Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

bazaki je kiyi aikinki bah. Uban wa kikeso ya miki shara da wanke wanke"
d'an dagowa Sulthana tai hawaye na gangarowa a idonta
"Dan Allah yaya Ameenatu kiyi hakuri banida lapia neh"
Duka takai mata dai dai nan Hafsatu ta k'araso wajan tana Murmushin Mugunta
"A'a yaya Ameenatu yau kuma Y'ar son ake duka"

Tsaki Ameenatu ta k'arayi tana nuna Sulthana da yatsa
"Wallahi idan baki tashi kinyi aikin daya kamata bah sai na miki dukan tsiya"
Kallanta hafsatu tai da mamaki, Yau kuma Ameenatu kecewa zata duki Sulthana, Lallai abin babba neh.
Kasa tashi Sulthana tai sai kuka datake Mara sauti, dakyar ta mik'e ta zauna tana k'allan Ameenatu data hada girar sama data k'asa
"Dan Allah yaya Ameenatu kiyi Hakuri"
Ai kamar zugata take nan da nan ta rufeta da duka, Hafsatu taga bati itama ta tayata. Bah abinda Sulthana take in banda ihu. Ihunta ya fito da Mama ta K'araso wajan dasauri..

Dakyar ta kwace Sulthana a hannunsu a fusace tace
"Wannan wanne irin iskanci meh Ameenatu, wai meke daunki me? Metai muku kuke dukanta haka kamar Allah ya aiko ku"
Ameenatu ta hade rai tana huci
"Dan wulakanci tun dazu yarinyan nan batai aikin gida bah, jibi gidan nan sannan ina mata magana tana cemin wani batada lapia"
K'allan Ameenatu Mama ta tsaya yi
"Lallai Ameenatu baiwarki ce ita da zakice dole sai tamiki aiki, ai rashin lapia ya wuce komai sai kuyi mata uzuri"
Hafsatu ta chuno baki
"Haba Mama ke kullum sai ki rinka hana ana hukunta yarinyan nan, Gaskiya..
Saukan Mari Hafsatu taji a fuskanta, a fusace Mama tace
"Wallahi ki kiyayeni Hafsatu, na lura abubuwanki nema suke su wuce wuri"
Nunasu da dan Yatsa tayi tana cewa
"Tho bari kuje, daga yau Sulthana bazata k'ara aikin gidan nan bah ku zakuyi. Meye ku anfanin ku"
Baffa ne ya bankado kyauren gidan ya shigo jin hayaniya, cirko cirko ya samesu a tsaye sai Sulthana dake Zaune a kasa tana kuka duk jini a hancinta da baki..

"Lapia??" Baffa ya tambayi Mama, Hafsatu ce ta koromai bayanin duk abinda ya faru. Nan ko Baffa yahau sababi ta inda yake shiga batanan yake fita bah, Ameenatu ta kalla yana cewa
"Ku cigaba da dukanta ai wannan ma iskanci neh"
Hafsatu ce ta cigaba da dukanta Mama na tsaye tana k'allan Baffa cikeda takaici, batace komai bah ta koma dakinta ranta bace. Itama Ameenatu daki ta koma a fusace, ligi ligi Hafsatu taima Sulthana Baffa na Tsaye. Saida ta duketa san rai Sannan ta kyalleta, Sannan Baffa yasata tai duk aikin Gidan yana Tsaye. Tanayi tana kuka dakyar tai aikin ta gama ta koma zaure ta zauna ta cigaba da kukanta..

Nan da nan wani sabon Zazzabin ya rufeta. Ana Sallan Azahar Baffa ya kwalla mata kira, ta nufi Cikin gidan dasauri, gyada ya mik'a mata. Ta amsa dasauri ta hau wankewa, tana gamawa ta daura a wuta ta zauna bakin murhun ko sanyin datake ji zai ragu. Bata gama bah sai bayan La'asar sannan tadau Gyadan ta nufi bakin kasuwa. Inda ta saba zama ta aje gyadan, zama tai ta hada kanta da guiwa ta fashe da wani sabon kukan, murya taji a kusada ita mai sanyi yana cewa
"Meke damunki Sulthana whats wrong"
Dago runanun idanunta tai duk a tunaninta likitan nan neh, Ganin Masroor yasa ta maida fuskanta ta cigaba da kuka. Runtse ido Masroor yayi ya dunkule Hannayenshi, jin kukanta yake har cikin Ranshi nan da nan shima idanunshi suka chanza launi..

"Sulthana, meke damunki? Tel me pls"
Dago kai tai tana turo baki, ganin yanda take karkarwa yasa ya mik'e dasauri
"Sulthana are you sick?"
Dauke kai tai tana cigaba da turo baki, dakyar ta iya mai magana shima tanayi hakoranta na karo da juna
"Nidai ka daina zuwa inda make, idan Yaya hafsatu taganni zata fadama Baffa kuma dukana zaiyi"
Tsugunawa yayi gabanta cikeda damuwa
"Sulthana fadamin meke damunki, nasan kina cikin damuwa. Me hafsat take miki itada Baffa"
Mik'ewa tai dasauri tana k'akabe Riganta, trayn gyadan ta sunkuya zata dauka yayi saurin rik'ewa
"Please Sulthana ki tsaya ki saurareni, Am here to help uh. Taimakonki zanyi, ki fadamin ko menene nikuma na miki alkawarin zan kawo karshen koma menene"
Tsayawa tai ta tana K'allanshi da Alamar mamaki...

Tho fah ga *Doctor Fareed* Ga *Masroor*
Shin Fans wah kuka zabarma Sulthana ya taimaka mata?? Nidai nace......

Ummy Abduol✍🏻
[28/08, 01:12] Friend Hussaini: 💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐

By *Ummy Abduol*

*Page 101 to 105*

Tsaya tai tana K'allanshi da Alamar mamaki. kai ya gyada mata
"I mean what I said"
Sai a Sannan ya K'alleta da kyau, a rudeyace
"Sulthana maiya sameki a fuska? Wayaji miki ciwo?"
Shafa wajan tai, batace komai bah
Trayn Gyadanta ta fuzge ta daura akai ta soma tafiya. Binta yayi yana mata magana anma ko sauraranshi batai bah tayi tafiyarta. Ranar Sulthana batai ciniki nah hakanan ta koma gida, Duka kuwa saida tasha shi Wajan Baffa. Haka tai kukanta ta gaji ta kwanta, yauma k'amar jiya Yaro ya shigo yace Ana Sallama da ita, turo baki tai tacema yaron yace bazata zo bah haka koh akai, Yaron ya koma yagayama Fareeed Sakon da Sulthana ta bashi..

Baice komai bah ya bude mota ya dauko wani k'aton leda, yaron ya mik'ama wah
"Dan Allah gashi ka kai mata kaji"
Hannu Yasa a Aljihu ya ciro dubu daya ya mik'a ma Yaran
"kai kuma ga naka"
Washe baki Almajirin yayi tareda godiya, ledan ya shiga dashi cikin zauren ya bah Sulthana, zaro ido tai tana k'allan almajirin
"Dan Allah ka maidan mai kada Baffa ya gani kace nace banaso"
Niki niki yaron yadau leda ya koma dashi, yana fita yaga wayam bah motan Dr Fareed. Dawowa yayi ya shaida mata ya aje ledan ya fita, jikinta neh ya soma rawa yanzu idan Baffa yaga ledan nan tasan duka zataci. Sadiya ce ta fado mata a rai ta dau ledan dakyar ta nufi gidansu sadiya cikeda Fargaba..

Da sallama ta shiga Allah ya taimaketa Baban Sadiya baya nan, saida ta gaida Maman Sadiya sannan ta zaiyana mata duk abinda ke Faruwa, ga mamakinta sai gani tai Maman Sadiya ta washe Baki.
"A'a Sulthana wannan ai abin farinciki neh"
Hannu ta daga ta godema Allah sannan ta k'alli Sulthanan data sake baki tana k'allan Mama
"Ina tayaki murna Sultana, insha Allahu komai ya kusa zuwa karshe. Ni nasan wannan likitan sanki yake"
Gwalalo ido Sultana tai idanunta suk'a ciko da kwalla, Mama ta cigaba da cewa
"Kinga idan kikai aure komai zai zamo tarihi, zaki fita daga cikin wannan wahalan da kike ciki"
Rufe fuska Sulthana tai tana murmushi. Rungumeta Sadiya tai tana cewa
"Iyeh! Amarya"
Dukan wasa Sulthana takai ma Sadiya, kyalkyalewa da dariya Sadiya tai cikeda farinciki.

Mik'ama Mama ledan tai tareda mik'ewa
"Mama idan Baffa yaga wannan kayan dukana zeyi"
Amsan kayan Mama tayi ta hau dubawa, Hadaddun kayane kala kala. Dogayen riguna, Atamfofi da lesuka ready maid. Sai takalma da turaruka. Sakin baki sadiya tai
"Tab ni ban taba ganin irin wannan kayan bah"
Tabe baki Sulthana tai
"Mama kiyi anfani dasu keda Sadiya"
Dago kai Mama tai tana k'allanta, girgiza mata kai tai
"A'a bazamuyi anfani dashi bah Sulthana, na miki alkawarin zan aje miki su har lokacin da kika bukata"
Girgiza kai Sulthana tai tana cewa
"A'a kiyi anfani dasu"
Tsofafin Silifas dinta wari daban daban tasa tace
"Mama na tafi kada Baffa ya fito bai ganni bah"
Sallama Mama tai mata Suka fito tareda Sadiya, kara kyalkyalewa da dariya Sadiya tai
"Amarya knan"
Duka Sulthana ta d'aka mata tana hararanta
"Banaso fah"
Murmushi Sadiya ta rik'e haba tace
"Niko inasan naga wannan saurayin d'an birni"
Turo baki Sulthana tayi tana yatsine Fuska
"Nidai bana sansa"
Sakin baki Sadiya tai batace komai bah, a haka sukai sallama Sulthana ta nufo gida dasauri...

A kofar gidansu taga Ahmad saurayin Hafsatu, K'allanshi tayi da nufin gaidashi ganin ya balla mata harara yasa sum sum ta shiga Gida, kan buhunta ta zauna tai shiru. Haskota akai da torchlight ta mik'e dasauri muryan Hafsatu taji tana cewa
"Gatanan ta dawo"
Gabanta ne ya fadi Dam! Shiknan yau tasan nata ya K'are..

Baffa ne ya kwalla mata kira ta amsa ta shiga cikin gidan jikinta na rawa, Cirko cirko ta samesu a tsakar gidan, Ameenatu sai Balla mata harara take. Tsugunawa tai Sannan tace gani.
Baffa rai bace yace
"Waye Saurayin nan da hafsatu taganku dashi Ranan"
Gaban Sulthana ne ya fadi
Daka mata tsawa Baffa yayi
"Badake nake magana bah"
Muryanta na rawa tace
"Baffa wallahi ban sanshi bah, ranan kudin gyada na zai bani"
Mari Baffa ya dauketa dashi yana huci
"Bazaki fadamin Gaskiya bah"
Kuka Sulthana ta fashe dashi ta soma Rantse rantse
"Wallahi Baffa bansanshi bah"
Ameenatu ce ta amshe da cewa
"Karya kikeyi, wato Sulthana kin Fara kula kulan maza koh? Ai dama tunda naga wannan likitan nasan dan iska neh"
Sai a sannan Sulthana ta gane inda maganansu ta dosa
Daki Baffa ya shiga ya dauko Bulala, Sulthana na ganin haka ta kwala ihu tana kuka sosai

"Dan Allah Baffa kai hakuri Wallahi bansanshi bah"
Hafsatu tace
"Rannan Ahmad yake gayamin ya ganshi, kyaleta nai kawai ban fadaba sai yau kuma ni da idona naganshi Yazo yaba wani yaro katon leda ya kawo mata, shiyasa dana tambayi Mama sulthana ta kawo mata leda tace wani leda"
Tsula mata bulala Baffa yayi ta saki ihu ta fashe da kuka. Tana kururuwa
"Dan Allah Baffa kai hakuri bazan Sake bah"
K'asa magana Mama tai ta koma daki abinda cikeda bakin ciki
Saida Baffa yaga bata numfashi Sannan ya kyalleta Sukai shigewansu daki suka barta nan warwas a tsakar gidan...

Mamace ta fito jin sun shige daki, kuka ta fashe dashi mara sauti ganin Sulthana kwance. Daki ta koma ta debo ruwa ta yayafa mata, ajiyan zuciya tai ta K'ara fashewa da kuka tana ihu
"Baffa kai hakuri, Wayyo baffa zai kasheni. Yaya Ameenatu ki taimakeni"
Saurin rufe mata baki Mama tai itama tana kukan, Dakinta ta kaita ta dawo ta hada wuta ta daura mata ruwan wanka, ruwan na zafi ta surka ta kai mata ban daki. Da taimakon Mama tai wanka, nan da nan Zazzabi ya rufeta, magani Mama ta bata tasha Barci mai nauyi ya dauketa. Sai gaf da Asubah Mama ta tasheta ta koma zaure gudun kar Baffa yazo fita massalaci bai ganta bah...

A Bangaren Masroor kuwa koda ya koma gida kasa sukuni yayi, Falon k'asa ya zauna yayi shiru, Mami ce ta sauke zuwa falon ganin Masroor zaune ya k'urama tv ido anma daga gani hankalinshi ba'a tv take bah. Zama tai kusa dashi tadan Tabashi, Razana yayi ya juya ganin Mami yasa ya saki ajiyan zuciya.
"Lapia Meke damunka son" cewar Mami
D'an Murmushi yayi yana girgiza kai
"Nothing Mom"
Kauda kai Mami tai gefe fuskanta bah Walwala
"Masroor bakada kamana, ni yakamata ka fadama damuwanka."
Sumar kanshi daketa kyalli ya shafa yana y'ar Murmushi
"Mami bah komai karki damu"
Bell aka danna, Cikin Maid din gidan ta shigo dasauri ta bude kofan, Mahnoor ce ta shigo dagudu ta wurgama Maid din jakan Makarantan tah tana Murmushi
"Mamina I'm back"
Ganin Mami yasa ta nufeta dagudu ta rungumeta tana dariya
"I Missed you Mami"
Masroor ta k'alla taga sai hararanta yake..

chuno baki tayi
"Mami wai meyasa ya Masroor sai ya rinka eyeing dina"
Sumar kanshi ya shafa
"Mami K'arya take"
Hararanshi Mami tayi
"Banasan Haka fah, ka daina hararan min Y'a"
Baice komai bah yabar Falon..

Ummy Abduol✍🏻
[28/08, 01:12] Friend Hussaini: 💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐

By *Ummy Abduol*

*Page 106 to 110*

*Masoya Littafin Sulthana naga sakonin ku da dama wasu ban samu na karanta bah. Abinda nikeso ku gane a nan shine* _labarin Sulthana ya faru ne dagaske_ *So duk abinda kuka gani a ciki bah k'irkira nai bah abu ne daya faru dagske. Sannan Fans din Masroor da na Dr Fareed kowacce tasa ido taga Yadda labarin zai k'arke, yanda yazo a labari hakan zan baku a rubuce insha Allah. Ina fatan zaku fahimceni*..

Wannan Shafin Naku neh *Sulthana Fans* Allah yabar k'auna

Hararanshi Mami tayi
"Banasan haka fah, ka daina hararan min y'a"
Baice komai bah yabar falon. Bell aka k'ara dannawa Maid ta fito dasauri ta bude kofan, Yasir neh ya shigo da sallama ya karasa inda Mami ke zaune ya tsuguna har K'asa ya daidata. Da fara'a a fuskanta ta amsa tareda tambayanshi mutan gidan, ya amsa mata da lapia lau. Mutum nashi ya tambaya Mahnoor ta fadamai yana daki, mik'ewa yayi ya hau sama ya nufi side din Masroor..

Kwance ya sameshi kan Three seater cikin hadadden Falon shi yana k'allan celien, Zama yayi k'an 1seater kusa dashi tareda dafashi
"Friend its anything wrong"
K'akaro murmushi Masroor yayi yana k'allanshi
"No I'm fine"
Ajiyan zuciya Yasir ya sauke harya bude baki zaiyi magana aka danna bell din Falon, mik'ewa yayi ya bude kofan, cikin ma'aikatan gidan neh dauk'e da tray cikeda kayan ciye ciye, kan center table din falon ta aje ta fita tareda jawo kofan. Komawa Yasir yayi ya zuna yana facing Masroor da yanayinshi ya chanza..

"Friend tel me something, meke damunka coz bah haka kake bah"
Mik'ewa zaune Masroor yayi yana k'allan Yasir. Bai boyema Yasir komai game dashi kamar yanda shima Yasir din bai boyemai komai. Sumar kanshi ya shafa ya fara magana cikin sanyayar muryanshi
"Kah tuna yarinyan nan da naso bigewa ranan da mukaje kauyen nan"
Kai Yasir ya daga alamar eh, cigaba da magana Masroor yay
"I donno why I always think of her, kullum cikin tunaninta nake. Ina tausaya mata coz alamu sun nuna she need help"
Murmushi Yasir yayi mai sauti har saida Masroor ya kalleshi da mamaki
"Just tel me san yarinyan nan kake"
Saurin girgiza kai Masroor yayi yana cewa
"No friend bah santa nake bah, kawai tausayinta nake. Yarinyan taki tsayawa muyi magana just becoz of dat useless sistern nata"
Jinjina kai Yasir yay
"Nima na lura da haka anma tunda bataso y not kawai ka kyaleta"
Shiru Masroor yayi baice komai bah..

Ganin yanda Masroor din ya damu yasa Yasir ya dafashi
"Look friend uh are in love kawai kaidai bakaso ka fadane"
Mik'ewa tsaye Masroor yayi dasauri yana girgiza kai
"No Yasir kawai tausayi neh. Kamasan wani abu?"
Kai Yasir ya gigiza,
"Kasan guy din nan da yake tareda sistern tah a nan gidan yake aiki"
Yasir ya mik'e dasauri
"Kai haba"
Gyada kai Masroor yayi sannan yace
"I'm serious"
Shiru sukai nasamu mintina chan Yasir ya dago ya k'alli abokin nashi
"Ga shawara"
Dasauri Masroor ya zauna yana cewa
"Am all ears"

"Why not mu samu guy din mu biyashi ya fada mana labarin yarinyan, Coz am sure yasan komai tunda yana tareda sistern tah. Daga nan kaga sai mu nemi solution"
Shiru Masroor yayi yana cigaba da shafa sumar kanshi tareda furzar da iska
"No Friend bana tunanin haka zai yuwu, besides banasan yasan wani abu gameda wannan"
"Buh we dn't have any choice" cewar Yasir
Dago kai Masroor yayi da murmushi dauke a fuskanshi
"Yes! Nasan meh zanyi"
K'allanshi Yasir ya tsaya yi
"Meh knan"
Tasowa Masroor yayi ya dawo kusada Yasir ya zauna
"Zan Hadata da Parrot neh"
Dariya Yasir ya fashe dashi
"Do uh think it wil work"
Gyada kai Masroor yayi yana murmushin jin dadi...

Dukda irin dukan da Sulthana tasha a haka Baffa ya bata gyada ta dafa, da taimakon Mama ta dafa ta juye. Mama da kanta ta daura mata akai tai mata Fatan Alheri ta fito.. Yanke Shawaran ta tafi bakin kasuwa tai, tafiya take ahankali jikinta duk Ciwo yake mata, dakyar ta k'arasa bakin kasuwa ta samu guri inda tasaba zama ta zauna. Tagumi tai ta lula cikin tunanin Mahaifiyarta nan da nan hawaye ya soma gangaro mata, Muryan yarinya taji a kanta ta dago dasauri. Murmushi ta mata tareda
Mik'a mata Dari biyar
"Gashi ki bani gyada"
K'allam yarinyan Sulthana ta tsaya yi, kyakyawa da ita Sanye take cikin bakin dogon Riga mai kyau. Yarinyan bah K'aramin burge Sulthana tai bah, k'asa dauke idonta tai daga k'allan Yarinyan. Har saida Tace
"Bakya jina neh"
Zabura Sulthana tai ta maida dubanta ga kudin tana cewa
"Na nawa zaki siya? Banida chanji"


Saurin Girgiza kai tayi tana cewa
"Ai na duka zaki bani"
Jiki na rawa Sulthana ta soma nema ledan dan dama gyadan bazai wuce na haka nah"
Juyawa Mahnoor tai ta k'alli Masroor dake cikin mota nesa dasu, kai ya gyada mata. Ta juyo ta tsugunna tana taya Sulthana zuba gyadan a Leda
"Menene Sunanki" cewar Mahnoor
Dagowa Sulthana tai tana k'allan Mahnoor da manyan idanunta, Yarinyan ta burgeta sosai. Dan murmushi tai tace
"Sunana Sulthana"
Dariya Mahnoor tayi tareda maimaita sunan
"Woaw nice name, ni kuma sunana Mahnoor"
Kurri Sulthana ta mata itama ta maimaita sunan. Dai dai nan ta juye gyadan a Leda ta mik'ama Mahnoor.
Mik'a mata kudin tai tasa hannu biyu ta k'arba. Mahnoor tace
"Inaso ki zama k'awata"


Dan Dariya Sulthana tai dimple dinta suka lotsa
"Nima haka" cewar Sulthana
Mik'ewa tai tana cewa Shiknan zan tafi gida tunda na siyar. Mahnoor ta turo baki
"Bafa mu gama hira bah zaki tafi"
D'an zaro ido tai
"Kinga yau na saida gyadata dasauri barin tafi gida nasan Baffa idan yaga na dawo da wuri bazai dakeni bah"
D'an Shiru Mahnoor tai sanna tace
"Tho gobe zaki zo?"
Kai Sulthana ta gyada
"Ehmana, Anma inane gidanku"
Shiru Mahnoor tai ta rasa abin cewa har saida Sulthana tace
"A Birni kike ko"
Gyada kai Kawai Mahnoor tai tana y'ar murmushi. Sallama suk'ai Sulthana ta nufi gida dasauri itama Mahnoor ta shiga mota tareda fadama Masroor duk y'anda sukai. Murmushin jindadi yayi
"Dats my Lil Sis am proud of uh"
Itama Murmushin tai suka bar Cikin Kauyen.
Yinin ranar Sulthana tayishi neh cikeda tunanin k'awarta y'ar birni. Tayi murna sosai da haduwa da Mahnoor. K'ullum sai Masroor ya kawo Mahnoor wajan Sulthana idan ta taso School, shaquwa sosai ya shiga tsakaninsu duk da Har yanzu bah abinda Sulthana ta fadama Mahnoor dangane da halinda take Ciki...

*Anya kuwa Wannan Shawaran na Masroor mai bullewa ce*
Mudaije zuwa..

Ummy Abduol✍🏻
[28/08, 01:12] Friend Hussaini: 💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐

By *Ummy Abduol*

*Page 111 to 115*

Shaquwa sosai ya shiga tsakaninsu duk da har yanzu bah abinda Sulthana a fadama Mahnoor dangane da halinda take ciki...
Yauma kamar kullum tana dawowa daga makaranta taci lunch tai Sallah, side din Masroor ta nufa knocking tai a bakin kofan falonshi taji shiru, ta dad'e tana knocking jin shirun yayi yawa ta juyo ta koma side dinsu. Tana k'okarin Saukowa k'asa taci karo da Mami ta fito dak'i, tsaya tai tana k'allanta da Mamaki
"Wai Mahnoor na tambayeki"
Gyada kai kawai Mahnoor tai, Mami ta cigaba da cewa
"Kullum da kuke fita din nan keda Masroor ina kuke zuwa?"
Turo baki tai dan Masroor ya jamata kunne K'ar ta sake ta fadama kowa. Mami tace
"Badake nake magana bah"
Harta bude baki zatai magana sukajiyo Muryan Masroor ta bayansu yana cewa
"No mami bafa wani guri muke zuwa bah, just ina wanke lefuka na neh danai kinsan fushi take dani wai tunda na dawo bama zuwa yawo"

Gizgiza kai kawai Mami tai dan Tasan k'arya ya fada
Mahnoor ta K'alla tana cewa
"Zo ki daukomin wannan abin" ta juya ta shiga dakinta, matsowa Masroor yayi ya sassauta murya yace
"No matter now karki fada mata"
Gyada kai Mahnoor tayi ta shiga dakin Mami da sallama shikuma ya dauko k'asa..

Zaune ta samu Mami bakin Katafaren Gadonta, kusada ita mami ta nuna mata
"Zo ki zauna nan"
Bah musu taje ta zauna, Mami ta fara magana cikin sigan Lallashi
"Mahnoor ina kuke zuwa"
Chuno baki tai
"Nifah Mami bafa wani guri muke zuwa bah yawo kawai yake kaini"
Jinjina kai Mami tai
"Mahnoor bakya min k'arya meyasa yanzu kika fara, tunda bazaki fadaba Shiknan"
Ajiyan zuciya tai sannan ta cigaba
"Uh should be very careful kina jina?"
Kai ta gyada ma Mami ta mik'e tana Kakkabe skirt dinta
"Mami bye sai mun dawo"
D'an murmushin yak'e Mamin tai
"Ai bari Daddynku ya dawo zance ne Islamic Lesson teachern ki ya daina zuwa bayan isha'i ya koma zuwa bayan Asr. Sai muga yanda za'ai a rinka fitan"..

Bubbuga k'afa Ta fara ta fita daga dakin tana gungunai, a cikin Hadad'iyar doddge dinshi ta hangoshi zaune, k'arasawa tai ta shiga ya tada suka bar gidan..

Yau Masroor yaci Alwashin koma mai zai faru saidai a faru anma dole sai Sulthana ta sanar dashi halin datake ciki. suna cikin tafiya a mota Mahnoor tace
"Bro Masroor ka tsaya nasai ma friend chocolate da ice cream"
D'an murmushi yayi
"Kinada kudi neh"
Turo baki tai
"Tho bah kai kanada shi bah"
Baice komai bah ya juya k'an motan, tare suka shiga ta zabar ma Sulthana k'ayan ciye ciye k'ala kala suka fito suka nufi kauyen..

Yau abin mamaki bah Sulthana bah alamar tah, dasauri Mahnoor ta k'alli Masroor idonta cikeda k'walla
"Bro Friend bata nan"
Shiru Masroor yayi yana k'allan wajan cikeda damuwa. Kamar ance ya dago ya hangota tafe da trayn gyada akai tana matsar kwalla, dasauri ya bude motan ya fita Mahnoor tabi bayanshi..

Zama Sulthanan tai inda ta saba zama tana cigaba da matsar k'walla, mahnoor ce ta k'araso wajan ta zauna tana cewa
"Friend meyasa kike kuka"
Jin muryan k'awarta y'ar birni yasa ta dago dasauri tasa hannu tana share kwallan daya gangaro mata. Murmushi tama Mahnoor
"Bah komai k'awa"
D'an turo baki Mahnoor tai
"Nifah Friend dinki neh, kifadamin waye yake dukanki"
Murmushi Sulthana ta k'arayi
"K'awa bah kowa"

Muryan Masroor sukaji a bayansu yana cewa
"Lokaci yayi daya kamata ki fada mana abinda ke damunki, ki daina boyewa dan cutar dake zeyi"
Daga k'ai tai suka hada ido ta mik'e dasauri tana k'allanshi tareda nunashi da yatsa
"Kah daina zuwa inda nake, idan Baffa ko yaya Hafsatu taganmu dukana xasuyi"
Baiji wani d'ar bah ya kama hannunta tana turjewa mutane sai k'allansu suke bayan mota ya sakata ya rufe, Mahnoor ta dauko trayn gyadanta ta saka a booth, sannan ta shiga Masroor ya bar Kauyen a guje..

Ihu kawai Sulthana take
"Sun Saceni, Jama'a ku taimakeni"
Bah wanda yayi yunk'urin taimakonta saima bin motar da ake da K'allo
Gudu yake sosai k'amar zai tashi sama, bai tsaya ko ina bah sai Gidansu Yasir, horn yayi mai gadi ya bude ya shiga yayi parking. Itako Sulthana tunda aka bar Kauyensu tai shiru ta fara rarraba idanu dan tunda take bata taba barin kauyensu bah sai yau, bin titi take da k'allo tana shafa Glass din motan tana murmushi..

Wayanshi ya dauka ya soma neman Layin yasir, yana cikin kira ya fito daga side dinshi yana murmushi.
"Yau suprise akai min"
Karasowa yayi bakin motan, Ganin Sulthana a baya tanata Zare ido yasa yayi turus yana k'allan Masroor daya hade girar sama data k'asa. Sulthana ta dafa Mahnoor cikeda damuwa
"K'awa ina kuka kawoni? Dan Allah karku ciremin kaina ban muku komai bah"
Kyalkyalewa da dariya Mahnoor tai tana cewa
"Mu ai bama cire kai"
Bude Murfin motan Masroor yayi ya fita tareda jan Hannun Yasir, side dinshi suka nufa a falo suka zauna, Yasir ya kada baki yace

"Masroor what do uh think uh are doing?, ka dauko yarinya hakanan kawai. Ko kasanar da Iyayenta neh"
Mikewa Tsaye Masroor yayi cikin daga murya yace
"I Cn't hold it any more Yasir, inaso na taimaka ma yarinyan nan. I donno why I always think of her, kullum sai tazomin a mafarki"
D'an Murmushi Yasir yayi ya mik'e ya dafashi
"Look at me Friend"
Dagowa Masroor yayi ya kalli Yasir, Murmushi yasir yamai
"Uh are in love Masroor, santa kakeyi. Beleive me"
Girgiza kai Masroor yayi idanunshi sun k'ada sunyi ja. Suman kanshi yaja tareda furzar da iska
"No Friend, forget abt dis lets find solution"
Kamashi Yasir yayi ya zaunar dashi yana cewa
"Abinda kayi bah daidai baneh Friend, bai kamata ka daukota bah. A hankali zakabi komai har kasamu abinda kakeso."

Masroor baice komai bah saima mik'ewa dayayi yabar falon, mota ya koma yaga Mahnoor a baya kusada Sulthana daketa kuka kamar ranta zai fita. Bude kofan yayi ya janyo hannunta. Ihu ta saki tana turjewa, daka mata tsawa yayi tai gum da bakinta, bai saketa bah saida ya shiga Falon Yasir Mahnoor na biye dasu...

Yasir na ganinsu ya mik'e tsaye
"Masroor whats all dis? Pls ka maida yarinyan mutane. Kada Mum ta dawo ta samemu a nan pls"
Baice komai bah ya zaunar da Sulthana k'an kujera shima ya zauna ana kusa da ita. Murya a sanyaye yace
"Sulthana!"
Dago jajayen idanunta tai jikinta na rawa tace
"Na'am"
Suman kanshi ya shafa Yace
"Ki fadamin meke faruwa dake karki boyemin komai"
Shiru tai nadan mintina, ganin dagaske masroor yake yasa yasir yaja hannun Mahnoor suka bar falon..

Saukowa Masroor yayi daga kan kujeran dayake ya tsugunna a gabanta, hannunshi yasa ya dago fuskanta
"Kiyi

Please Login or Register in order to submit comment