Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kuka ya nuna Mallamin yace

"Ka cuceni, Allah ya isa tsakanina dakai."

Mama ta matso tana kuka itama

"Kai hakuri Mallan shima ai gafaranka yazo nema"

Kuka baffa yake wuiwui

"Bah irin rantsuwar da batayi bah akan bah abinda ya shiga tsakaninku anma ban yarda bah. Ashe dagaske ne"

Ya k'ara rushewa da kuka

"Ki yafeni Rabiatu, ban miki aldarci bah naci amanar dana dauka naki. Ki yafeni"

Kuka yake sosai yana cigaba da cewa

"Kah cuceni ka rusamin farinciki, yanzu dama Sulthana y'ata ce naketa mata wannan kiyaiyar"

Zumbur ya mik'e yana k'okarin sa takalmin shi. Mama itama ta mik'e

"Ina zaka Mallan?"

Yana kuka yana cewa

"Zanje neman Sulthana ta dawo gida, ta yafeni rashin sani neh"

Mama ta rik'eshi

"Kayi hakuri Mallan Kaga bakajin dadi, kuma Sulthana shekara d'aya fa knan da rabi rabonmu da ita. Bbu wanda yasan inda take"

Dakyar ta Lallabashi ya zauna, kowa a wajan kuka kawai yake bama kamar Baffa. Yana kuka hannunshi akai

"Allah ka yafeni, Rabi ki yafeni. Sulthana ki yafeni"

Sun d'ade a haka bah wanda yake rarrashin wani har na wasu lokuta sanna Mallamin yace

"Duk inda y'arka take indai tana raye tana rayuwa ne tareda Aljani, ma'ana akwai aljani a jikinta"

Baffa baice komai bah ya mik'e ya shiga dakinshi yana cigaba da kuka. Dakyar su Ameenatu sukaba Mallamin Hakuri ya tafi...


Mami na barin Falon d'akin da Masroor ke kwance ta nufa. Ga mamakinta sai ganinshi tayi tsaye yanasa Burtin din shirt dinshi da Alama wanka yayi

Kallo d'aya zakamai kaga ramar dayayi. Dasauri ta k'araso wajan baki bud'e

"Son idona gizo yakemin ko gaske meh? Kaine a tsaye a nan"

Juyowa yayi ya rik'e kafadanta yana Murmushi

"Nine Mami, am now fine"

Mahnoor ce ta shigo dakin a rud'e tana haki, hannun Masroor ta rik'e tana nunamai Kofar fita. Sakin Hannunta yayi yana k'allanta

"Menene? Waya biyoki?"

Haki take tayi saida yad'an tsagaita tace

"Mami wallahi yanzu naga Sulthana a wata mota sun fita d'aga nan gidan kuma a motar gidansu Aisha neh"

Tun kanta k'arasa maganan Masroor ya nufi kofar fita, Mami ta rik'eshi tana girgixa mai kai

"Ina zaka kaida Bakada lapia"

Idanunshi cik'e da kwalla yana k'okarin kwace kanshi daga rikon da Mami tamai

"Mami ki kyalleni naje dan Allah I want to see her"

Kallan Mahnoor tayi fuskanta a had'e

"how sure are you itace??"

Nan Mahnoor ta fara inda inda. Masroor sai kokarin kwace Hannunshi yake ya kasa saboda jikinshi daba k'arfi. Hannunshi taja ta zaunar dashi kan gado

"Kah kwantar da Hankalinka indai itace komai yazo k'arshe tunda tare suke da Aisha"

Baice komai bah k'anshi na k'asa baisan Mami taga hawayen dake zuba a idonshi taja hannun Mahnoor suka bar dakin..

Ummy Abduol✍🏻

💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐

By *Ummy Abduol*


DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION

*Page 186 to 190*

Baice komai bah k'anshi na k'asa baisan Mami taga hawayen dake zuba a idonshi, taja hannun Mahnoor suka bar dakin..

Sun danyi nisa da government house, Sulthana ta rik'e kanta tana k'allan Aisha

"Ayoush ku kaini gida kawai kaina wanni irin ciwo yake"

Ayoush tamatso tareda taba goshinta

"Kuma jikinki bah zafi, kanne kawai ke ciwo?"

Kai kawai Sulthana ta gyada batace Komai bah. Gida suka kaita lokacin Fareed baya nan sukai Sallama ta tafi. Falo ta shiga ta zauna kanta na mata ciwo sosai, rintse ido tayi tareda tafe kan tun daga nan bata k'ara sanin inda kanta yake bah...


Ganin halinda ake ciki yasa Mami ta d'au waya ta soma neman layin Abba, lokacin yana tsaka da aiki ya daga tareda fada mata aiki yake. Saurin katseshi tai ta fadamai dalilin bugowanta daneman izinin fita. Bai musa bah ya amince ta kashe kiran..

Aminiyarta ta kira wato matar duty governor suka nufi gidansu Ayoush tareda rakiyan bodyguards dinsu. Masroor na ganin sun fita ya dau makulin motanshi ya mara musu baya..

Tarba sosai Mum din ayoosh tai musu, saida Suka natsa sannan suka sanar da ita dalilin zuwansu. Batareda batalokaci bah tayo kiran Aisha, tafito ta tsugunna har k'asa ta gaidasu. Mami ce tafara magana tana cewa

"Aisha menene Sunan Yarinyan da kukazo tare"

D'an dagowa Aishan tai sannan tace

"Queen!"

Mami ta girgiza kai tana y'ar murmushi tace

"Sunanta na gaskiya nake magana"

Batareda bata lokaci bah tace

"Sulthana!"

Masroor dake mak'e jikin labule ya fito dasauri ya k'araso inda Aisha ke tsugunne shima ya tsugunna

"Aisha dan Allah aina take?? Fadamin pls"

Kowa dake falon mamakin ganin masroor yayi bama kaman Mami. Aisha ta kalleshi tareda sauke ajiyan zuciya

"Classmate dita ce, a nan kano suke itada brothern tah"

Saurin girgiza kai Mami tayi tana cewa

"Wannan bah Sulthanan ka bace Masroor, kaji wannan fah y'ar kano ce kuma tanada yaya"


Hannun Aisha ya kama idanunshi cikeda da kwalla

"Pls ki kaini wajanta, ni nasan Sulthana na neh."

Kai ta gyada ta mik'e tadauko gyalenta ta fito, dukansu suka dunguma zuwa gidan..


Shigowan Fareed kenan cikin gidan tun daga haraban gidan yakejin k'aran fashewan abubuwa, dagudu ya k'arasa cikin falon. Bin falon ya somayi da kallo komai a hargitse, center table a fashe abubuwa duk a fashe. Jin wani k'aran a dakinshi yasa ya nufi dakin dasauri, ganin Sulthana yayi tsaye duk gashin kanta a barbaje hannayenta na jini sai fashe fashe take tana ihu kamar bah itaba.

Jikinshi ne ya soma rawa ya k'arasa kusada ita ta daga sauran mirrown dake hannunta za wurga mai, dasauri yaja da baya mirrown ya fadi gefenshi ya fashe...

Ihu ta saki mai k'ara ta nufeshi dagudu ta rikeshi tana dukanshi tako ina. Kallanta kawai Fareed keyi jikinshi a mace hawaye na gangara daga idonshi, dakyar ya tattaro karfinshi ya rik'eta murya na rawa yace

"Queen meya sameki? Why all this"

Dukanshi kawai take a k'irji da iya karfinta. Janyota yayi dakyar zuwa falo ya zaunar da ita k'an kujera sai kokarin tashi take tana ihu da karfi..

Motocin su Mami neh suka tsaya a kofar gidan, umman Fareed ta k'alli Aisha da Mamaki

"Nan neh gidansu Yarinyar?"

Kai Aisha ta gyada sannan tace

"Nan neh nasan tanama ciki"

Da mamaki umman Fareed ta k'alli Mami tana cewa

"Nan fah gidan Fareed neh"

Dasauri Aisha tace

"Eh sunan yayanta knan"


Umman fareed ta kwalalo ido ta fito daga motan dasauri, tuni Masroor ya fito daga tashi motar yana jiran fitowansu dan ta nunamai gidan. Aisha ce ta musu jagora zuwa bakin kofar gate din. Kofar a bud'e take dan haka suka shiga gidan kai tsaye..

Ihun da sukaji neh yasa suka tsaya chak, Masroor ya saki kuka mai sauti dagudu ya shiga falon dake gidan. Sulthanan shi ya gani rungume jikin Fareed tana kuka da ihu tana kokarin ture Fareed daga jikinta

Tsugunawa Masroor yayi ya runtse idonshi yana girgiza kai bakinshi na furta

"Noo! Noo!! Sulthana"

Juyowa Fareed yayi firgice jin murya a bayanshi, dai dai nan su Mami suka shigo falon kowa na kallansu da Mamaki. Umman Fareed ta k'araso ranta b'ace

"Fareed meh nake gani haka? Ka aje yarinya a gidanka"

Baice komai bah har yanzu kuma yana rik'e da Sulthana daketa ihu tana dukanshi, kokarinta kawai ya saketa. Hawayen dake mak'alle a idanunshi suka sauka muryanshi na Rawa yace

"Umma I'm very sorry, its not what uh think. Yanzu abinda yafi shine mukaita asibiti"

Kasa cewa komai Mami tayi ta k'arasa inda Masroor ke tsugunne yana kuka kamar yaro. D'agoshi tayi tsaye tasa hannayenta tana sharemai hawaye

"Stop crying son, karka jama kanka wani ciwo"

Muryan Fareed yaji yana cewa

"Friend help me mu kamata mu kaita Asibiti"

K'ara k'allan Sulthana yayi yaga yanda take ihu da bige bige, ya rintse ido ya bude. Daky'ar suka kamata sukasa a mota suka nufo asibiti dukansu..

batareda wani bata lokaci bah aka amsheta ganin manyan mutane kuma tare da likita. Dr Sa'ood da wasu likitoci ke kanta, aluran barci sukai mata sannan suka hau mata gwaje gwaje. Sun d'au lokaci suna dubata, Fareed na tsaye har lokacin hawaye yake ya kasayin komai..

Saida suka natsa sannan Sa'ood ya kira su Mami Office dinshi. Bayan sun zauna ya soma magana

"Ur excellency duk binciken daya kamata muyi duk munyi anma bamuga komai bah. Ni sai nake gani kamar Cutar bata asibiti baneh inaga..
"

Saurin katseshi Umman Fareed tai da cewa

"Wanne irin magana kakeyi Sa'ood, yarinyan da kowa yagani tana abu kamar mahaukaciya zakace bana asibiti baneh"

Ajiyan zuciya ya sauke sannan ya cigaba da cewa

"Umma! Bata lokaci kawai za'ayi, a shawarce shine a nemo malami dazai mata ruk'iya"

D'an Murmushi Mami tai ta mik'e

"Mun gode doctor insha Allahu hakan za'ayi"

Office din suka fito a bakin kofa sukaga Masroor tsaye kanshi a k'asa. Hannunshi Mami ta kama ya d'ago jajayen idanunshi yana k'allanta

"Son muje gida kasha magani"

Girgiza mata kai yayi dasauri

"No Mami zan zauna tareda Sulthana"

Rungumoshi jikinta tayi tana shafa bayanshi

"I know how uh feel Son, be Strong everything wil be fine. Baga Aisha bah she wil take care of her"

Dakyar ta lallabashi suka koma gida. Sai dare suka natsa Mami ta samu Abba a dakinshi ta sanar dashi duk abinda ke faruwa. Ya cika da mamaki sosai, shi kanshi yanajin son yarinyan musamman yanda yaji batada gata. Washe gari da safe shima mutanenshi sukaje gaisheta, Maman Aisha suka samu a wurinta da Fareed..

Sun gaisheta tareda mata addua coz har lokacin bata farka bah sannan suka tafi..

K'arfe 10 na safe a Asibiti tayi mah Masroor shida Yasir, direct dakin suka shiga kai tsaye. Aisha suka samu da Fareed a dakin. Masroor baice komai bah ya nufi bakin gadon yana K'allan Sulthana tareda tambayan Aisha jikinta. Ganin Masroor baimai Magana bah yasa ya mik'a mai hannu yace

"Morning Friend"

juyowa Masroor yayi ya galla mai harara ya juya ya maida Fuskanshi ga Sulthana. Daidai lokacin idanunta suka fara rawa Masroor ya kara matsowa kusada gadon yayi kneeldown yana k'allanta da hawaye cike idonshi

"Beauty open ur eyes its me Masroor"

Bud'e idonta tai dasauri tareda mik'ewa zaune ta k'uramai ido idanunta taf da hawaye. Ganin tana neman kuka yasa ya girgiza mata kai hawaye na gangara a idonshi

"Karkiyi kuka Beauty, nine dai Masroor naki"

hawayen daya gangaro mata ta share ta t'aba hannunshi taji tabbas shine, k'ara fashewa da kuka tayi ta rungumeshi. Shima kukan yake a hankali yana shafa suman kanta..

Duk yan dakin yan K'allo suka koma, Fareed ko gabanshi ne keta faduwa zuciyarshi ta shiga masa zafi ganin yana kokarin fashewa da kuka yasa yabar dakin dasauri. Direct Office dinshi ya nufa ya zauna akan kujeranshi ya daura kai kan table ya fashe da kuka mai tsuma zuciya. Kuka yake sosai anma bah mai Lallashin shi

A haka Sa'ood ya shigo Office din ya sameshi, Zama yayi yana kallan Fareed batare dayace komai bah. Saida ya bari yayi kukan mai isarsa sannan ya mik'e ya dawo kusa dashi tareda dafashi..

"Na barka kai kukan neh saboda ka samu relief, tel me whats wrong"

Idanun Fareed taf da hawaye ya d'ago yace

"Sa'ood na rasa Sulthana, na rasata."

Dasauri Sa'ood ya zagayo ya tsugunna yana facing dinshi dakyau

"Bangane kah rasa Sulthana bah Fareed"

Runtse ido Fareed yayi hawayen da suka makale suka zubo ya d'ago yana k'allan Sa'ood wanda shima shi yake kallo

"Friend dina Masroor yana san Sulthana, kuma kasan yanda muke dashi da kuma yanda iyayenmu suke."

Shiru yayi yana share kwallan dake idanunshi. Sa'ood ya nisa yace

"And so what Fareed, kanasan Sulthana?"

Dagowa yayi dasauri yana k'allan Sa'ood shekeke

"I so much love her, I cnt do witout her. And banasan abinda zai kawo matsala tsakanin wannan zumuncin dake tsakanin mu"

Sa'ood yaja dogon tsaki tareda mik'ewa

"Fareed fight and get wat uh want, karka kasa wannan a ranka. Kayi kokari ka yaki har kasamu abinda kakeso ka.."

Wayan Fareed dake ringing neh ya katse shi, ganin mai kiran yasa ya d'auka tareda Sallama Sannan ya mik'e yace

"Ganinan zuwa"

K'allan Sa'ood yayi

"Zanje gida Umma na nemana"

Gyada kai kawai Sa'ood yayi sukai Sallama yabar office din.

Ummy Abduol✍🏻

💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐

By *Ummy Abduol*


DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION

*Page 191 to 195*


Fita yayi daga Office din ya nufi motarshi dasauri direct gida yayi, saida ya shiga side dinshi dake gidan yayi wanka da Sallah sannan ya shiga side din Umma gabanshi na faduwa..

Zaune ya sameta itada bak'i, zama yayi kan Carpet suka gaisa da mutanen falon. Yana nan zaune har suka gama ta sallamesu Sannan yad'an duk'ar dakai murya na rawa yace

"Ina kwana Umma"

Shiru tayi tana kallanshi, jin shirun yayi yawa yasa yad'an dago suka hada ido yayi saurin maida kai kasa. Umma ta nisa ranta b'ace ta soma magana


"Fareed ina hankalinka yaje ina iliminka? Bantaba expecting haka daga gareka bah"

A hankali ya d'ago cikin sanyin murya yace

"Dan Allah Umma kiyi hakuri nasan nayi kuskure"

Ajiyan zuciya ta sauke

"Fareed kasan matsayinda mahaifinka yake kai yanzu, bai kamata haka na bullowa bah. Bakama gudun maganganun mutane kadauko yarinya ka ajeta a gidanka har na tsawan shekara"

Hawaye cike da idanunshi ya dago

"Umma kiyi hakuri d'an Allah wallahi it was'nt my fault, gani nai kamar bazaki yarda ta zauna dake bah. And yarinyan need help babanta ne ya koreta witout any serious reason"

Umma ta girgiza kai tana murmushin takaici

"Fareed uh are stil young, bazaka ganeh abinda nake nufi bah."

Baice komai bah kanshi a kasa. Nasiha Umma ta soma mai mai ratsa jiki, Sannan tace ya tashi yaje. Godiya yayi ya mik'e ya koma side dinshi jiki a sanyaye..


A asibiti kuwa ta dad'e a jikin Masroor tana kuka mai ban tausayi daga bisani ta janye jikinta daga nashi tana kallanshi

"Ya Masroor meyasa zaka tafi ka barni, meyasa kak'i yarda dani."

Hawayen idanunshi ya share

"Kiyi hakuri Beauty nasan nayi lefi i'm sorry"

Batace komai bah ta koma kan gadon ta kwanta ta juya mai baya. Hannunshi Yasir ya kama yajashi suka fita. Aisha ta matso kusada gadon tad'an taba ta tana cewa

"Sannu Queen ya jikin"

Tashi zaune tayi tana yatsine fuska

"Ayoush meya kawoni asibiti? Bah gida kuka kaini bah"

Murmushi Aisha ta mata

"Kin tuna kince gabanki na faduwa? To shine ya Fareed da kikayi barci ya kawoki asibiti"

Tana kokarin jeho mata wani tambayan tai saurin katseta da cewa

"Yauwa Queen inaso na tambayeki"

Gyada kai tayi tana kallanta, Aisha ta cigaba da cewa

"Aina kikasan Masroor, Sannan keh wacece coz ance ya Fareed bah brodanki baneh?"

Murmushin takaici tayi

"Zakisan duk abinda baki sani bah dnt worry, yanzu ina ya Fareed"

D'an jim tayi tace

"I donno myb yana office"

Batace komai bah ta koma ta kwanta zuciyanta a jagule..

Kwanan Sulthana biyu a asibiti, tun daga ranan da aka kwantar da ita bata k'ara ganin ya Fareed dinta bah. Masroor kuwa kullum yana tare da ita shida Aisha, haka Mahnoor tazo dubata itama. Sulthana tasha Mamaki sosai jin su y'ayan gwanma neh. Ranar da Dr Sa'ood yayi discharging dinta ta tareshi da tambayan ya Fareed baice mata komai bah yabar dakin..

K'allan Aisha tayi fuskanta bah walwala

"Aisha d'an Allah ki kaini Office din ya Fareed"

Nan da nan fara'ar dake fuskan Masroor takau ya hada girar sama data k'asa. Sulthana na ganin haka tasha jinin jikinta ta koma ta zauna. Waya ya dauka ya kira Mami ya sanar da ita sallamansu da akai, batareda bata lokaci bah tace ya d'aukota suzo gida. To yace ya kashe wayan ya kalleta fuska bah walwala

"Mami tace na daukoki muje gida"

Batace komai bah ta mik'e tadau gyalanta ta yafa Aisha ta soma hada musu kayansu. Ganin suna abu slow yasa yad'au wasu kayan ya fita yana cewa

"Ku sameni a mota"

Aisha ce ta amsa. Bayan fitanshi Sulthana ta kalli Aisha idanunta cike da hawaye

"Aisha ina Ya fareed? Meyasa yak'i zuwa inda nake? Duk wanda na tambaya shi sai yayi banza dani."

Aisha batace komai bah ta k'ama hannunta suka fita daga dakin, Office dinshi suka nufa a kofar office din Aisha ta tsaya itakuma ta tura kofar ta shiga jikinta na rawa

Zaune ta sameshi yayi tagumi ga tulin folders a gabanshi, jiki a sanyaye ta k'arasa kusadashi ta dafa kujeran dayake kai

"Ya Fareed! Ya Fareed!!"

Zabura yayi ya juyo a tsorace yana kallanta. Ta shagwabe fuska

"Ya Fareed inata nemanka shine kaki zuwa ka dubani koh bayan kuma kaine ka kawoni"

Kirkiro murmushi yayi

"I'm sorry Queen ayuka neh sukaimin yawa"

Dawowa tayi ta zauna kan kujerun dake Office din tace

"Ya Fareed meyasa zanje gidansu Ya Masroor? Bah gidanmu zamu koma bah"

Mik'ewa yayi dasauri yana kallanta

"Gidansu Masroor?" ya furta da Alamar Mamaki

Kai ta gyada tace

"Eh haka yace"

Kafin yayi Magana aka banko kofan Office din aka shigo, a tsorace Sulthana ta kalli kofan ganin Ya Masroor tsaye yana huci kaman zaki yasa jikinta ya soma rawa. Karasowa wayanta yayi rai bace yace

"Fita ki wuce mota ki jirani"

A guje tabar Office har tana kokarin faduwa
A harzuk'e Fareed yace

"What do you think you are doing Masroor? Na lura san Sulthana kake to ka sani bazaka taba cin nasara bah becoz sulthana tawa ce!"

Dariya Masroor ya fashe dashi yana numa Fareed da hannu

"Kai har kana tunanin zan iya tsayawa ina musayan yawo dakai? No! Coz nagaba yayi gaba na baya sai labari"

Bai jira mai Fareed din zaice bah yabar Office din tareda bugo kofa. A mota ya samu Sulthana zaune itada Aisha sai zazzare ido take. Baice komai bah ya tada motan yabar Asibitin a guje, bah Sulthana kawai bah Har Aisha saida ta tsorata da yanda yake tukin. Government house suka nufa kai tsaye suna shiga suka tarar da Mahnoor da Maids bakin kofan Side din Mami suna tsaye suna jiran k'arasowan su. Yana parking Mahnoor ta nufo motan a juye, Sulthana na fitowa ta rungumeta tana dariya. Mahnoor tace

"Uh welcome friend"

Dariya Sulthana kawai tai mata duk hankalinta nakan ya Masroor ganin yanda yawani d'aure fuska. Mahnoor ce tai musu jagora zuwa cikin gidan, wani hadad'en daki takai Sulthana tana cewa

"Sis wannan shine d'akinki inji Mami"

Bin dakin da kallo Sulthana tayi tana Murmushi, gyallenta ta aje kan katafaren gadon dakin ta hau juyi cikeda jin dad'i sannan ta juyo da fara'a sosai akan fuskanta ta rik'e hannun Mahnoor tace

"Kicema Mami nagode Sosai, I'm so greatful"

Itama murmushi Mahnoor din tayi, Aisha tace

"Dak'in yayi kyau sosai"

Ledojin Hannunta ta aje tana cewa

"Zanje gida"

A tare suka fito duk'asuka rakata, Mahnoor tasa driver ya kaita gida sannan Mahnoor ta shiga nunama Sulthana Cikin gidan..

Sosai Sulthana taji dad'in kasancewa gidan, ko bakomai ta kafa tarihi ta zarce su Ya ameenatu dan ita yau gata a Cikin gidan gwamnati..

Basu samu had'uwa da Mami bah ranar dan batanan sai washe gari, Mahnoor ce keta d'ebe mata k'ewa. Da safe tare suk'a sauko da Sulthana Family dinning din dake gidan, Suma neh kawai Sulthana bataiba Ganin Mutumin datake Gani a tv yau a gabanta zahiri

Kanta a k'asa suka k'araso wajan Dinning din, Mami ce zaune da Abba sai Masroor dake gefe fuskannan nashi bah walwala. A hankali ta tsugunna har k'asa ta gaida Abba, cikeda kulawa ya amsa sannan ta gaida Mami itama ta amsa mata da Fara'a.

D'an dagowa tayi ta k'alli Masroor sannan tace

"Ina kwana ya Masroor"

Kamar bazai amsa bah chan kuma yace

"Lapia"

Bah Sulthana kadai bah har Mami da Abba sunyi Mamakin yanda ya amsa mata gaisuwan. Kujera Mahnoor taja mata ta zauna Sannan ta soma serving dinta.. Ganin tak'i sakin jiki taci abincin yasa Abba ya tashi yamusu sallama yabar Wajan..

Itama Mami ta mik'e tana cewa

"Ina zuwa"

Ganin haka yasa Masroor d'aukan plate dinda ke Gabanshi yabar wajan. Sai a sannan ta kalli Mahnoor idanunta taf da hawaye tace...


Ummy Abduol✍🏻Abduol✍🏻

💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐

By *Ummy Abduol*


DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION

*Page 197*


Gudu yake sosai yabi ta bayan gidan inda zai sadashi da filin basket ball. Ganin tuk'in nashi bana hankali baneh yasa Sulthana k'ara fashewa da kuka

"Dan Allah ya Masroor kayi hakuri ka daina gudu"

Wani wawan burku yaja ya juyo yana k'allanta idanunshi a rune

"Sulthana bakya sona ko? Fareed kikeso?"

Batace komai bah k'anta a kasa, fita yayi daga motan ya jingina yasa hannayenshi a aljihu ranshi a b'ace. Tana ganin haka tafito jikinta na rawa ta tsugnna gabanshi kanta a k'asa

"Kayi hakuri ya Masroor, ya fareed na d'aukeshi yayana saboda shiya taimakeni. Ban tab'a sanshi bah kuma bai tab'a cemin yana sona bah"

D'agota yayo daga tsugunnen datake ya tallafo fuskanta suna kallan juna

"Ina Sanki Beauty, ina sanki sosai. Pls ki soni kar sanki yasa na shiga wani hali"

Rungumeshi tayi ta fashe da kuka, a hankali tace

"I love uh to ya Masroor"

D'agota yayi daga jikinshi ya kura mata manyan idanunshi da Mamaki

"What do uh just say"

D'an Murmushi tayi tasa hannu tana share hawayen fuskanta. Da lebbunanta ta furta

"I lav uh"

Tsalld yayi yace

"Woaw!"

Ta kyalkyace da dariya tana kallanshi. Motar Fareed neh tazo wucewa ganinsu awajan yasa yayi parking dan yau ji yake saidai duk abinda zai faru ya faru..

Parking yayi ya fito ya karaso inda suk'e tsaye, Masroor na ganinshi ya had'e rai ya juya ya kalli Sulthana yana cewa

"Shiga mota ki jirani"

Bah musu ta bud'e kofan tana kokarin shiga Fareed yayi maza ya k'ama hannunta, a tsorace ta juyo ta kalleshi. Masroor ya fizge hannunta daga nashi yana huci

"Fareed ka kiyayi kanka, meyasa kake kokarin shiga hurumin daba naka bah"

A hasale Fareed yace

"Hurumin daba nawaba ko hurumin daba naka bah"

Ya kalli Sulthana suka hada ido yace

"Tun ranar da Yayarki ta kawoki chemist din kauyenku Allah ya d'auramin Sanki. Nayita k'okarin in sanar dake ban samu daman hakan bah. Naje neman aurenki wajan Mallan anma yacemin an miki miji. Bayan kin dawo gurina inata kokarin na sanar dake abin yacitira"

Ya d'ago yana kallanta

"Ina matuk'ar sanki Sulthana. Na dad'e ina dakon soyaiyarki a zuciyana"

Fashewa tayi da kuka ta fadi a wurin zaune tana kuka sosai, harga Allah bata tab'a zatan Ya Fareed zai Furta Mata Kalmar so bah.
K'arasowa wajan Masroor yayi yana huci

"Fareed kana b'ata lokacin ka neh a banza, karka taba tunanin Sulthana a matsayin matarka. Na fada zan kuma k'ara fada Sulthana Tawa ce!"

Bai ankara bah yaci Fareed ya kai mai wani mugun naushi a baki nan da nan bakin ya fara jini, Fadane Sosai ya kaure tsakaninsu, Sulthana ta mik'e dasauri tana kuka ta shiga tsakiyarsu

"Ku daina fada d'an Allah"

Ta juya ta kalli Fareed dashima gefen idonshi ke jini tace

"Ya fareed ku daina fada, indai saboda nine na hakura banayi"

Ai kamar k'ara zuga Fareed take ya wawuri Masroor ya soma kaimai nushi, Shiko Masroor kasa dukanshi yayi dan sam baiso hakan ta faru tsakaninsu bah. Ganin Fareed na neman halakashi yasa shima ya fara maida Martani, dukan juna suke bana wasa bah Sulthana na gefensu tana kuka da ihu dan neman agaji. Daidai nan mottocin su Mami suka k'araso wajan a guje dan tun dazu bayan fitansu Mahnoor ta sanar da Mami abinda ke faruwa. Yawo suketayi har Allah yasa suka biyo ta wajan..

Umman Fareed ce ta fara fitowa ta k'araso wajan a zuciye, lafiyayyen Mari ta wanke Fareed dashi tana huci

"Bantaba sanin bakada hankali bah sai yau Fareed, yanzu akan mace shine kuke kokarin Kashe junanku?"

Kasa ma magana Mami tayi anma kana gani kasan ranta bah k'aramin Baci yayi bah. Mahnoor ta k'araso wajan ta rik'e Sulthana daketa kuka kamar ranta zai fita tasata a mota. Motar y'an sandan dake bayan nasu Mami Umman Fareed tasa aka shigar dasu Masroor aka kaisu Asibitin dake Cikin gidan..

Daddy da Abban Fareed suma Ransu bah k'aramin baci yayi bah bama Kamar Abban fareed dan shi cewa yayi Fareed ne baida gaskiya dan koma menene bai kamata ya biyo Masroor har gidansu ya dakeshi bah. Dole hakan yasa aka hadu dan Sulhu wuraren K'arfe sha d'aya na dare a babban Falon Daddy..

Daddy da Abban Fareed a a gefe zaune sai Mami da Umman Fareed suma suna gefe. Su Masroor kuma suna k'an Carpet zaune kowa da kumburaren Fuska. Daddy neh ya soma magana fuskanshi bah walwala

"Banji dadin abinda ya faru bah, haba Masroor haba Fareed. Yanzu akan mace kuke kokarin kashe kanku"

Abban Fareed yayi saurin amshewa da cewa

"Yanzu idan abun nan yakai waje duniya zatai mana dariya akan cewa ga y'ayanmu suna fada tsakaninsu akan mace. Sam wannan abin bai dace bah"

Masroor ne ya soma d'agowa yace

"Daddy, Abba kuyi hakuri"

Abba ya nuna Fareed da yatsa

"Duk abinda ya faru ga babban mai lefi nan, haka kawai Masroor baya kamaka da dukaba dan kazo gidansu. kaida nakema Kallan mai hankali ashe bakada shi, karka manta kaifa babba neh ka

Please Login or Register in order to submit comment