Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Muna sayar da sabulan gyaran jiki dilka da man gyaran gashi, muna kuma bayar da sari a fad'in najeria da nijar muna tura kayanmu kowane gari da ikon Allah.*
*Muna garin kano duk inda kake za mu aika maka da kayanmu. Domin neman karin bayani sai a yi mana magana ta Whasap ga lambobin da za a same mu a kai.*
*07084653262 ko*
*08089965176*
*SIYAN NAGARI!!!!!!*
*A JARRABA A SAMU BIYAN BUKATA DA YARDAR ALLAH*
[11/26, 10:38 AM] Aunty B: *GUDUN AURE!*
*NA*
*BINTA UMAR ABBALE 🍒*
*M.W.A*
*TALLAH!*
*Gidan 'kawa ne da kece raini.💯*
🛍️ “Ko ba ki da niyyar siya ba, ki zo ki shiga ki kalla kayayyaki — wallahi sai kin bude ido! Ballantana kuma nasan za ki tashi da kaya saboda kyau da araha.” ✨
🌸✨ “Shigo duniyar da kyau da jin daɗi suka haɗu — daga kyawawan laces na alfarma, Atamfa , abaya masu salo, zuwa kayan ado masu kyalli, kayan girki na zamani da sauran ƙarin abubuwa. A Meerah B Collection , muna adashen kayan kitchen daily 1k to pack 100k items weekly Monthly ✨🌸We are sale kitchen items, electronic, WE ALSO DEAL WITH CONTRIBUTE monthly weekly daily after 10 days for kitchen items or electronic gaba daya wanna package 60k nake had'a sa zaku iya mallaka ta hanyar adashi

https://chat.whatsapp.com/KXsuo5E7syZ879Gcid3wCm?mode=ac_t https://chat.whatsapp.com/KXsuo5E7syZ879Gcid3wCm?mode=ac_t

*@Arewa books*
*Bintuumarabbale*
*17*
*Free pege*
Ashe akan ga'ba muka yi wannan sa'insar. Sai maigidan gabad'aya ya d'auki laifi ya d'ora mini, yadda yake yin fad'a shi ya kara tabbatar mini da cewa a kufule yake da ni, dama yana Jin haushina.
"Zaman aure ki ka zo gidana Amina, na gaji da rabon fad'a, kusan koyaushe Jamila sai ta kawo mini korafi akanki, na gaya miki tuntuni matan nam suna zaune lafiya, ban saba da irin wannan tashin hankalin ba, me zai sanya daga zuwanki ki d'aga mana hankali, muddin ba za ki bi umarnina ba, kamar yadda na sanya ki ka ajiye aiki, to d'inkin ma za ki daina yi mini a gida, domin ba zai yiwu ki zo kina neman kudi a gidana ba, kuma kina watsi da umarnina, ni kaina ba na samun kulawa a ranar girkinki, kin fi bawa neman kudi muhimanci, ki gyara muddin kina so ki zauna da ni."
Ban katse shi ba har sai da ya kai 'karshen maganarsa na ce."Ka yi hakuri don Allah, in sha Allahu zan gyara, maganar kuma na zo zan lalata maka gida babu wannan ajandar raina, da zuciya daya na shigo gidanka, sai kaine ma ka 'boye mini wasu abubuwa, amma hakan ba zai sanya na ce ka sake ni ba. Abu na biyu kuma ina kara gaya maka babu wata mace da zan yi wa biyayya, idan lallai sai na bi tsarin da matanka suka ginu akai ne to lallai ba ka shirya zama da ni ba, zan dai yi maka biyayya tunda kai ka ajiye ni. Sannan don Allah ina neman alfarma a wurinka idan zan samu."
Na kai 'karshen maganar ina dubansa. Ya ci kunu sai girgiza kafa yake yi da kyar ya ce."Wace irin alfarma ce?"
"Ina so na nemi mai aiki 'yar matashiya wadda za ta dinga taimaka mini, ka ga Allah Ya sanyawa lamarina albarka, ina so na yi amfani da damar kafin ta kubce mini."

Ya nisa kafin ya ce."Ita Iyami da take zuwa tana yi muku wanke-wanke da shara menene laifinta? Ba fa na son neman fitina Amina, idan ki ka ce zaki d'auki mai aiki ki ke kad'ai zai iya kawo hayaniya a gidan."

"Ba ka fahimta ba, zan samu wadda za ta taya ni aiki ne ranar girkina, tunda kun ce yara suna makara a makaranta, kai ma baka samun kulawa daga wurina, shiyasa na yi wannan shawarar."
"Ban yadda ba."
Ya fada hankalinsa yana kan wayarsa. Shiru wurin ya yi gabad'aya raina ya gama baci da abinda yake yi mini. Ya ce." Sai dai ki dauko wata daga cikin yaran dangi, zan yi miki wannan alfarmar. Amma ban yadda da d'auko mai aiki ba, bayan kuna da ita, na gaya miki babu wani tsari da za ki zo dashi da zumar rusa mini zaman lafiyar gida."

Ya tashi ya kama hanyar fita ba tare da saurari abinda zan ce ba. Yadda na fahimce shi ya fi tsoron Jamila fiye da anti Maimuna, ko meye dalilin haka oho! ko da yake 'yar kauye ce ai, Allah kadai ya san irin surkullen da take yi a gidan.
Gabad'aya sai ya jefa ni a cikin tunani. Ba yarinyar da zan je na nemi alfarmar iyayenta su ba ni kai tsaye sai Yusura yarinyar Sahura. To kuma idan na yi hakan ban yi wa kawata adalci ba, itama tana zuwa aiki, kuma yarinyar itace take d'awainiya da 'kananta tunda ta yi wayo.
Na yini ina nazarin yadda zan yi, domin fa zahiri idan ba mai'aikin nan na samu ba abubuwan ba za su gyaru ba, ni kuma ba zan fasa neman kudina ba, gashi daga farawa ta zuwa yanzu na samu kudi sun kai dubu dari biyu da hamsin, babu yadda za a yi na yi watsi da wannan damar da Allah Ya kawo mini, dole na yi wa marayun yarana digin da zasu amfana a gaba, ubansu bai bar musu komai ba.
Da yamma bayan la'asar yara duk suna makaranta, ina kan keke Sahura ta yi sallama. Cike da farinciki na tare ta. Ina fad'in." Wallahi yau yini na yi da tunaninki."
Ta zauna kan kujera tana cewa." Sai gashi Allah Ya kawo ni, daga aiki nake sai kawai na ce bari na karaso mu gaisa, kin san babu wata nisa fa tsakanin nan da wurin aikin na mu."
Na ce." Aikuwa kin kyauta mini wallahi bari na kawo miki ruwa.

Na kawo mata ruwa da d'an snacks da lemo na zauna ina fad'in." Me zan girka miki, na san kina tattare da yunwa daga ganinki."

"Wallahi a koshe nake, ai ba daga wurin aikin nake kai tsaye ba, mun je can gidan ogan mun duba mahaifiyarsa bata da lafiya, yau kwana biyu kenan da dawowarta daga egypt ganin likita, shine fa muke tattara mukaje dubata, mun ci mun sha ba na tare da yunwa."
Na ce." Ayya, to ko ruwa ai kya sha Sahura." Ta d'auki d'aya ta kai bakinta tana fad'in."To shikkenan."
Bayan ta ajiye ragowar ruwan na dubeta a nutse na ce." Sahura ya aikin fatan komai lafiya, na ga fa kin yi kumatu, ko ya yi muku karin albashi ne ."

Sai ta fashe da dariya tana cewa." Muna sa rai dai 'kawata, kin san ma na nemi alfarma a wurinsa za a mayar da ni daya daga cikin kamfanoninsa dake kusa da mu, saboda kafin na je Ina makara gaskiya, to da ya tambayi dalili sai na gaya masa, na kuma nemi alfarma."

Na ce." Hakan zai fi miki gaskiya, to Ina yi miki fatan alheri kawata, Allah Ya hadamu da rabonmu na alheri ."

Ta amsa da Amin tana bin falon da kallo. Ta ce." Su Kamalu suna makaranta kenan?"
"Suna makaranta wallahi, kin san wani abu kuwa?"
Ta girgiza kanta tare da mayar da hankalinta gare ni.

"Alfarma nake nema a wurinki, ban sani ba ko Idiris zai amince buk'atar tawa dai ta wucin gadi ce, idan ma zan samu a ba ni duka har aure zan fi son hakan."

"Wace alfarma ce wannan ki fad'a kai tsaye muddin Ina da iko, zan yi miki ai mun zama daya."
Yadda ta fadi maganar da karsashi, shine ya bani kwarin guiwar fayyace mata halin da nake ciki. Na d'ora da cewa." Sai kuma na yi tunanin yarinyar tana taimaka miki kema, sannan tana kula da 'yan'uwanta a duk lokacin da ki ka tafi aiki, shine dalilin da ya sanya na janye maganar a zuciyata."
Murmushi ta yi tare da dafa kafad'ata ta ce." Ki daina fad'in haka, idan ta ni ce yau ma Yusura ta dawo hannunki, ai da kai da kaya duk mallakar wuya ne, na san za ki kula mini da ita, maganar kula da gida da yara kuma, ba ki ji Ina gaya miki cewa wurin aiki za su dawo da ni kusa da gida ba, ai kin yi maganar akan ga'ba in sha Allahu kuma Abbansu ba zai k'i amincewa ba."
Ajiyar zuciya na sauke mai sanyi na ce." Na gode kwarai da wannan karamcin kawata, in sha Allahu duk sabgar makarantarta zan yi mata kokari sai ta dora daga inda ta tsaya tunda akwai makarantu anan din."
Ta nisa tana kallona." Kina ganin dai babu matsala a wurin abokanan zamanki ko?"

"Babu wata matsala Sahura, ai tunda maigidan ya amince magana ta kare, Jamila ce matsalar gidan itama na san inda zan yi da ita.

Ta sauke ajiyar zuciya a nutse ta ce.'" in sha Allahu rabbi ina komawa gida zan sanar da Abbansu duk yadda muka yi za ki ji ni a waya."
Na ce." To shikkenan, ina godiya k'warai, Allah Ya bar mana zumunci."

To cikin ikon Allah ba a sha wata wahala ba a wurin Idiris ba ya amince. Sahura ta kira ni a waya tana gaya mini na tura a d'auko yarinyar domin babanta ya amince tare da tabbatar mini da cewa ya yi farincikin hakan saboda shedar da ya yi mini yana da tabbacin yarinyarsa za ta samu ingantaciyar rayuwa."

Na ji dadin dawowar Yusura hannuna. Dama tun fil'azal yarinyar ta horu da aiki, shekararta goma sha hudu ta iya komai, sai dai ba duka nake sakar mata aikin ba, ina sanya mata hannu saboda yawan aikin ba irin wanda take yi ba ne a gidansu, na nan da yawansa. Ranakun da ba ni da girki kuwa, idan na fita na gaisa da matan gidan na koma wurina ba na sake fitowa, za mu dukufa aiki ni da yaran gabad'aya, lokacin makaranta da sallah ne yake tashinmu.
Kafin ki ce kwabo al'amurana sun 'bunkusa, duk sati sai na hada bacco na kaya sama da set talatin an kai Maiduguri. Tun ina lissafin dubu dari biyu uku hudu a cikin acct dina, sai na dawo lissafin miliyan. Al'amarin ya dinga ba ni tsoro da mamaki. Sai kawai na ajiye a raina cewa 'Allah ba yadda ba ya shirya lamarinsa'

Ranar da muka wayi gari da Azimi na farko. Baba Sule ya dira a gidan. Dama ya kan zo sa'i da lokaci da matsalarsa na d'auki kudi na bashi. Wannan karan kuma da buk'atar na saya masa kayan abinci ya zo, saboda wai Usaini ya gaya masa harkokina sun bud'e yanzu, gashi babu abinda na nema a gidan aurena, tunda dai kowa ya sheda gidan Alhaji Muntari da kulawa ta fanni abinci da suttura babu yunwa. A cewarsa neman da nake yi sai na wahalta musu tunda suna raye sai na samu lada."
Na riga na san son zuciyarsa sarai, idan ba haka ba mai zai sanya ya dinga zuwa yana cewa na bashi kudi, har binciken halin da nake ciki yake yi. Na dube shi a tsanake na ce." Baba ka koma gida in sha Allahu zan aiko muku da kayan abinci kai da Babanmu dama na yi niyyar hakan, amma don Allah ka dan rage zuwa, tunda ka ga ba ni kadai ba ce a gidan ina da kishiyoyi kada hakan ya janyo mini matsala."
Ya ce." To, zan rage zuwa idan kin san abinda ya dace, ni dana had'a auranki da Alhaji Muntari ai kamata ya yi ace ina da kaso a wurinki, amma sai na ro'ka k'i, ki dinga tunani"

Na ce." Ni fa ba wani abin nake samu da mutumin nan ba Baba, don Allah ka daina wannan maganar, duk alherin da nake yi muku daga aljihuna yake fitowa, saboda haka don Allah ka d'auke 'kafarka ba na so wani ya ta'ba muku mutumcinku."

Da kyar na rarrashe ya kama hanya ya tafi bayan na d'auki dubu biyar na bashi a matsayin kudin mota. Kwana biyar da zuwansa na gama had'a komai. Sai na fara tunanin yadda za a yi a fita da kayan domin kuwa matan gidan za su iya zargin na mijinsu ne na d'iba tunda yana ajiyesu da yawa. Da daddare aka shigo mini dasu lokacin kowacce tana wurinta, sai na yanke shawarar kawai a fitar dasu da daddare. Na kira Usaini a waya na gaya masa ya zo da adaidaita sahu ya d'auka kowa ya kai masa, na dora musu dubu talatin talatin akai.

Cikin rashin sa'a, lokacin da Usaini ya zo d'aukar kayan maigidan yana nan, tare da abokanansa a waje dama suna zaman shan ruwa idan sun yi asham sai su watse, abinda na cewa Usaini kenan bayan sallar asham zai zo. Minti goma da fitar Usaini ya shigo d'akin Muna zaune da yara gabad'aya a falo, ina yanka wasu riguna su kuma suna kallon tibi. Ya zauna kan kujera, suka dinga jera masa sannu da shan ruwa, ya amsa a takaice. Na daga kaina na dube shi. Babu fara'a, a fuskarsa, zaman da ya yi ya nuna yana buk'atar magana da ni, ga kuma yara.
Na dubi Yusura a nutse na ce." Ku je d'aki ku yi kallon a can tunda da tibi. Suka tashi da saurin na ajiye almakashin hannuna. Na ce."Barka da shan ruwa."
Ya dube ni. "Barka dai, wanene yanzu ya fita da buhunhunan shinkafa da su taliya?"
"Usaini ne k'anina su Baba na sayawa."
Ya zuba mini ido na minti daya kafin ya ce." A ina ki ka ga kudin sayan wad'annan kayan abincin Amina, rankatakaf fa komai akwai kayan sun tassama dubu dari uku a yadda rayuwar nan take tsada."

Dariya na yi na ce.'' Ka raina wannan sana'ar da nake yi kenan, wallahi da ita na saya domin neman lada."
Ya hade fuskarsa. " Gaskiya ban yarda ba, idan kin sayi wani abu da kudinki, to za ki ta'ba nawa da nake ajiye muku idan kin yi hakuri ma ai duk shekara ina fitarwa da surukaina abin bud'e baki."

Cikin zuciyata na ce' an zo wurin' Zuciya ba ta da 'kashi zaman da ya yi, sai da na hasashi zargi a fuskarsa.
Na ce." To, Allah ne dai shahidi kuma shine zai yi mana hisabi bisa zargin da ka yi mini, ba zan yi rigima da kai a wannan watan ba, amma na barka da Allah ."
Daga haka ban sake magana ba, na d'auki almakashina na cigaba da aikin gabana.
Jikinsa a sanyaye ya tashi ya fita bai sake ce mini komai ba.
Duk yadda na so na daure zuciyata na cigaba da kyautatawa mutumin nan kasawa na yi. Da na kalleshi zan ji haushinsa ya turnukeni. Zama fa kawai nake yi dashi, har yanzu ba na jin sonsa a raina amma shine yake ko'karin gaya mini magana.
Ya dinga raragefe neman shiri, na share shi, da kyar ya shawo kaina na ha'kura na sakar masa jiki yana ta fad'in shi fa ba zargina yake ba, kawai su'btar baki ce ya yi.....✍️
*Gudun aure 1k on talgram via 0542382124...Binta Umar gtbank*
*07084653262*
*GARKUWAR MATA*
*BINTA UMAR ABBALE*



*TALLA!*
🌲🌳🌿☘️
*DA MAGANI A GONAR YARO!!*
*08089965176*
*07084653262*
*Dayawa akwai matan da suke da matsala ta lalacewar nono yamushewa da kuma fad'uwarsa. Wasu ma 'yan mata ne basu kai ga matakin aure da shayarwa ba amma sai su samu matsalar faduwar nono. To gaskiya akwai magani sai dai kawai idan ba a yi dace ba. Wasu zasuyi ta faman kashe kudi amma buk'ata bata biya ba, wasu kuma zasuyi ta fargaba kada su je garin neman gira a rasa Ido, ma'ana su sayi abinda zai cutar dasu da kudinsu. Kuma yanzu dai tsakani da Allah rijalu sun riga sun gama nuna abinda suka fi karkata a kansa a jikin 'ya mace kirji da kuma baya. Wasu Allah ya hallice su dashi har ya yi musu yawa, wasu kuwa basu dashi kuma mai saurin zubewa ne. To mu dai duk wanda ya san maganinmu ya san ingantacce ne, kuma Yana aiki kwarai da gaske wurin dawo da daraja da martabar nono da izinin Ubangiji. Sahihin magani ne da ya samu sheda da lambar yabo, kuma Islamic ne da akayi masa hadi mai inganci domin gyara jikin mace ba ma iyakacin nono kawai ba. Babu nadama haka zalika babu dana sani da asarar dukiya wurin sayan maganinmu. In sha Allah matsalar ki zata gushe idan kin jarraba amfani dashi. Ba mu tsaya ina nan ba, muna da na gyaran hips sahihi dana k'iba idan kina fama da matsalar rama. Haka zalika muna dana tumbi, da kuma maganin sanyi mai mugun kyawun da yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye wanda zaku hadu da maigidanki kuyi amfani tare. Akwai ingantattun supplement wad'anda basu da illa balle su cutar da GARKUWAR jiki. Sai dai su gyara su kuma tayar da komad'a ina nufin inda ya samu nakasu a jikinki. Muna sayar da sabulan gyaran jiki dilka da man gyaran gashi, muna kuma bayar da sari a fad'in najeria da nijar muna tura kayanmu kowane gari da ikon Allah.*
*Muna garin kano duk inda kake za mu aika maka da kayanmu. Domin neman karin bayani sai a yi mana magana ta Whasap ga lambobin da za a same mu a kai.*
*07084653262 ko*
*08089965176*
*SIYAN NAGARI!!!!!!*
*A JARRABA A SAMU BIYAN BUKATA DA YARDAR ALLAH*
[11/27, 10:17 AM] Aunty B: *GUDUN AURE!!*
*NA*
*BINTA UMAR ABBALE 🍒*
*M.W.A*

TEEMAH DATA SERVICES MTN
1GB @550
2GB @950
3GB @1450
4GB @1550
5GB @1700
CHECK CODE *323*4#
VALIDITY 30DAYS
CHAT@08112392177
CALL @08037026306
8037026306 fatima musa ibrahim opay
*TALLAH!*
🛍️ “Ko ba ki da niyyar siya ba, ki zo ki shiga ki kalla kayayyaki — wallahi sai kin bude ido! Ballantana kuma nasan za ki tashi da kaya saboda kyau da araha.” ✨
🌸✨ “Shigo duniyar da kyau da jin daɗi suka haɗu — daga kyawawan laces na alfarma, Atamfa , abaya masu salo, zuwa kayan ado masu kyalli, kayan girki na zamani da sauran ƙarin abubuwa. A Meerah B Collection , muna adashen kayan kitchen daily 1k to pack 100k items weekly Monthly ✨🌸We are sale kitchen items, electronic, WE ALSO DEAL WITH CONTRIBUTE monthly weekly daily after 10 days for kitchen items or electronic gaba daya wanna package 60k nake had'a sa zaku iya mallaka ta hanyar adashi
https://chat.whatsapp.com/KXsuo5E7syZ879Gcid3wCm?mode=ac_t https://chat.whatsapp.com/KXsuo5E7syZ879Gcid3wCm?mode=ac_t

*1k on talgram via 0542382124...Binta Umar gtbank mutanan nijar dala dari katin Airtel. Ga masu karatu a arewa book akwai more peges domin na yi nisa a can din.*
*07084653262*
*08089965176*
*@arewa books*
*Bintuumarabbale.*
*Free pege*
*18*
Wannan ya wuce da wasu kwanaki wani abu bai sake faruwa ba, tunda Ina iyakacin bakin kokarina wurin ganin na fita hakkin maigidan da abokanan zamana a duk ranar girkina. Sosai Yusura take taimaka mini da wasu ayyukan, itama Iyami tana nata bakin ko'karin. Goman karshe hada-hada ta yi yawa. Ya Falmata ta sake jibgo mini wasu ayyukan tare da sharad'in ana buk'atarsu kafin sallah. Babu abinda nake hangowa sai ruwan kudin da zan samu. Wannan dalilin ya sanya na hana kaina sukuni bacci arziki ba na yi. Yanzu haka kekuna biyu gareni ni na hau daya Yusura ma ta hau tunda ta fara iya wasu abubuwan ina nuna mata. Kamalu da Yusi suna aikin jera stone's da sauransu.
Ranar girkina kuwa Iyami na sakarwa ragama duk da na san da cewa ba haka tsarin gidan yake ba. Iyakacinta shara da wanke-wanke, sai zuwa cefena da 'yan aike aike, amma ni kam har girkina na bar mata, muka yi da ita zan dinga bata dubu biyu kullum idan zata tafi. Ita kuma Yusura la'asar ta na yi zan tashe ta ta je ta feraye doya ta soya ita na dorawa alhakin hakan.
Anti Maimuna ba ta ta'ba tankawa ba ila iyaka idan an kammala ta zo ta dibi abinci. Babu korafi a tsakaninmu tana dannewa koda taga abinda bai yi mata ba, gashi dai itace uwargida amma bata neman fitina da kowaccen mu, dalilin da ya sanya ma kenan na sayi shadda mai tsada yadi goma sha biyar na bada yadi bakwai a dinkawa Kamalu da Yusi sauran Kuma nake da kudirin yi musu d'inki na gani na fad'a ita da Yusura duk da cewa maigidan ya yi musu kala uku Yusura da su Kamalu bai bambamta da yaransa ba, hakan ya sake ba ni karfin guiwar yi wa 'yarsa duba da irin kara da kawaicin da uwarta take yi mini, uwa uba kuma yarinyar tana kaunar Yusi sosai, komai ka ji tace Yusifa.

Yau bayan shan ruwa da kadan ina bandaki na ji sautin muryar Jamila a falona.
Da sauri na cud'a jikina na zuba ruwa na fito. A gurguje nake yi komai dalili girkina ne, ba na so kuma maigidan ya shigo ya riskeni a hargitse, dama na fahimci kwana biyu a wuya yake da ni, dalilin baccin da yake riskata ina yi bayan ya gama zaman majalisarsa ya shigo, duk ranar girkina baya samun wani Abu a wurina saboda mugun gajiyar da nake yi. Shiyasa yau na sauka daga kan keke da wuri domin ina so na faranta masa.
Tana tsaye sai fad'a take yi wa Yusura. Ita kuma yarinyar ta yi shiru idonta ya ciko da hawaye. Raina ya baci ainun. Na ce." Ke kuma menene haka don Allah za ki tasa yarinya a gaba kina fad'a mata wasu maganganu ko zamanki take yi ne a gidan?"
Ta kalleni kafin ta ce." Amma dai kin san abinda ki ke yi ba kya kyautawa, ya za a yi ki dinga bawa wannan yar yarinyar aikin da bata iya ba, idan ita Maimuna ba zata iya yi miki magana ba to wallahi ni ba ki isa ba, ba zai yiwu mu dinga cin abu da 'karni ba, domin koyaushe doyar da yarinyar nan take yi ba ta soyuwa zubarwa muke yi ni da yara, wallahi ba zai yiwu ba dole maigidan ya ji abinda yake faruwa domin tun wuri ya yi wa tufkar hanci."
Na ce." To sai ki bi shi ki gaya masa ai yana waje ba nisa ya yi ba, idan ya shigo sai ki sanya ya sake ni, ko ya kori Yusura tunda ta soya doya ba ta soyuwa ba."

Ta bude baki kenan za ta yi magana ya shigo. Ganinta a tsaye ya sanya ya ce." Da azimin ma sai kun yi mini masifa a gida, menene kuma?"

Ta fara gaya masa abinda ya kawota. Ya dube ni tare da cewa." Amina ba karya Jamila ta yi ba doyar nan bata suyuwa karni take yi yau ni kaina ban iya ci ba wallahi, bayan kunyar da ki ka ba ni a cikin abokai, ashe dama ba ke ki ke yin aikin nan ba?"
Shiru na yi masa ban tanka ba. Ya dubeta tare da cewa" Tafi wurinki zan yi maganin abin." Ta juya ta tafi ba ta sake cewa komai ba.
Yana shigowa falon na sake daure fuskata. Yaran suka tashi suka bar wurin.
Bai ce mini komai ba, ya wuce cikin kuryar d'aki. Minti biyu na ji yana fad'in." Ina ki ka ajiye mini dabinon nan dana shigo dashi kwanaki?"
A cunkushe na ce." Ka duba cikin doruwa."
Gabana ya buga da karfin gaske tuna abinda na ajiye a dorowar. Da sauri na tashi na shiga d'akin na same shi a tsaye hannunsa rike da kwalin maganin, daya hannun kuma robobin dabinon ne.
Jikina ya yi mugun sanyi. Kai a kasa na nufe shi.
Ya dubeni ya jijjiga kansa. Cikin mamaki da al'ajabi ya ce." Maganin hana d'aukar ciki a gidana Amina, Ashe ha'intata ki ke yi dama, ina ta wahalar banza wuri zuba kwaya-kwayena ke kuma ki sha magani su tsinke su bi rariya, dama da wannan nufin ki ka shigo mini Amina? me ya sa ki ka yarda da haihuwa da tsohon mijinki wanda bashi da ko kwabo sai ni da Allah Ya rufawa asiri ki ke gudun had'a zuri'a da ni bayan tun kafin mu yi aure na gaya miki ni mutum ne mai burin tara zuri'a."
Cikin sanyin jiki na ce." Wallahi ba haka ba ne, na yi hakan ne domin ni da kai mu huta, mu mori amarcinmu, amma mai zai sanya na guji haihuwa da kai bayan kana da nasaba, kuma Allah Ya rufa maka asiri, idan na yi haka ai na yi butulci ga Allah, don Allah ka yi hakuri."

Babu sassauci a tare dashi Ya ce." Watanki takawas a gidan nan Amina don Allah ki gaya mini amarcin da ki ka bari na ci dake, tun baki fi sati biyu ba a gidan nan ki ka daina ba ni kulawa, bayan kin san ni din namaji ne mai buk'ata, kin fi bawa neman kudinki muhimmanci, a gaskiya wannan lamarin ba

Please Login or Register in order to submit comment