Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

a yi mini wata fassara ne. Ni kuma akwai dalilin da ya sanya bana son tarayyarsu. Ban dai ta'ba gani da idona ba, kuma bai ta'ba yi mini ba,
amma a unguwar ana rad'e rad'in yaron yana d'auke-d'auke, idan kayi wasarare da abinka sai ya d'auka. Wasu lukutan ma yakan yi wa uwarsa ta kulle shi a d'aki ta yi ta duka.
Ina jin tsoron yau da gobe mu'amularsu ta canza mini yaro. Tunda Kamalu ko nawa zan ajiye a gabansa ba zai d'auka ba. Yana bud'e jakata ya d'auki kudi idan ina bacci ya dawo da canjin ya ajiye mini, idan na duba kudina na gansu cif a yadda suke. Wannan dalilan ya sanya na ke fargabar abotarsu.

Da yake idan na d'auki albashi abinci nake saya da d'an yawa. Dan sai na auno shinkafa kwano biyar na sayo 'karamin buhun taliya na auno garin towo. Da su mangyad'a da manja da hadin maggi. Da har buhun gawayi nake jinginewa, yau da gobe ta sanya na daina saboda idan na sa 'kafa na fita aiki sai na dawo naga an kwashe mini gawayin. Ba damar kuma na tambaya. Sai su ce na 'kala mu sata. Sai na daina sayan buhu nake aikawa gidan Mairo a sayo mini.

Dana gama abinci na zubawa Ashiru tunda shine k'arami a dakinsu. Ita kuma Ummansu Hadiza bata da k'ananun yara duk sun girma tunda itace uwargida. Amma dai dukda haka ina zuba mata itama.
To sai wajan biyu da rabi Babanmu ya Aiko musu da kudin abinci sannan Kowacce ta fara fafutukar abinda zata girka har zuwa lokacin Kamalu da Saminu Basu dawo ba. Raina ya baci ainun! domin lokacin makarantar allo ya kusa, ni kuma a rayuwata na tsani wasa da karatu ganin kamar shine gatan da za ka yi wa yaro, bayan haka kuma ni ma a yanzu karatun ne yake ri'ke da ni bayan d'inkin da nake yi....

Uku saura suka shigo gidan a firgice duk'un-du'kun 'kafafuwa da hannuwansu duk daud'a. Saminu ya yi d'akinsu da kud'i a hannunsa. Shi kuma ganina a bakin rijiya ina jan ruwa ya tsaya. Na kalleshi sama da k'asa kafin na ce." Daga ina kuke?"
Ya yi shiru bai ba ni amsa ba.
Saminu ya fito ya na cewa." Kai Kamalu ungo kudinka." Ya kar'ba da sauri yana fad'in." To ya na ga ka ba ni dari uku da hamsin, bayan gabad'aya abinda aka sayi kayan dubu daya da dari bakwai ne."

"E, Ummanmu ce tace mu bata aron kud'in. Zan cika maka sauran tunda tace gobe za ta bayar."
Cikin takaici na ce." Saminu yawon tsince tsince a bola kuke yi ko?"
"E, ai ni, na kwana biyu ina yi, shine Kamalu shi ma ya ce zai dinga bina. Idan mun samo k'arafuna sai mu kai kangon Adahama ya saya." Hankalinsa a kwance ya ba ni amsa.
Na girgiza kaina ban sake cewa komai ba, na d'auki botocina dana cika da ruwa na wuce na bar su a wurin. Kamalu Yana cewa ba zai kar'bi dari uku da hamsin ba.

Ban iya jurewa ba. Haka nan raina idan ya baci ban iya duka ba. Sautari akan fad'a mini duka ba zai tarbiyantar ba. Cikin wayo da dubara da ja ajiki ake ladabtar da zuriyar yaro. Hakan ya sanya na rage dukansa. Nake yi masa nasiha da kuma kawo masa misalai da hadisai. Amma a yau, raina ya 'baci sosai, na gaza ha'kuri sai da na bari ya sakankace tukkuna na rufe d'akina na kamashi da duka.
A lokaci Baba Sule ya shigo gidan. 'Kanin Babanmu ne. Ya zo ya tsaya bakin kofar d'akin Yana cewa." Amina an fad'a miki ki daina dukansa kin 'ki ji ko? Wato matan gidan saboda ba su suka haifeki ba shiyasa babu wadda za ta fad'a miki kiji. Dama tuntuni ina jin labarin abinda ki ke yi, kina yawo da mu a duniya kina cewa babu wanda yake taimaka miki dake da marayunki. To bari ki ji wad'annan yaran dole ne ki mayar dasu wurin kakarsu tunda tana raye, ba za su lalace a hannunmu ba, azo a yi kuka da mu. Wannan yaron Kamalu takad'iri ne, wa yasan abinda zai zama anan gaba tunda kowa baya furta alheri a kansa."
✍️
*GARUWAR MATA*
*BINTA UMAR ABBALE*
*07084653262*
[11/12, 10:23 AM] Aunty B: *GUDUN AURE!*
*NA*
*BINTA UMAR ABBALE 🍒*
*M.W.A*

*Marubuciyar*
*Yar bangar siyasa*
*Ba'aboren namiji*
*Madadi*
*Ga irinta nan*
*Goje*
*Babban yaro*
*Sadauki Omar*
*Nida Yaya sadam*
*Da sauransu..!*


'Yan uwa
Barkanku da zuwa FAMAS SCENTS OF LEGENDS,
duniyar turarukan wuta masu kamshi na musamman mai samar da nutsuwa da kwanciyar hankali.
Mun tanadar muku da turarukan wuta masu dadin kamshi kamar su
Sandal flakes
Hawee
Gabgab
Halut
Dorot
Coconut chips
Dufr(farce)
Black khumra
Brown khumra
White khumra
Oil perfumes da
Body sprays
Dan turara gidajenku,tufafinku da jikinku.
Ga duk mai buqata zai iya tuntuban mu ta lamba kamar haka
Call/WhatsApp
07037489958
Location:Gonan Ganye,zaria
Kaduna state
Nationwide Delivery

*3*
Na bude d'akin na fito ina kuka sosai na ce." Haba baba Sule wannan wace irin magana ce. Idan ba ku taimaka mini wurin kula da yaran nan ba ai ba za ku dinga furta munana kalamai a kan su ba. Wallahi ko kai ka ji abinda suka aikata sai ka yi musu hukuncu, a gaskiya maganganun nan da kake fad'a akan yaronan Kamalu sun yi tsauri da yawa."

Sai ya harzu'ka yana ce wa." Rashin kunya za ki yi mini don ubanki, ni za ki nunawa ban san abinda nake yi ba, an fad'a din Kamalu takad'iri ne ba ya ji, ko za ki musanta mini ne? yaron da kullum cikin d'auko miki magana yake, kaf zuri'armu babu fitinanne a can dangin ubansa ya samo wannan bakin halin. Akan ya je yana d'auko abin mutane ai gwara ya d'auki buhun ya tafi ya yi jari bola, ai sana'a ce, yara nawa ne suke yi, ko za ki gaya mini naki yaron ya fi na kowa, akan hakan ki ka zage karfi akansa kina dukansa, Murja ta yi mini bayanin komai, to wallahi idan ba ki yi wasa ba da kaina zan d'aukesu na mayar da su can wurin kakarsu su je su 'karata."

Cikin kuka mai cin rai na ce." To baba Sule duk mai ya kawo wannan maganganun? Wahalar nan wai wanene yake yi mini ita ne? yaran nan fa kwanciya kawai suke yi su tashi a gidan nan, duk d'awainiyarsu ni ce, na d'auka ai sai ana wahala da mutum tukkuna za a nuna gazawa akansa. A tsaye nake akansu ba zan iya bari su yi wannan sana'ar ba gaskiya magana kenan, Allah ma sai ya tuhume ni, tunda ya taimaka mini da yadda zany..... Ban yi tsammani ba na ji ya tsinka mini mari a fusace yana ce wa." Za ki nuna mini ba ni na haife ki ba kenan, tunda har zan iya fad'in Magana ki mayar mini da raddi, don ubanki ni ba kanin babanki ba ne, Ina ce ni ne na bada auranki ga uban yaran. Wato Ke har abada bakinki ba zai mutu ba ko?"
Ummansu Saminu ta ce." Ni abin ne ya ba ni mamaki Sule ashe duk zaman da muke yi a gidan nan, Amina ta na yi mana kallon sakarkaru wad'anda ba su iya tarbiya ba. Wato yanzu na gane nufin ki kina so ki janye yaronki a ganinki kamar ana so a lalata shi ko?"
Na ce." Ba haka nake nufi ba. Ni dai na ce ban yadda yarona ya yi jari bola ba, karatu nake so ya yi."
Baba Sule ya ce." To ke ma don ubanki gidan za ki bari aure za ki yi, ai ba a ce don ubansu ya mutu ki sarayar da k'uruciyarki ba. Tun wuri ki fito da miji ki yi aure." Ban ce masa komai ba na bar wurin zuciyata a cunkushe da tunani da fargabar mummunan kalubalen da yake fuskantoni.

Wannan ya wuce da kwana biyu wani abu bai sake faruwa ba. Kamalu ya ji fad'a da dukan da na yi masa. Ya rage wasu abubuwan mussaman da ya ga Baba Sule ya mare ni, sai ya dinga kuka a lokacin yana ba ni ha'kuri da al'kawarin ba zai sake ba.

***
Ranar juma'a da wuri suka yi wanka suka shirya tsaf cikin kaya iri d'aya hula da takalmi ma duk iri d'aya. Yusi ya kalle ni a sanyaye ya ce." Mama me yasa ba za ki je ba, don Allah ki shirya mu tafi tare."
Na ce." Yusi ba na jin dadi, zan bari zuwa wani satin idan muna raye sai mu je tare, idan kun je ku gaishe mini da Gwaggwo da kyau." Na kalli Kamalu dake tsaye a jikin bango sai 'bata rai yake yi, na ce." Kai na gane abinda ya sa duk lokacin da za ku je gidan Gwaggwo kake jin haushin saboda tana yi maka fad'a ko?"
Ya yi shiru bai ce mini komai ba. Na girgiza kaina tare da furta. " Ka d'auko ledar can shinkafa ce rabin kwano da taliya guda uku a ciki, ka kai mata, ungo wannan dubu biyu ce sai ka bata. " Ya kar'ba ya sanya a aljihu. Ya kama hanyar fita yana fad'in." Dallah malami taho mu tafi."
Da sauri na ce." Wallahi tallahi ka ci zalinsa a hanya sai ranka ya 'baci, muddin ka ta'ba mini yaro kasan karon mu da kai." Ya zum'buri baki ya fita."
Na kalli Yusi da yake ta walwala duk ranar da za su je wurin kakar tasu yana kasancewa cikin farinciki da nishadi. Sai na ji kwalla ta ciko mini a Ido. Yanayin sanyi da d'abi'a' sak mahaifinsa, mutum ne mai walwala da sanyi hali, baka ta'ba ganin fushinsa. Yusi kamar Yaya Aminu ya yi kaki ya tofar kamarsu d'aya.
Kamalu kuma wasu suna cewa da ni yake kama.
Na d'auki naira hamsin a cikin jakata nasa masa a aljihu ina fad'in." Idan ka ga wani abu a hanya ka saya. Ka yi kyau sosai
d'an saurayina."
Sai ya fashe da dariya yana cewa." Mama ki saya mini gilashi sannan ba ki fesa mini turare ba."
Da sauri na bude 'yar sif dina na d'auko turare ina fad'in." Kash an yi tuya an manta da albasa yarona d'an gayu ne."
Na fesa masa turare ko'ina a jikinsa. Na ce." Ku gaisa mini da ita da kyau."
Yasa takalminsa Yana cewa.'' To zan fad'a mata Mama zan ce sai wani satin za ki zo." Ya kama hanyar fita da sauri.
Na janye idona, a sanyaye na zame na kwanta kawai sai wasu hawaye masu d'umi suka fara sulmiyowa suna bin kumatuna. Ban yi yun'kurin gogewa ba tunda ni kad'ai ce a d'akin. Kukan kuma shi zan yi na samu sassaucin cunkusar da zuciyata ta yi. Abu biyu ne suka tarar mini. Duk lokacin da zan yi al'ada na kan kasance cikin k'unci da 'bacin rai. Sai kuma matsaltsalun da nake fuskanta. Matsalar Kamalu itace ta fi damuna a halin yanzu ba ni da wanda zai taya ni a gidan. Duk wanda zai bud'e baki sai ya ce masa fitinanne. Na san illar baki domin ana cewa har ya fi maita. So nake yi ni da yara mu yi nesa daga gidan da unguwar gabad'aya domin mu canza wata rayuwar, amma yin hakan ma kalubale ne mai zaman kansa.

Na 'kudindine a cikin mayafi na ci kukana na k'oshi. Cikin zuciyata na dinga nanàta addu'ar nan (Rabbi Inni Lima Anzalta Ilayya Min Kairin Fa'kir) ina ta kiran Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un! Har Allah ya sassauta mini k'uncin da nake ji a raina. Na tashi na juye ruwan wankan dana d'ora.

A gurguje na yi wanka na shirya jikina tsaf. Lokacin na dan ji sassauci ciwon marar da ya matsanta mini kasancewar abin ya fara zuba. Na shirya na fito duk suna cikin d'aki. Na kulle 'kofata. Sannan na tsaya kowacce daga bakin kofarta na yi mata sallama.
Har na kai bakin kofar fita Ummansu Hadiza ta kira ni.
Na shiga na sameta tana d'aura dakakken yajin da take sayarwa na daddawa dana barkono. Ta ce." Ina ta zuci-zucin yi miki magana gashi kuma kin shirya za ki fita, Ina za ki je ne? Na ga an yi hutun makaranta ko kayan d'inki za ki sayo?"
Na ce." A 'a ba kasuwa zan je ba, gidan Sahura zan je."
Sai ta ce." Ayyo, to dama babanku ne ya ce na fad'a mini za ki yi ba'ko yau, Alhaji Mutari ne ya ce yana sonki da aure."

Cikin fad'uwar gaba da tsananin tashin hankali na ce." Wanene kuma Alhaji Mutari Umma sai kuma akace masa ni aure zan yi, ko ni kad'ai ce bazawara?"
Ta zuba mini ido na minti biyu kafin ta ce." Matsalarki kenan Amina rashin tauna magana, ni sa'arki ce da za ki ba ni amsa cikin gatsali."
Na sassauta fuskata na ce." Umma zancen ne na ji shi kamar saukar aradu wallahi, ki yi hakuri don Allah."
Ta ce." Alhaji Mutari Ubangidan Babanki Sule shine ya nuna masa hotonki, shi kuma ya yi Allaragaf dake."
Na ce." To ba za ta yiwu ba, Umma ba aure zan yi ba, tarbiyar yarana ce a gabana a yanzu, kuma ko zan yi aure ni zan duba mijin da zan aura wanda ya cancanta babu ruwana da dukiya nagarta nake nema kamar dai Yaya Aminu, in sha Allahu zan samu."

Ta ce." To, ni dai na isar da sa'kona Amina, amma ki yi nazari sosai akan maganar kafin ki yanke hukunci."
Na yun'kura na tashi ina cewa." To zan yi, in sha Allahu Umma sai na dawo."
Ta ce." Ki gaishe da Sahura da yaranta." Na kama hanya na fita ba tare da na sake cewa komai ba tsabar tashin hankalin da nake ciki.

Cikin zullumi da tunani mai zurfi na isa gidan Sahura. Na same ta tana shirin fita. Ganina a hargitse ya d'aga mata hankali.
Na nemi wuri na zauna kawai sai na rushe da kuka!
Ta kid'ime ainun! Ta rirri'ke ni tana fad'in." Sis menene don girman Allah ki yi shiru kada ki jazawa kanki lalura, ba fa ke kad'ai ba ce, kuna nan da yawa iyayen marayu, kuma ki godewa Allah da ya ba ki sana'ar da za ki yi d'awainiya da yaranki, wallahi akwai wad'anda aka mutu aka bar musu marayun ba su da yadda za su yi, wasu ma sai sun yi bara da ro'ko suke samun abinda za su ci, ni kaina da nake da mijin kullum cikin fafutuka nake, kin san komai ba sai na fad'a miki ba, Abbansu Yasir bashi da tartibiyar sana'a, kasuwa yake shiga Yana tare mutane idan an yi katari sai ya kai su shagon da suke nema, da haka fa yake samun abinda zai kawo gida, ki yi hakuri ki godewa Allah, ki kuma cigaba da yi wa Mijinki addu'a, Allah Ya gafarta masa."

Hannu nasa na goge hawayen da yake zuba. Na ce." Na san Allah Ya yi mini Sahura, ba zan butulce masa ba, yana taimakona ta fannoni da yawa. Amma sis ina da damuwa sosai, ba zan iya aure yanzu ba sai yarana sun yi 'kwari, sis Baba Sule kwana biyu ya sani a gaba, ga Kamalu Yana nema ya fi 'karfina."

"Wace irin magana ce wannan Amina, ki haifi 'dan a cikinki sannan ki ce yana nema ya fi karfinki, me yake yi? kuma me Baba Sule yake yi miki, na ga dai ke kike hidima da kanki da yaranki, na d'auka ai ba ki da wani kalubale da mutanan gidanku."

Naja majina cikin jin ciwon abubuwan da suke faruwa na fara bata labarin abinda ya wanzu kwanaki biyu da suka wuce.
Ta ce." Ki yi hakuri, kada damuwar hakan ta janyo miki ciwo, aure dai a yanzu sai kin yi ra'ayi za ki yi tunda dai ke ba yarinya ba ce, bazawara ce muddin za ki ri'ke mutumcinki ki cigaba da sana'arki domin ki kula da yaranki, Ubangiji zai shige miki gaba, ki yi ta addu'a dai, sannan maganar Kamalu kada ki dinga yi masa kuka domin hakan zai sake jefa shi a garari, ki yi ta yi masa addu'a. In sha Allahu lamarin zai tsaya iyakacin 'kuruciya, kuma wallahi irinsu idan sun girma ba su iya hankali ba. Suna da biyayyar iyaye. Kowane yaro da irin 'kuruciyarsa.

Zuciyata ta sassauto sakamakon irin rarrashi da tausasan kalamanta. Sahura k'awata ce tun ta k'uruciya tare muka dinga fa'di tashi muna 'yan mata. Daga gidansu na samu taimako sosai a harkar karatuna. Sai dai ta riga ni aure har sai da ta yi haihuwa ta biyu tukkuna Abbansu Yusi ya yi fito da zummar aurena.

Ta ce." Tunda kin zo na samu abokiyar tafiya dama ba na son zuwa ni kad'ai wallahi, duk da hakan ba wani abu ba ne, amma dai bibiyu tafi dadi.
Na kalleta cikin nazari sai a lokacin ma na hangi ramar da ta yi, yanayinta ya nuna tana cikin damuwa.
Na ce." Da Ina za ki je ne?" Ta sauke ajiyar zuciya a sanyaye ta ce." Hotoro zan je sabon kamfanin Alhaji Tajo na leda suna buk'atar ma'aikata. Maman Anisa makociyar nan tawa ta kar'bar mini form a wurin mijinta kin san shi ma yana aiki a 'karkashinsa amma dai Yana da matsayi ba 'karamin ma'aikaci ba ne, to shine suke neman ma'aikata da na gayawa Abbansu Yasir ya amince, yanzu na cike form din zan je na kai wata'kila ma a yi mini interview."

Idona a kanta har ta ajiye maganar. Na ce." Sahura ba wai zan dakile ki ba, don Allah kada ki yi aiki a kamfanin nan, ki cigaba da neman aiki na gomnati, ni ma zan cigaba da nema miki har Allah Ya sa a dace, amma hankalina bai kwanta ba wallahi tunda Abbansu Yusi ya yi aiki a kamfanin mutumin nan aka zalince shi nake jin tsoro. Kin san suna amfani da lafiya da kuzarin mutum ne, duk wahalar da za ka yi musu da lafiyarka daga ranar da Allah Ya jarrabeka da ciwo ka kwanta sai suce ba su san wannan ba, 'karshe a rubuto maka takardar sallama kuma babu ko sisi."

"Amina ni kaina akan dole zan yi wallahi, na fad'a miki tun farko Abbansu Yasir ne ya cuce ni, farkon auranmu na samu aikin rabon magani 'kauye-k'auye ya ce ba zan yi ba saboda mugunta. Gashi kuma yanzu muna nema Ido rufe dalilin hidimar gida da ta Yara tunda shi ba k'arfi ne dashi ba, wallahi idan lokacin biyan kudin makaranta ya yi hankalina yana tashi Amina, wasu lukutan Ina ji ina gani za'a koro mini Yara daga makaranta. Kin ga kuwa idan Ina aikin zan samu hanyar da zan dinga biya musu da yin wasu hidindimun babu fargaba."

Na ce." To yanzu kina da tabbacin idan mun je za a d'auke ki, wulakanci nake gudu Sahura, shiyasa ki ka ji ina wannan maganar wallahi."
"A a ai ina da hanya kai tsaye muna zuwa zan kira wayar mijin Maman Anisa d'in tunda shi ya kawo mini form din, in sha Allahu ba za a samu matsala ba."
Na gyad'a kai tare da cewa." Daga nan ja'in zuwa hotoro nawa za ki kashe Sahura, kuma nawa ne kud'in albashinki komai fa d'an lissafi ne?"
Ta ce." Gaskiya ba zai haura dubu saba'in ba, bayan haka kuma an ce sa'i da lokaci yana yi wa ma'aikatasa alheri, har da su kayan abinci Yana bayarwa."
Na ce." To ni dai tsayin shekara biyu da Abbansu Yusi ya yi aiki a k'arkashinsa bai ta'ba gaya mini ya samu wani abu ba bayan albashinsa. Kin ga fa koda aka sallame shi ma fa ba'a bashi ko kwabo ba."

A sanyaye ta ce." Zan dai jarraba na gani Amina, idan na ga babu ci sai na ajiye, don Allah ki taya ni da addu'a, ki kuma cigaba da nema mini wani aikin ko koyarwa ne irin naki."
Cikin kulawa na ce." In sha Allahu rabbi, zan taya ki da addu'a kawata, zan kuma cigaba da yi miki fafutuka, Ubangiji Allah Ya sa mu dace gabad'aya."
✍️
*GARKUWAR MATA*
*BINTA UMAR ABBALE*
*07084653262*
[11/13, 9:30 AM] Aunty B: *GUDUN AURE!*
*NA*
*BINTA UMAR ABBALE 🍒*
*M.W.A*

*Marubuciyar*
*Yar bangar siyasa*
*Ba'aboren namiji*
*Madadi*
*Ga irinta nan*
*Goje*
*Babban yaro*
*Sadauki Omar*
*Nida Yaya sadam*
*Da sauransu..!*

*Tallah!*
Albishirinku mata 'yan gayu yan gwalisa ku yi maza kugar zayo shagon
(Aysha/Addah beauty saloon and spa).
Shin kin taba zuwa ingancaccen saloon din Aysha/Addah, idan baki taba zuwa ba ki yi maza kar a barki a baya domin sun qware a wajen aikinsu wanda suke services dinsu cikin sauki tare da annasuwa
Suna wanke kai(wash and set)
suna wanke qafa(pedicure)
And sunayin steaming iri iri suna saida (supplements)suna kitso dama duk wani abu daku so Wanda akewa mace ta amsa sunanta mace yar qwalisa
Address dinsu nanan a Federal low-cost opposite open University *GOMBE STATE*
Ko kuma ku tuntune mu a wannan number kamar haka,
08037925676
Or
08167764242
Whatsapp ko kuma Call we’r available 24/7..
Tabbas ni ma na shaida ingancin ayyuka da kayayyakin shagon anti adda mutuniyar kirki. Babu tsada komai ana samunsa cikin sau'kin farashi mutanan gombe kada ku bari wannan sau'kin ya wuce ku.🥰

*@Arewa books*
*Bintaumarabbale.*
*Free pege4*
Ba mu fita ba sai da yaran suka dawo daga cefane tukkuna. To abin dai gashinan a hannu a hannu. Na ce." Yanzu Sahura shinkafa gwangwani biyu ce zata ishe su har su uku?" Tana gyara zaman hijabin wuyanta ta furta." To ya zan yi Amina, babansu da wuri ya fice don ma kada na tambaye shi kudi, ko sallama bai yi mini ba. Jiya dai da daddare na gaya masa zan fita. Wallahi dubu dayan kenan ta rage mini na ba su suka yo cefanan nan. Kudin mota kuwa dama cewa na yi zan kar'ba a a wurin Maman Anisa, idan na samu daga baya sai na bata.
Na dubi Yusra dake juye shinkafar a faranti domin tsincewa. Na ce." Tashi ki je ki auno kwana daya sai ki dafa muku yadda za ta ishe ku. Ki karo man'kuli da maggi da wake." Na zuge jakata na d'auko dubu biyar na mi'ka mata." Duk abinda babu ki saya a ciki." Sahura ta yi sakato tana kallona. Na tashi ina fad'in." Wannan rayuwar Allah Ya magance mana. Ta ce." Sis, anya kuwa ina lefin ki bata kudin rabin kwano."
Na ce." Don Allah kada ki bata mini rai Sahura." Yadda na fadi maganar cikin fushi shi ya sanya tayi shiru da bakinta ta juya kan yaran tana cewa.'' Yusra ki rufe gidan idan mun fita, duk wanda zai k'wankwasa kofa kada ki bude, ki ce bana nan."
Ta ce." To Ummi sai kun dawo."

Ba mu wani jima a bakin titi ba muka samu abin hawa. Ya ce sai dai mu bashi dubu daya da d'ari shida duk mutum daya d'ari takwas kenan. Na ce." Sahura shiga mu tafi a hakan ya yi mana adalci, tunda gaskiya tsakanin hotoro da ja'in akwai tazara mai tsayi.
Wajan d'aya saura muka isa. Ya ajiye mu daidai bakin kamfanin duk da sabo ne hakan bai hana masu sana'ar adadaita sahu saninsa ba idan an yi duba da shuhurar mamallakinsa.

Masu tsaron wurin ba su bari mun shiga kai tsaye ba sai da ta yi musu bayani ta fito da takardu ta nuna musu tukkuna suka bari muka shiga. Wurin ya yi sosai an ka'wata shi ga ko'ina a tsaftace ma'aikata na ta shawagi tare da tashin sautin injina.
Sai dibi dibi take yi tana zare Ido. Na ce." To Sahura ina zamu nufa ne yanzu?"
A rikice ta ce." Bari na kira Abban Anisa a waya."
Na yi shiru ina kallonta ta d'auko wayarta ta kira shi bai daga ba har sau biyu.
Jiki a sanyaye ta ce." Kin ga bai daga ba."
Na ce.'' Na ji, wata'kila ko yana wani uzurin ne, kin ga yanzu lokacin shiga massalaci ne. Mu bari an jima kad'an sai ki sake kiransa."
Muka je muka samu wani wuri muka zauna muna tattaunawa. Wani ma'aikaci da uniform ajikinsa irin na tsaro ya zo ya tsaya akanmu fuska a daure Ya ce.'' Me kuke yi anan?"
Da sauri ta ce." Form din da aka ba ni na cike shine na kawo, ina neman Sulaiman sha'abu ja'in." Ya yi jim na minti biyu kafin ya ce." Ba anan yake dindin din ba. Amma yana iya zuwa da kowane lokaci. Ku tashi ku shiga cikin nan akwai wad'andasu a ciki irinku." Yadda ya fadi maganar cikin izgili shine ya bata mini rai.
Na ce." Ranka ya dad'e. Ubangiji shi ya karrama dan'adam, ya kuma fifita shi akan kowace hallita. Kaga kuwa wani mahalu'ki bai isa ya

Please Login or Register in order to submit comment