Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

girme ma Masroor anma ace haka na faruwa tsakaninku"

Daddy yace

"Ai bashi k'adai bah harda Masroor din, shima kana ganinshi bashida hakuri."

Abba ya nisa yace

"Sam baku kyauta mana bah. Banji dadi bah kun bamu kunya"

Daddy ya nunasu da yatsa

"Sannan ku sani yarinya bazata taba aurenku bah duka tuna abin haka neh"

Mami tai Saurin cewa

"Ur excellency inaga hakan kamar tauyewa neh. Yakamata ita yarinya ta fadi wanda takeso sai a bata, wanda kuma bataso saiya hakura"

Gyada kai Abba yayi

"Wannan Gaskiya neh"

Daddy yace

"Abinda za'ayi gobe in Allah ya kaimu da Sassafe dukanmu zamu dunguma muje kauyensu dan mu samu asalinta. D'an duk wannan abin da mukeyi kamar munyi tuyane mun manta da Albasa"

Umma tace

"Gaskiya neh"

Abba yace

"Hakan ma yayi, daga chan sai ayita ta k'are ta fadi wanda takeso mu nema masa aurenta kawai"

Kowa dake falon ya amince Abba yace su Fareed su tashi su tafi, duk suka mik'e suka bar falon kowa jiki a sanyaye..

A daren Mami ta samu Sulthana a dakinta kwance tana aikin kuka, karasawa tayi ta zauna kan gadon ta dagota tareda share mata hawaye.

"Wannan kukan duk na menene? Ya isa haka kinji"

Kai ta gyada kawai kanta a kasa dan yanzu kunyan yan gidan takeji. Mami tace

"Gobe dasassafe ki shirya zamuje kauyenku dan.."

Kuka Sulthana ta fashe dashi ta rik'e hannun Mami gam

"Dan Allah Mami karku maidani wajan Baffa kasheni zeyi"

Rufe mata Baki Mami tayi cikeda tausayawa

"Bah barinki zamuyi bah, zamuje neh dan yasan kina wajanmu"

Dakyar Mami ta shawo kanta ta amince, saida taga Barci ya dauketa Sannan tabar dakin..

Ranar Fareed da Masroor babu wanda ya runtsa kowa da abinda yake s'akawa a ranshi. Ganin bacin ya gagara yasa Masroor mik'ewa yayo Alwala ya soma kai kukanshi gurin Ubangiji..

Kamar yanda akayi da Sassafe Abban Fareed da Umma sai shi Fareed din suka iso gidan, Already su daddy sun shirya. Wasu motoci daban suka d'auka bana gwamnati bah suka dau hanyar kauyensu Sulthana..

Fareed ne yakema Drivern kwatance har suka kawo kofar gidan. Gaban Sulthana ne ya fadi sanda ta kalli gidan, duka suka fifito daga mota anma banda Sulthana, Mahnoor ta bud'e kofan

"Sulthana fito mana"

Dakyar ta sauko kafa ta fito tana bin kofar gidan da Kallo, bah abinda ya chanza har yanzu komai na nan yanda yake, saidai ta lura kamar yanzu bah almajirai a runfar su. Yaro su Abba suka samu yamusu Sallama da Baffa.

Ba'adau lokaciba ya fito daga gidan, Kallo d'aya zakaima Baffa kaga ramar da yayi. Duk ya fige kamar bashi bah, ganin Manyan Mutane Yasa jiki na rawa ya shiga cikin gida yasa aka shishimfida tabarma sannan ya fito yace

"Bismillah ku shigo"

Sam bai lura da Sulthana dake jikin Mami a makale bah. Tsakar gidan suka shiga Suka zazzauna, Ameenatu ta fito daga dakin Mama dauke da kwanun sha ta aje Sannan ta gaidasu, harta mik'e suka hada ido da Sulthana. Mik'ewa tayi dasauri tana nuna Sulthana bakinta na rawa

"Su..Sul...Sulthana"

Baffa ya mik'e yana kallan inda Ameenatu ke nunawa, jin kamar an kira sunan Sulthana yasa Mama fitowa daga dakinta hakama Hafsatu

K'ara shigewa jikin Mami tayi tana boye Fuska, Baffa ya soma Hawaye yana cewa

"Sulthana ki gafarceni, nasan nayi kuskure. Sharrin shedan neh da kuma rashin sani"

Jin abubuwan da Baffa yake cewa yasa ta d'ago tana kallanshi da Mamaki. Mama ta k'araso wajan itama tana hawaye

"Sulthana dama kina raye, bah inda bamuje nemanki bah. Baffanki kullum ke yake anbata"

Sai kallansu Sulthana take da Mamaki, Abban Fareed neh yace

"Mallan zauna muyi magana"

Bah musu Baffa ya zauna yana matsar kwalla. Tunkan Abba ya sake Magana Baffa ya soma zaiyane musu duk abinda ya faru yana hawaye. Kuka Sulthana take na farinciki da Allah yasa ita bah shegiya bace. Bayan ya gama Abban Fareed shima ya dora da basu labarin zaman datai tareda fareed da kuma wanda tayi a gidansu Mami..

Zabura Baffa yayi ya gyara zama yana rarraba ido

"Dama da Gwamna da Mataimakinshi nake zaune"

Ya juya ya Kalli Mama dasu Ameenatu tana mai cikeda Farinciki. Hafsatu da yanzu ta zama salaha tace

"Sulthana ki yafemin lefukan dana miki, nasan nayi kuskure"

Yau Sulthana na Cike da Farinciki yau ga yan uwanta na santa suna neman gafaranta.. batareda wani dogon tunani bah tace

"Baffa, Mama, yaya Ameenatu, yaya Hafsatu duk na yafemuku tuntuni, dama ban rikeku bah. Ina sanku sosai"

Mik'ewa tayi ta rungume Baffa, ya fashe da kuka yana cewa

"Allah ya jikan Mahaifiyarki Allah ya gafarta mata. Ke kuma Allah ya miki Albarka"

Ameen tace Sannan ta janye jikinta ta rungume Mama da sauran Y'an uwanta..

Su Daddy yan kallo suka koma kowa yana tayata Murnar sassantawa da Mahaifinta da y'an uwanta

Mama ta mik'e ta soma kici kicin d'aura girki na musamman Dan tarban manyan Bakinsu...

Saida aka natsa, Sulthana tana d'akinsu Yaya Ameenatu itada Mahnoor sunata basu labarin Birni sukuma su Daddy suna kam tabarma cikin ihuwa sunata hira da Baffa kamar sun saba. Su Masroor kuwa suna chan gefe zaune sunyi jugum jugum kowa da abinda yake sakawa a ranshi...

Ummy Abduol✍🏻

💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐

By *Ummy Abduol*


DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION

*Page 198*

Su Masroor kuwa suna chan gefe zaune sunyi jugum jugum kowa da abinda yake sakawa a ranshi sannan Abba ya gyara zama yaba Baffa labarin Soyaiyar dake tsakanin Sulthana da y'ayansu sanna ya d'aura da cewa

"Dole yanzu zamu kirata neh ta zaba wanda takeso a cikinsu"

Baffa ya b'ata rai

"Haba ranka ya dad'e ai duk wannan bai taso bah, kuma fah iyayenta neh ku da kanku kawai ku zaba mata wanda zata aura"

Daddy yayi murmushi yana k'allan Baffa

"Aa baza'ayi haka bah, idan mukai haka kamar mun tauyeta neh. Tho idan kuma muka zaba mata wanda ita bai kwanta mata bafa?"

Shiru Baffa yayi baice komai bah. Abba yad'au waya ya kira Umma yace su fito duka, duk suka fito daga dakin Mama itada Mami suka zauna k'an tabarman. Baffa Yacema Mama ta kira Sulthana tace tho

Dakin ta shiga ta kirata suka taho tare, koda sukazo sun samu Fareed da Masroor xaune a wajan. Kusada Mami ta zauna k'anta a kasa, Abba ya kalleta da fara'a

"Y'ata mun kiraki neh dan muji ra'ayinki. Munaso ki fada mana tsakanin Masroor da Fareed wa kikeso"

Gabanta neh ya fadi ta d'ago ta kalli Masroor taga kanshi a kasa ta maida dubanta ga Fareed shima kanshi a kasa. Kasa magana tayi gabanta na cigaba da bugawa. Mami ta tabota

"Sulthana kiyi Magana mana karkiji Tsoro ki Fada abinda ke ranki"

Shiru tayi nad'an mintina Sannan tad'an dago bakinta na rawa tace

"Ya Fa..."

Dasauri Fareed ya d'ago ya kalleta da Alamar Mamaki, Masroor ko runtse idonshi yayi zuciyarshi na bugawa da sauri. Umman Fareed tace

"Kiyi Magana mana Sulthana keh muke jira"

Ta maza tayi ta saukar dakanta kasa tace

"Yah Masroor"

Sauke kai Fareed yayi yana girgixa kai ahankali, dasauri ta tashi tabar wajan. Abba yace

"Tho Alhamdulillah tunda yarinya ta fadi wanda takeso yanzu sai ayi maganan sadaki koh"

Su Umma najin haka suka mik'e suka bar wajan, Su Fareed suma suka mik'e suka fita waje. Fareed ya share hawayen idonshi yace

"I'm very sorry friend"

Ya mik'ama Masroor hannu yace

"Congratulations am very happy for you, Allah ya sanya Alheri"

Jikin Masroor neh yayi sanyi shima ya mik'amai hannu

"Ni yakamata nabaka hakuri, bakai bah"

Fareed ya girgixa kai ya shiga mota ya zauna ya daura kanshi jikin stering motan ranshi jagule..

Sulthana na shiga d'akinsu ta fada kan gado ta fashe da kuka, Ameenatu ce ta dafata tana cewa

"Meke faruwa Sulthana?"

Mik'ewa zaune tayi hawaye chabe chabe a idonta, tace

"Bansan da wani ido ya Fareed zai kalleni bah. Gani nake kamar namai Butulci"

Hafsatu ta dafata tana Murmushi

"Mahnoor ta mana bayanin komai, kuma bakida laifi saboda bai sanar dake bah Sannan kuma na lura bah wai sanki yake bah tausayinki neh"

Sulthana ta k'ura mata ido da Mamaki, gyada mata kai Hafsatu tayi sannan ta juya ta Kalli Ameenatu wacce itama su take kallo ta juya ta maida dubanta ga Sulthana tace

"Ya Ameenatu ta dad'e tanasan Likitan nan, tun sanda ta soma ganinshi ta fara sanshi, kullum sai tayi min maganar shi."

Mik'ewa Ameenatu tayi rai b'ace

"Baki kyautamin bah Hafsatu Ashe bazaki iya rik'emin d'an sirrin nan dana baki bah"

Murmushi Sulthana tayi ta share hawayen Fuskanta ta mik'e ta fito tsakar gidan, ganin su Fareed basa wajan yasa tasa takalmanta ta fita kofar gida. Zaune ta sameshi cikin mota shida Masroor suna hira jefi jefi, nesa dasu ta tsaya Masroor na ganinta ya fito ya karaso inda take yana murmushi

"Har na cire rai Beauty, sai gashi nine gwaninki"

Hannu yasa ta rufe fuskanta tana dariya

"Dan Allah ya Masroor inaso nayi magana da Ya Fareed"

Murmushi ya mata

"Bbu komai ki sameshi a mota"

Dariyan jindadi tayi

"Thank uh Bro Masroor"

Da Sassarfa ta k'arasa bakin motan ta bud'e ta shiga tana Kallanshi

"Ya Fareed kayi hakuri dan Allah"

Sai a Sannan ya d'ago ya kalleta tareda k'irkiro Murmushi

"Bakimin komai bah Queen, Laifina neh da ban fadamiki tun tuni bah naiyi zurfin ciki, haka Allah yaso. Allah ya nufa ke bah Matata bace"

D'an dukar dakai tayi tana wasa da zoben dake hannunta tace

"Nagode ya Fareed, bazan t'aba mantawa dakaiba a rayuwata. Kayimin Abubuwa da dama wanda banida bakin godiya, ka taka muhimmiyar rawa a rayuwata thank uh v...."

Saurin katseta yayi ya d'aura yatsanshi a lebenshi

"Uh dn't have to thank me"

Jim tayi nad'an wani lokaci sannan tace

"Ya Fareed akwai wani abu danakeso kayimin dan Allah"

Batareda wani bata lokaci bah yace

"Menene shi Queen?"

Tacigaba da cewa

"Inaso dan Allah Ya Fareed ka auri ya Ameenatu"

Dasauri ya juyo yana kallanta da mamaki, gyada mai kai tayi tana y'ar murmushi. Kasumbar dake fuskanshi ya shafa

"Ita tace miki tana sona?"

Girgiza kai tayi alamar Aa. Ya numfasa yace

"But queen I have no feelings for ha, and zai iya yuwuwa bata sona. Kawai ki barshi nagode"

Ta turo baki ta soma gungunai

"Nidai Dan Allah Ya Fareed ka aureta, shes kind kuma batada matsala. Nasan zata soka and kuma kagani zaku saba"

Dariya yayi Mara sauti yana k'allanta kasa kasa, baisan ya musa mata kuma a ganinshi wannan karamci tamai and kuma bah lefi yarinyan tanada kyau Sam bata kamo k'afar Queen dinshi bah dukda ita b'akace.

Ya juyo da Fara'a kwamce kan Fuskanshi yace

"Shiknan Queen na Yarda"

Ihu ta saki tana dariya har saida Masroor ya K'ara sako wajan dasauri. Fitowa daga motan tayi ta shiga cikin gida da gudu. Dakyar suka shawo kan Ya Ameenatu ta fita wajan Fareed, a waya Sulthana ta fadama Masroor abinda ke faruwa, Yaji dadi sosai shima. Ameeantu da Fareed sun fahimci juna kuma har ya Amince zai aureta, su Daddy sunyi Mamaki sosai jin Maganan. Basu bar Kauyensu Sulthana bah saida aka tsaida Ranar Bikin Masroor da Sulthana sai Fareed da Ameenatu wata d'aya, Aka ba Baffa sadakinsu Dubu D'ari d'ari dan Baffa yace baison Asa Sadakin dayawa..

Mama ta rok'i Alfarman a bar mata Sulthana har zuwa ayi bikin. Baffa ya tambayi Sulthana ta amince batai Gardama bah, Masroor sam baiso haka bah bah yanda zaiyi hakanan ya hakura sukai musu Sallama suka tafi bayan Sun Cika Baffa da kudi. washe gari Mami ta turo Driver da Kayan Sawan Sulthana da Kayan Abinci dana sawa nasu Mama cike da Mota...

Kula Sosai Sulthana take samu a gidan Mahaifinta ta bangaren Mama da Baffa har takan rasa wayafi kula da ita. Kullum suna Makalle da Masroor a waya haka soyaiya Suke mai Tsafta da Shiga rai. Fareed na Xuwa wajan Ameenatu hakan yasa suka k'ara shakuwa da ita, ya sai mata waya itada Hafsatu. Shima Masroor na xuwa shida Yasir..

Mama ta zage tanata gyara Y'ayan nata daidai karfinta, Mami ma Tana aiko Mahnoor da Wasu kayan gyaran jikin anaba Mama dan tayi Musu. Yau Saura kwana biyar Biki, Yau Sulthana take expecting Mahnoor dan tace mata zatazo har a gama biki. Tana gidansu Sadiya K'awarta Wayan Sulthana yahau Ruri, ta d'auka da Fara'a tana cewa

"Kin iso neh"

Harta mik'e ta koma ta zauna tace

"Yah Hafsatu tana Nan kice ta kawoki"

Bata jira mai zatace bah ta kashe kiran. Sadiya dake gefenta tace

"Ta iso neh?"

Da Fara'a tace

"Eh wai da lefe suka zo"

Dariya Sadiya tayi ta mik'e dasauri

"Ah bari muje muga Lefe"

Tab'e baki Sulthana tayi sadiya tad'au mayafinta ta fita daga gidan dasauri. Tana fita Mahnoor ta shigo gidan itada ya Ameenatu, sulthana ta mik'e dasauri ta rungumeta tana Dariya

"Uh welcome"

Dagota Mahnoor tayi daga jikinta tana k'are mata kallo

"Friend kinga yanda kika koma? Kin K'ara kyau sosai"

Turo baki Sulthana tayi tana doka kafa a kasa. Nan suka zauna suka soma hiran yanda bikin zai kasance basu bar gidan bah sai Yanma lis lokacin sun tabbatar yan kawo lefe sun tafi..

Ummy Abduol✍🏻

💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐

By *Ummy Abduol*


DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION

*Page 199*

Lefe na gani na Fada aka kawo kowaccen su akwati dozin biyu akai mata. Mutanen Kauyen sai shiga suke suna kallan kaya kowa na tofa Albarkacin bakinshi..

Ranar Alhamis Ameenatu da kawayenta Sukayi k'auye day, su kuma su Sulthana dukayi Fulani day itama itada nata k'awayen. Ranar Juma'a aka sasu Lalle da daddare. A Daren Masroor da Fareed sai d'an rakiyansu Yasir dukazo gidan, a tare amaren suka fito kowacce ta k'araso wajan angon nata. Masroor sai Kallan Sulthana yake da Murmushi

"Beauty kin k'ara kyau meye sirrin?"

Rufe fuskanta tayi da Hannayenda da sukasha had'adden kunshi. Ya rik'o hannunta yana kallo yace

"Waya miki wannan design din yayi kyau sosai"

D'an murmushi tayi ta turo baki

"Ya Masroor ka daina wannan maganan kanasa inajin kunya"

Dariya yayi yana shafa sumar kanshi

"Ki daina jin kunyana beauty, nidake yanzu mun zama d'aya karki manta gobe za'a daura mana aure ki zama tawa na xama taki"

Hannu tasa ta rufe fuskanta tana dariya K'asa kasa, daidai nan Yasir ya karaso wajan yace

"Ni kun barni chan gefe"

Ya kalli Sulthana

"Madam kinsan meye?"

Ta girgiza kai tana kallanshi, ya gyara tsayuwa ya sassauta Murya

"Nifah Sistern nan naki nakeso"

Tace "wah kenan?"

Yace "Hafasat"

Da zumud'i tace

"Dagaske?"

Kai ya gyada Mata, Masroor yayi saurin cewa

"Dallah kyalle wannan, mayaudari neh karki yarda
kadama ki fadamata"

Duka Yasir yakaimai

"Kai bansan fah iskanci i'm serious"

Sulthana tace

"Karka damu Ya Yasir zansan Yanda zanyi"

Godiya ya mata yabar wajan. Sun d'an taba hira sannan suka musu Sallama Suka tafi..

Washe Gari ya kasance ranar Sati, a ranar duban mutane suka shaida d'aurin auren Fareed da Ameenatu, sai Masroor da Sulthana. D'aurin auren daya samu hallartar Manyan Mutane tun daga kan shi kanshi shugaban k'asa, Gwamnoni, sarakuna da saurayan Manyan mutane masu fada aji a nigeria..

Har hawaye saida Baffa yayi dan bai taba tunanin zaiga irin wadannan Mutanen bah a rayuwarshi. Masroor baki yak'i rufuwa, Ana gama d'aurin aure yad'au wayanshi ya soma nemqn layin beauty. Ya dad'e yana ringing kamin a kawo mata ta d'auka tana y'ar Murnushi, cikeda Farinciki yace

"Beauty am now urs uh are mine. An d'aura"

Dariya tayi ta kashe kiran tad'au buta tayi alwala tazo ta tada nafila. Addua tayi sosai har tana hawaye musamman data tuna ana aurenta Ummanta bata raye, tayimata Addu'a sosai. Sannan ta tashi ta koma cikin k'awayenta..

Anyi d'aurin aure lapia kowa ya koma gudanshi. Wuraren k'arfe hudu na yanma aka d'au Amare dan kaisu Gidajensu, Ameenatu da Sulthana sai kuka suke bama Kamar Ameenatu, Nasiha mai ratsa jiki tayi Baffa da Mama sukai musu sai Maman Sadiya. Sannan aka d'aukesu zuwa government house..

Su kuma achan ake shagalin bikinsu Fareed da Masroor dan sun hada taron ne shi yasa gidan ya cika mak'il bah masaka tsinke. Yan kauye nan suka saki baki suna kallan Aljannar duniya, Wani had'aden Part dake gidan aka kai Sulthana, ita kuma Ameenatu sai daga baya za'a kaita. Mai make up aka kira ta d'andasa musu kwaliya sukasa had'aden golden gown dan zuwa dinner. Yau k'auye duk an basu anko sunsha sunata washe baki cikeda Murna. Kowacce Amarya tareda angonta suka tafi wajan dinnern, suma angon nan cikin Babban riga Fari tas dah aikin Golden. Sunyi kyau ainun gwanin ban sha'awa

A gurin dinner anci ansha anyi nak, su deejatou harda zuba abinci a leda lol. Bayan an gama an dawo sannan Aka kai Ameenatu gidanta. Washe Gari da safe akayi bud'an kai, shima wani buki akai na musamman Bayan an gama akasa yan kauye a mota aka maidasu bayan an cikasu da alheri sunata godiya. Aka bar Sulthana daga ita sai Mahnoor, Aisha batasamu zuwa bikin bah dan ta koma makaranta...

Mahnoor batabar Side dinbah saida sukai sallan isha. Wuraren k'arfe tara ango ya shigo sanye da fara k'ar din yadi sai zuba kamshi yake Hannunshi rike da leda, k'ara rufe fuskanta tayi cikin gyale tana wasa da zoben zinarin dake hannunta. Kan gadon ya zauna gefenta a hankali yasa hannu ya yaye gyalen ya d'ago fuskanta, runtse ido tayi tana murmushi shima murmushin yayi yace

"Open ur eyes beauty, Masroor dinki neh."

Tad'an bude ido kadan tareda janye fuskanta ta dan kauda kai. Hulan dake kanshi ya aje gefen bedside ya mik'e tsaye tareda riko Hannunta

"Tashi muyi Alwala muyi nafila dan mugodema Allah"

Bah musu ta mik'e shi ya fara shiga yayi alwalan ya fito Sannan itama ta shiga. Ko kamin ta fito ya shinfida musu Sallaya, tana fitowa ta yafa gyalenta suka tada sallah.

Bayan sun idar ya d'auko ledan daya ajiye yace

"Dauko mana plate Beauty"

Bah musu ta mik'e ta aje gyalanta akan gado ta fito daga dakin, shige shige ta soma yi dakyar ta gano kicin din. Tsayawa tayi tana k'arema wurin kallo dan kaya neh mak'il a ciki masu tsada da daukar ido, murmushi tayi dan tasan wannan aikin Mami ce. Kwalin dinner set ta d'auko dakyar ta bud'e ta ciro plate ta wanke sannan ta d'auko cups shima ta wanke ta koma dakin. A gabanshi ta ajiye tana kokarin mik'ewa, dasauri ya rike hannunta ya jata ta fado jikinshi

"Ina zaki? Ai tare zaki zauna muci"

Turo baki tayi tana kokarin fizge jikinta daga nashi

"Nifah na koshi dazu muka gama cin abinci da Mahnoor"

Yanda tayi maganan bah k'aramin burgeshi yayi bah har saida ya kwaikwayi yanda tayi. Dariya tad'anyi ta k'ara shagwabe Fuska

"Nidai ka daina"

Kazan ya saka a plate din ya bud'e fresh youghut ya zuba a cup dinda ta ajiye Sannan ya soma bata a baki. Kauda kai tayi tana yatsine fuska

"Nifah ya Masroor na koshi"

Matso da fuskanshi yayi daidai nata har numfashinsu na had'uwa

"Wai yaushe za'a chanza min suna neh daga Ya Masroor"

Batace komai bah sai murmushi datayi. Tura mata kazan ya somayi tana ci tana bata fuska kamar xatai kuka, shi kuma yana mata d'ariya. Tadanci bah lefi sannan ta mik'e ta xauna kan gado tana cigaba da yatsine fuska

"Kagani koh kasa cikina ya cika dayawa"

Mik'ewa yayi ya kamo hannunta

"Tho zo na miki doki nasan cikin zai sassauta"

Tsugunawa yayi a kasa sannan yace tahau. bako kunya ta d'ane bayanshi ya soma tafiya ita kuma sai dariya takeyi, sun dad'e suna haka sannan ta sauka tana hanma a hankali

"Bacci nakeji"

Kai ya gyada yace yana zuwa ya fita daga d'akin. Kamin ya dawo ta shiga toilet tayi wanka ta fito ta sauya kayan jikinta zuwa na barci tahau gado nan da nan barci ya d'auketa

Wanka ya shiga yayi a d'akinshi, koda ya dawo nata ta dad'e dayin bacci. Hannun jalabiyar jikinshi ya nad'e ya d'auketa chak ta bud'e ido dasauri tana kallanshi Murnushi ya mata ganin yana kokarin fita da ita daga dakin yasa ta soma zulezule, bai direta ko inaba sai lumtsatsiyar gadonshi.

Mikewa tayi ta zauna a tsorace

"Ya Masroor Bacci fah b
Nakeji"

Bako kunya yace

"Kazana da kikaci zan amsa abuna"

Bata gane me yake nufi bah tace

"Tho bah kai kace naci bah ni yanzu ina zan samu kaza na biyaka"

Tana magana cikeda shagwaba. Fitilan d'akin ya kashe ya rage na side lamp sunada haske sosai dan su kadai mah sun wadata d'akin. Kan gadon ya hau ya matso kusada ita tad'an mata, ya kara Matsowa ta k'ara Matsawa

"Beauty ni dodone? Meyasa kike matsawa"

Shagwabe fuska tayi

"Ni tho ka kwanta a gefe nima na kwanta a gefe"

Maganar tazo mai a bazata anma ya share yace

"Anma ai keh matata ce xan iya kwantawa a kusa dake ai"

Batace komai bah sai chuno baki datayi, matsowa yayi kusada ita ya rikota tareda matseta a jikinshi. Bud'e baki tayi zatai magana ya had'a bakinshi da nata. Ina ganin haka na tattara inawa inawa nabar musu gidan gaba d'aya na koma k'auyenmu..

*Bayan Wata hud'u*

Masroor ne zaune a falo yana daddana system dinshi, hankalinshi duk ya tattara ga abinda yakeyi. Sulthana ta fito cikin wani riga pink iya cibi da wani matsatsen short, kayan sun mata kyau sosai. Jikin Masroor ta fada tana maida numfashi. Dasauri ya aje system din ya k'ara matseta a jikinshi

"Beauty naji jikinki ya k'ara zafi, nifa zafin jikin nan na. Cutana gashi kinki yarda muje asibiti"

Batace komai bah saima janye jikinta datayi daga nashi ta koma chan gefe ta zauna. Kara matsowa yayi yana kokarin tabata, bai ankara bah ta soma kwararo mai Amai, Aman take sosai jikinta na rawa. Riketa yayi har saida ta gama sannan ya mik'e ya dauko ruwa ya bata ta kuskure baki ya dauketa ya kaita daki ya kwantae da ita. Masu aiki ya kira suka gyara wajan ya koma dakin

Kwance ya sameta tana juye juye jikinta bah dad'i, daukanta yayi chak ya kaita bayi ya mata wanka ya fito da ita. Da kanshi yasa mata kaya ya d'auketa yasata a mota sukad'au hanya. Tana ganin sun nufi asibiti ta soma bata fuska, baice mata komai bah. Da kanshi ya d'auketa suka gida, bah tareda wani b'ata lokaci bah aka dubata tareda mata gwaje gwaje, a nan neh aka gano cikin datake d'auke dashi na wata biyu.

murna sosai Masroor yayi, d'aukanta yayi suka nufi gidan Mami bayan an rurubuta mata magunguna tareda bata shawarwar..

Ummy Abduol✍🏻

💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐

By *Ummy Abduol*


DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION

*Page 200*

🔚

Da Farinciki suka k'arasa gidan Mami bah ko kunya ya mik'a mata takardan test din itadai Sulthana na zaune k'anta a kasa. Mami na gama karantawa ta girgiza kai tana mai cikeda farinciki

"Allah ya raba lapia"

Ga Mamakin Mami da Sulthana saijin Masroor sukai yace

"Ameen Mami"

Kunya sosai Sulthana taji har ta k'ara duk'ar dakai, shiko gogan ko a jikinshi. Tun daga ranar Sulthana ta k'ara samun kula daga wajan Mami da Masroor da duk sauran yan gidan mah. Tattalinta sukeyi sosai kamar kwai hakan bah k'aramin sata farinciki yayi bah..

A bangaren Fareed da Ameenatu basuda Matsala zama suke na soyaiya da mutunta juna. Ita tana d'auke da nata cikin na wata uku, Mama da Baffa bah k'aramin farinciki sukayi bah da samun labarin cikin da y'ayansu suke d'auke dashi. Yasir da Hafsatu sun hada kansu har anma Ranar biki. Haka Sadiya k'awar Sulthana da S'aood wanda ya ganta lokacin biki ya lik'e mata.

Bayan wata shidda Ameenatu ta haifi santalelen d'anta namiji inda akasa mai suna Farhan. Bayan wata d'aya Sulthana ta xankado santaleliyar Y'arta mai kamada Masroor sak. Murna wajan su Mami ba'a magana. Inda yarinya taci sunan Mahaifiyar Sulthana wato Rabiatu anma ana kiranta da Mimi. Kula Sulthana take samu itada jaririyarta sosai daga bangarorin biyu hakan yasa ta saki jikinta tana shayar da y'arta hankali kwance..

Ban k'ara komawa government house bah sai bayan Shekara biyu. Anan nakejin Labarin Ansha bikin Hafsatu da Yasir haka na Sadiya da Sa'ood dukanninsu suna d'auke da tsohon ciki haihuwa yau ko gobe. Sai Mahnoor dake karatunta na likita a k'asar Masar

Had'adiyar Mace mai jida kanta na gani ta fito a wata lumtsatsiyar Mercedes benz, saida na k'ara matsawa dakyau naga Ashe Sulthana ce. A gajiye ta shiga gida ta fada kan kujera tareda fadin wash. Y'ar yarinya ce fara sol kana ganinta kaga Masroor saidai tafi Masroor din haske ta taho dasauri da tafiyanta dabai gama k'wari bah ta fada jikin Sulthana. Rungumeta ta k'arayi tana y'ar Murnushi

"Mimi ina kikanar nannyn naki"

Dai dai nan nannyn ta karaso wajan a guje tana kwalla ma yarinyan kira. Ganin Sulthana yasa tayi turus ta tsugunna tana

Please Login or Register in order to submit comment