Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

fah sai bro fareed ya rink'a kaini"
Kanta fareed ya shafa yana y'ar murmushi
"Sis ki bari idan akai hutu da kaina zanzo na daukeki kinji"
Kai ta gyada ta mik'e tabar wajan tana gungunai..

"Likita bokan turai aure fah?"
Sosa kai yayi kanshi a k'asa
"Mami na kusa, kiris ya rage"
Gyada kai Mami tai tana murmushi
"Gaskiya kah kyauta kaga wadannan"
Ta nuna Yasir da Masroor
"Sunk'i aure suna nan sai gantali"
Dariya mai sauti Yasir keyi ya dafa kafadan Masroor
"Mami ai shagwababen naki ya kusa, hmm zan baki labari anjima"
Dukan wasa Masroor yakai mai
"Mami k'arya fah yake"
Tabe baki tai ta kauda kai kudai kuka sani..

Fareed ya mike yana cewa
"Mami zan tafi, dama na shigo ne mu gaisa inada patients a asibiti"
Mami itama ta mik'e da Fara'a
"Kah gaidamin dah hajiya sai nazo, wallahi duk hidimar campaign din nan neh ya hanani zuwa"
"Ai itama bata zama kullum bata nan itama dai campaign din neh" cewar Fareed
Yasir yace
"Inafa zama wajan matan governor dana duty governor"
Dariya sukasa duka, Masroor da Yasir suka raka Fareed har Bakin motarshi, sukai Sallama ya tafi...

Lokaci nata tafiya, shakuwa sosai ta shiga tsakanin Sulthana da Masroor harda Yasir, kullum a bakin tasha suk'e haduwa da Masroor suyita hiransu har tayata Saida gyadan yake taitamai dariya wai bai iya badawa bah. A bangaren Dr Fareed ma yakanzo lokaci zuwa lokaci wajanta watarana ta fita wata rana bata zuwa, santa yake bana wasa bah. Yanke hukunci yayi kawai zai samu mahaifinta da magananta ko Allah zai dace.
Tareda abokinshi Sa'ood sukaje gidansu Sulthana, a k'ofar gida suka samu Baffa xaune yana koyarda Almajiransa. Suka karasa inda yake, yana ganinsu ya soma washe baki ganin zankadediyar motar da zukayi Parking.
"Sannunku da zuwa karku zauna a wannan tabarmar yara duk sun bata" cewar Mallan

Gida ya shiga jikinshi na rawa ya dauko sabuwar tabarma ya shinfida bakin kofa sannan yace
"Bismillanku ku zauna"
Zama sukai, Mallan ya mik'a musu hannu dan suyi musbaha, mak'e hannu sukai yaxe
"Aa mu gaisa mata ya haka"
Dak'yar Fareed ya mik'a mai hannu suka gaisa
Mallan yace
"Ban shaidaku bah"
Sa'ood neh ya duk'ar dakai yace
"Sunana Sa'ood sai Abokina Fareed" ya nuna Fareed daya duk'ar dakai yana murmushi
Sulthana ta fito gida rik'e da kofin silver, slippers dinta ta cire ta tsugunna
"Ina wuninku"
Sa'ood neh ya masa yana kallanta,
D'an dagowa Fareed yayi suka hada ido tai saurin dauk'e kai ta aje Kofin tabar wajan..

Sa'ood ya cigaba da Magana
"Mu y'an cikin garin Kano neh a gwanma ja, Mahaifinshi d'an siyasa neh, shike neman mataimakin Gwamna na wannan jaha. Shi kuma cikakken likita neh"
K'ara washe baki Mallan yayi

"Aa Madallah sannunku da zuwa, ina fata dai lapia"
Sa'ood ya k'ara duk'ar dakai
"Abokina nah neh Yaga y'ar wajanka yanaso shine mukazo mu nemi izini"
Mallan ya k'ara gyara zama
"Kai Madallah nayi farinciki da jin wannan maganan, tho wacecce daga ciki hafsatu koh Ameenatu"
Murmushi Sa'ood yayi yace
"A'a Sulthana"
Nan da nan fara'ar fuskan Mallan takau ya hada girar sama data k'asa. Jin Mallan yayi shiru Yasa Fareed yad'an dago ya kalleshi, ganin yanda ya murtuke fuska yasa yasha jinin jikinshi
"Sae dai kuyi hakuri dan na riga nama Sulthana miji"
Dago kai Fareed yayi da sauri yana K'allan Mallan
Sa'ood yace
"Tho shiknan bbu damuwa mun gode Allah ya saka da Alkhairi. Allah kaimu ya basu zaman lapia"
Ameen Mallan Yace atakaice

Hannu Fareed yasa a aljihu ya ciro bandir din y'an dari biyu ya ajema Mallan.
"Gashi bah yawa"
Washe baki yayi ya taba kudin
"A'a ayi haka"
Sa'ood yayi murnushi
"Babu komai ai"
Ganin suna k'okarin tafiya yasa yace
"Nace bah"
Fareed ya dago dasauri yana k'allan Mallan, cigaba da magana mallan yayi
"Akwai yaninta su biyu da hafsatu da Ameenatu, duk wacce yakeso ai sai abashi"
Fareed ya yatsine fuska
"A'a Mallan mun gode, zamu tafi"

Mik'ewa sukai Mallan ya rakosu har bakin mota yanata godiya, sukaja mota suka bar k'ofar gidan cikeda takaici. A hanya Sa'ood ya nisa yace
"Doctor akwai wani abu danai observing"
Fareed ya juya kadan ya kalli Sa'ood sannan ya maida dubanshi ga titi,
" kamar na meh fah?"
Naga k'iyaiyar yarinyan nan a idonshi, bakaga k'allanda yake mata sanda ta kawo ruwan nan bah..

Murmushin takaici Fareed yayi
"Na dad'e da gano akwai matsala a gidan, yarinyan tak'i bani hadin kai naji damuwanta"
Sa'ood ya gyara zama
"Ga shawara"
Parking Fareed yayi ya juya yana k'allanshi
"Mai zai hana mu samu wani ya bamu labarin yarinyan?"
Lallausan Murmushi Fareed yayi
"Yes! Uh ryt, y not gobe sunday sai mu dawo"
Sa'ood yace
"Haka za'ayi"
Haka suka kama hanyan gida suna tattauna yanda zasu bulloma Alamarin..

Rai bace Mallan ya shiga gida, baiga Sulthana a zaure bah, ya k'arasa gidan ya soma kwallama Sulthana kira da k'arfi rai bace. Jin yanda yake kiran yasa Ameenatu ta fito itada Hafsatu dan idan sukaji wannan kiran to bah lapia bah. Jiki na rawa Sulthana ta fito daga bayi ta aje butan ta k'araso wajan, Mama ta fito tana tambayan lapia. Nuna Sulthana yayi da yatsa ranshi bace Idanunshi sunyi ja..

"Indai ina raye tho ki sani bake bah aure, keh kina tunanin akwai mai abinda zai rabaki da gidan nan? Sai dai mutuwa"
Mama tace
"Lapia Mallan wai meke faruwa neh"
Zayyana musu duk abinda ya faru yayi, hankalin Ameenatu ne ya tashi, dama likita d'an babban gida neh? Hafsatu koh tabe baki tai tana cewa
"Ai Baffa duk sune suke fita da ita, dama ka kyaleta anyi auren kwana biyu neh ya sakota"
Kunnen Sulthana baffa ya kama
"Idan na K'ara jin an ganki da likitan nan, keh ko kallanshi kika karayi balle har ki gaidashi saina kasheki a gidan nan"
Gyada kai Sulthana tai hawaye nabin kuncinta,
"Tashi ki bani waje"
Mikewa tai jiki na rawa ta nufi zaure ta saki matsanancin kuka..

"Abinda kakeyi Mallan baka kyautawa, tunda bakasan ka bude ido kaga yarinyan nan a gidan nan bah saikai mata auren bah tunda ta samu wanda ya fito yana santa"
Jin haka yasa hawaye ya zuboma Ameenatu ta shige daki ta fada kan gadonsu ta fashe da kuka.
Tsaki Baffa yayi
"Likita babba, wanda mahaifinshi ke kokarin hawa babban matsayi shi zan dau wannan dabban naba? Ina! Tunda abin yazama haka cikin Almajiraina zan aura mata kuma anan zasu zauna tare dani ta cigaba damin bauta dan shi yafi dacewa da ita"
Shekewa da dariya hafsatu tai harda tafawa
"Gaskiya neh Baffa haka yayi"

Ummy Abduol✍🏻
[28/08, 01:12] Friend Hussaini: 💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐

By *Ummy Abduol*

*DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION*

*Page 141 to 145*

K'arfe hudu a kauyensu Sulthana tayi musu, bayan layinsu Sulthana sukai Parking motarsu, yaro sula samu suka hadashi da sabuwar dari biyar ya musu k'iran Babban Almajirin Mallan. Sai washe baki yaron yak'e dagudu ya nufi runfar Almajiran, yakoyi Sa'a ya sameshi zaune shi kad'ai a dakinsu yana karatu. Tare suka k'araso wajan sannan yaran yabar gurin cikeda murna..

Musabaha suk'ai Sannan Sa'ood yace
"Sunana Sa'ood sai abokina Fareed, mu yan cikin garin kano neh. Munzo akan maganar wata yarinya Sulthana munasan musan labarinta dan gwamnati na buk'atar a taimaka ma yara masu irin shekarunta"

D'an jim yayi Sannan ya dago yace
"Ni sunana Sani kuma Almajiri neh ni, kuyi haquri bazan iya fadan wani abu dangane da cikin gidan Malamina nah"

Hannu Fareed yasa a Aljihu ya ciro bandir din y'an dari biyar ya mik'a mai yana cewa
"Kah taimaka, ka fada mana munaso neh mu taimaka mata"

Jim Sani yayi yana tunani Shi kanshi bayasan abinda akema Sulthana a gidan, yanke shawara yayi kawai ya fada musu dan haka yace

"Kuzo ga Bakin bishiyar chan akwai inuwa sai mu zauna"

Bah musu suka nishi suka zauna, nan Sani ya soma basu labari tiriyan tiriyan iya abinda ya sani. Kuka neh kawai Fareed beyi bah anma idanunshi sunyi jah, shi kanshi Sa'ood hankalinshi bah k'aramin tashi yayi bah. Sa'ood neh yayi k'arfin halin cewa

"Mallan Sani anya kuwa Mallan neh ya haifeta"

Dagowa yayi dasauri yana k'allanshi da Mamaki

"Shine mahaifinta mana"

Girgiza kai Fareed yayi fuskansh bah Annuri

"No bashi ya haifeta bah, dan mahaifi bazai taba muzgunama D'anshu haka bah"

Sani yayi murmushin takaici Yace

"Mallan jamilu shine ya haifi Sulthana, duk kuma wanda zaka tambaya a kauyen nan abinda zai fadama knan"

Fareed neh ya mik'e dasauri yana k'arkade rigan jikinshi, Sa'ood ma ya mik'e yana k'allan Sani

"Mungode sosai Sani, zamu tafi idan bukatar k'ara ganinka ta taso zamuzo mu sameka"

Shima mik'ewan yayi ya basu hannu sukai musabaha

"Bbu komai ai ina maraba da dawowanku matukar za'a san yanda za'ayi a taimaka ma Sulthana"

Kudin Fareed ya mik'a mai, ya nok'e yaki k'arba

"Kubar kudinku, Allah dai ya baku sa'an niyyan da kuka dauka"

Ameen sukace suk'a k'arami godiya. Kasa driving Fareed yayi Sa'ood ya amsa keyn motan suka bar wajan kowa da abinda yak'e sakawa a Ranshi..
Fareed yayi ajiyan zuciya yana k'allan Sa'ood

"No mattet how hard the situation will be, no matter how bad. Sai na fitarda Sulthana daga k'angin nan datake ciki, koda kuwa zanyi asarar dukiyana da matsayina matsawar zata kasance cikin farinciki da Annashiwa"

Girgixa kai kawai Sa'ood yayi baice komai bah har suka k'arasa gida..

Ala ala Mami tak'e Daddy ya dawo, bai dawo gidan bah sai wuraren k'arfe goma da rabi na dare. Saida yaci abinci ya huta sannan Mami ta sameshi a office dinshi dake cikin gidan, zama tai kusa dashi
"Sannu da hutawa"

Da Fara'a yadan juyo yana k'allanta

"Sannu uwargida sarautar mata"

Murmushi tayi Sannan tace

"Alhaji inaso neh muyi magana dakai kuma naga kamar kana busy"

Takardun hannunshi ya aje ya matsar da system din dake gabanshi

"Ina jinki"

Jim tai tana k'allanshi Sannan tace

"Akan Maganan Masroor neh, yana daki tun dazu yak'i cin abinci sai aikin kuka yake, saima danai ma Yasir.."

Saurin katseta Daddy yayi hankali tashe

"Meke damunshi? Meyasa yake kuka?"

Nan Mami ta kwashe duk abinda ya faru ta sanar dashi Sannan ta fadamai yanda sukai da Yasir .

Baice komai bah yadau waya ya soma neman layin Masroor, yana dauka yace

"Kah sameni a falona"

Bai jira mai zaice bah ya kashe wayan sannan ya mik'e yana k'allan Mami

"Muje falona"

Koda suk'a karasa falon sun sameshi zaune akan Carpet kanshi a k'asa. Daddy ya zauna kusada shi yana k'allanshi

"Son meke faruwa? Karka boyemin fadamin damuwanka"

Baice komai bah k'anshi na k'asa, k'ara magana Daddy yayi Sannan ya d'ago jajayen idanunshi yana k'allan Daddy

"Daddy inada wacce nakeso but.."

Shiru yayi ya kasa k'arasa maganan

Daddy yayi murmushi

"Go on ina jinka"

Masroor ya sunkuyar dakai sannan ya cigaba

"Sunanta Sulthana ina santa daddy kuma babanta yace zai aura mata almajiri"

Daddy ya k'alleshi da mamaki

"Almajiri"

Kai Masroor ya gyada, daddy ya nisa yace

"Wanene Mahaifinta a garin nan"

Gaban Masroor neh ya fadi jin abinda ya fada, Mami tai saurin amshewa

"Alhaji inace munyi wannan maganan tun achan"

Hannu Daddy ya d'aga mata alamar tai shiru yace

"Ina jinka"

K'ara sunkuyar dakai yayi

"Daddy babanta bah kowa baneh a kauye suke"

Har daddy ya bud'e baki zaiyi magana Mahnoor ta shigo falon dagudu, jikin Mami ta d'ane tana kallan Daddy tana dariya

"Daddy uh welcome"

Murmushi daddy ya mata
"Thank uh my baby, ya school?"

Ta amsa da lapia lau. Hade rai Mami tai

"Tashi min a jiki, bakiga muna magana baneh kin wani shigo bako Sallama"

Zumbure baki tayi ta mik'e zatabar wajan, daddy yace

"Kyalleta zo nan abinki babyna"

Da d'an murmushi ta k'arasa ta zauna kusada Daddy.

"Maminku ta fadamin duk yanda kukai da ita, da kuma yanda zukai da yasir. So zan fara sawa a bincika min Yarinyar da Asalinsu idan har babu matsala insha Allahu she will be ur wife"

Dago kai yayi da Fara'a yana k'allan Daddy

"Daddy dagaske?"

Murmushi Daddy yamai tareda kyada kai. Mahnoor ta k'alli Masroor

"Bro Sulthana?"

Kai ya gyada mata Cikeda farinciki

Tsalle sukaga Mahnoor tahauyi tana murna, Mami da mamaki tace

"Ina kika santa"

Tsagaitawa tai tana k'allan Masroor. Da rarrafe ya matso kusada Daddy ya zauna kusada k'afarshi yanatamai Godiya Sannan ya mik'e yana hararan Mahnoor yabar wajan. Tasan mai yake nufi, murguda baki tayi ta juya tahau bah su Mami labarin zuwanda sukeyi gurin Sulthana..

Mami ta tausaya mata sai taji tanasan yarinyan tun bata hadu da ita bah...


Kwana biyun nan da Masroor baizo bah kullum Sulthana batada aiki sai kuka. Hakan yasa takanje gidansu Sadiya idan tadau tallan dan ta debe mata kewa. Yau tana zaune bakin tasha tayi tagumi tana k'allan hanyar da Masroor ya saba biyowa. Kamar a mafarki taga motarshi ya doso wajan, dasauri ta mik'e ta karasa inda yayi parking. Fitowa yayi yana mata murmushi, zumbure baki tayi ta juya ta koma inda take zaune

Murmushi yayi yabi bayanta, kusa ita ya zauna yana k'allanta. Kauda kai tayi ya juyo da fuskanta. Hawaye ya gani na gangarowa daga idonta

"Omg! Haba Beauty meya faru? Meyasa kike kuka"

Ai kaman jira take ta fashe da kuka harda shesheka, kanshi ya dafa

"Pls stop crying banasan kukanki beauty"

Hankie ya dauko ya soma goge mata hawayen dake fuskanta yana murmushi

"Me aka miki kike kuka?"

Zumburo baki tai

"Bakai baneh ka daina zuwa bah kullum sai nazo nan ina jiranka"

Kallanta yayi da Mamaki

"Kinyi kewana neh?"

Hannu tasa ta rufe fuskanta tana murmushi, shima murmushin yake cikeda Farinciki

"Oh come on! Fadamin kinyi kewana?"

Kai ta gyada mai, murmushi yayi mai sauti

"Nima nayi kewanki beauty, idan natambayeki wani abu zaki fadamin?"

Eh tace tana kallanshi, saida yayi jim sannan yace

"Kina sona?"

Dasauri ta mik'e tabar wajan tana dariya. Shima dariyan yayi kasa kasa, dakyar ya lallabata ta dawo ta zauna yace

"I so much love uh my beauty ina sanki sosai"

Hannayenta biyu tasa ta rufe fuskanta tana murmushi...

Shakuwa mai k'arfi ya k'ara shiga tsakaninsu, har Mami da daddy sun saba da hiran Sulthana da Masroor ke musu kullum. Lokaci nata tafiya, har yanzu bah abinda ya chanza dangane da k'iyayar da Baffa kema Sulthana...

*Bayan wata d'aya*

Alhamdulillah anyi Election Allah yaba Daddy sa'a yanxu shine gwamnan Jahar Kano, Alhaji shuaibu mahaifin Fareed shine mataimakinshi. Bayan komawansu government house Masroor ya matsama Mami akan zuwa gidansu Sulthana saboda nan da sati d'aya zai koma school, Mami na samun Daddy da maganan yace

"Nima abin na raina mantawa nai ban fada miki bah, gobe in Allah ya kaimu za'aje nema mai aurenta"


*tho fah* anya kuwa?

Ummy Abduol✍🏻
[28/08, 01:12] Friend Hussaini: 💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐

By *Ummy Abduol*


*DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION*

*Page 146 to 150*

*Masroor Fans* Wannan shafin naku neh... fatan Alheri gareki *Hajiya Fateema* kinfi kowa san littafin ina godiya da soyaiyarki gareni.

"Nima abin na raina mantawa nai ban fada miki bah, gode in Allah ya kaimu za'aje nema mai aurenta"
Dad'i sosai Mami taji ai dasauri ta fita ta k'ira Masroor a waya Tareda fadamai Albishir. Murna wajan Masroor ba'a magana suna gama wayan ya kira yasir ya sanar dashi lokacin shi yana hanyar zuwa wajan Fareed dan kwanakin nan da akai election tare suketa shige da fice hakan yasa suka k'ara sabawa sosai..

Yana isa Asibitin yamai waya ya sanar dashi isowarsa. Fitowa Fareed yayi yana murmushi

"Old friend na d'auka fah wasa kakemin"

D'an dariya Masroor yayi yana shafa suman kanshi

"Ai nafika zumunci"

Hannu Fareed ya mik'a mai suka tafa suna dariya

"Kaji talle kema audi gori, duk bah wannan bah friend. Naga sai annashuwa kakene fadamin meya faru?"

K'ayattacen murmushi Masroor yayi

"Gobe in Allah ya kaimu za'aje nema min aure"

"Woaw" Fareed yace cikeda farinciki

"Who is dis lucky beb"

Masroor ya girgiza kai

"Sunanta su...koda yake zaka ganta wata rana da kanta zata fadama sunanta"

Hannu Fareed ya mik'a mai

"I'm very happy 4 uh Friend, Allah ya kaimu musha biki"

"Ameen, tho kaifa yaushe ne nakan?" cewar Masroor

Ajiyan zuciya Fareed ya sauke

"Nikam bah yanzu bah"

Da mamaki Masroor ya kalleshi

"Why?"

Juyowa Fareed yayi yana fuskantan Masroor

"Wata yarinya na gani shes young n beautiful. Saidai yarinyan na cikin Matsala infact namadai je naga mahaifinta yak'i amincewa"

Gaban Masroor neh ya ya fadi. Zuciyarshi ta shiga zargin kodai shine wanda sulthana take fada mishi likitan dayaje nemanta. Dagowa yayi da Alamar damuwa

"Y'ar wacece aina take?"

Murmushin takaici Fareed yayi yana girgiza kai

"Bah y'ar kowa bace, a kauye ma suke."

Kan Masroor neh ya soma sara mai, juyawa kawai yayi fareed ya matso yace

"A'a Old friend bamu gama hiran bafa ina kuma zaka?"

Da hannu ya nunama Fareed kanshi dak'yar ya iya cewa

"Gida zani kaina ke ciwo"

Bai jira mai fareed din zaice bah ya figi mota yabar Asibitin da sauri ya nufi gida...

Hankali tashe ya k'arasa gida, side dinshi ya wuce kai tsaye bai kuma fitowa bah har washe gari...


Safiyar Ranar lahadi da wuri Abokanan daddy su biyu suka shirya Yasir ya musu jagora zuwa k'auyensu Sulthana. Kasancewar bai taba zuwa bah da kwatance Suka gane gidan, a kofar gidansu sukai Parking motarsu. Mallan na ganin Katuwar mota ya mik'e dasauri ya fito daga runfar Almajiransu..

Yasir ne ya fito ya k'arasa suka gaisa da Mallan sannan ya fada mai tareda baki suke. Nan da nan Mallan yahau washe baki ganin mutanen da suka fito daga motan daga gani bah k'ananan mutane baneh..

Tabarma ya dauko ya shimfida suka zazzauna, Mallan ya soma gaidasu suka amsa, d'aya daga cikinsu ne ya fara magana

"Sunana Alhaji ilyasu sai kuma abokina Alhaji Tanimu, daga Cikin Gari muke. Alhaji Aminu Datty gwamna maici yanzu shine ya turo mu dan mu naima ma d'anshi auren Y'arka"

Nan da nan Mallan ya rud'e,

"Anya bayin Allah ni kuwa Mallan Jamilu?"

Alhaji Tanimu yayi Murmushi ganin Yanda ya rud'e

"Kwarai kai"

Gyara zama yayi jikinshi na rawa

"Wacce daga ciki Ameenatu koh Hafsatu?"

Yasir dake gefe yace

"Sulthana"

Had'e rai Mallan yayi baice komai bah, ganin yanda ya sauya fuska yasa Alhaji ilyasu cewa

"Koh Akwai damuwa neh"

Dagowa yayi ya kallesu d'aya bayan d'aya sannan ya bud'e baki ya fara magana

"A gaskiya bazan cuceku bah, saboda d'an babban gida kaman wannan bai kamata na rufeshi bah"

Shiru yayi na wasu lokuta, Alhaji tanimu yace

"Mallan muna jinka"

Abinda Mallan ya fadane yasa ni Ummy Abduol na mik'e dasauri har saida Wayata ta fadi garin fargana

" *A Gaskiya banine uban Sulthana bah, Sulthana shegiya ce batada Ubah*"


Tabdi Jam!...

Kuyi Managing wannan

Ummy Abduol✍🏻
[28/08, 01:12] Friend Hussaini: 💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐

By *Ummy Abduol*


*DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION*

*Page 151 to 155*

"A gaskiya banine uban Sulthana bah, Sulthana shegiya ce batada ubah"

Mikewa Yasir yayi dasauri yana nuna Mallan da Yatsa

"Mallan k'iyayar da kakema y'arka har takai haka? Kace bakai ka haifeta bah"

Alhaji tanimu ya had'e rai yana k'allan Yasir

"Wanne irin rashin hankali neh wannan? Wayasa bakinka a maganan nan"

Zama Yasir yayi yana huci ranshi bace. Alhaji tanimu ya maida dubansa ga Mallan fuskanshi bah walwala

"Tho Mallan tunda kace bakai baneh ka haifeta, tho ina mahaifinta yake"

Mallan ya yatsine fuska

"Bansan inda Mahaifinta yake bah, kawai dai ni rik'onta nake"

Mikewa Alhaji ilyasu yayi, Alhaji tanimu ma ya mik'e yana cewa

"Mun gode Mallan mu zamu tafi"

Baice musu komai bah suka kakkabe babban rigansu suka shigaa mota Yasir yajasu suka bar kauyen kowa ransh b'ace..


Yanmacin ranar Sulthana tadau gyadanta kamar yanda ta saba, Bakin tasha ta nufa ko kamin ta k'arasa ta hango motar Masroor pake a inda suka saba zama, da sauri ta k'arasa tana murmushi. Ta mirrown motan ya hangota zuwa ya fito dasauri ya nufeta yana huci

"Dama labarinda kika fadamin duk k'arya neh Sulthana? Ke ashe shegiya ce bakida uba"

Trayn kanta neh ya fadi ta k'walallo ido tana kallanshi da Mamaki, cigaba yayi da Magana cikin kakkausan Murya

"Kin cuceni Sulthana, dama duk abinda kika fadamin k'arya neh? Duk sanda nake miki? Duk lokacinda na bata akanki"

Tsugunawa Sulthana tai ta fasa ihu tareda daura hannu aka

"Yaya Masroor waya fadama wannan maganan? Wallahi k'arya neh Baffa shine Babana"

Ranshi b'ace ya juya Mata baya
"Shi Baffan zai miki Karya neh? Haba Sulthana Kinsa Mahaifina dani munji kunya, why Sulthana why?? Nasan baki sani bah Mahaifina neh Gwamna mai ci yanzu Alhaji Aminu"

Dagowa tayi da Mamaki tana K'allanshi

"Danasan Abinda zai faru knan daban bari Aminan mahaifina sunzo bah. Yanzu da wani ido zan kalli Daddy nah?"

Kuka sosai Sulthana take Hankalinta tashe

"Dan Allaha yaya Masroor karka gujeni, kai kad'ai ke sona kake tausaya min. Idan ka tafi ya zanyi"

Tsugunawa Yayi kusada ita zuciya na cinshi

"Sulthana Bazan iya bah"

Bai jira mai zatace bah ya shiga mota ya bar wajan a guje. Kuka ta k'ara fashewa dashi kamar ranta xai fita, hakanan ta d'au trayn gyadan ta nufo gida tana cigaba da kuka.

Zaure ta zauna ta cigaba da kukanta, saida tai mai tsarta Sannan ta mik'e rai bace ta shiga cikin gidan. Zaune ta samu duka y'an gidan a k'atuwar tabarma da Alama iska suk'e sha. Karasawa tai ta aje trayn a gaban Baffa ta tsugunna akan tabarman k'anta a kasa ta fara magana

"Baffa mai nai maka ka tsaneni baka sona? Idan na maka laifi neh kai hakuri. Meyasa kace bakai ka haifeni bah"

Da mamaki Mama ta k'alli Mallan Gabanta na faduwa

"Mallan Abinda Sulthana ta fada Gaskiya neh"

Tsaki yayi tareda kauda kai

"Hakaneh mana, bazai yuwu bah ace d'an gwamna guda yazo neman aurenta batareda na fadamai abinda ke faruwa bah. Tho yau ku shaida zan amayar da Abinda yake cikina"

Hafsatu ta mik'e dasauri tareda dafe k'irji

"Dan gwamna"

Daga kai Mallan yayi yana k'allan Hafsatu

"Kwarai kuwa"

Hankalin Ameenatu neh ya tashi tace

"Baffa muna jinka me kace zaka fada"

Sulthana ya nuna da Hannu yana cewa

"Sulthana bah y'ata bace, Shegiya ce batada uba. Cikin Shege uwarta tai ta haifeta"

Ihu Sulthana ta saki ta mik'e Dasauri ta daura hannu a kai ta fashe da kuka, rasa inda zatasa kanta tai ta dawo gaban Mallan ta tsugunna tana kuka sosai

"Baffa kai hakuri karka ce haka, ni yarinyanka ce haka Umma tace"

Tsaki yayi

"Karya umman naki takeyi, niba ubanki baneh"

Mutuwar Zaune Mama tai itada Ameenatu, Hafsatu ko cewa take

"Ashe gado tai, shiyasa itama take bin maza. Lallai gwara Baffa daka fadamana"

Kamar mahaukaciya Sulthana ta zama a cikin gidan, ihu kawai take tana kuka kwi kwi. Mama tai k'arfin Halin cewa

"Tunda nake ko a tarihan da mahaifana suka bani ban tabajin inda Uba yakema Y'arshi hakaba sai kai. Kaicona da aurenka Mallan"

Mik'ewa Mallan yayi yana huci

"Ni kike jifa da irin Wadannan Kalaman?"

Kauda kai Mama tai Ranta bace. Baffa ya dakama Sulthana Tsawa yanacewa

"Tunda abin naki ya zama haka maza ki tattara inaki inaki ki tafi ki nemi ubanki. Kada ki kuskura na fito daki na ganki a cikin gidan nan"

K'ara rushewa da kuka Sulthana tai ta rungume Mama tan kuka kamar ranta zai fita

"Dan Allah mama kice Baffa yayi Haquri ni y'arshi neh. Kadaya koreni dan Allah, wayyo Allah na"

Ameenatu ta rarrafo inda sulthana take rungume da Mama itama tana hawaye

"Kiyi haquri Sulthana, Baffa shine Babanki. Kada..."

Muryan Baffa dataji a kanta neh ya hanata k'arasa Maganan datai niya

"Kul! Karna k'araji Sam bah y'ata bace. Maza ki tattara ki bar min gida"

Dorinan daya fito dashi ya d'aga Sulthana na gani ta mik'e dasauri ta fice Zuwa zaure da gudu tana cigaba da kuka..

Mama ta shiga Dak'inta tadauko Mayafinta tana cewa

"Allah wadaranka Mallan, bazan iya cigaba da zama dakai a gidan nan bah"

Takalmanta tasa ta fice daga gidan tana kuka...

Gudu sosai Masroor yake yana kuka kamar K'aramin Yaro. Gidan da suk'a baro ya nufa wanda yanzu shine gidanshi, yana shiga ko k'wakwaran Parking beyi bah yahau hada kayanshi a Trolley yana cigaba da kuka. Waya yama Yasir akan su Hadu a Airport, dama Tun kwana biyu da suka wuce visan shi ya fito. Yana gamawa ya fitoda Akwatin yasa a mota ya kulle gidan ya nufi Airport..

Yana zuwa Yasir na K'arasowa, fitowa yayi daga nashi motan ya dauko Akwatinshi ya k'araso inda Yasir ke tsaye yana k'allanshi da Mamaki

"Friend meye haka?"

Hawayen idonshi ya share yana kallan Yasir

"Sulthana betrayed me, bazan iya cigaba da zama a k'asan nan bah."

Hannunshi Yasir ya kamo Cikin sigan Lallashi

"No Friend, Ni inaji a Jikina Sulthana nata yaudareka bah. She's young and batada wani ilimin da zata fadama K'arya, think of dis"

Girgiza kai Masroor yayi hawaye na gangara a idonshi

"I love her so very much Yasir, meyasa zatamin haka? Ni nasan Mutumin nan bazai mata k'arya bah"

Hannunshi Yasir yaja

"Pls Friend be strong muje gida mu tattauna"

Kai Masroor ya girgiza, duk yanda Yasir yaso Masroor ya hak'ura fafur yak'i yarda dole hakanan ya hakura ya barshi yahau jirgi zuwa lagos shi kuma ya tuk'a motar masroor din ya nufi government house jiki a sanyaye

Bayan dogon bincike Aka bari ya shiga gidan, nan ma kamin ya samu

Please Login or Register in order to submit comment