Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

su taka ni, tunda na girma na san abinda yake yi mini ciwo.
Aka yi bikinsu Hassana kowace aka kaita dakinta. Sai na zama ni kadai a d'akin, idan zan fita na kan kulle tunda anti Yagana ta saya mini keken d'inki. Akwai kayan mutane a ciki na aikatau huluna da jakunkuna. Da nake yi suna biyana. Sannan wasu lukutan na kan d'auko aikin da nake dashi a shagon Maman bokola na yi a gidan. Shiyasa na sayi katon kwad'o nake kullewa a duk lokacin da zan tafi makaranta.

Muka dinga fa'di tashi da zurga-zurga makaranta tare da Sahura, kuma kamar yadda Yayansu ya yi alkawari bai bambamta ni da ita ba, duk abin buk'ata da ya danganci karatunmu tare zai saya mana Wanda ita a d'akinta ta kammala. Ni kuma har lokacin ba ni da wani tsayayye. Ina dai ta addu'a da neman yadda asirina zai rufu domin a lokacin na mayar da hankali sosai wurin neman aiki, da kuma fitar da style na din'kunan mata. Sosai nake neman kud'i a gidan. Hakan ya janyo mini kwarjini da mutunci a wurin matan Babanmu Mussaman Ummansu Hadiza da ta watsar da makamanta a kaina ta fara jana a jiki tana nuna mini k'auna. Hadiza da a can take ganin tafi karfin ma ta kula ni idan ta zo gidan sai ya zamana tana shakkata don ganin irin sutturar da nake sanyawa tana nema tafi karfinta ita da take da miji. Babanmu kuwa yadda nake taimaka masa shiyasa koyaushe cikin sanya mini albarka yake. Anti Sakina itace muke sama-sama Hakan ya samo asali ne dalilin 'kin auran 'kaninta da na yi saboda binciken da na yi akansa aka tabbatar mini da cewa ba shi da wata cikakkiyar sana'a sai maning, sannan uwa uba yana shaye-shaye, kullum yana shagonsa a kwance da waya a hannu wasu ma suna zargin yana harkar yahoo (damfara) ita kuma ta kawo mini shine a ganinta ta rufa mini asiri ganin yadda duk na tsofe a gida, an aurar da 'yan uwana, 'yan matan unguwarmu a yanzu duk babu sa'ata. Shine ta yi mini wannan gwanintar. Tabbarar mini da munanan halayensa ya sanya na ce ban amince ba. Babanmu ya goya mini baya, shine dalilin da ya sanya take jin haushina har tana fad'in dama can na yi masa girma tunda na girmeshi kawai dai ta tausaya mini ne shiyasa tace masa ya aureni . Maganarta ta ba ni dariya sosai a lokacin sai na shareta ban tanka mata ba, muka cigaba da zama a haka ina ko'karin kaucewa duk abinda zai janyo mini samun matsala da su a gidan, amma ba na yarda su zo mini da son zuciyarsu....✍️
*GARKUWAR MATA*
*BINTA UMAR ABBALE*
[11/22, 10:12 AM] Aunty B: *GUDUN AURE!*
*NA*
*BINTA UMAR ABBALE 🍒*

*@Arewa books*
*Bintuumarabbale.*
*Na yi nisa a arewa idan ba kya son jira ki yi maza ki garzaya can Kisha karatu!*
*Domin biyan kudin karatu a talgram kuwa 1k ne ga hanyar biya 0542382124...Binta Umar gtbank mutanan nijar dala dari ne katin airtel sai ku kankare hoton a turo mini sheda ta wannan lambobin*
*Whasap kawai*
*08089965176*
*07084653262*
Astagfirullah jiya na yi mistake typing error inda zan rubuta Alhaji Halilu wato mijin da Hadiza ta aura sai na rubutu akasin hakan. Wad'anda suke bibiyar littafin nasan za su gani bisa kuskure ne, ina neman afuwa.
*Free peges*
*13*
Watarana katsam Yaya Aminu ya zo yana gaya mini ya sama mini offer ta aikin koyarwa. Saboda murna kamar na rungumeshi na rasa ina zan tsoma kaina. Na dinga yi masa godiya wanda har na gaza ha'kuri na tambaye shi yadda aka yi ya sama mini aikin da har na fitar da raina da samuwarsa. Nan yake gaya mini wani abokinsa ne da suka yi harkar siyasa. To shine mutumin da suka wahaltawa da ya samu kujera ya raba musu offer biyar domin su taimaki makusantansu. Cikin ikon Allah ya kaiwa kanwarsa daya ya rabar da sauran. Tunda lokacin shi yana aiki a karkashin kamfanin Alhaji Tajo. 'Kanwar tashi sai ta rasu, shine ya nema mini alfarmar maye gurbinta da ni. To komai dai rabo ne, kuma na tabbata addu'ar da nake yi ita Allah Ya kar'ba ya kawo mini aiki cikin sau'ki da rangwame. A daidai lokacin ne itama Sahura ta samu aikin rabon magani 'kauyika amma mijinta Idiris ana ta turzawwa dashi ya 'ki amincewa bayan kuma ba haka akayi dashi ba kafin auran.
Cikin hukuncin Allah na fara zuwa aiki da zuciya daya. Sai dai yadda 'yan gidanmu suke ko'karin juya mini manufa shi ya fi damuna. Mutanan unguwarmu ma suna ganin kamar yanzu na yi karfin da babu wanda ya isa ya gaya mini na ji, tunda babu uwata a gidan matan Babana ban d'auke su a bakin komai ba. Wasu ma suna fad'in duk an yi wa 'yan'uwana aure ni kuma na tsaya za'be sai mai kudi. Kowa dai da irin kallon da yake yi mini akwai masu cewa ma zaman kaina nake yi, na fi karfin Babanmu tunda ina bashi kudi na toshe masa baki. Wannan maganar kuma daga bakin Ummansu Hadiza ta fita, domin itace mai yawan fad'in haka har jama'ar unguwa suka d'auka.

To da yake komai ya yi farko yana da k'arshe. Idan kaddara ta gifta babu yadda bawa zai yi dole ya kar'beta hannu biyu, ya kuma roki Allah Ya sa alheri ne faruwar Hakan.
Budurwar da Yaya Aminu yake nema da aure har an kai kudi da sa ranar d'aurin aure rana tsaka ta bijire tace ta fasa. Kuma kada ku d'auka lafiyayayyace kamar kowa. Bai yi gigin haka ba saboda shima ya san ga yadda Allah ya yi shi, sai ya nemi daidai dashi don har ya fi ta lafiya ma tunda shi yana yawo da 'kafafunsa, sa'banin ita da kafafun suke a nanna'de a keke take yawo. Sai dai kyakykyawar gaske ce fara tas da ita. A haka suka kulla soyayya har suka kai matakin aure rana tsaka wani gurgu d'an wani attajiri ya ganta a wani taro da suka yi irin nasu. Ya ce Yana sonta. Ganin daga gidan da ya fito ya sanya iyayenta da ita kanta suka dawowa da Yaya Aminu kudinsa wai ya nemi wata.
A lokacin ya shiga rud'u sosài, domin ya d'okanta da auran da ya shafe shekaru sama da arba'in a kasa bai yi ba, har furfura ta fara feso masa, kuma a hakan ma bashi gwaggo ta fara Haifa ba, ta yi haife-haife kafin zuwansa yaran suna rasuwa. Sai da shekarun girma suka cimmata ta haife shi, Allah Ya raya shi tare da d'an'uwansa Hamusu da tazarar da take tsakaninsu take da yawa. Wannan dalilin ya sanya hankalinsa ya tashi. Ita kanta Gwaggo ta shiga damuwa. A lokacin ne ya zo har kofar gidanmu ya aiko nazo.
Na fita na same shi muka gaisa ba yadda yake duk ya yi rama. Ya fara tambayata ko Ina da tsayayyen wanda zan aura. Na ce masa babu. Sai ya bijiro mini da bukatarsa akan na share masa hawaye, idan kuma da takura ko ba na sonsa kada na cutar da kaina na gaya masa sai ya ha'kura.
Na ce wallahi ko ka fi haka nakasa da talauci zan aureka Yaya Aminu, kuma da zuciya daya, na amince Ubangiji Allah Ya tabbatar mana da alheri.

Ba'a ja dogon lokaci ba iyaye suka shiga lamarin. Ummansu Hadiza ta dinga fad'in dama tuntuni na fahimci soyayya kuke yi, tun kina yarinya. To tunda shi ki ka gani, ai ba mu da abinda za mu ce akan haka. Anti Sakina kuwa dariya take yi tana fad'in. Ai ta gwammace ta auri nakasashe an kawo mata mai lafiya da aikin yi ta ce ba ta so. To za mu ga zuwan da dawowar ai. Duk maganganunsu akan lamarin bai dame ni ba. Kawai dai ni na tsananta da addu'a Allah Ya sanya mana alheri da albarka a cikin auranmu.
Danganin Mamanmu ba su k'yamaci lamarin ba sanin wacece Gwaggo ya sanya suka nuna faricikinsu da hakan. Kuma suka yi mini shatara ta arziki a lokacin auran duk abinda ake Yayi da buk'ata sai da suka saya mini aka shirya mini dakunana biyu wanda Yaya Aminu ya kama hayar gidan a can sharad'a wajejen kamfanin da yake aiki ya yi hakan ne domin ya samu sau'kin zuwa neman abincinsa.
Zaman lafiya muka gudanar a zaman auranmu, tunda aka yi babu wanda ya ta'ba jin kanmu, Muna ta rufawa juna asiri, duk wanda zai zo gidana sai ya yi sha'awa domin ba na yin girki lami sai da nama ko kifi, kuma idan mutan zai tafi na bashi kudin mota. Na ri'ke aikina da sana'ata hannu bibbiyu, muka dinga cud'a rayuwar har na yi haihuwar fari, wata matsala ba ta faru. Irin sa'banin nan na zama ba mu taba samu ba, tunda kowa yana ko'karin kiyayewa da kyautata mu'amula da abokin zamansa.

WANNAN SHINE ABINDA YA FARU GA RAYUWATA TA BAYA.

Saukar hannu na ji a kumatuna. Da sauri na bud'e idona, sai na ga Yusi a gurfane a gabana Yana kuka harda shashsheka. Gefe kuma Kamalu ne ra'kube a jikin kusurwa sai ajiyar zuciya yake saukewa.
Ganin haka ya sanya na yi namijin ko'karin daidaita kaina. Na tashi na dan gyara abinda ya samu a d'akin. Na gyara musu shimfida kafin na kira Usaini na bashi kudi ya sayo mana abinci, don ba zan iya yin komai ba saboda gajiya da fargaba.
Suna cin abincin na ce dasu su kwanta sai da safe kuma.
Suka shiga net din a tare Ina kallon yadda Yusi yake ta rirri'ke dan'uwan nasa da har yanzu yake a tsorace Yana ganin zan shammace shi ne kamar yadda na saba na zane shi.
Kiran anti Yagana ya shigo wayata dake cikin jaka. Na d'aga da sauke ajiyar zuciya. Tambayar da nake hasashe ita ta jefo mini.
Na ce." Ai an gama komai sun ba mu yaran. Amma sai da aka yi dauki ba dad'i sosai da jama'ar unguwar.
Ta ce." Ubangiji Allah Ya kiyaye faruwar hakan anan gaba, ki yi ta addu'a watarana sai labari."
Na ce." In sha Allahu rabbi anti, sai da safe."
Muka yi sallama na ajiye wayar na fita na d'auro alwala domin ban yi magariba da isha'i ba. Da kyar na iya tsakurar abinci, hakan ma don dai kada na kwanta ban ci ba, na cutu, shiyasa na ci kad'an, na zame na kwanta a kan daddumar ina lumshe ido. Bacci ya fara fizgata kira ya shigo wayata a karo na biyu, ban kawo kowa ba sai Alhaji Muntari, shine ya kan kira ni a irin wannan lokacin, sai na kan rasa azancin hakan, mutumin da yake da iyali ai a irin wannan yanayin ya kamata ace yana tare da wadda ta yi girki.
Ban saki jikina ba sosai, dalilin damuwar da nake ciki, da kuma fargabar kada hakan ya haddasa masa rikici a cikin gida domin na san ba kowace mace ba ce za ta iya daurewa da hakan, na dinga yin hamma ina amsa masa magana a kasalance. Hakan ya sanya shi yi mini sallama yana fad'in da safe zai sake kirana mu k'arasa tattuna maganar tunda na dawo a satin yake so a yi komai a gama.
Na ajiye wayar. Idona a lumshe na cigaba da nazarin yadda abubuwan za su kasance anan gaba, ko na'ki ko na so, dole na auri Alhaji Muntari domin katange kaina da mummunar kaddarar da take shirin rufto mini. A zahiri na furta 'Allah Ka takaita mini wahala'

Ban yi wani baccin kirki ba dalilin tunanin da ya'ki barina, akan kunne da idona asubahi ta yi. Na yi sallah, yaran ma na tashe su kamar koyaushe suka daura alwala suka fita. Ban koma bacci ba domin na san akwai wad'anda za su dako mini sakammako abinda ban k'arasa ba, na kammala. Duk wadda ta zo kar'bar dinkinta ba na yarda na bata sai ta cake mini kudina tukkuna. Domin zurga-zurgar nan, da wannan matsaltsalun kudin hannuna duk sun kare, don dai ma Alhaji Muntari ya taimaka mini da wasu.
Yusi ne ya shigo shi kadai jikinsa sanyi kalau saikace wanda ya tashi daga ciwo fatar samar idonsa duk ta tasa, tamkar shi ya aikata lefin duk ya shiga damuwa. Na kalleshi a nutse na ce ." Ina Kamalun yake?"
"Yana can massalaci a kwance Yana bacci, wai kafarsa ce take ciwo. Mama kin ga har ta kumbura."
Na ce." Je ka taso shi, ka ce ya zo in ji ni."
Ya kalle ni. "Mama tsoro yake ji kada ki dake shi, shiyasa ya kwanta a can.
Na ce."Ai da zan dake shi da tuni na dake shi Yusi, addu'a na ke yi masa, Allah Ya shirye shi." Ya saki ajiyar zuciya Yana fad'in." Bari na je na kirawo shi."
Ya fita da sauri.
Minti uku da fitarsa Hamusu Ya shigo. Muka gaisa ya ce." Tun jiya na so na shigo mu tattauna Allah bai nufa ba, da yake ban dawo da wuri ba, Gwaggwo duk ta sheda mini abinda ya faru, anti Amina jama'ar gari suna ta zaginmu akan mun sakar miki wahala, don Allah wannan karon kada ki ce a a, ki ba mu yaran nan, su koma hannunmu da zama, komai Yana da lokaci, kuma in sha Allahu yaran nan, sai duniya ta amfana dasu."

A nutse na ce." Ban ki maganarka ba Hamusu, kuma ban ce kun gaza mini ba, ni dai har duniya ta nade babu kalmar zagi ko 'batanci akanku, duniya ban ga abinda za ku yi mini ba Hamusu, domin Iya k'auna kun nuna mini. Ba wai ba na son ba ku yaran nan ba ne, ina tausayawa Gwaggo da shekarun tsufa suka cimmata. Ta rainin yaranta cikin nutsuwa da kwanciya hankali, ba zai yiwu ace kuma yanzu da take buk'atar kulawa a kai mata wahala ba. Ku barni da yaran in sha Allahu babu abinda zai gagare ni."
Ya ce." Ai kin san na kusa aure, zaman da yaran za su yi a hannun Gwaggo na hucin gadi ne, daga zarar na yi aure da 'yan watanni sai su koma hannuna da zama, in sha Allahu zan ri'ke su da kyau, haka nan yarinyar da zan aura na sanar da ita duk abinda yake faruwa kuma ta ce ta amince za ta ri'ke su."

Na dube shi cikin nazari. Wato wasu lukutan maza suna da gajeran tunani. Ta ya za a yi amarya daga aure ta fara jigila da yaran ma da bana mijinta ba. Akwai matsala babba wadda shi ba zai fahimta ba a yanzu sai zama ya yi zama tukkuna. Yanzu yarinyar zata furta karya domin tabbatuwar auran, idan ta ga ta shiga daga ciki sai ta canza alkibula.

"Hamusu wannan karon ma dai Ina ba ku hakuri, kuma ma dai har gida zan zo wurin Gwaggwo mu tattauna, aure zan yi nan da sati biyu in sha Allahu, kuma wanda zan aura ya amince mini, zai kula mini da yaran nan, ba ni na nuna ina son hakan ba, shi da bakinsa ya furta, ka ga kuwa bai kamata mu watsa masa kasa a Ido ba, sannan ina so da ni da yaran gabad'aya mu yi nesa da unguwar nan, Kamalu ya canza abokai, muna cigaba da addu'a sai ka ya dabi'un nasa sun canza gabad'aya.

A sanyaye ya ce.' Anti Amina surutun mutane shi yake damuna wallahi, Baba Sule sai ka ce babu dangatanka duk inda ya zauna sai ya zagi Gwaggo, ya aibata mu, kuma kin ga ba lefinmu ba ne, duk talaucincmu ba zamu kasa ri'ke yaran nan ba."

Cikin takaici da b'acin rai na ce." Ka yi hakuri Hamusu, don Allah kada ka sanya damuwar Baba Sule a ranka, ni kaina bai barni ba, kuma Allah da zuciya yake amfani, kai dai ka cigaba da yi musu addu'a. Komai zai zama tarihi."
Ya ce." In sha Allahu rabbi anti."
Yaran suka shigo d'akin. Gabad'aya muka dube su. Da gaske dai d'ingisa k'afar yake gefanta ya kumbura kadan. Ya zube a bakin k'ofa, murya na rawa yake gaishe da kanin Uban.
Bai amsa ba hankalinsa yana kan kafarsa ya ce." Garin tura kurar ruwan ka ji ciwo, domin an ce kaine jami'i wurin d'aukar kurar ko?
Ya girgiza kansa yana fad'in." Ba ni ba ne, Shamsu ne ya tura kurar ni kuma na d'auki jarakuna biyu, muka nufi kasuwa, sai Saminu da ya cire wili da taya ya sayar."
Ya girgiza kansa tare da furta." Allah Ya shirye ku. Ya dube ni kaina a kasa domin duk sanda na kalli yaron Ina ji kamar na fasa ihu.
Ya ce." Bari na je na kira Abdullahi mai chamis ya zo ya duba shi.
Na ce." Anya Hamusu kafar nan, ba targad'e ba ne, dukansa fa suka yi 'yan sandan."
Ya ce." Ai dole su dake shi tunda ya yi yun'kurin guduwa, idan suka riga suka kamaka, kawai ka mika wuya.
Sai ya fashe da kuka Yana cewa." Ban yi yun'kurin guduwa ba, wani daga cikinsu ne ya rike ni ya dinga dukana da takalmin kafarsa."
Babu wanda ya tanka masa a cikinmu.
Hamusu ya tashi ya fita. Ni kuma na cigaba da abinda nake yi. Sai kawai na tsinkayi muryarsa yana cewa." Mama ina kwana?"
Na dube shi a nutse na amsa.
Ya yi shiru fuskarsa duk hawaye a bushe. Ya furta." Don Allah ki yi hakuri kin ji."
Na ce." Ai na ha'kura tuntuni."
Sai ya rarrafo kusa da ni, yana fad'in." Ki dake ni, idan hakan zai sanya ki daina damuwa a kaina, jiya na ga ba ki yi bacci ba, kina kuka."
Na ce." Yaushe ka ga ina kuka Kamalu? Idan ka ce ban yi bacci ba wannan na yarda, amma ban yi kuka ba."
Ya yi shiru yana sauke ajiyar zuciya.
Na ce." Na yafe maka, Kai ma ka yi mini alkawari ba za ka sake ba."
Da sauri Ya ce.'' Wallahi ba zan sake yi ba, kuma ba zan kara kula Saminu ba."
Na ce." Allah Ya kyauta, Kai be Yusi d'auko kofi a kwando ka je ka sayo kunu, ina da sugar, sai ka wuce gidan awara."
Da sauri ya yi abinda na umarce shi, ya kar'bi kudin ya kama hanya ya fita da saurin gaske.....✍️
*GARKUWAR MATA*
*BINTA UMAR ABBALE*
[11/23, 10:21 AM] Aunty B: *GUDUN AURE!*
*NA*
*BINTA UMAR ABBALE 🍒*
*TALLAH!*
'Yan uwa
Barkanku da zuwa FAMAS SCENTS OF LEGENDS,
duniyar turarukan wuta masu kamshi na musamman mai samar da nutsuwa da kwanciyar hankali.
Mun tanadar muku da turarukan wuta masu dadin kamshi kamar su
Sandal flakes
Hawee
Gabgab
Halut
Dorot
Coconut chips
Dufr(farce)
Black khumra
Brown khumra
White khumra
Oil perfumes da
Body sprays
Dan turara gidajenku,tufafinku da jikinku.
Ga duk mai buqata zai iya tuntuban mu ta lamba kamar haka
Call/WhatsApp
07037489958
Location:Gonan Ganye,zaria
Kaduna state
Nationwide Delivery

*DATA Mai karfi da quality 💯*
TEEMAH DATA SERVICES MTN
1GB @550
2GB @950
3GB @1450
4GB @1550
5GB @1700
CHECK CODE *323*4#
VALIDITY 30DAYS
CHAT@08112392177
CALL @08037026306
8037026306 fatima musa ibrahim opay

*@Arewa books*
*Bintuumarabbale*
*Ga wad'anda ba su san jira akwai more peges a arewa na gode🙏*
*Free pege*
*14*
Hamusu ne ya yi duk abinda ya kamata akan rauninkan dake jikin Kamalu. Abdullahi mai chamis ya zo ya duba shi sosai, ya bashi maganin da ya dace. Sannan ya bi bayansa yana tambayarsa abinda za a ba shi.
Da k'yar na lallab'i Yusi ya shirya ya tafi makaranta. Babanmu ya leko yana fad'in." Ina Kamalun yake ne, ban ji motsinsa ba."
Na ce." Gashi nan, a kwance yana bacci, Abdullahi ne ya ba shi magani.
Ya shigo d'akin sosai yana duba kafartasa. Ya girgiza kansa babu kuzari a tare dashi ya furta." Allah Ya taikaita muku wahala."
Na amsa da "Amin Ya Allah."
Ya dube ni kafin ya ce." Maganarki da Alhaji Muntari tana nan ko?"
Kai na d'aga a hankali na ce." E, Baba." Sai ya kama hanyar fita yana fad'in." Allah Ya tabbatar miki da alheri."
Na amsa da "Amin." Cikin sanyin jiki.
Ummansu Hadiza ta le'ko ta duba jikin Kamalu, mun d'an jima da ita muna tattaunawa kafin ta fita daga d'akin. Na dinga zuba Ido ko zan ga Anti Sakina ta le'ko, ta duba shi, tunda dai ta san bashi da lafiya, amma shiru ba ta le'ko ba, kuma ina jin kayaniyarta da yaranta a tsakargida.
Na nemi wayar Sahura domin tunda na rakata neman aiki ba mu sake had'uwa ba, ko a waya.
Tana d'agawa take fad'in." Kina raina wallahi sis, kuma yau nake cewa zan kira ki kwana biyu network Yana yi mana wahala a unguwarmu."
Na ce." 'Kwarai kuwa, kuna da matsalar network a nan wuraran, ya gida, da yara?"
"Wallahi duk suna lafiya, ina su Kamalu fatan kowa lafiya."
Na ce." Alhamdullahi wallahi, kin ga har na je bikin Babandi na dawo, anti Yagana tana gaisheki da kyau."
"Ina amsawa wallahi, ina son zuwa garin nan k'awata."
Na ce." Sai ki bari idan auran Fadila ya tashi sai ki je."
Dariya ta yi tana fad'in." Ubangiji Allah Ya nuna mana, ai kaya ma zamu had'a ni da Yara mu je mu cashe da biki."
Dariya na yi, a hankali na ce." Sahura aure zan yi nan da sati biyu masu zuwa."
Da mad'aukakin mamaki a tare da ita ta furta "Aure sis!"
Na ce." E, wallahi Sahura."
"To ya aka yi ki ka canza shawara da gaggawa haka, wanene wannan da lokaci guda ya canza ki?"
"Ba wani ba ne Sahura Alhaji Muntari ne dai
wanda na baki labarinsa ranar da na zo gidanki...... Gabad'aya na kwashe duk abubuwann da suka faru na gaya mata, domin bahaushe yana cewa 'Abokin kuka shi ake fadawa mutuwa'
A sanyaye ta ce." Sis, kin yi bincike sosai a kansa ko? Ni fa ba na son irin wannan gaggawar a sha'anin aure Amina, ki nutsu don Allah, kada wata matsalar ta sanya ki jefa rayuwarki cikin garari, na tsorata da na ji kin ce matansa biyu yaransa takwas, ba ki hango matsala ba."

"Sahura ya zan yi? wallahi kaina ya kulle gabad'aya, gida sun takura mini, Kamalu Yana nema ya fi 'karfina, wannan ce kawai mafita a gare ni. Idan na ce ba zan yi aure ba, zan je na kama haya na zauna jama'a su canza mini manufa, ya zanyi ne Sahura, dole ko ba na so na amincewa mutumin nan domin na rufawa kaina asiri, yadda ya nuna alama kamar akwai nagarta a tare dashi, da bakinsa ya furta zai ri'ke mini yarana ba ni ce na nema ba, shiyasa na amince da auransa."

"To, shikkenan sis, amma don Allah ki tsananta da addu'a akan lamarin, Ubangiji Allah Ya tabbatar miki da alheri, Allah Ya sa abinda muke hasashe a kan mutumin ya tabbata."
Na ce." Amin Ya Allah Sahura na gode sosai, in sha Allahu ai kafin d'aurin auran zan zo mu tattauna."
"To Allah Ya nufe ki, sai ki zo ranar da ba aiki, mu yini muna hira."
Na yi dariya tare da ce wa." Sahura Ya aikin kuwa? Ina fatan babu wata matsala."
"Wallahi babu matsala, ai na gaya miki na fara a sa'a, sati daya da fara zuwana ma'aikatar ya yi mana rabon kayan abinci. Harda kudin cefane.
Na ce." A lallai, ma sha Allah, na taya ki murna, Allah Ya sa a d'ore."
Na fad'a cikin barkwanci.
Tana dariya ta ce." Za a dore in sha Allahu rabbi, ai kamar yadda ya gaya mana idan mun bi dokokinsa, zai kyautata mana, wallahi akwai alamun tausayi a tare dashi, shiyasa nake ko'karin ganin ban sa'ba dokokin aikinsa ba."
"Ai kam Sahura ba girin-girin ba, Inji hausawa ta yi mai, Alhaji Tajo ne fa, ni dai ba na yinsa, tunda ya yi sanadin uban 'ya'yana."
Ta dinga kyalkyala dariya tana fad'in." Ho 'kawata, idan ki ka tsani abu, duk inda makusa take sai kin nemo, wallahi mutumin arziki ne, ga kyauta da sakin fuska ga ma'aikatansa."
Na ce." To a ba ni hakkin mijina kawai a zauna lafiya, shekara kusan goma yana yi masa bauta, ai ya ci ya bashi fansho."

Ta ce." A rigimarki ba, ai ko gomnati ce sai mutum ya zartar shekara goma suke biyan fansho da garatuti, balle kamfani da babu wannan yarjejrniyar. Amina nifa na fi zargin akwai wad'anda suke cin amanar mutumin nan a bayan fage shiyasa ki ke ganin kamar bashi da Imani."
Na ce." Ai duk wanda yake aiki a k'arkashinsa ba zai ga aibunsa, mussaman idan Ya na amfanuwa dashi, shiyasa idan na fadi abinda ya yi mana sai jama'a su karyata ni, ke dai kin sani, ba sharri ba ne ko?"
Ta ce." Na sani, shiyasa ma ai ki ka ji na ce miki akwai masu ha'intarsa a bayan fage, wallahi na san da saninsa ba zai wulakanta wanda yake moruwa dashi ba."
Na ce."

Please Login or Register in order to submit comment