Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

zanji baƙin cikin wannan abin."

Ta ce "Eh mana."

Ibrahim ne da Muhammad su ka shigo bakin su ɗauke da sallama su ka ce
"Assalamualaikum"

"Waalaikumussalam" su ka amsa ma su.

Su Rashid da gudu su ka tarbi mahaifan su amma abin mamaki Ibrahim Rufa'i kawai ya amsa wa sannu da su ke ma sa shida Ma'aruf.

Ma'aruf ya ce "Abba sannu da zuwa."

Nan ma shiru Ibrahim ya yi ma sa.

Muhammad ya ce "Wai Ibrahim mene ne haka, baka ji sannu da Ma'aruf ke ma ka bane?."

Ya ce "Yaya ban ji ba ne ba."

Ma'aruf yi ya yi kamar zaiyi kuka sai Muhammad ya ce "ma sa yazo."

Maryam ranta ba ƙaramin ɓaci ya yi ba amma haka ta share shi.

Ya ce "Balkisu sa ka min abinci na."

Ta ce "Gaskiya ba na iyawah saboda cikina ciwo ya ke min ka ce wa Maryam ta haɗa ma."

Ya ce "Maryam haɗa min abincin."

Tashi ta yi ta yi tafiyar ta ta bar su nan a dainnin ɗin.

Sakin baki su ka yi ga baki ɗayan su .

Rashid sauka ya yi daga jikin Muhammad ya ce "Abokina mu je in da Umma."

Shima Ma'aruf sauka ya yi su ka yi tafiyar su in da Umman su.

Muhammad ya ce " Wai Ibrahim me ya sa har yanzun kai yaro ne, yanzun dan Allah wulakanta yaron nan na ta da ka yi a gabanta daidai ne ehhe?."

"Nifa Yaya ban kula da shi ba ne"

Amina ta ce "Wallahi Ibrahim ban taɓa ce ma ka ƙarya ka ke ba, amma yau kam zan faɗa wallahi ƙarya ne, ka ce wai baka ganshi ba."

Ya ce "Wai dan Allah a kan wannan yaron ne kowa zai zo ya na gaya min Magana."

Muhammad ya ce "Toh fa ko ramawa za ka yi?."

Balkisu ta ce "Ibrahim ka min shiru dan Allah duk kunci ka min kunne da surutu."

Shiru Ibrahim ya yi bai sake magana ba.

Amina ta ce "Innalillahi wa'inna ilaihin raji'un Maryam kin banu, tashi ta yi ita ma."

RASHIDA


By
Sha'awanatu Faruk diggi ✍️ ✍️
Wtspp 08084277827☎️

11

📝
Muhammad ji jiga kan sa kawai ya yi shima ya bi bayan Amina.

Sallama ya yi. "Assalamualaikum"

"Waalaikamussalam." Amina ta amsa.

Ya ce. "Maman yara mai ya sa ki ka tawo ba a gama cin abincin ba?."

Ta ce. "Wallahi Maryam na cikin matsala sosai, shi ne ke wayan sa ka ta ciwo kenan amma ba ta faɗa min ba."

Ya ce. "Ban fahimci zancenki ba."

Ta ce. "Abin da na ke wa Ibrahim gudu kenan ga shi ya faru."

Ya ce. "Amina ki faɗa min yan da zan fahimci maganar ki."

Ta ce. "Ta asirce Ibrahim sai yan da ta yi da shi dan Allah ku ta ya shi da addu'a, ni dai zan ta ya Maryam in sha Allah."

Ya ce. "Ai ba yau ba na ke ganin Maryam cikin wani hali, kawai saboda ta na jin nauyi na ne ya sa ban yi mata magana ba."

Rashid ne ya zo da gudu ya ce. " Mama Mama Umma ba ta da lafiya sai kuka take yi."

Barin ɗakin Amina ta yi, da sauri Muhammad ya riƙe hannunta ya ce. "Ki bi a hankali kar ki ji ciwo kema."

Ta ce. "Toh".

Sakin ta ya yi amma duk da haka sai da ta haɗa da gudun.

Ɗakin Maryam ta je ta tarar da Maryam a kasa sai kuka take gata riƙe da kanta .

Ta ce. "Maryam mene ne haka, idan ki ka hallaka kanki fa, kuma gaki da ciki, haba dan Allah ki yi hakuri ki barwa Allah komai shine zai saka maki, ba wani ba ke dai addu'a ne ta ki."

Ta ce. "Amina na shiga uku tun auren nan na Ibrahim ban da kwanciyar hankali, kullum da abin da zai min wallahi na ga ji gidan mu zan ta fi."

Ta ce. "Haba Maryam kenan ta yi galaba a kan ki?, ki yi aiki da hankalin ki ba zuciyar ki ba."

Ta ce. "Amina Ibrahim ba ya sona kuma ba ya son yaron ki, ai idan bai soni ba toh ya so yaronki amma mu duka bama samun hakan."

Ta ce. "Maryam ki yi hakuri zan ta ya ki da addu'a in sha Allah, na san Mama tana can tana ta ya ki da addu'ar in sha Allah zai dawo dai dai kamar yadda ki ka san shi."

"Toh" kawai Maryam ta ce.

Jikin ta Amina ta taɓa zafi ta ji sosai ta ce. "Maryam ba ki da lafiya ne har haka?."

Ba ta tanka mata ba kawai kai ta ɗaga mata.

Ta ce. "Rashid ya je ya kira Abban su yazo ya duba Umman ku."

Da gudu su ka fita a ɗakin sai part ɗin Balkisu.

"Assalamualaikum."

"Waalaikumussalam."

"Momy wai Mama ta ce Abba yazo ya duba Umma."

Ta ce "Baya nan sai ya dawo."

"Toh" su ka ce

Fita su ka yi sai ɗakin Umman su.

Mama ta ce "Mai ya ce ne?."

Su ka ce.
"Wai cewa ta yi baya nan sai ya dawo, kuma Mama mun gan shi a zaune."

Mama ta ce "Zaune fa ku ka ce?."

"Eh" Mama

Ta shi ta yi ta je ta kira Muhammad ta faɗa ma sa halin da a ke ciki.

Ran Muhammad ya ɓaci sosai ɗakin ya nufa, ya na zuwa ya wankawa Ibrahim mari har sau biyu ya ce.

"Ibrahim ka na da hankali kuwa ehe, maike damunka ne da za ka hallaka ƴar mutane?."

Amina ta ce. "Na shiga uku Daddyn yara dan Allah ka yi hakuri, wallahi da na san abin zai kai ku haka da ban faɗa ma ka ba."

Muhammad ya ce "Za ka bani amsa ko sai na ci uban ka a nan ne?."

Ya ce. "Yaya ka yi hakuri ni wallahi ba na son ta ne."

"Baka son ta fa kace Ibrahim?."

"Eh" Ibrahim ya faɗa .

Amina ta ce. "Innalillahi wa'inna ilaihin raji'un, Ibrahim kai ne wai kuwa gaskiya ba kai ba ne, Ibrahim da na sa ni mai son Maryam sosai."

Maryam da ke ba kin ƙofa ta ce. "Ai na sa ni Ibrahim ba sai ka faɗa masu ba, kuma na gode sosai da sakayyar da kai min."

Cikin kuka ta ke maganar abin tausayi.

Muhammad fita ya yi ya kira Inna ya faɗa mata duk abin da ke faruwa.

Inna ta zo ta ɗauke shi da mari ta ce "Sha-sha-shan banza mutumin banza, toh yadda ka yi mata nima na san za ka iya yi min shi."

Balkisu ta ce "Wai wane irin wulaƙanci ne wannan, a ga ba na a zo a na ciwa mijina mutunci toh wallahi ba zan yarda ba."

Mari ta ji a kuncenta da sauri ta dafe kuncin na ta .

Muhammad ne ya ce "Duk wulaƙancin ki ya tsaya a kan shi, idan ki ka ce za ki wulakanta, mahaifiya ta a ga ba na, toh wallahi komai zai iya faruwa."

Amina ta yi saurin riƙe shi ta ce. "Haba Daddyn yara bafa muharramar ka ba ce ba fa, kuma har ka iya ɗaga hannu ka dake ta?."

Wayar Maryam ce riƙe a hannun Rashid kiranta a ka yi sai kawai Rashid ya ɗaga kuma bai yi magana ba.

Maryam ta ce. "Dan Allah Yaya ka yi hakuri in dai a kai na ne wannan abin ke faruwa, wallahi na warware sosai jiki na ya ji sauƙi dan Allah mu ta fi."

Ya ce. "Maryam mu je part ɗin Inna zan yi magana da ke."

"Toh" kawai ta ce.

Fita ya yi itama Maryam bayan shi ta bi.

Inna ta ce "Ka sa me ni a ɗakina ina jiran ka."

Sannan su ka fito ita da Amina.

RASHIDA

PAGE NA 12

BY
SHA'AWANATU FARUK DIGGI✍️
WhatsApp number08084277827 ☎️

12

📝
Tashi ya yi da niyyar fita ta ce "Ina za ka je ne?."

Ya ce "Zan je wajen kiran Inna ne."

Ta ce "Ba za ka je ba."

Ya ce "Toh shi ke nan."

Zama ya yi sai bacci.

Kiran hajara ta yi ta ce "Hajara wallahi bokan aikin shi na kyau, ga shi sai juya dan iskan nan na ke yi, yanzun kuɗin sa na ke son na fara ɗibawa."

Ɗaya bangaren ta ce "Ai Balkisu gara ki juya ɗan iska, ai shi ma ya san ruwa ba sa'ar kwando ba ne."

Ta ce "Ke dai bari yanzun haka ana kan wata dirama a gidan nan, kuma ba zan ba shi hanyar zuwa can ba."

"Hahaha kai ƙawata shegiya ce ke wallahi."

Ta ce "Balkisu wai ya maganar ƴar iskar kishiyar nan taki ce, har yanzun ta na nan da addu'ar tan ne."

Ta ce "Ai ki barta wallahi ba zan kya le ta ba, kuma ba zan kyale yaranta ba, saboda suma ina jin kamar kishiyoyina ne."

Hajara ta ce "Gaskiya ne kinsan da zafi zafi a kan duke ƙarfe."

"Gaskiya ne kam" cewar Balkisu

Sallama su ka yi.

Amina ji ta yi cikin ta na mata ciwo amma ba ta yi magana ba.

Maryam ta ce "Amina meke damunki ki ne naga kamar ba Kya jin daɗi?."

Ta ce "Maryam cikina ne na ke jin yana min ciwo sosai."

Inna ta ce "Ayya ko naƙodan ce?."

Muhammad ya ce "Naƙoda kuma Inna cikin wannan halin."

Amina ta ce "Maryam dan Allah ka ma min na tashi zan je ɗakina."

Ta taimakon Maryam Amina ta isa ɗakinta.

Tana shiga ɗakin cikin ikon Allah ta haihu lafiya.

Maryam da gudu ta yi part ɗin Inna ta ce "Inna Amina ta haihu."

Inna ta ce "Yanzun idan kika ji ciwo fa wannan gudun haka."

"Inna wallahi ina murna ne ban san yadda zan yi ba, saboda farin ciki ƴa mace fa ta haifa."

Muhammad ya ce "Kai Maryam ki rage wannan abin, yanzun idan kika hallaka min ƴarinya ko yaro fa?."

Cikin jin kunya ta ce "Yaya yi hakuri wallahi ina son ƴa mace ne sosai da sosai."

"Ya ce "Toh Allah ya baki mai albarka."

Ta ce "Ameen Yaya na gode sosai."

Tashi su ka yi zuwa in da Amina ita da Balkisu su ka tarar zaune.

Balkisu ta ce "Maryam ko baki faɗa min ba toh na ji sai hakuri."

"Amma Balkisu yanzun nake da niyar kiranki, kawai dai na kira su Inna ne."

Ta ce "Amma ai na ga kamin ki kai ga resu sai kin wuce ni."

Maryam ta ce "Amina meki ke bukata yanzun?, dan Allah ki yi hakuri kwanciya nake son na yi."

Ibrahim ne ya shigo Inna ta lallai Muhammad ya ce

"Ibrahim Ina ki ran da Inna ta yi ma ne, ko kafi ƙarfin zuwa ne?."

Ya ce "Ni fa wallahi na gaji da wannan abin, kullum ana takurawa mutum."

Inna ta ce "Ai sai ka koma in da ba'a takura ma."

Su Ma'aruf ne su ka shigo ɗakin su ka ga jariri, sai Ma'aruf ya ce "Laa Mama waye ya haihu?."

Balkisu ta ce "Ai Mamarka ce ta haihu."

Rufa'i ya ce "Laaa wallahi Mama ta na da kyau sosai."

Rashid ya ce "Umma sai yaushe za ki haifa min ƙanwa ne?."

Umman ta shi ta ce "Yarona sai lokacin fitowar shi ya yi."

Ya ce "Shi ke nan."

BAYAN SATI ƊAYA

Anyi suna yarinya ta ce sunan Goggonta A'ishah ma sha Allah.

Har da A'ishah ta zo sunan dan sun dawo da tafiyar ta su ka yi .

A'ishah ta ce "Aunty Maryam wai Aunty Balkisu nan na da hankali?."

Ta ce "A'ishah saboda mii za ki kirata da maras hankali, kin ganki idan Yayanki ya ji ki, toh wallahi sai kunyi faɗa tam."

Ta ce "Yanzun aunty Saboda na ce mata maras hankali shine za mu samu matsalar?."

Ta ce "Eh sosai ma."

"Allah ya kyauta" kawai A'ishah ta ce

Amina ce ta kira Maryam ta ce "Ta zo ta karɓi A'ishah."

A'ishah ta ce "Wallahi aunty ni zan karɓe ta, saboda yanzun ba zama na ke ba tafiya zan yi na barki da ita."

RASHIDA

SHA'AWANATU FARUK DIGGI ✍️
WhatsApp number0808427727 ☎️

13

📝
"Toh shi ke nan ɗauke ta ɗin ba damuwa."

"Yauwa aunty na."

Wata yarin ce tafi toh rike da lemo ta ce "Mama wai ina so Yaya Rashid ne?."

Umma.
"Su Rashid na can lambo."

Mama.
"Ba ki iya gaisuwa ba ne?."

"Na manta ne ina wuni Umma."

Umma.
"Ba damuwa yi tafiyar ki ƴar albarka."

Mama.
"Wallahi aunty na rasa laifin me na yi
wa Allah da ya bani wannan yarinyar, bata dubin kowa da idon rahama, aunty wallahi har mahaifin ta bata bari ba, ya yi dukanta har ya gaji ya daina."

Umma.
"A'ishah ki yi hakuri kici gaba da yi mata addu'a in sha Allah za ta nutsu da yarda Allah, ki yi addu'a ki riƙa yawan yin sadaka, shi ma ya riƙa fitar da Zakka in sha Allah,Allah zai cire mata wannan abin."

"Toh shi ke nan aunty na gode sosai, shi ya sa nake son faɗa maki damuwa ta saboda kina bani shawara mai amfani."

"Hahaha toh ai nima yarinya tace saboda ai dole zan baki shawara, saboda nima ban san wace irin yarinya zai ban ba ko yaro."

"Na gode sosai Allah ya saka da alkairi Allah ya mayar maki hankalin Yaya."

"Ameen".

Inna su ka ji a bayan su ta na faɗin toh mata da miji ai sai ku tashi kuje dubin Balkisu, ta haihu amma bakwa wajen.

Umma ta ce.
"Inna me ta haifa ne?".

Inna.
"Yarinya ce".

"Toh ma sha Allah."

Tashi sukayi dan zuwa in da Balkisu.

"Assalamualaikum".

"Waalaikumussalam".

"Balkisu a she kin haihu bamu sa ni ba, muna can muna shan fira."

Balkisu.
"Ai dole zaku barni ni ɗaya tunda ni ba sona ake yi ba daga ke har su Innar."

A'ishah.
"Dakata Balkisu karki sa ke ki zagi mahaifiyata a gabana, dan wallahi na fiki rashin mutunci, idan kika sa ke zagin ta wallahi sai naje har gidan tsofinki naci mutuncin su."

Balkisu kuka ta saka ta ce.
Yanzun A'ishah ni kike zagi saboda nace Maryam ta kawo min ruwa."

Ibrahim.
Ya kwashe A'ishah da mari sai da ta yi tingil tingil za ta faɗi.

Umma ta ce.
"Haba Abban yara mene ne haka daga faɗan gaskiya sai duka, Inna ce fa take ciwa mutunci, kuma kake sa ran A'ishah ta barta."

Ibrahim.
"Wallahi kema zan ɗauke ki da mari idan ba ki bar wajen nan ba."

Umma.
"Ai da ka bala'i wallahi dan ba zan kwanta ka dakeni akan kishiya ba, ko kishiyar wacce bata san darajar mahaifan ta ba bale ta san na mahaifan wani."

Ɗago hannu ya yi ta niyar sharara mata mari sai ya ji saukan mari a kumatunsa.

Inna.
"Yanzun kana nufin za ka daketa akan Balki?, lallai yau ka nuna min kai ba Ibrahim ɗina bane, saboda Ibrahim ɗina ba ragoh bane."

Balkisu.
"Yanzun kana nufin kyale ta za ka yi marin ka fa ta yi."

Ibrahim.
"Inna yanzun ni kika mara saboda wannan bagi dajiyar ƴar talaka?."

Umma.
"Ibrahim yau kaine ke kirana da ƴar talaka?, na gode sosai Allah ya saka da alkairi."

Fita ta yi daga ɗakin, ɗakinta taje ta ɗauki mayafin ta tana fita A'ishah da Amina na kawowa.

Amina.
"Umman yara ina zuwa haka, ba dai tafiya za ki yi ba?."

Umma.
"Wallahi tafiya zan yi kuma ba zan dawo ba sai ya ne meni da kansa sannan zan dawo."

A'ishah.
"Haba aunty dama haka ne take so fa kenan kina nufin taci galaba akan ki."

Umma.
"A'ishah Amina ba galaba ta yi akaina ba kawai ina son in ni santa kaina da shi ne ."

Amina.
"Humm haka kika ga yafi maki."

"Eh"

"Toh shi ke nan ki tafi kawai".

Tafiya ta yi A'ishah da Amina sai kuka suke yi.

Amma Maryam Ma'aruf fa idan ya dawo me zamu ce ma sa.

Maryam.
"Dan Allah karki tura min shi, ya yi zaman shi in da kike, ga su Rashid da Rufa'i nan."

RASHIDA

BY
SHA'AWANATU FARUK DIGGI ✍️
WhatsApp number08084277827☎️


14

📝
Ga su Rashid da Rufa'i nan sai ya zauna in da suke.

Cikin kuka ta ja hanun Maryam tana cewa

"Yanzun da gaske tafiya za ki yi, ki barni bayan kin san cewa kece ƙawata a gidan nan, amma duk da haka za ki tafi?."

Cikin kuka ta janye hanunta tana cewa

"Haba Amina ai ba mutuwa zan yi ba kuma zan dawo in sha Allah".

"Haba aunty ya za kice za ki dawo ai tafiyar ce bama so, yanzun idan Ma'aruf ya nemi mahaifiyar shi me kike son a ce ma sa?."

"A'ishah karki damu ai baiyi rashin uwa ba saboda ga mahaifiyar shi nan."

Bata sa ke magana ba ta yi waje abinta.

Fita tayi daga cikin gidan cikin sanɗa dan kar ƴan gidan su san fitar ta.

Tana fita ta tare mai machin ta mai kwatancen gidan sai ƙofar gida, kuɗi ta biya mai machin ɗin ya yi tafiyar shi.

"Assalamualaikum"

"Waalaikimussalam"

Oyoyo oyoyo Gwaggo sannu da zuwa, wasu ƴan yara ne su ke gaida ta.

"Yauwa sannu ƴan albarka ina kabar ne?".

"Gwaggo yana can yana bacci."

"Ok toh ma sha Allah."

"A a a ƴata sannu da zuwa, amma yana ganki da kaya niƙi niƙi haka ina zuwa?."

"Mama ba komai kawai na kawo maki ziyara ne fah."

"Toh shiga daga ciki dai ina zuwa."

Kayan ta je ta ajiye sannan ta dawo tana cewa

"Mama wai su Yaya nan kuwa?."

"Eh lafiya dai."

"Ba komai kawai na tambaya ne saboda na yi missing ɗin su ne sosai?."

"Toh Allah yashirya min ke." ta faɗa cikin dariya.

"Ina Ma'aruf ne?."

"Yana can na barshi idan yazo baya barina na sa ke sosai."

"Toh shi ke nan."

Faɗa min meke faruwa ne Maryam na san zuwan nan naki ba a banza yake ba.

Mama wallahi na gaji da wulaƙancin da Ibrahim yake min saboda gaba ki ɗaya baya sona baya ƙauna ta.

Haba Maryam kin san ba a cikin hankalin shi yake ba sai kici gaba da hakuri har Allah ya yi ma sa sauƙin walahar nan.

Ni kam yanzun sai dai na yi ma sa addu'ar shi a nan amma ba zan da wai ba sai yazo biko na da kan shi.

Toh wannan cikin fa idan kika tashi haihuwa fa.

Haihuwa ba yanzun ba sai nan da wata uku in sha Allah.

Toh shi ke nan.

Cikin sanyin jiki ta ce .

"Mama meke damunki ne naga duk kin rame haka kamar ba ke ba wallahi?."

"Ba komai lafiya ƙalau nake."

"Haba Mama ki faɗa min dan Allah."

"Maryam ina son ki riƙe mijinki tsakanin ki da Allah idan kika cuce ɗan mutune wallahi ban yafe ba ko bayan raina ne, kuma ki riƙe addu'a ban da wasa da ita yanzun ke ba ƙaramar yarinya bace, ki riƙe ibada ki riƙe karatun azkar safe da yamma kar ki bari maƙiya suyi nasara akan ki, ki riƙe Allah shine gatan ki shine mahaifiyar ki shine Mahaifin ki, sannan ki riƙa roƙon Allah ya shirya mana zuri'ar mu, ki kula da yaran ki sosai ki ɗaura su akan hanyar daidai kar kuɗi su ja ki ki bar yaranki su lallace."

Cikin sanyin jiki take cewa

"Mama in sha Allah zan yi duk abin da kika ce in sha Allahu ba zan ba ki kunya ba."

"Maryam bana da lafiya sosai olsa ce ke damuna kuma taci ƙarfi na ban so, faɗa maki ba amma ba yanda na iya dole sai na faɗa maki."

"Olsa Kuma mama me ya sa ba ki faɗa min ba bane, yanzun Mama idan kika mutu wallahi sai nafi kowa damuwa...." Bata ƙarasa ba saka makon kukan da ya ci ƙarfin ta.

Ke kukan mi kike ne haka ce maki na yi ance mutuwa zan yi ne ehhe.

A a amma ..

Yi min shiru bana son Wata magana.

Kiran sallah magarib aka yi hakan ya sa suka tashi zuwa yin sallar.

BAYAN WATA UKU

Maryam ce zaune a cikin daƙi Mama na a waje zaune ita ma .

Cikin ta ne ya murɗa mata sosai wani danshi danshi taji aiko tana dubawa taga jini na bin kasan ƙafarta.

Cije baki ta shiga yi saboda a zabar da take ji cikin ikon Allah ta haihu lafiya.

Mama jin kukan jariri ya sa ta tasowa ɗakin ta shiga jariri tagani cikin murna ta furta cewa

"Ma sha Allah Allah na gode ma."

Dubawa ta yi sai taga ƴa mace ce aka haifa murna ba ƙadan ba ta ji .

Gyarata Mama ta yi sosai da sosai sannan ta gyara Umma .

"Kira ƴan gidan can ki faɗa masu haihuwar."

Bangaren Ibrahim kuwa komai yake yi sai yaga Maryam idan bacci yake yi ita yake gani abin ya dame shi ba kaɗan ba ya je wajen Amina yana sanne kai ya ce

"Aunty dan Allah ki taimaka min ki dawo min da matata wallahi ina son ta kamar raina amma wani lokacin sai naji na tsane ta ba kaɗan ba."

RASHIDA

BY
SHA'AWANATU FARUK DIGGI ✍️
WhatsApp number08084277827☎️

15

📝
Shiryawa su Amina suka yi sai ga Ma'aruf, Rashid, Rufa'i sun dawo daga school.

"Ma'aruf Mama ina zuwa naga kin shirya haka?, kuma ni Umma nake son na gani Mama".

"Gidan Ummarku zamu je ita ta haihu dan haka je ka shirya mu tafi Rufa'i je ka shirya kai ma."

Toh suka ce sannan suka je shiryawa .

Rashid ya ji daɗi sosai da a kace Ummarshi ta haihu sai ji ya matsu baiga yarinyar ba.

Fitowa suka yi sai gidan su Maryam Rashid yariga kowa shiga gidan sallama kawai ya yi sai cikin daɗi da yake ta saba zuwa dashi .

Yana shiga ya tarar da yarinya kwance sai bacci take hankali ƙwance kafe ta da idanu ya yi haka kawai ya ji yana son yarinyar fiye da su A'ishah.

"Umma yarinyar nan akwai kyau ji bakinta jawur kamar janbaki a ka saka mata, kuma ga ta fara ga ta kyakkyawa, kai ma sha Allah."

"Hahaha kai Rashid wannan yabawan haka, ko kana son ta ne a baka ita har sai ka tashi aure."

Hahaha kai shirme ke kam ko neman mu bazaki yi ba.

"Ayya yi hakuri Maman yara wallahi ban kula da ku bane."

"Wai ina kishiyar tawa ne naji shiru?." Cewar Inna

"Da yake ba kya da ido ba ai ba za ki ga in da take ba ya cilla mata harara."

"Kai ɗan baƙin rai wallahi ka kiyaye ni in ba haka ba sai na saɓule Yanzun ka ji min mai ƙatun kai."

"Mtsww sai ki saɓule ni ɗin mai warin goro kawai."

Kai Rashid ya isa haka .

Toh ai saika bamu yarinyar ko, Inna ta faɗa tana shararar shi.

"Ba zan bada ba sai ki yi ta ƙarfi ni wallahi kin saka min ciwon kai saboda wannan surutun naki mai bakin aku kawai."

"Ga mai bakin aku nan zaune ba ni ba."

Banza ya yi da ita saboda gaske kanshi ciwo yake ma sa ɗan wannan maganar da ya yi.

Maryam ta kalli in da Inna ta nuna wa Rashid kawai sai taga Ibrahim yana kallon ta.

"Umma nayi kewarki sosai dan Allah ki dawai gida."

Yi ta yi kamar bata ji shiba.

Ibrahim Maryam dan Allah ina son magana da ke idan babu damuwa.

Bana da lokacin magana da wanda ba ya sona kuma baya ƙaunata.

"Haba Maryam cikin yara muke fa, kuma yanzun sun mallaki hankalin kansu, ba yara bane. Cewar Amina

Yi hakuri Maryam yanzun ya fara jin sauƙi, saboda addu'ar mu ta taimakon Allah dan Allah ki saurare shi.

"Toh" kawai ta ce dan ko ba komai ta ɗauki Inna a matsayin Uwa.

Tashi suka yi dan basu waje su gana.

"Dan Allah Maryam ki yi hakuri wallahi bana cikin hankalin kaina, kema kin sani dan Allah ki yi hakuri wallahi idan ina tare da ita, duk abin da take so shine zan yi,

Please Login or Register in order to submit comment