Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

da alama da wa ta ƙawarta ce ta ke waya ta can ɓangaren aka ce, "wai Balkisu ke shegiya ki na can ki na can ki na jin daɗi kin manta da abin da Boka ya ce kuma na ji ya ce za ki dawo Nigeria gobe ba shiri dan ha ka sai kin ba da bakar akuya a yanka saboda zafi-zafi ake dukan ƙarfe".

Balkisu ta ce "kamar nawa ne zan bada saboda wallahi natsani Maryam da yaranta sannan kuma inason arabamin Rufa'i da shegen yaronnan na ta yanzun dai zan ba da dubu ɗari biyu na san dai za su yi ko"?.

Hajara ta ce "toh sai dai an ji wajen boka shi zai faɗa idan sunyi kin san aikin ba ɗaya ba ne".

Eh Hajara zan kira ki anjima yanzun tsohon banzan nan ya shigo zan kashe waya,ɗim ta yanke kiran.

Balkisu ta ce "ka ce gobe za mu koma gida amma banga tikiti ba kuma ban ga tsaraban yarana ba mai ka ke nu fi ne toh"?.

Abban Ma'aruf ɗin ya ce "ai na yi tunanin kin yiwa yarannaki tsaraba ne yanzun toh ki shirya mu je siyayyar ko".

Balkisu ta ce "toh shi ke nan ni ma akwai abin da na ke son siyawa Maryam da Amina ni ma na kai mu su".

Toh shi ke nan ga tikitin na siyo jirgin safe za mu bi. Toh kawai ta ce.

Shiryawa ta yi amma kayan ne a jikinta fita suka yi, siyayyar mai yawan gaske su ka yi sannan su ka koma gida, ko wanka bata yi ba ta yi kwanciyar ta abin ta.

Nigeria

Kiraye kirayen sallah ne ya tashi ƴan gidan mazan su ka wuce masallaci matan ma sallah su ka yi, sannan yaran su ka koma bacci Umma ɓangaren ma su aiki ta je ta ce su gyara gidan da kyau saboda za su yi baƙi sannan ta ce ita za ta yi abinci da kan ta.

Aiko Mama ita da Mama suka yi abincin farfesun naman kaza, dambu naman rago, Farfesun kayan cikin rago, da sauran su kai komai ma sha Allah.

Bangaren ma su aikin ta sa ke komawa ta ce su je su bangaren Balkisu su gyara ma ta shi sosai ha ka kuwa akayi an gyara shi sosai da sosai.

Bangaren Mama kuwa ha ka ne ita ma an gyara ɗakin ma sha Allah.

Bangaren su Balkisu su ma sun shirya tsab za su airport jirgi safe su ka shiga sai gida Nigeria.

Mama ta ce "Maryam yanzun sai yaushe yarannan za su yi hankali dan Allah kinji sunce idan su ka dawo ba su fitar da matar aure ba toh za su yi sadakar su ne amma gashi shiru".

Uhmm wallahi yaranan ba sa ji ko kaɗan ai idan aka yi sadakar su za su huta ne ai.. ba ta ƙara sa maganar ba sakamakon wayar ta mai neman agaji.

Ta ce "Assalamualaikum"

Ta can ɓangaren aka amsa "waalaikimussalam"

Barka da safiya Abban yara ko kun iso ne.

Eh gamu a airport kicewa Ma'aruf yazo ya ɗauke mu har da Daddyn su gashi a airport ɗin mu ka tarar dashi.

Laaaa har da Yaya kenan amma ko bai faɗawa Amina zai dawo ba saboda ga mu tare amma banji ta na maganar dawo War sa ba.

Toh mu ma anan muka tarar da shi sai kicewa yaran suzo su ɗauke mu.

Toh Abban yara zan kira Rashid ɗin.

Ma'aruf ɗin fa.

Am toh ai duk ɗaya ne ni dai sai ka gansu.

Amina kinji wai har da Yaya ya na airport ɗin.

Wane Yaya ɗin cewar Mama.

Wane Yaya ne a gidan nan in ba mijinki ba.

Uhmm kawai Mama ta ce.

Rashid Umma takira tace suje su ɗauko Mahaifan su a airport su na jiranku. toh Umma kawai ya ce ya kashe wayar.

Kiran Ma'aruf ya yi amma har wayar ta katse bai ɗauka ba sa ke kira ya yi nan ma shiru ba amsa.

Bangaren Ma'aruf kuwa ya na ganin kiran amma yaƙi ɗagawa saboda haushen sa da ya ke ji.

Kiran Rufa'i ya yi sannan ya faɗawa Rufa'i cewa su Daddy na airport ya zo su je ɗauko su.

Shiryawa suka yi su ka nufi hanyar airport su ka ɗauko su sai gida.

A hanyar ta zuwa gida Rashid ya ma su barka da fita jirgi lafiya.

Shima Rufa'i barka da fita jirgi lafiya ya yi ma su.

Sannan Rufa'i ya ce "Daddy munyi kewarku fa sosai wallahi".

Abbah ya ce "au Daddyn ku kawai ku ka yi kewa ban da mu kenan?.

Rufa'i ya ce "ai Abba har da kai da momy duk munyi kewarku sosai".

Daddy ya ce "toh za ka haɗa kan ka da mahaifin su ne .

Rashid ya ce "Daddy yaranka sun gagara su ganku fa saboda kullum tambayar ku suke yi.

Momy ta ce "ayya ni ce kawai ba wanda yadamu da ni saboda ga shi Rufa'i ko kallo na bai ba.

Wace irin magana ce wannan Balkisu ba sunyi mana barka da fita jirgi lafiya ba, ba yanshi mai ki ke son su yi ma ki ehhe.

Allah yabaka hakuri Abban Ma'aruf.

RASHIDA

By
Sha'awanatu faruk diggi✍️✍️
Wtspp 08084277827☎️📱


Saƙon miƙa gaisuwa ga sister's
Ina miƙa gaisuwa ga aunty Saratu
Ina miƙa gaisuwa ga sister Shamsiyya
Ina miƙa gaisuwa ga bro Abubakar
Ina miƙa gaisuwa ga ƙawata Firdausi
Ina miƙa gaisuwa ga ƙawata Rashida
Ina miƙa gaisuwa ga sister Yasira
Ina miƙa gaisuwa ga ƴata Salma
Ina miƙa gaisuwa ga my son hafeez
Ina miƙa gaisuwa ga duk kannin musulmi Allah ya barmu tare da masoyan mu ameen ya Allah.

3

📝
Da haka dai har su ka isa gida, su na shiga gidan su ka tarar da mutanen gidan har da Kaka, ran da Ummi ta ga sun sa ka hancin motar cikin gida ta sheƙo a guje ta budewa Daddy ƙofa, ya na fitowa ta ɗale shi ta na ehun ganin su shima rungume ta ya yi sosai ya sakar ma ta kiss a goshi ya ce "innan Daddy har yanzun ba ki girma ba ko"?.

Hahaha dariya ta yi sannan ta ce "ai Daddy ni yarinya ce ga su aunty A'ishah da aunty Fatima can gefe da ya ke su sun girma", ta na maganar ne cikin shagwaɓa da ita ma ba ta san da ta na da ita ba .

Rashid ga ba ki ɗaya hankalin shi ya koma kan Ummi dan shagwaɓar ba ƙaramin kyau ta ƙara ma ta ba, ya na nan ya na tunani ji kawai ya yi an mangare ma sa kai da sauri ya dawo hayyacin shi, Kaka ya gani ba kowa har su Rufa'i sun tafi su ka barshi.

Kaka ta ce "ashe Bokan turai ka na nan amma ba mai laiƙani saboda Allah daga kai har su Ma'arufa ba mai laiƙani". (Ma'aruf ta ke nu fi).

Ya ce "kai Kaka surutun ki ya yi yawa kin cika min kunne da surutu toh yanzun dai yaranki su zo ai sai kije Ku zanta ko".

Tafiyar shi ya yi ya barta a nan sa ke da baki.

Falon ya shiga ya ƙara gaida iyayen nasu sannan ya zauna a kasan ƙafafun Abba.

Abba ya ce "inna ina wuni mun sa me ki lafiya"?.

Inna ta ce "lafiya ƙalau Iro barkanku da fita jirgi lafiya".

Yauwa barka dai Inna cewar Daddy.

Ummi ta ce Abba mu je dainnin ko dan ni kam yunwa nake ji.

Umma ta ce "ba in da zashi sai sun yi wanka tukunna sannan ai maganar cin abinci", sannan Balkisu ki je ki yi wanka ke ma ki zo mu ci abinci.

Balkisu ta ce "uhmm ni ai sai na gyara ɗaki na dan nasan ba gyara min aka yi ba".

Mama ta ce "haba Balkisu ya za'ayi ace kuna ta fe mu ƙi gyara maki ɗakin dan Allah kiriƙa tauna magana kamin ki fitar da ita ".

Balkisu ta ce "atoh ni kam nasani dan naga ba a murnar dawo wa ta".

Abba ya ce "wai Balkisu mai yasa ke kullum fitina ce kawai ke ma ki daɗi yanzun yaushe rabon da mu yi zama da yaran mu da sauran ƴan uwanki yanzun gashi mun samu dama kina shirin warga za ta haba dan Allah ".

Abban yara ki yi hakuri dan Allah mu je ka yi wanka sai ku ci abinci, Ummi ku je ra mana abincin a dainnin ɗin.

Ƙin tashi ya yi hanu ta sa ta kama hannun shi kamar yaro su ka shiga ciki .

Ummi ta ce "Umma mu na nan fa ko kin manta ne"?.

Mama ta ce "kai Ummi kin cika sa ido", fa ta na maganar ta na dariya saboda ita abin ya ba ta dariya.

Mama ta ce "Daddyn yara ta shi mu je ka yi wankan kai ma ko sai na goya ka ne".

Hahaha su Ma'aruf su ka sa ka dariya.

Rufa'i ya ce "kai Mama mu ma Allah yabamu matan da za su yi mana ha ka dan naga ko ƙunyar mu Umma ba ta ji ba kema Mama ha ka".

Abba ya ce "ku na nufin ba ko tsaida matan aure ba shi ke nan zan ba da ku sadaka ga mai bukata ".

Ma'aruf ya ce "haba Daddy ka san mu yara ne har yanzun ba mu san dai-dai ba da ba dai-dai ba saboda yara ne mu dan Allah ku yi hakuri Daddy har mu girma Please".

Mama ta ce "ai ba ku isa auran ba amma ku ka san Allah ya ba ku matan aure irin mu".

Dariya su Ummi ke yi sosai .

Fatima ta ce " Mama jiya fa Yaya Ma'aruf cewa ya yi shi kam aure ya ke so dan Allah na bashi ƙawata Ihsan".

Ma'aruf ya ce "wallahi Mama ba gaskiya bane ina ma naga ƙawar ta da zance inaso".

Dariya su ka sa ka sosai har da Rashid sai da ya dara.

Mama ta ce "Daddyn yara ta shi muje tun kan su fito".

Ta shi ya yi su ka yi shigewar su ɗakin Mama.

Ma'aruf ya ce 'ke Fatima ni za ki wa sharri a gun Daddy saboda ki na son a yi sadaka na ko".

Fatima ta ce "haba Yaya ai wasa ce na ke yi ai ni nafi da son ka sama mana aunty Mai kyau da hankali".

Rufa'i ya ce "ka san mai za ka yi ka rama abokina"?.

Ma'aruf ya ce "a a sai ka faɗa".
Rufa'i ya ce "ka cewa Daddy ai Fatima ta ce ta na sonka kuma kai za ta aura idan babu kai ba za ta iya rayuwa ba", nan ta ke Daddy zai yi amanna da ha ka shi ke nan ka rama abin da ta yi ma ka.

Yaya dan Allah ka yi hakuri wallahi ba zan sa ke ba yau idan ka faɗi maganar nan ai nasan ba zanyi sati a gidan nan ba dan Allah ka yi hakuri na rantse da Allah ba zan sa ke ba. Cewar Fatima kamar za ta yi kuka.

Dariya su Ummi su ka sa ka ma ta Ummi kam kan dariya har hawaye ta ke yi.

Ma'aruf da Rufa'i ma dariya su ke ma ta sosai shima Rashid ɗin ya na murmusawa sakamakon dariyar da Ummi ke yi.

Balkisu ta na shiga ɗakin ta tarar da shi fes-fes-fes kiran Hajara ta yi a waya ta ce ma ta "sun iso a Nigeria yanzun ha ka ta na gida ".

Hajara ta ce "toh shi ke nan sai na zo zan faɗa ma ki abin da Boka ya ce".

Toh ta ce "sai kin zo ɗin ina jiran ki fa Hajara " yanke wayar ta yi.

Wanka ta yi ta canza kaya sannan ta fito falo ta tarar da su Ummi sai dariya su ke yi.

Ummi ta ce "kai ma Yaya Rufa'i sai mu ce kai ka ce ka na son A'ishah shi ke nan mu kam musha shagali a gidan nan wallahi".

Rufa'i ya ce "ai da A'ishah za ta kashe ni wallahi wannan ƴar Bala'in zan aura.

Su ka suka dariya har da Rashid.

Momy ta ce "yau nishaɗi kawai ku ke yi toh na ji kamai kai Ma'aruf zance kai ka ce ka na son Fatima, kai ma Rufa'i ka ce ka na son A'ishah, kai ma Rashid ka ce ka na son Ummi duk ku bari Abban ku yazo sai na faɗa ma su".

Rashid ya ji gaban shi ya ba da tim, sai da ya dan rufe idanunshi kaɗan kamin ya biɗe a kan Ummi.

Ummi ta ji kamar Momy ta zuba ma ta ruwan zafi ta ce "Momy dan Allah ki yi hakuri wallahi ba ha ka ba ne kawai mu na faɗa ne amma ba gaskiya ba ne dan Allah". ta na maganar ta na hawaye.

Momy ta ce a zuciyar ta dole tun da ta ga Ummi ba ta son ana haɗa ta da Rashid dole ne ita za ta yi shiga da fice sai an ɗaura auren Ummi da Rashid duk a zuciyar ta ke zan cen nan.

A fili ta ce "mai ya sa ki ke kuka ne Ƴarinyata ai basai kinyi min a sarar hawayen nan na ki ma su daraja ba kawai faɗa na ke yi amma bazan faɗawa Abban ku ba kinji ƴata hankalin ya kwanta, Fatima kawo min ruwan sanyi ta sha ko ranta zai yi sanyi.

Fatima ruwa ta kawowa Ummi tasha sannan hankalin ta ya dawo kan ta.

Su Umma su ka fito, ba su jima ba su Mama su ka fito Umma ta ce "su je dainnin Ummi wajen tsakanin Abba da Daddy ta kai kujeran ta ta zauna.

Umma ta ce "Ummi sa ka wa kowa abincin", Abba ya ce "ba za ta sakawa kowa ba sai dai kar su ci", haka Umma ta tashi zuwa sakawa kowa abinci.

FARKON LABARIN

Wani dan karamin ƙauye ne mai suna gada a jahar sokoto.

Wata mata ce mai kimanin shekaru 24 ta na aiki a tsakar gida.

Wata mata ce mai kimanin shekaru 55 tana aikin masifa ta ce "ke Rashida wai wannan abin aikine ki ke yi haka a bu kamar ba ki da jini a jiki tun da ki ka ki haihuwa toh wallahi aiki yanzun ki ka fara".

Iya dan Allah ki yi hakuri bana son musu da ke saboda ke mahaifiyata ce amma kin san da rai da mutuwa da haihuwa duk suna ga Allah

Yee-yee kuka Iya ta saka tana cewa Rashida yau ni ki ke zagi lallai yau kin tabbatar min cewa ke ba tagari bace saboda ko uwar ki ba ki bari bale ni uwar miji tana maganar ne tana kuka sosai har da fece majina.

Rashida ta ce "haba Iya yaushe na zageki wallahi ban zage ki ba dan Allah ki yi hakuri ". tana maganar ne tana kuka ita ma.

Wani matashi ne ya shigo ɗauke da sallama a bakin sa "Assalamualaikum" Iya Mai yasamai ki ne ehhe, Rashida Mai yasami Iya ne naga tana kuka"?.

Ai dole za ka tambayi uwarka tun da ni kam banza ce ba ni na haife ka ba kuma ka sa ni wallahi na gaji zama da wannan juyar dole ka zaɓa ko ni ko ita.

Ita dai Rashida kuka kawai take yi saboda da mutum ba shi ba kan shi cikin da sai ta bawa kanta.

Ya ce "Iya dan Allah ki yi hakuri ki bani ɗan lokaci in sha Allahu za ki ga jikan ki amma dan Allah ki yi hakuri yanzun wallahi bazan iyawa Rashida kishiya ba saboda ina son ta sosai".

Toh ni za ka faɗawa cewa kana sonta lallai Mustapha dole za ka yi min yan da ta ke so.

Ita dai Rashida kuka kawai take yi da taga abin yaƙici yaƙican yewa ya sa ta bar wajen da gudu ta na kuka.

Mustapha dai gabaki ɗaya hankalin shi ya tashi saboda ya na son Rashida sosai.

Bin Rashida ya yi ɗaki ya na ba ta hakuri ya ce "Rashida dan Allah ki yi hakuri wallahi Ni ma na gaji da wannan abin da Iya ke yi ma ki kuma nasan bakya jin daɗi amma ha ka za ki yi hakuri dan Allah".

RASHIDA


By
Sha'awanatu faruk diggi✍️
Sha'awa marubuciya✍️

Wtspp 08084277827☎️📱

PART 4

📝
Amma fa cewa ta yi dole cikin mu ka zaɓi ɗaya ko ita ko ni yanzun dan Allah saboda ban sa mu haihuwa da wuri ba ne za ta tsane ni har ha ka, ai ba ni ke ba wa kai na kuma shirun da haihuwa ta yi min ba shi zai sa Allah ya manta da ni ba Kum.... Kuka ya ci ƙarfin ta ya sa ba ta ƙarasa maganar ba.

Nisawa Mustapha ya yi ya ce "ni dai ba zan gaji wajen ba ki hakuri kuma da ki ke maganar cewa wai na zaɓa wallahi bazan sake ki ba saboda ina son ki sosai dan Allah Rashida ki dai na sa ka damuwa a ranki.

Toh shi ke nan ba na son yin musu da kai mijina ka yi hakuri na dai na amma dan Allah idan ta buƙaci ka sake ni dan Allah kar ka yi ya yayya da ita saboda ba na son fushin iyayye akan mijina.

Hahaha toh shi ke nan amma fa ba na fata ki ka san ko na yi ajiya a cikin cikin nan na ki.

Hahaha dariya ta yi sosai sannan ta ce "toh Allah ya sa da gaske ne mijina, mijina ina son ka ina ƙaunar ka."

Matata ina son ki ina kaunar ki ina ma ki son da idan Iya ta matsa rabuwa na ta ke toh wallahi za ta yi biyu babu bu.

Rufe ma sa baki ta yi sannan ta ce " haba mijina mai ya sa ka ke faɗan wannan maganar dan Allah ka dai na in sha Allah a tare zamu yi rayuwa har lokacin da Allah zai bamu yara".

Rungume ta ya yi sosai a jikin shi ya ce "ina son ki matata" ai da ga nan na fito na bar ma su dakin saboda um a bar shi kawai.

A kwana a tashi a sarar mai rai yau Rashida ta shi da matsanancin ciwon ciki abu kaɗan ta ci sai amai, Mustapha ya ga ciwon ya yi yawa ya ɗauke ta zuwa ɗan ƙaramin asibiti likita ya yi yawan da ya ke yi ya ce idan za ta iya tashi ta je ta yo fitsari ya bata ƴar ruba ya ce ciki zata yi fitsarin ta je tayo ta ba shi ya yi awon da ya ke yi ya ce "ta na da aure ne"?.

Mustapha ya ce " eh".

Likitan ya ce "ina mijinta"?.

Mustapha ya ce "likita ga ni ko wa ni abun ne ke damun ta saboda wallahi ta ji jiki sosai dan Allah kar ka ce min ta na da matsala ne likita".

Likitan ya ce "kwantar da hankalin ka abokina ba abin da ke damun matar ka ta na nan lafiya, congratulations abokina matar ka na dauke da cikin wata biyu.

Mustapha ya ce "mai ka ce likita ban ji da kyau ba dan Allah ka sa ke faɗa min wallahi kunne na wani abun ya ji da ban"?.

Hahaha dariya likitan ya yi ya ce "abokina na ce matar ka na ɗauke da juna biyu na wata biyu".

Mustapha sujada ya yi ya na wa Allah godiya, sannan ya ce "likita da mai zan saka maka wallahi da mai kuɗi na ke ta yau zaka sha kyauta ta musamman saboda wannan albishir ɗin da kai min".

Likitan ya ce "akwai abin da za ka bani amatsayin tukuici".

Mustapha ya ce "likita kafaɗa min menene shi har in baifi ƙarfi na ba zan ba ka shi in sha Allah".

Likitan ya ce "abota kawai nake son mu yi idan ka amince saboda wallahi kabirge ni sosai ina son namiji mai irin halayyar ka".

Mustapha ya ce "yau kam tazo min a Sa'a Allah na gode maka da wannan alkairin da ka ke nuna min, na amince in sha Allah ba zanci amanar ka ba sai dai idan kai kaci tawa amanar".

Likitan ya ce "abokina na gode sosai nima saboda wannan abin da kace min yasa na ƙara jinka a rai na, Allah yabawa matar ka lafiya Allah ya sauke ta lafiya abokina".

Tashi ya yi likitan ya ce mu je na raka ka saboda bana son iska ya ta ɓaka, hahaha dariya su ka gabaki ɗaya.

Barin asibitin su ka yi sai gida su na shiga Iya ta tasu su da bala'i sunje sunyi zamansu a can.

Rashida ta je wucewa ɗaki sai Iya ta riƙe ma ta hijab ta ce "ai daga nan gidan ubanki za ki koma dan nagaji da wahalar min yaro da ki ke yi ".

Mustapha ya ce "Iya ba dai haihuwa ce matsalar ba toh shi ke nan tazo ƙarshe in sha Allah, yanzun daga asibiti muke kuma sunce ta na ɗauke da cikin wata biyu".

Ciki fa kace Mustapha Rashidar ce mai ɗauke da cikin ko aure ka yi ban sa ni ba?.

Iya Rashidar dai ce mai ɗauke da cikin yanzun kam ai sai ki nuna ma ta soyayyar da ba ta samu ba tun da.

Allah sarki Rashida ƴar albarka Allah ya maki albarka Allah ya rabaki lafiya dan darajar Annabi Muhammad s a w ameen ya Allah.

Ameen ya Allahu Iya cewar Mustapha.

Iya ta ce "ƴata sannu kin ji mai zan dafa maki yanzun eh dan nasan ki na buƙatar wani abun ta ɓawa"?

Iya ba komai Na gode sosai yanzun ba na jin yunwa bacci daina ke ji.

Toh shi ke nan ƴata ki je ki kwanta ai nasan kina bukatar hutawa.

Iya toh yanzun ya maganar ƙara auren kisama min mata kawai .

Iya ta ce "Mustapha ai yanzun kam ba zancen ƙara auren dama jikokina na ke son ga ni shi ya sa wallahi nace sai ka yi aure amma yanzun kam ba wannan zancen".

Toh shi ke nan bara na shiga ciki sai na fito.

Ɗakin ya shiga ya tarar da Rashida na riƙe da cikin ta tana kuka.

Ya ce "Rashida lafiya daina ga ki na kuka ko wani abun ya faru dan Allah ki faɗa min"?

Cikin kukan ta ce "ba komai mijina kawai ina tunanin maganar Iya ne kenan idan ba wannan cikin ba yau rabamu za ta yi".

Haba Rashida kawai Iya na faɗa ne ba gaskiya bane ki dai na wannan tunanin ba mai rabamu in sha Allah mu na ta re da ke har abada.

"Allah ya nufa".

A kwana a tashi sai yaro ya za ma babba .

Rashida na ga ni da ƙatan cikin ta sai wa ni ni shi take yi da alama na ƙuda ce tazo ma ta ta ce "Iya Iya ki na ina cikina zai zube".

Iya taji ehun ya yi yawa taje ta leƙa sai taga Rashida a yashe a kasa.

Ta ce "Rashida Meya same ki ne ha ka ko naƙudan ce"? tazo aiko ta taimakon Iya ta haihu ɗanta namiji murna wajen Iya ba a magana.

Ruwan wankan mai jego Iya ta haɗawa Rashida taje ta yi wanka sannan ta zauna, Iya ta ce "ƙarfe shi ki bashi madarar shi yasha".

Rashida ta ce "Iya kibari har Mustapha ya zo sai na bashi madarar dan Allah Iya".

Iya ta ce "yau ni naga ta kaina toh idan yazo shine zai bawa jaririn mamarshi ne".

Haka ba dan tasu ba tabawa yaron madarar shi, tana cikin bashi madarar sai ga Mustapha ya ce "Rashida kice kuwa nake gani da jariri a hanu?.

Iya ta ce "eh itace ko da wani abun ne"?.

A a kawai na tambaya ne ya ce "Iya

Please Login or Register in order to submit comment