Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Yana Shiga Yaga Mama ta fito Sanye da Hijabi, Ya kalleta da Mamaki, Ina Zaki?
"Gaskiya Mallan bazan cigaba da zama a gidan nan kana Azabtar da Yarinyan nan bah Na gaji Gaskiya"
Kafada Ya daga Tareda Cewa
"Idan Har kika fita kofar gidan nan tho ki sani a bakin Aurenki"
Ameenatu da har lokacin tak'e Tsugunne a Kasa tana Kuka ta dago ta Kalleshi da Mamaki...

*Ummy Abduol*✍🏻
[28/08, 01:12] Friend Hussaini: 💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐

By *Ummy Abduol*

*Page 26 to 30*

Ameenatu da har lokacin tak'e tsugunne a kasa tana kuka ta dago ta kalleshi da mamaki
"Mallan Yanzu dah bakinka kake Fadin irin wannan maganan" cewar Mama Tsaki yayi batare da yace komai bah yayi shigewarshi dak'i
Dosar kofan fita Mama tai Ameenatu ta mik'e dasauri ta kamota tana cigaba da kuka
"Mama dan Allah karki tafi, kiyi Hakuri"
Hawaye ne ya gangaro a idon mama

"Na gaji da zama ana Azabtar da Yarinya ina kallo banida halin magana, Duk inda naji sai aita nunani ana gulmana mutane sai suyita tunanin ni nake wahalar da Sulthana"
Hawayen idonta Ameenatu ta Share
"Mama karki manta idan har kika fita kin saku, Dan Allah Mama karki fita kiyi Hakuri, Idan Kika fita Zamu Shiga wani hali"
Murmushin takaici Mama tai
"Ameenatu duba ki gani yanda ya Kori yarinyan nan da Daren nan, Ina Yake tunanin Zata? Yanda Kauyen nan Yakeda Hatsari kuma gata K'arama"
Shiru Ameenatu Tai nadan wani lokaci.

Sallaman Hafsatu sukaji ta shigo Gidan Rik'e da Bak'ar leda ganinsu Mama a tsaitsaye Yasa Ta K'araso kusa dasu
"Mama lapia meya Faru?"
Ameenatu ce ta shiga zaiyana mata duk abinda ya faru, Dan Murmushi tai tareda Girgiza Kai Sannan ta Kalli Mama
"Tho Mama mu ina ruwanmu, tunda ya koreta ai shiknan mun munma huta wallahi"
Tsaki Ameenatu taja
"Hafsatu kinada Matsala, Bansan Keh inda kikasa gaba a rayuwarki bah"
Turo baki tai ta kauda kai..

Mama ta dafa Kafadar Ameenatu
"Ameenatu kuje ku nemo Sulthana dan Allah, Kunga Dare neh Akwai hatsari"
Kara turo baki hafsatu tai tana Gungunai
"Ni Mama na Gaji Wallahi"
Tsawa mama ta daka Mata, Hijab Ameenatu ta koma ta dauko suka fito itada Kawarta Habiba suka Fita Hafsatu na Binsu a Baya, Sallama Habiba tama Ameenatu ta wuce gida, Ameenatu ta juya ta Kalli Hafsatu dake tafiya kamar wacce kwai ya fashema a ciki
"Haba Hafsatu ki dago kafa Mana Wai meye Haka"

Dogon Tsaki Hafsatu taja nifa Gaskiya Ya Ameenatu kun Takura min, Allah badan Mama ta matsaba bah Abinda zai kara fito dani da Dadaren nan. Girgiza kai Kawai Ameenatu tai ta cigaba da Tafiya tana haske hasken Hanya da Torch light..

Sulthana kuwa tana Fitowa Gudu kawai take batareda tasan inda ta nufa bah, Saida tai mai isarsa Sannan ta Samu guri ta zauna Tana kuka sosai mai Sauti, Kuka take kamar ranta zai Fita
"Umma meyasa kika tafi kika barni? Meyasa baki bari mun tafi tare bah. Ina sanki Umma, ina Kewanki"
Kuka ta cigaba dayi gwanin ban tausayi, duk ilahirin Jikinta zugi yake mata bin jikinta tai da K'allo taga duk Baffa ya fafasa mata jiki. Nan da nan jikinta yayi zafi, Idanunta suka fara Lumshewa. Kangon Ginin Kasan dak'e Gefenta Ta mik'e dakyar tana Ganin Jiri ta k'arasa ta Shiga Cikin Kangon ta zauna, Jin Jirin tai na K'aruwa ta lumshe ido da k'arfi ta Bude tareda Girgiza kai. A hankali ta Sulale a Wajan..

Bah Indah su Ameenatu basu jeh bah, Tun daga Gidan Kawayen Sulthana Har Wuraren dah suk'e zaton Zata Iya boyema, Anma bata bah Alamarta. Hankalin Ameenatu Yakai Kololuwa Wajan Tashi, Ganin Dare Yayi sosai Yasa Suka Koma Gida. A tsakar gida Suka samu Mama sai kaiwa da komowa take, Tana ganinsu ta K'araso dasauri
"Yaya kun Ganta?"
Kasa magana Ameenatu tai, Hafsatu ce ta Yatsine Fuska
"Duk inda Muke tunanin Za'a sameta munje bamu ganta bah"
Bata jirah mai Mama zatace bah ta Wuce dakinsu..

Kuka Ameenatu tahau yi a hankali Kanta a K'asa, Mama ta dafata itama hankali tashe,
"Kiyi Hakuri Ameenatu, Insha Allahu Za'a ganta jeki kwanta kinji"
Kai kawai tai k'arfin Halin Dagawa ta Nufi dakinsu jiki a Sanyaye...

Hasken daya Haska mata Fuska neh Yasa ta Bude ido dak'ar, Ganin Gari ya Waye Tangaran da Alamar Rana mah ta Farayi Yasa ta Mik'e Zaune Dakyar tana Yatsine Fuska. Wanne Irin Mugun Ciwo Kanta keh mata da duk ilahirin Jikinta, dakyar ta mik'e tsaye Ganin Har yanzu tana Jin Jiri Yasa ta koma ta Zauna Tana Hawaye a Hankali. Abubuwan da Suka Faru jiya suka Dawo mata, Kuka ta Fara Sosai Tareda Daura Hannayenta Biyu akai
"Umma Ki Dawo dan Allah, Ina Sanki meyasa zaki tafi ki Barni, Wallahi Baffa naso ya Kasheni. Dan Allah Umma ki dawo mu zauna tare, Kin Barni Cikin..."
Kukan neh Yaci Karfinta, Sulalewa tai ta kwanta Tana Shafa Ciyayin Dake Kasan wajan tana Cigaba da Kuka..

Ta dade a haka Sannan Ta daure ta Mik'e ta Fito daga kangon Tana tafiya Saboda Yanda Takejin Jikinta yana mata Ciwo. Duk inda Ta Wuce K'allanta ake, Sai Yanzu ta Tuna Koh Dan kwalli babu a kanta. Runtse ido tai wasu Sabbin Hawaye suka gangaro Mata, Direct Gidansu Sadiya Ta Wuce dan Duk Kauyen nan ita kadaice Tasan Zata iya Taimaka mata da Wani abun...

*Ummy Abduol*✍🏻
[28/08, 01:12] Friend Hussaini: 💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐

By *Ummy Abduol*

*Page 31 to 35*

_kuyi min afuwa jina shiru da kukai, Hakan ya faru neh bisa Rashin Lapia danai. Anma Alhamdulillah naji sauqi, Nagode Sosai da Kulawarku a Kaina_


Dis page x 4 uh besty *Ayoosh Gidado Yar'adua "My Gidos"*

Direct Gidansu Sadiya ta wuce dan duk kauyen nan ita kadai tasan zata iya taimaka mata da wani abun. Dakyar ta karasa gidan ta Shiga da Sallama, A Tsakar gida ta Samu Sadiya tanayi ma Mamanta Sallama Zata tafi makaranta.
Juyowa tai ta K'alleta da Mamaki
"Sulthana! Daga ina kike? Jiya su Yaya Ameenatu nata nemanki"
Waje ta samu ta zauna a tsakar gidan tareda tafe kai, Dasauri Sadiya ta karaso inda take
"Mama! Mama!! Fito kiga Sulthana"
Mama da Baba suka fito a Tare dasauri,
"Lapia Sulthana meke Faruwa" cewar Mama
Kuka ta Fashe dashi Kanta a Kasa, Baban Sadiya neh ya K'alleta Cikeda tausaya wah
"Sulthana, Yi Magana Mana"
Kasa magana tai sai kukan data K'ara Fashewa dashi, Mama ta K'alli Baba tana nunamai Sulthana Hankali Tashe
"Mallan Kalli jikin Yarinyan nan, Duk yanda akai Duka Akai mata"
Sai a Sannan Baba ya lura da Raunukan dake Jikinta.

Girgiza kai yayi
"Hajjo dau Yarinyan nan ki kaita Ciki, Taci abinci tai wanka. Idan ta huta sai muji Koma menene"
Rungumeta Sadiya tai itama tana Kukan
"Kiyi Hakuri Sulthana, Mallan meh koh?"
Kasa cewa komai Tai sai kanta kawai tada Gyada. Da taimakon Sadiya da Mama ta Mik'e Mama ta kaita Dak'inta Ta zaunar da Ita, Dumamen tuwon dayaji man Shanu Mama ta kawo mata
"Sulthana ci abinci nasan Bakici Komai bah"
Kallan Abincin tai Sannan ta maida dubanta ga Mama
"Dagaske inci"
Gyada mata kai Mama tai Cikeda tausayawa wah, Hannu tasa Cikin Abincin ta soma ci tana Lumshe ido, Ganin Yanda takecin Abincin Hannu baka Hannu Kwarya Yasa Hawaye ya Gangaro ma Mama, Dasauri ta Mik'e tabar dakin Tana sharan Kwalla..

A tsakar Gida tai Kicibus da Sadiya tanata Safa da Marwa
"Keh Sadiya, Makarantan fah"
Turo baki tai tareda Kauda Kai
"Ni Mama bazanje makaranta bah, Kinga fah Sulthana batada lapia"
Sakin Baki Mama tai da Mamaki, A Ranta Fadi take
Lallai Sadiya Nasan Sulthana. Batace Komai bah Sai Girgiza kai datai tabar wajan, Sadiya na Ganin Tabar wajan ta Shiga Dakin Dah Sultanan keh Ciki. Zaune ata sameta Tana Cin Abinci, Kusa da Ita ta Zauna Tana Kallanta

"Sulthana Baffa neh koh?"
Nan da Nan hawaye suka cika Idonta, Sheshekan kuka ta Fara kanta a kasa
Matsowa kusa da Ita Sadiya tai ta Dafata
"Kiyi Hakuri kinji, Zancema Baba ya dawo dake nan gidan mucigaba da zama tare muna zuwa makaranta"

Dagowa Sulthana tai Da Fara'a
"Dagaske Sadiya"
Kai Sadiya ta Gyada itama da Fara'a kwance a Fuskanta.
Saida ta Cinye Tuwon Tas Sannan ta Dago ta Kalli Sadiya dake zaune kusa da ita
"Sadiya Kaina na Ciwo tun Jiya"
Dasauri Sadiya ta mik'e batare datace komai bah ta fita daga dakin, Chan Sai gata dauke da Wani jikon Magani
"Gashi Mama tace Kisha, Sai kizo kiyi wanka"

Jim tai tana K'allan Sadiya, A Sanyaye Tasa Hannu ta K'arba Maganin Tasa Sannan Ta Mik'e, Zani Sadiya ta mik'a mata ta Amsa sannan tabar dakin. Kayan jikinta ta cire ta daura zanin Sannan ta Fito, A tsakar Gida tasamu Mama Bakin Murhu Tana Iza Wuta
"Sulthana kin Fito?"
Kai Ta gyada kanta a kasa
Murmushi Mama tai
"Maza kije ga Ruwa chan a kewaye kiyi Wanka"
Tho Tace ta Nufi Bandakin Idonta Cike da kwala, Zama Tai a Bayin Ta Fashe da Kuka a Hankali, Kuka take Sosai mara Sauti
"Umma meyasa zaki tafi ki barni, Dan Allah ki dawo nima kirinka sona kamar yanda Maman Sadiya ke santa"
Jin Muryan Mama a Wajan Yasa tai Saurin Goge hawayenta ta Fara wankan..

Tana Gamawa ta Fito tasamu Mama ta fito mata da Kayan da Zatasa, Saida ta kimtsa Sannan Baba Ya shigo dakin shida Mama, Tana Ganinshi ta Zame ta Zauna a Kasa. Kallanta yayi cikeda kulawa
"Sulthana fadamin meya Faru"
Hawaye neh ya Gangaro a Idonta, Duk abinda ya faru ta Sanarmusu.

Shiru Dukai Mama ta Kalli Baba
"Mallan Abinda Mallan Jamilu yake Baya Kyautawa, Sai kace Bashi Ya Haifeta bah, Niko a Mafarki Bantaba Ganin Irin Wannan bah, Abinda yakamata kishiyar mahaifiyarta tayi Sai kuma a Sameshi Wajanshi"
Shiru Baba yayi na Wasu mintina, Chan Ya dago Ya Kalli Sulthana
"Kiyi Hakuri Sulthana, A Matsayina na Aminin Mahaifinki Zanyi kokari Naga nayi mai magana ki koma Makaranta Sannan Ya daina Daura miki Talla"
Turo Baki Sulthana tai Idonta Ya kawo Kwalla
"Baba Ni bazan koma bah, ni Anan zan Zauna"
Mama neh Tai Saurin Cewa
"Mallan idan shi Mallan Jamilun Baya Santa Akwai Masu so dayawa, Wallahi da Zai amince ni Zan Iya rik'e Sulthana."
Murmushin Takaici Yayi tareda Mik'ewa
"Hmm Hajjo knan"

Ummy Abduol✍🏻
💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐

By *Ummy Abduol*

*Page 36 to 40*

Murmushin takaici Yayi tareda mik'ewa
"Hmm Hajjo Knan"
Bai jirah mai Mama zatace bah yabar Gidan...

Harya Fita ya dawo
"Sulthana dauko Hijabinki Muje"
Narai Narai da Ido tai Tana K'allan Mama
"Mama Dan Allah Kada mu Maidani ni banasan Gidan Baffa, Kullum Dukana Yakeyi"
Sadiya ce Ta Shigo dakin Dasauri Tareda Durkusawa
"Dan Allah Baba Kada a Maida Sulthana a Batta mu Rinka zuwa makaranta"

Hade Rai Baba yayi ya Kalli Mama
"Miko mata hijabi mutafi"
Jiki a Sanyaye Mama ta mikama Sulthana Hijabin Sadiya dak'e ratayi jikin Gado mai runfan dake dakin. Karba Sulthana tai tana kuka sosai, Saida tasa Sannan suka fito daga dakin, Kuka sosai Sadiya take tana Rokon Baba, Baiko Saurareta bah ya kama Hannun Sulthana suka bar Gidan..

Gidan Mallan Suka nufa, A Runfan da Almajiranshi Suke Baba ya hangoshi, Juyawa yayi ya K'alli Sulthana daketa Sharan Kwalla
"Tsaya a nan ina zuwa"
Tho Tace Ya nufi Runfan Mallan da Sallama
"Hade Rai Mallan Yayi Ganin Tareda Sulthana Suke"
Baba ya Mik'a ma Mallan Hannu suka Gaisa
"Mallan Jamilu Wurinka Nazo" cewar Baban Sadiya
"Tho Mallan Sani ina Sauraronka"
Jim Baban Sadiya yayi tareda Girgiza Kai

"Mallan Jamliu a matsayina na amininka mai kuma baka shawara, kuma kana Dauka. Yauma nazo da Nasihar nan da nasha maka Akan Y'arka Sulthana"
Tsaki Mallan Yaja Tareda Kauda Fuska
"Mallan Sani Na fada maka ka daina sa bakinka a Wannan maganar dan Sam bazan fasa abinda nai niyya bah"

Murmushin Takaici Baban Sadiya yayi Kanshi a Kasa
"Mallan Jamilu Knan, Nasan kasha fadamin haka Anma a matsayina na Aminin kah ya kyautu na Baka shawara ka dauka. Dubah kaga yanda kaima Yarinyan nan duka, Haba Mallan Sulthana Fah Amana ce a Gurinka"
Shiru Mallan Jamilu Yayi yana Cika yana Batsewa
"Ina mai rokon arzikin Kai hakuri yarinyan nan ta koma gida, saboda bai kamata Yarinya karama kamar Sulthana na Gararanba a Gari bah. Dan Allah kai min Wannan Alfarman"
Guntun Tsaki Mallan Jamilu yaja Sannan Ya Kalli Baban Sadiya
"Taci Darajan Kah, Anma dah bah haka bah bazata zauna min a gida bah"
Murmushi Baban Sadiya yayi ya Mik'a mai Hannu sukai Musabaha Sannan sukai Sallama..

Inda Sulthana take tsaye Baban Sadiya ya Nufa
"Sulthana Maza Shiga Gida Baffanku Ya hakura"
Nan da nan Fuskanta ya Chanza
"Dan Allah Baba ka tafi dani gidanka ni banasan Gidan Baffa dukana Yakeyi shida Yaya Hafsatu"
Jim Baban Sadiya yayi na Dan Lokaci, Shi Kanshi Yana Tausaya mata Yana kuma San Rik'eta Anma sam Mallan Jamilu ya Hana. Jin Tana Kuka Yasa Ya Lallasheta Tareda Rakata Har Cikin Zauren Gidan, Hannu Yasa a Aljihu ya Ciro Naira Hamsin Ya bata
"Gashi Ki siya wani abu kinji? Anma ki daina Kuka"
Kai kawai ta Gyada Ya mata Sallama Ya Bar Zauren..

Zama Tai Ta Fashe Da Kuka, Sai datai mai isarta Sannan Ta Mik'e ta Shiga Cikin Gidan. A Bakin rijiya Ta Hango Hafsatu Gabanta DaKwanonin wanke wanke sai Yatsine Fuska take. Sallama Tai a Hankali, Ameenatu dake Bakin Murhu ta Mik'e Dasauri
"Mama! Mama!! Fito ga Sulthana Ta Dawo"
Dasauri Mama ta fito da Fara'a ta K'araso inda Sulthana tak'e Tsaye
"Sulthana kin dagamin Hankali, Jiya bah Inda Su Ameenatu basuje bah Ba'a Ganki bah"
Hawaye neh Ya Gangaro mah Sulthana tai Saurin Sharewa Sannan Ta K'alli Mama
"Mama Dan Allah Kicema Baffa Ya barni na Koma gidansu Sadiya ni nafisan Chan"

Wata Uwar Ashar Hafsatu ta daka,
"Wallahi Kinyi kaddan, Idan Kika tafi Uban wah zai rinka Aikin Gidan"
Hararanta Ameenatu tai
"Kedai Hafsatu Bakida Hali Wallahi, Jiba Tun dazu Mama tasaki Wanke Wanken nan anma Baki koh Fara bah"
Tsaki Hafsatu Taja Tareda Turo dankwalin Kanta Gaban Goshinta
"Nifah Ya Ameenatu kin Fara takuramin a Gidan nan"
Bakinta Mama ta bige rai bace
"Hafsatu Bakinda Hankali, Ameenatu Yayarki ceh fah, na Lura Abubuwanki k'ara gaba gaba Sukeyi"
Turo baki tai Tabar Wajan Tana Gungunai..

Ameenatu ta K'araso inda Sulthana take tsaye
"Sulthana Ina Kika kwana? Waya baki wannan Kayan"
Kayan Jikinta ta K'alla sannan ta Dago ta K'alli Ameenatu
"A Wanchan Kangon na Kwana, Kayan Sadiya neh Mama ta bani"
Jim Ameenatu tai Batace Komai bah. Mama ta kama mata Hannu suka Shiga Dakinta, Lallashinta ta soma yi tana Bata baki har bacci ya dauketa a Wajan...

Sai bayan Azahar Mallan ya Shigo Gidan, Har lokacin Sulthana bacci tak'e. Dakinshi Ya wuce batareda tacema Kowa komai bah, Saida Ya gama Abinda Yake Sannan Ya Daga Labulen Dakin Mama dan ya sanar da Ita zai Fita. Sulthana ya hango kan Gado tana Bacci Hankalinta kwance
"Bude baki yayi da Alamar Mamaki, Lallai Yarinyan nan Wato har lokacin Bacci tasamu a Gidan nan"
Dakinshi ya koma ya dauko dorina Ya Tsula mata, Dasauri Ta mike Tareda Sakin Kuka
"Dan Allah Baffa Kai Hakuri Bazan Sake bah"
Jin Kukan Sulthana Yasa Mama dake Bandaki ta Fito dasauri
"Haba Mallan kaji tsoron Allah, Duk dukan dakama Yarinyan nan Bai isheka Bah"

Tsaki yaja ya koma Dak'inshi Ya Dibo Gyada Ya Fito, a Gaban Sulthana Ya direshi yana K'allanta
"Kinje Kin Kai K'arana wajan Aminina, Tho ki sani bai isa yasani na Sauya abinda nai niyya bah. Maza ki dau gyad'an nan ki Dafa, Kada ki bari na dawo na Tarar baki tafi Talla Bah"
Dasauri ta Amsa da
"Tho"
Jiki na Rawa tadau gyad'an ta Nufi bakin Rijiya Dashi. Babban Rigansh Ya kakkabe Yayi yabar Gidan Rai Bace, Binshi da K'allon Takaici Mama tai Tareda Girgiza kai.

Ummy Abduol✍🏻
[28/08, 01:12] Friend Hussaini: 💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐

By *Ummy Abduol*

*Page 41 to 45*

Babban riganshi ya kakkabe Yabar Gidan rai bace, binshi da K'allon takaici Mama tai tareda Girgiza kai. Bakin Rigiyan tah K'arasa ta taya Sulthana Wanke Gyadan suka daura a wuta, Abinci ta zubo mata Taci ta koshi. Gyadan na Dahuwa Mama ta juye mata ta daura mata ta Fita..

Kamar zata Shiga Gidansu Sadiya Sai kuma ta Fasa dan Fushi take dasu Saboda sun maidata Gida. Bakin Kasuwa ta Nufa da Gyadar, takoyi Sa'a Anata Siya. Kudi taga an Mik'o mata Naira Dari biyar, Ta zaro ido Batareda ta Dago bah, Bah Chanji.
"Kidai dubah, Gyadar tabani Saha'awa"
Muryan dataji neh yasa ta dago da Sauri sukai ido hudu da ita, Da Mamaki Ta K'alleta
"Sulthana Dama kina nan? Kullum idan na Tambaya Sadiya sai tacemin Kunyi tafiya har yanzu baku dawo bah, Meyasa kika daina zuwa makaranta Kika koma Talla"
Idon Sulthana neh ya Ciko da K'alla
"Baffa na neh ya Hanani"

Jim Matar tai tana K'allanta
"Laifi kika mai knan"
Dasauri Sulthana ta girgiza kai
"Aa malama banmai komai bah"
Kallan Gyadan tai
"Wannan Gyadan zaikai na Nawa?"
Dasauri Sulthana ta Amsa
"Nah Dari Uku ya Rage"
Murmushi malaman Tai ta Mik'a mata Dari biyar din
"Na Siya duka, Mik'e muje ki Rakani gidanku inaso nai magana da babanki"
Bah Musu ta Mik'e ta Juye mata gyadar a Leda ta mik'a mata, Turan ta daura Akai suka Kama hanyar Gida..

Da Sallama Suk'a Shiga Gidan, Mama ta amsa tana Zaune Kan Tabarma Gefenta Ameenatu Suna Shan iska, K'arasawa Mallaman Tai Ta Zauna Suk'a Gaisa da Mama. Dasauri Ameenatu ta gaidata dan ta koyar dasu a Makaranta, Gyaran Murya Mallaman tai tana Cewa
"Ni Mallama ce a G.G.S.S dake Garin nan"
Da Fara'a Mama ta k'ara Gaisheta, Mallaman Ta amsa tareda Cewa
"Mahaifin Sulthana Nake nema"

Dan Jim Mama tai Sannan Tace
"Ameenatu Yimai Magana Yana Waje Wajan Dalibai"
Tho Tace Ta mik'e tadauko hijab Ta Fita, Chan Sai Gasu Tare sun Shigo, Da Fara'a Ya Karaso
"Barka da xuwa malama"
Murnushi tai tana K'allanshi
"Barka dai Mallan"
Zama yayi Mama da Ameenatu Suka mik'e suka bar wajan, ya K'alli Sulthana dake gefe tanata Raba ido
"Keh Bazaki tashi bah sai kin Gama ji kiji dadin barbadawa Gari"
Dasauri ta mik'e Jiki na Rawa tabar Wajan. Maido da dubanshi yayi ga mallan
"Ina Fata dai Lapia Malama"

Murmushi ta kuma Yi
"Gaskiya bah Lapia bah Mallan"
K'allanta yayi da Alamar Mamaki
"Meh ya Faru Mallama"
Dago kai tai ta K'alleshi
"Zaikai Shekara daya knan dah bana ganin Sulthana Jamilu a Makaranta, nakan tambayi kawarta Sadiya Sani Kullum sai tacemin Sunyi tafiya basu dawo bah, Yau kuma Sai Gashi na Ganta a bakin Kasuwa tana Talla"
Shiru tai tana k'allanshi Ganin Yanda Ya Hade Girar Sama data K'asa
"Eh Hakaneh Sulthana ta dena zuwa makaranta"
Da Mamaki Mallama ta K'alleshi
"Saboda meh Mallan"
Kauda Fuska Yayi sannan Yace
"Saboda na Cireta, Banida Kudin dah zan Rinka biya mata Kudin Makaranta"
Mamaki neh ya kama Mallaman Saboda tasha jin Labarin Mallan Jamilu da kuma dukiyarda Mahaifinshi yabar mai..

Girgiza kai Tai
"Mallan Sulthana tana Cikin Yaranda Keda Matukar kokari a Makarantan nan, Ka daure ta cigaba da Zuwa makaranta. Ina mai tabbatar maka insha Allahu wata rana zakai Alfahari da Ita"
Tsaki Mallan Yaja Yana K'allanta a hassale
"Bazata komah bah ko dolene"
Murmushin Takaici tai
"Tho Shiknan Mallan ka Yarda ta cigaba da zuwa ni nayi Alkawarin zan cigaba da daukan Dawainiyar tah"
Mik'ewa Mallan Yayi Dasauri Rai Bace
"Ce Miki Akai Banida Kudin dazan Biya mata? Makaranta neh Kuma nace bazata Koma bah ko Yarki ce"
Ran Mallaman neh Ya Baci itama ta mik'e a Hasalle
"Anya Mallan Jamilu kai ka Haifi Sulthana Kuwa? Dan ni koh a Karance Karance da yawan Karatu danai ban taba ganin Irin Wannan bah"..

Kofa Mallan Ya nuna Mata
"Maza ki tattara kibar min Gida, Karna Kara ganinki a Gidana, Itakuma Sulthana'n zataxo ta Sameni Wato K'arana Ta kawo Miki koh"
Tsaki Mallaman Taja Tabar Gidan Rai Bace, Jin ta fita Mama ta fito daga Daki
"Haba Mallan Abinda kai ya dace? Gaskiya abinda kake Baka kyautawa, Mallan Kaji Tsoron Allah Haba sai kace bah Mallami bah"
Baice komai bah Sai Hucin Dayakeyi, Dakinshi Ya shiga ya Dauko dorina ya nufi Zaure, Duka Yama Sulthana Sosai Sannan Ya bar Gidan Cikeda Bacin Rai..

Ummy Abduol✍🏻
[28/08, 01:12] Friend Hussaini: 💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐

By *Ummy Abduol*

*Page 46 to 50*

Wannan Shafin naki neh *Bilkisu Jibril* Nagode Sosai Allah Yabar K'auna

Dasauri ta Mik'e tana Zaro ido, Trayn dake gefenta ta dauka ta Fara tafiya tana waigensu. Tsaki Yasir Yaja Yana Cewa
"Yara basajin Magana musamman na Kauye, Ji Wannan yarinyan dan Allah, Yanxu haka aikenta akai ta tsaya nan ruwa ya mata duka"
Shidai Masroor shiru yayi yana Bin Hanyan da Sulthana ta nufa da Kallo. Taboshi Yasit yayi Tareda Yatsine Fuska
"Yadai Shagwababe"
Dukan Wasa Masroor yakai mai
"Bansan Iskanci fah Yasir I hate dis name"
Dariya Yasir Yayi harda Kyakyatawa
"Ni kuma kaga I love the name, Shi zan Cigaba da Kiranka"
Tsaki Masroor yayi batareda Yace Komai bah yayi shigewarshi Motan Ya Zauna, Murmushi Yasir yayi shima Ya shiga motan ya Kunna suka Bar wajan..

Sauri Sulthana take Hannunta na Hago Rik'e da Tryan Gyadarta na Dama ta Dafe Kirjinta tana Numfashi Dasauri dasaur, Gajiya ta soma yi dan haka ta rage Saurin datake Ta cigaba da Tafiya. A kwanan dazai kaita gidansu tai arba da Ameenatu, Ganin Halinda take ciki yasa Ameenatu ta rik'eta Dasauri
"Sulthana Lapia? Meke Damunki"
Kasa magana Sulthana tai Sai K'irjinta datake nunama Ameenatu, kamata tai suka nufi gida. suna shiga gidan Ameenatu ta soma kwallama Mama, Mama ta fito dasauri ganin Halinda Sulthana take ciki yasa Ta K'araso inda suke ta kama Sulthanan ta nufi dakinta da Ita...

Ameenatu ta Fita dasauri ta Dauko wani Kaya ta shigo ta cire mata na jikinta ta Chanza mata, Mama ta fita ta Dibo Garwashi a kasko ta soma Gasa mata Jikinta. Lokaci Guda Sulthana ta fita Hayyacinta Numfashinta na cigaba da Fita sama sama, Hankalin Mama da Ameenatu bah K'aramin tashi Yayi bah, Duk abin nan da ake Mallan na Dakinshi kwance abinshi. Ganin halinda Sulthana take ciki yasa Mama ta nufi dakin mallan dasauri, Da Sallama ta shiga ya amsa yareda dagowa
"Lapia meke Faruwa naganki a rude"
Hankali tashe Mama tasoma magana
"Mallan Sulthana fah batada lapia Sosai gatachan Kwance bata numfashi sosai"
Tsaki Mallan Yayi ya koma ya kwanta
"Wallahi Saratu kinada Matsala, Tho ina ruwana dan batada lapia"
Da Mamaki Mama ta k'alleshi
"Haba Mallan, wai meyasa kake haka ai yarinyan nan ko tsintanta kai baka kamata irin wannan rik'on bah Balle Y'arka daka Haifa"

K'ara jan Tsaki yayi tareda juyawa
"Saratu kina damuna Ki Fita kiban Guri Barci Nakeji"
Girgixa kai Mama tai cikeda takaici ta fito daga dakin, Hafsatu ce ta fito daga bandaki Ta aje buta ta kokarin shiga dakinsu, Mama ta tareda dasauri
"Hafsatu dan Allah idan kinada Dari Uku ki ranta min Zankai Sulthana Chemist ne batada Lapia"
Tabe baki Hafsatu tai
"Ni Mama ina naga Dari uku banida ko sisi nan da kika ganni"
Mamaki ne ya cika Mama harta kasa boyewa
"Haba Hafsatu Dazu fah dasafe naji kina fadama Ameenatu saurayinki ya baki dubu daya"
Turo baki Hafsatu tai tana gungunai
"Inadashi anma gaskiya Mama bazan bada dan Akai Sulthana Wani Chemist bah"
Bata jira mai Mama Zatace bah tabar wajan tana Surutai a Hankali. Binta da Kallo Mama tai tai Cikeda Bakin Ciki..

Dakinta ta koma yanda tabar Sulthana haka ta dawo ta sameta, Ameenatu ta dago ta K'alli Mama Hankali tashe
"Mama meh Baffan yace"
Girgiza kai Kawai Mama tai batace komai bah, Ameenatu ta gane mai Ake Ciki ta Mik'e tsaye Tana Share Kwalla
"Mama barinje Gidan Baba Sani nasan Zai Taimaka"
Saurin Rikota Mama tai tana girgiza mata kai
"Aa Ameenatu karkije Kinsan idan kikaje idan ranmu yayi dubu ya baci a gidan nan saboda kinsan sai Mallan Sani yamai magana"
K'allan Sulthana Ameenatu tai ta Fashe da Kuka
"Mama haka zamu zuba ido muna K'allan Halinda Sulthana take Ciki bamuda Bakin magana. Wai meyasa Baffa yake Haka Neh"
Bata jira mai Mama zatace bah ta nufi dakin Baffa Idonta rufe Saboda bacin Rai..

Sallama tai a dakin, Baffa ya amsa tareda mata izinin ta Shigo, ta Shiga ta Samu Guri Kusa da Gadon K'arfenshi ta zauna. K'allanta Baffa Yayi Yana yar Murmushi
"Ameenatu lapia"
Dagowa tai ta K'alleshi Bako digon Tsoro a ranta
"Baffa Abinda kakeyi Babu kyau, Meyasa kake Wahalar da Sulthana. Dan

Please Login or Register in order to submit comment