce, kada ki daka ta baffa dan abinda ya fada bah gaskiya bneh. Ki natsu kiyi tunani kada rud'in duniya ta kwasheki, ranar danasani nake gudan miki Hafsatu, ranar da batada wani anfani"

Dagowa Hafsatu tai tana K'allan Ameenatu fuskanta bah walwala da Alama magananta ya fara tasiri. Ameenatu ta zauna kusada ita ta rik'o hannun hafsatu tana hawaye

"Hafsatu ke k'anwata ce kamar yanda Sulthana take kanwata. Haka kema Sulthana kanwarki ce, bai kamata muk'i yar uwarmu bah jinnin mu ce ki tuna"

Hawayen idonta ta share tana jan magina

"Kinyi karatun Addini daidai gwargwado akwai hadisi da manzo Allah tsira da Aminincin Allah su tabbata a gareshi yake cewa imanin d'ayanku baya cika har sai kasowa d'an uwanka abinda kakd soma kanka. Kiyi tunani cikinmu bah wanda yakeso ya kasance cikin rayuwar da Sulthana take ciki bama muba har y'ayanmu"

Hawaye ne suka gangaro daga idon Hafsatu

"Haka neh ya Ameenatu, tho menene dalilin Baffa na cewa Sulthana bah y'arshi bace"

Girgiza kai Ameenatu tayi

"Ki cire wannan Maganan a ranki, bah gaskiya baneh wannan"

Hafsatu ta mik'e tana share hawayen Fuskanta

"Yaya Ameenatu yanzu ya zamuyi? Gashi Baffa ya koreta"

Itama ta mik'e tana cewa

"Zamu fita neh nemanta ta dawo gida mu zauna mu nunama Baffa rashin Amincewan mu akan abinda yake mata"

D'aukan Hijabi hafsatu tai suk'a fito tsakar gidan, a nan suka samu Mama zaune tayi tagumi, basuxe komai bah suka fita suka soma nemanta.

Duk inda suke tunani Sulthana zatace bah inda basu jeba anma duk maganar d'aya ce batazo bah. Hankalinsu bah k'aramin tashi yayi bah, koda Suka samu Mallan sani Aminin baffa da maganan bah K'aramin Mamaki yayi dajin abinda Baffa Yayi bah.

Sadiya sai kuka take jin k'awarta ta bata, haka ma Mamanta ta shiga Cikin tashin hankali sosai. Ganin hadarin dake garin yasa suka dawo gida duk'ansu jikinsu a sanyaye. Tun daga nesa suke hango Almajirai tsaitsaye a kofar gidansu, dasauri suk'a karasa aka matsa musu suka shiga cikin gidan. Nan ma mutane suka gani zagaye, Hafsatu ce ta k'usa ganin Baffa tayi kwance kan tabarma yana numfashi Sama sama Mama na kusa dashi tana kuka..

Hankali tashe Hafsatu ta shiga tambayan meya faru, Mama ce ta bata amsa da cewa

"Wai a bakin Masallaci ya fadi shine aka kawoshi gida"

Ameenatu ta k'araso wajan ta tsugunna kusada Baffan itama tana hawaye

"Allah gamu gareka, idan Laifi mukai maka Allah ka gafarce mu. Mun tuba, Mun tuba.."

Kuka take sosai tana k'allan Baffa dake kwance rai a hannun Allah. mutanen dake wajan kowa ya watse aka barsu su kadai sunata kuka..

Da taimakon Babban Almajirin Mallan da wasu almajirai aka shiga dashi d'akinshi saboda hadarin dake garin..

Magani aka hau yima Mallan Anma kamar ba'ayi, mallan Sani duk inda yaji Mallami sai ya nemoshi ko ya amso maganin Anma Abin dai gaba yake. Su Ameenatu da Hafsatu idan ka gansu gwanin ban tausayi, abu ya hadu musu biyu ga rashin Sulthana ga rashin Lapian Baffa...

Mallan ya koma kamar bashi bah ko magana baya iyayi, idanunshi kullum a bud'e yana k'allan sama komai saidai aimai baya iya komai... _niko Ummy Abduol cewa nai Allah ya k'ara_


Fareeda yayi Parking a haraban gidanshi ya d'an kalli sulthana daketa bin Gidan da Kallo

"Muje koh?"

Bah musu ta bud'e kofan motan kamar yanda taga yayi dazu ta fito shima ya fito suka nufi cikim gidan. Kofan main palour ya bud'e Ya shiga Sulthana na biye dashi, zama yayi kan Kujera ita kuma ta zauna k'asa kan Carpet ta makure tana bin Falon da Kallo cikeda kauyanci

"Meyasa kika zauna a k'asa tashi ki zauna kan kujera, ki saki jikinki ki rink'a min magana kinji"

Kai ta d'aga ta mik'e ta zauna k'an kujera tana cigaba da bin Falon da k'allo. D'an dariya yayi k'asa kasa yace

"Falon ya miki kyau neh?"

Murmushi tayi wanda saida dimples dinta suk'a lotsa. Kallanta ya tsaya yi ganin irin kallan dayake mata yasa ta duk'ar dakai. mik'ewa yayi yaja Trolleyn kayanta Yana cewa

"Taso na nuna miki"

Bah musu ta mik'e tabi bayanshi, wani bedroom dake hannun dama ya bud'e ya shiga juyawa yayi bai ganta bah ya lek'o ya ganta bakin kofa tsaye yace

"Shigo mana"

Zuciyanta na bugawa ta shiga dakin, wow tace a ranta dan tunda uwarta ta haifeta bata taba ganin daki mai kyau irin wannan bah. Murmushi ya mata ya kamo hannunta ya zaunar da ita kan katafaren gadon dake dakin

"Meyasa kike d'ari dari dani neh. Bazan cutar dake bah, daga yau nan neh dakinki"

Batasan lokacinda ta saki lallausan Murmushi bah har saida Fararen Hak'oranta suka baiyana

"Dagaske?"

Shima murmushin yayi dan Yaji dadin yanda tad'an saki ranta. Gani yayi kuma ta bata fuska tana k'okarin kuka, hankali tashe yace

"Menene"

Bai ankara bah ta fashe da kuka tana shesheka

"Shiknan bazan koma gidanmu bah? Meyasa Baffa baya sona. Dan Allah kaje ka bashi hakuri idan namai laifi neh, ni y'arshi ce"

Tausayi ta bashi ya zauna kusada ita tareda rik'o hannayenta

"Ki daina kuka, insha Allahu nan bada dad'ewa bah komai zai daidaita zaki koma wajan Baffanki kinji"

Kai kawai ta gyada tana cigaba da matsar k'walla. Kawar mata da damuwan yayi ta hanyar cewa

"Tashi na nuna miki yanda ake anfani da komai"

Bah musu ta mik'e tana binshi a baya, da cikin d'akin suka fara sannan suka shia toilet nan ma ya nunnuna mata suka fito zuwa sauran sauran wurare dake cikin gidan..

Ummy Abduol✍🏻

💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐

By *Ummy Abduol*


*DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION*

_Mak'i Gani Ya Kauda Idonsa_

*Page 166 to 170*


Kwanan Sulthana Uku a gidan Fareed, Kullum cikin tunanin Y'an uwanta take dakuma Masoyinta Masroor, takanyi kuka idan ta tuna koranda Baffa ya mata da kuma gudunta da Masroor yayi. Har yanzu sanshi da kewanshi na mak'alle a zuciyarta, bah lefi cikin kwana ukun sun d'an saba da Fareed yakan jata da hira duk da ba wani amsan kirki take bashi bah.

Aranan na hudun Sa'ood yazo gidan suna zaune a falo suna hira Sulthana na dak'i tana barci. Sa'ood ya nisa yace

"Magana nakeso muyi dakai Fareed"

Gyara zama Fareed yayi Sannan yace

"Ina jinka"

Sa'ood ya soma magana yana k'allan Fareed

"Zamanka da mace ku biyu bah abu baneh mai kyau, shedan ake gudu."

Ajiyan zuciya Fareed yayi

"Gaskiya neh Sa'ood, saidai kasan Matsalan Ummah bazata taba yarda Sulthana ta zauna da ita ba kuma ma kagani yanzu bah zama take bah"

Shiru Sa'ood yayi yana tunani chan yace

"Dole mu nemi mafita dan wannan bah abu mai yuwuwa baneh"

Fareed ya d'ago yana cewa

"Ga shawara"

Sa'ood ya ce

"Ina jinka"

"Mezai hana nasata a boarding school har zuwa sanda zan sanar da Abba da ummah"

Murmushi Sa'ood yayi

"Yes haka ya kamata"

Sun aje akan ranar monday da Sassafe zasu kaita zaria academy dan mata registration..

Abubuwan sunma Yasir yawa gashi kullum sai Masroor ya kirashi akan Zuwa kauyensu Sulthana. Yau yana barin School kauyen ya nufa kai tsaye. Batareda wani d'ar bah yasamu Almajiri yace yamai Sallama da Sulthana. Almajirin yace

"Ai Sulthana ta b'ace ba'a ganta bah yanzu sati uku knan"

Hankali tashe Yasir yace

"Garin yaya?"

Almajirin ya tab'e baki yace

"Nima ban sani bah, andai ce Mallan ne ya koreta."

Ran Yasir ba karamin Baci yayi bah yace

"Mallan din na nan"

Yaran yace

"Ai mallan bashida lapia tun ranar data bace ya fadi a bakin Masallaci har yanzu bai warke bah"

Hannu yasa a Aljihu ya ciro d'ari biyu ya mik'ama yaran yana murmushi

"Gashi abokina nagode"

Amsa yaran yayi tareda godiya shi kuma ya shiga motanshi yabar kauyen Hankali tashe. Yanzu taya zai gayama Masroor wannan mummunan labarin.

Yini yasir yayi cikeda fargaban yanda zai fadama abokin nashi wannan labarin. Yakoyi sa'a bai kirashi bah sai washe gari, da kyar ya dauka suka gaida Masroor yayi saurin cewa

"Yasir kakoje?"

Shiru Yasir yayi har saida Masroor yace

"Kana jina kuwa?"

Ajiyan zuciya Yasir ya saki yace

"Ina jinka friend, naje anma ban samu ganinta bah"

Nan da nan Masroor ya rud'e ya shiga jeromai tambayoyi

"Meyasa baka ganta bah?? Bata nan neh? Ko taje talla?? Pls Yasir yimin magana uh sound strange"

Ta maza yasir yayi ya zaiyanema Masroor duk yanda sukai da Almajirin daya samu a kofar gidansu Sulthana. Wayan dake Hannun Masroor ne ya fadi hawaye suka cika idonshi, kuka ya saki mai sauti tana kiran sunanta da k'arfi. Neighbours dinshi suka fifito suka tsaya a bakin kofan hankalinsu tashe jin yanda yake kuka da k'arfi yana fashe fashe..

Saida yayi mai isarsa sannan ya mik'e idanunshi sunyi luhu luhu ya shiga toilet yayi alwala ya soma kai kukanshi ga ubangiji _oh Masroor I pity uh_

Washe gari da safe Fareed da Sulthana suna kan dinning suna breakfast kamar yanda suka saba y'an kwanakin. Maganan sata a makaranta ya mata. Tayi farinciki sosai daga baya kuma ta hade rai

"Yanaga kuma kin chanza meya faru?

Rau rau tayi da ido

"Yaya Fareed yanzu shiknan bazan k'ara ganin Mama da yaya Hafsatu da yaya Ameenatu bah"

Goshinshi ya dafa

"Oh God! Sulthana ki cire wadan nan mutanen a ranki su basa sanki kece kawai kika damu dasu"

Hawayen dake makalle a idonta suka zubo tana girgiza

"Ina Sansu Yaya Fareed suma suna sona"

D'an jim yayi ya mik'e yana cewa

"Shiknan yanzu dai bansan kukan, ki shirya gobe da Sassafe zamu tafi. Idan akai hutu saiki je"

Ihu ta saki tana Y'ar Murmushi

"Nagode Ya fareed"

Kai kawai ya gyada ya bar wajan a zuciyarshi yana raya. Lallai rashin kula da gata yasa Sulthana shiru shiru dan yanzu data d'an wartsake ya hango k'iriniya da shagwaba a idanunta..

Washe gari da wuri da wuri suka tashi, da kanshi ya shirya mata kayanta a trolley da duk abinda take buk'ata. Saida ya tsaya a wani babban supermarket yayi mata sayaiyya sosai sannan suka biya ta gidansu Sa'ood ya daukeshi suka nufi zaria..

Bayan gwajinda akai mata Mallaman sukace za'asata a js1 rok'onsu Sa'ood yayi asata a js3 saboda ta girma she is 15. Hakan ko akai saida akai mata komai aka kaita hostel dinsu sannan su Fareed suka dawo gida...

Haka rayuwa ta cigaba da tafiya. Ta bangaren Masroor kuwa
Kullum da tunanin Sulthana yake kwana dashi yake tashi, yanzu Masroor ya koma shiru shiru bashida hayaniya. Hoton Sulthana shi yazan mai tv, lokaci lokaci yakan sa Yasir yajemai Kauyensu Sulthana ko da wani labari gameda ita anma bbu. Yasir na matuk'ar tausayama abokin nashi hakama Mami dan Yasir ya sanar da ita duk abinda ke faruwa...

Sulthana taji dad'in makarantan sosai dan a ranar datazo tai k'awa mai suna Aisha ibrahim itama y'ar jahar kano ce. Yarinyar wani senator ne a gwamnatin dakaci yanzu. Y'ar gayuce sosai ga Rashin ji da Tsiwa, tasu tazo d'aya sosai da Sulthana, wajanta take koyan Abubuwa kamar karatu da sauransu..

*Bayan shekara d'aya*

Sulthana na hango tsaye a wajan makaranta sanye da k'ayan hostel hannunta Rik'e da trolleynta, ta k'ara tsawo da cika, fatanta ya murje tayi kyau sosai. gefenta k'awarta Ayoush itama tsaye da Alama hutu akai saboda yanda dalibai keta fitowa da jakunkunan su. Hira suk'e suna dariya chan saiga wata had'adiyar mota k'irar doddge tai parking. Fareed ne ya fito daga motan sabye da Farar yadi sai baza k'amshi yake. K'arasowa inda suke tsaye yayi yana y'ar murmushi,

"Am sorry Queen I know i'm late"

Zaumbure baki tai ta kauda kai gefe, dariya Ayoush take k'asa kasa ta gaidashi da kanta ta saka jakan Sulthana a motar sannan ta karasa inda take tsaye

"Queen kiyi haquri mana kuje kinji"

Murmushi Sulthana taima Ayoush suka rungume juna sannan Sulthana ta shiga yaja sai kano ta dabo..

Fushi Queen dinshi keyi dashi, bah yanda beyi bah daran ranar ta rakashi yanada Dinner anma taki wai ita barci take ji. Hakanan ya hak'ura ya kira Sa'ood sukaje tare..

Masroor ne xaune cikin jirgi yau cike yake da farinciki zai dawo nigeria wajan iyayenshi. K'arfe hudu na shidda na yanma jirginsu ya dauka a kano, koda ya dauko Yasir ya gani tsaye shida Mami da Umma'n Fareed sai wasu mata dake bayanshi dukansu fuskokinsu d'auke da murmushi..

Dasauri ya k'arasa ya rungume Mami cikeda farinciki sannan ya rungume Yasir sunama Juna Dariya. D'an rusunawa k'adan yayi ya gaida Umman Fareed ta amsa fuska a sake, Mahnoor ta fito daga mota da gudu itama ta rungumeshi

"I missed uh bro"

Kanta ya shafa yana murmushi

"I missed uh too lil sis"

Yasir ya k'araso wajansu yace

"Dare yayi muje gida kwayi maganan"

Hannun Mahnoor Masroor ya kama suka shiga mottoci

Please Login or Register in order to submit comment