Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tari.. Gashi tun safe ko ruwa baishaba, tari yacigaba dayi sosai kaman ranshi zai fita, shafa mashi kai Umma tafarayi, da sauri ya kauda kanshi yacigaba da tare, saida ya gama yacigaba dacewa
"Ki fadamin..please..." Wani tarin yafarayi, nan fa hankalin Umma yafara tashi, kokarin cire kafanta tayi amma Salem bai saki kafanba
"Son please sit up...you are hurting yourself.."
"Umma you don't care if I die...inda kinasona zakiso abinda nake so..." Tari yacigaba dayi kaman ranshi zaifita,,
"Son please ka tashi..." $ kara girgiza mata kai yayi, yacigaba da tari, saida tarin ya lafa yacigaba da kuka tare dacewa
"Wallahi Umma.. Bantaba tunanin zan kamu da son yarinya hakaba...but I can't help it...nidai ..." Coughing yacigaba dayi ahankali Umma tace
"Ita ta fada maka nayi mata wani abu?..."
"Ai hired guys dinki yarda mata waya sukayi...Umma why...tunda bakin son tawa na hakura daita..amma please tell me where she is.." Yafada cikin kuka, kokarin mikewa tayi amma yanda Salem ya rike mata kafa ya hanata tashi
"Ka sakarmin kafa kafin in bata maka rai..."
"Wallahi ki kashe ni...hakan zai fimin sauki..." Umma kwalawa guards dinta kira tayi suzo su dauke Salem daga dakin amma suna zuwa bakin kofan guards din Salem suka hanasu shiga,..duk yanda sukaso wucewa basu samu hanya ba, sunfi minti ashirin ahaka, Umma gani tayi da gaske Salem yake, gashi sai tari yake babu sassautawa, duk yanda Umma taso lallashin sa abun yaci tura, datace ya sakar mata kafa sai yace
"Please tell me where you took tawa.." Magiya Umma tafarayi sosai amma yaki sakinta, Sam bata son Abba yasan abinda ke faruwa don dukda yana da saukin kai baya tolerating nonsense, Salem kuka yake sosai Umma tarasa yanda zatayi dashi, abu kaman wasa har hour daya tayi Salem yaki sakar mata kafa wai dole saita fada mashi inda ta kai tawa. Ana cikin haka Abba ya dawo, tundaga nesa taga guards din Salem dana Umma tsaye suna kallon juna, kallon Mara dadi, ana parking mota Abba ya fito ya nufo wurin,
"Meke faruwa nan?" Ya tambaya yana kallon each and everyone, daya daga cikin guard din Umma yace
"Sir..Hajiya keta kiran mu amma sun hanamu shiga" Abba kallo guards din Salem yayi
"Meye haka?"
"Sir we are following orders" inji majed, Abba bai kara cewa komai ba ya shiga ciki, nan fa gaban Haj yafara disco ,Abba kallon Salem dake kwance kasa yana kuka,
"Me ke faruwa nan?" Ya tambaya yana kallon su, Salem baice komaiba yacigaba da kuka shi ita kuma Hajiya shuru tayi
"Baku jina ne?"
"Abba ka fadawa Umma tabani tawa..."
"What are you talking about?" Abba ya tambayeshi, cikin kuka ya fada mashi abinda ya faru
"Subhanallahi.. Hajiya is he saying the truth?" Umma shuru tayi, alaman bata da gaskiya, Abba dukawa yayi
"Son stand up..." Da sauri ya girgiza mashi kai
Abba ka fada mata ta gayamin inda ta kai Tawakaltu.. " Abba kallon Umma yayi
"Wai ina kika kai yarinyan mutane?" Ahankali Umma tafara cewa
"Son kayi hakuri... Babu abinda nayi mata...I just beg her to stay away from you.. And she promised..." Kuka sosai Salem yafarayi
"Umma why..." Tari yafarayi sosai yana nishi sama2, da sauri Abba ya dagashi, aikam sai jini hancinshi..kuka Umma tafara
"Wallahi nayi nadama...tun yarinyan na nan nafara nadaman abinda nayi.." Abba dirty look yayi mata sannan ya rike Salem
"Muje part dina in baka first aid kafin in kira doctor.." Ahankali Salem ya girgiza mashi kai
"No Abba.. Allah yasa wannan yazama ajalina..." Tafiya yafarayi, ko tsakiyan dakin bai kaiba ya fadi kasa, da gudu Abba da Umma suka karasa wajenshi, acikin tension Abba ya kira doctor, Umma kwalawa guards kira tayi tana kuka, gabaki dayan su suka shigo dakin, duk ahankali su tashi yayi especially personal guards dinshi. Daukan shi su Abdul sukayi,
"Follow me!" Dad ya umarcesu, da sauri Abba ya fita suka bi bayan shi.

Wani part my dauke da hospital equipment aka kaishe, Salem bude ido yayi yaga mutane triple, maidasu yayi rufe tare da dafa kanshi.

Bayan minti ashirin doc yazo, bai bata lokaci ba ya sa mashi drip.

๐Ÿ’šโค๐Ÿ’™๐Ÿ’œโค

Yau ya komawa ameera sabo cos yau ita kadai ta wuni, gashi da musassara ta wuni ga ciwon kai dana Mara, duk abin duniya ya isheta, bakin gate taje tayi knocking,
" meye?" Suka tambayeta, cikin kuka tace
"Dan Allah Ku kiramin hinde.." Banza sukayi daita,
"Kunji Dan Allah.. Bani da lafiya ne..."
"Kar ki kara aikanmu...darajanki daya da baki da lafiya.. Bari musa akira maki ita" daya daga cikin su ya fada sannan ya kira wani ya aikeshi ya kira hinde.

Bayan kaman minti ashirin sai ga hinde ta shigo gidan , gani tayi ameera durkushe kasa tana kuka hannunta kan maranta
"Lafiya?" Ta tambayeta tana karasowa wajen ta, cikin kuka tace
"Cikina...wayyo..menses zanyi..."
"Meye messes" tafada tana dagata tsaye
"Alada zanyi..." Tafada tana kuka tana yarfa hannuwa,
"Daman haka yake yi maki?" Kai kawai ameera ta daga mata,
"Sannu" hinde ta dinga yimata, ta maidata daki sannan ta dora mata ruwan , bayan yayi dumi ta saka daya daga cikin dankwali ameera ta dinga danne mata cikin ta da bayan ta,, aranan hinde nan gidan ta kwana, banda kuka babu abinda ameera takeyi don a gida in ta fara har Karin ruwa akeyi mata.

๐Ÿ’š๐Ÿ’™๐Ÿ’œ๐Ÿ’›โค

Sai wacegari around 8am tawa ta isa Ilorin, tunjiya ko ruwa bata shaba, kuka ta dinga yi although the way, cikin kwana daya ta rame sosai, ga idanuwanta sun yi ja, bakinta ya bushe, wayan mutane ta dinga amsa tana kiran mami har ta isa, wayan wani bayerabe ta amsa ta kira mami ta sanar daita sun isa park, baa dadeba wasu cousins dinta uku sukazo daukanta, dukkan su kallonta sukayi suna cewa.
"Ga Hausa Yoruba" tawa batace masu komai ba ta shiga bayan helux suka kara gaba, cikin wani babban flat suka tsaya, anayin parking tawa ta fito kasancewan tasan gidan cos mai gidan yayan mami ce, itakadai ce bata juyawa mami baya ba amma sauran 6 duk basu yiwa mami magana wai don ta zani talaka.
Afalo taga mami da yayanta zaune, mami na ganinta ta mike tana mamakin yanda yarta ta koma cikin kwana biyu, tawa fadawa jikin mami tayi tana kuka Mara fita, hankalin mami tashi yayi
"Ife...kiLode?" Tawa bata amsaba tacigaba da kuka, irin kukan da takeyi yasa mami tunanin kilan Salem raping dinta yayi mami with dirty mind. Tawa kneeling tayi ta gaida yan mami da mami, Matan amsawa tayi tana tambayan ta abinda ke sata kuka amma tace bakomai.
Daya daga cikin cousin dinta wanda suke same age mate ta daga ta sukayi wani daki, ruwan wanka ta hada mata, wanka ta shiga tana wanka tanajin kamshin turaren shi, sabon kuka tafara.

๐Ÿ’œ๐Ÿ’™๐Ÿ’›๐Ÿ’šโค
ZAKISAN KONI WAYE
๐Ÿ’š๐Ÿ’›โค๐Ÿ’™๐Ÿ’œ

ยฎzuwairat(ummu maryam)

3โƒฃ9โƒฃ

Tawa na wanka ta kuka, fitowa tayi daure da towel, kayan data cire ta fito rungume dasu, kamshin Salem kawai take shaka, bata ankara ba cousin dinta ta amshe kayan ta wulla cikin laundry basket sannan ta miko mata leggings da shimi,
"Ki ajiye wannan ki bani kayana in maidasu.." Tawa ta fada mata cikin low voice, kallon mamaki tayi mata
"Ya zaayi ki maida kayan daki kayi tafiyan hour ashirin dasu?..."
"Please just give me"
"Freaky one.." Ta fada sannan ta Dauko mata kayan daga inda ta ajiye su. Tawa maida kayan tayi tana hawaye. Daman lokacin breakfast ne, dukan su na zaune kan dinning sun fara cin abinci amma tawa bata fitoba, yan mami kallon autanta mai suna tima tayi ta kirawo tawa, tima bakin gado ta tarda tawa sai kuka take tana shafa kayan jikin ta,
," please sis meke damunki?..you look pale..." Ahankali tawa tace
"Nothing.." Tsoki taja
"Daman ke matsalan ki kenan..zurfin ciki...mom tace kifito kici abinci" tana kaiwa nan tafice, tawa goge hawaye tayi ta fito, mami sai kallon ta take, zama tayi kanta kasa, abinci suka faraci, amma ko chokali biyar tawa bata yi ba ta mike,
"Har kin koshi?..* babban Dan mom maisuna femi ya tambayeta ciki yarensu, kai kawai ta daga mashi, mami kalonta kawai take, tima tace
" something is wrong with you " ta fadawa tawa.

Bayan sun gama breakfast suka falo, tawa da mami tare da mom sukashiga dakin mom, nan mom ta tambayeta abinda ke faruwa, cikin kuka ta fada masu ko Salem waye amma bata fada masu yanda sukayi da Umma Salem ba, mami kallonta tayi
"Tawa ko yayi maki wani abune?" Girgiza mata kai tayi
"No mami... I just love him..and am missing him already.." Mami buge mata baki tayi, mom kallon mami tayi
"Wai meye haka... Kinci saa tawa Dana respect.. Meye na rabata da mutumin da take so..ke an rabakune?... Har iyayenki ki watsar saboda so..to gaskiya ban ga amfani abinda know keyiba" afusace mami tafara cewa
"Aini mutuwa ya rabani dashi amma hausawa don't have respect for marriage.. Kuma mutumin in questions..is beyond us..."
"Ohh stop it!..." Mom ta dakawa mami tsawa
"At least ko bansan Salem a zahiri ba nasan shi a news..I don't think he's a bad person.. Gaskiya kinason kisa yarinya nan ciki wani hali...I don't know why mother take their children's feeling for granted..." Tawa sai kuka take, mom ta cigaba dacewa
"Ni zan nemo contact..." Da sauri tawa tafara girgizawa mom kai
"Mom ki barshi..."
"Why?..." Mom ta tambayeta, kuka ta farayi sosai sannan ta fada masu yanda sukayi da Umma, mami ma kuka tafarayi, rungume tawa tayi tana cewa
"Kinyi kadan da wahalan da kike sha...am sorry for all you have been through.." Tawa ma rungume mami tayi, duk jikin mom yayi sanyi, at the same time tana cewa
"Gaskiya am disappointed in her...sai kace bata da addini?..ai in Allah ya hada, mutum yayi kadan ya raba. Sunfi hour zaune nan, daga baya bacci yayi gaba da tawa jikin mami.

๐Ÿ’›๐Ÿ’™๐Ÿ’œโค๐Ÿ’š

Salem bai sake farkawa ba sai 9pm, lokacin ana yi mashi Karin ruwa na biyu, ahankali ya bude ido ya kalli Abba da Umma, Umma sai kuka take,
" son am sorry... " Salem bai komaiba tacigaba dacewa
"Na yarda ka aureta" Salem lumshe idanuwa yayi
"Umma where is tawa?" Ya tambayeta ahankali,
"Ta tafi gidansu..."
"Bata Kano..." Sabon kuka Umma ta farayi, Salem mikewa yayi zaune tare da taimakon guards dinshi, Abba kallon Salem yayi
"Son ko ta tafi garin su" kan Salem kasa baice komaiba
"Son ya sunan garin su...sai insa a nemo ta" daga kai Salem yayi
"Abba ban San garin su ba..besides tunda Umma ta roki tawa ta rabu dani..bazata Kara saurarena ba..kawai na hakura daita..." Yafada yana komawa, hawaye na zubo daga idonshi
"Son kayi hakuri... Ni zansa anemota...zanje har gidansu in bata hakuri..."
"Stop it Umma... Ki rabani da ita...tawa bazata Kara saurarenaba...tana da bin umarnin manya..." Umma shafa kanshi tayi tacigaba da kuka
"Yanzu ta ya zamu fara Neman ta..." Salem shuru yayi yana tunanin yanda rayuwanshi zata kasance in babu tawa aciki, yasan life will be meaningless, ko yanzu ji yake kaman ya mutu don bakin ciki, shi bai ga laifin ummanshi sosai ba..yafi gani laifin Tawakaltu data gudu daga gareshi, ahankali yafara cewa
"Why...why..me.." Abba rike mashi hannu yayi
"Son tashi ka dan cin abinci sai kasha drugs.." Girgiza mashi kai yayi
"Abba am not hungry..."
"No son..you have to eat.."
"Wallahi Abba bazan iya cin komai ba.." Haka suka kyalleshi, sai around 12am Umma da Abba suka kwanta, yarage daga Salem sai guards dinshi, daya daga kai suka hada ido sai ya wulla masu harara, haushin dukan su yakeji don gani yake rashin kulansu yasa tawa ta samu hanyan fita, cikin ranshi kuma yana tunanin babu abinda zai hanashi ciwa tawa for playing with his heart.

Har garin Allah ya waye bai samu bacci ba tunani kala2 yake, don ji yake inda zai Iya cire tawa daga cikin ranshi da yaji dadi. Duk Wanda ya ganshi sai yasan yana cikin damuwa, don idanuwanshi sun koma ciki, ya fada sosai. Tunda safe Umma tafara calling mutane tana cewa su nemomata yarinya mai suna tawa, abun haushin shine yanda babu mai photo dinta.har daren rana Salem bai ci komaiba, so yayi ya koma abuja amma Abba ya hanashi tafiya. Saida Abba yayi da gaske sannan yasha tea.

๐Ÿ’›๐Ÿ’™๐Ÿ’œ๐Ÿ’šโค

With in kwana biyar kowanne part ya wahala, ita ameera ta jigata sosai saboda menstural pain don ta kara ramewa ta rage haske sosai don babu Wanda zai taba cewa classic ameera mai manicure, pedicure, zuwa spa..ce duk ta koma kalan tausayi, kullum cikin kuka take, yanzu sun shirya da hinde, don yanzu nan gidan hinde ke kwana.

Tawa kan cikin kwana biyar din ta koma kaman ba itaba don wannan hips din da Salem ke mutuwar so sun rage, mami ta kasa gane kanta, yar mom my shekara 22 ta sata gaba tana tambayan ta kasancewan babu Wanda yasan dalilinsu na dawowa Ilorin sai mom,
"Please tawa tell me what's the problem.. Remember we are family.. Matsalarki matsalar mune..." Deeja ta tambayeta, tima dake zaune cikin dakin tana chatting tayi karaf tace
"Anty deeja leave her... Babu tambayan da banyi mata ba..amma taki fadamin... Cikin dare bata barina inyi bacci.. Sai ta rungume kayanta ta dinga kuka..." Tawa daga red eyes dinta tayi ta gallawa tima harara.
"To tunda baki gayawa kawarkiba..ni in fidda ran zaki fadamin kenan" inji deeja, ahankali tawa tafara cewa
"Anty INA cikin matsaln da shuru yafi min alkhairi..." Da sauri tima ta ajiye wayan hannunta
"Meye Dan Allah?" Tawa kara hararan ta tayi sannan yajuya tana kallon deeja tafara bata labarin yanda suka hadu da Salem har ranar da taje gidanshi, baki dukkansu suka bude, da sauri deeja tace
"You mean Salem Yusuf sulaiman popularly known as slim.." Cikin kuka tawa tace
"Ni ban san ana ce mashi slim ba.."
"Kam...dan baki ganin shi asocial media ba...wow..I can believe this.. Kin taba ganin slim?.. Bari in rungume ki" deeja rungume tayi tawa ta gallawa bayanta harara
"Tunda kin taba runguman slim...."
"Anty stop it.." Tawa tafada cikin fada da kishi, dariya sukayi
"Babe kar ki biyewa mami wallahi in kina sonshi.. Kawai ki kirashi yazo nan.." Inji tima, mikewa tayi daga inda take suka bita da kallo ko wannensu tana mamakin yanda akayi tawa tasan Salem dukda gani suke karya take.

Dakin mami ta shiga ta ganta kwance tana bacci, ahankali ta dauki wayanta ta fita daga dakin

Abangaren Salem baka gane shine don raman dayayi, kullum sai anyi mashi Karin ruwa, Abba da Umma suna mamakin irin wannan so, sai sunyi da kyar yake Dan cin abinci, duk hankalin guards dinshi ya tashi, don gani suke kaman yana Iya mutuwa kuma hakan means problem for them.

Duk iyan kokarin da Umma da Abba keyi don su nemi garin su tawa yaci tura don har obasonjo aka kira shima ya yasa mutane su nemo Tawakaltu Lukman amma baa samuba.

Salem na zaune yayi tagumi duk abun duniya ta isheshi, sai tunani yake tawa bata sonshi don yanda ta iya kwana 6 bata ji muryanshiba, su Abdul na tsaye Dan nesa da inda yake, Wayanshi dake hannun majed yafara ringing, da sauri majed ya karasa wurin shi tare da mika mashi wayan,
"Who?.." Salem ya tambaya batare daya kalleshi ba
"No name sir" majed ya amsa mashi, shuru Salem yayi yana sauraron kiran, don baya daukan anyhow call, kaman an chunkuleshi yace.
"Tawa..." Sannan yayi saurin amsan watan, kafawa yayi ga kunne
"Hello.." Yafada cikin sauri, tawa najin muryan shi ta rike baki
"Hello...Tawakaltu is that you?" Tawa najin ya kira sunan ta ta fashe da kuka, mikewa tsaye yayi
"Tawa..the only way I will forgive you for playing with my heart is by telling me where you are..." Yafada afusace har jijiyan wuyanshi na tashi, tawa bata ce komaiba yacigaba dacewa
",I thought you love me...but I was wrong... Wallahi in har baki gayamin inda kike ba...." Hawaye ne yafara zubo mashi,
"What did I ever do wrong to you..." Yafada muryan shi na rawa
"Habibty tell me... Please", yafada ahankali, tawa bata ce kala ba, tari ya farayi sosai,
" am dying for you...wallahi habibty tunda kika gudu kika barni banci komai ba...tell me and I will forgive you..." Ahankali tawa tace
"Ife..am..."
"Don't you ever call me that.. Until you tell me where you are..."
"Am sorry..." Afusace ya kara katseta
"Don't say anything until you tell me where you are..." Tawa batace komai ba ta dinga kuka, hankali Salem yayi murmushin takaici
"So bazaki fadamin bako?.." Tawa bata bashi amsa ba tacigaba da kuka
"OK..ba matsala.. Did you know what I regret most?" Ya tambayeta, bata bashi amsa ba yacigaba dacewa
"That night you spent in my house.. I would have tear you..I would have given you something to remember.. Da bazakiyi gigin guduwa daga gareniba...but you know what?" Ya kara tambayan ta
"I will find you....you know why?..cos I love you.. But that will not stop me from landing you in the hospital the way you landed me..." Tawa kuka tacigaba dayi sosai, Salem ji yayi kafanshi baya daukan shi, wuri ya samu ya zauna, bai gama zamaba yaji wayan ta katse, da sauri yace
"Hello.." Yaji ta katse wayan, with out wasting of time Yayi dailing number amma switch off, tsayawa Yayi yana Tunanin abun yi don yasan he's going insane already, da sauri ya fara shiga cikin contact din wayan, nan ya dinga neman contact masu suna Yoruba, Mr kayode ya gani, da sauri ya kira number, mutumin na dagawa yayi yanason gaida Salem amma Salem ya katseshi dacewa
"Please kai Dan wane garine?" Ya tambayi mutumin
"Sir from osun"
"Please kasan sarki cikin sarkin yorubawa Wanda ya kori yarshi saboda ta zabi wani talaka?" Mutum shuru yayi for a while
"Sir yaushe hakan ya faru?" After few seconds yace
"I think it should be 19 to 20 years ago" mutumin shuru yakarayi da alaman tunani take
"Gaskiya sir I don't know.. Any problem?" Tsoki Salem yaja
"Please help me find out from you family and friends"
"OK sir" cikin few minutes Salem ya kira wayanda yasani yorubawa ya tambayesu amma babu Wanda yasani, sai yace masu please su tambayar mashi, mikewa yayi ya nufi part dinshi na gidan, su Abdul binshi sukayi, juyawa yayi ya kallesu
"Dalla Ku bar bina..sanda naso kuyimin guiding din gidana Baku yiba...kawai kuyi adua in ganta..in ba hakaba you will all be fired.." Ya fada yana kallon su dayan bayan daya, saida yazo kan Abdul ya nuna shi da Dan yatsa
"Most especially you..don duk kai kajamin wannan matsalan.

Salem komawa yayi ya kwanta yana tunanin Allah yasa agane ko waye, bai kai minti ashirin da kwanciya ba wayanshi yafara ringing, da sauri yayi picking,
$" sir ance its oba of kwara state" da sauri Salem ya mike zaune yana saka palm sandal dinshi
"You oba...ehmm...oba sadiku!?"
"Yes sir"
"Are sure?"
"Yes sir"
"Thank you.. " ya fada yana katse wayan, bai dade da katsewa ba yafara ringing kuma picking yayi
"sir ance its oba sadiku of kwara state"
"Thanks" kawai yace ya fita ya nufi side din abbanshi.

๐Ÿ’™๐Ÿ’œ๐Ÿ’›๐Ÿ’šโค
ZAKISAN KONI WAYE
๐Ÿ’›๐Ÿ’œ๐Ÿ’™โค๐Ÿ’š

ยฎzuwairat(ummu maryam)

4โƒฃ0โƒฃ

Salem na zuwa part din Abba ya zauna yana haki saboda yanda yayi tafiyan cikin sauri, saida numfashin sa ya daidaita sannan yace
"Abba.. Na gane waye grandpa dinta," da sauri Abba yace
"Really?.. Waye?"
"Can you believe it?.. Oba sadiku of kwara state ne grandpa dinta," kallon mamaki Abba yafara yiwa Salem
"Son are sure of what you are saying.."
"Yes Abba.. Investigation nasa aka yimin" Abba gyara zama yayi
"Wane investigation?" Sai lokacin Salem ya bawa Abba labarin da tawa ta bashi, baki Abba yabude
"Son shine kake cewa har talakawa ce?.. Ai sadikus linage are filty rich..." Dan murmushi Salem yayi
"Ai tawa a restaurant take saida abinci.." Abba shuru yayi for a moment sannan yace
"Ai abinda uwar yarinyan tayi bata kyauta ba..whatever parents come first... I think nasan lokacin da abin yafaru..I was the GCFR a lokacin..."
"To yanzu Abba meye abinyi?.." Salem ya tambayi Abba, Abba shuru yayi yana tunanin abinyi, bayan kaman 40 seconds yace
"Zan yiwa obasonjo magana sai ya rakani muje wurin oba.."
"To Abba inkuje ..." Shuru yayi sannan ya Dan doki kanshi sannan yace
"Abba am confused.. Kasan iyaye maza suke babanta ya kamata su bani ita..." Dariya Abba yayi
"I know.. Kasan am sure yarinya da mamanta basu gidan oba...so zamu shirya tsakanin ta da iyayenta..hakan zaisa mu gane whereabout dinsu"
"Gaskiya hakan yayi... Amma.." Sai kuma yayi shuru,
"Amma me?" Abba ya tambayeshi, yana Dan shafa keyanshi kaman mai jin kunya yace
"It will take a long time.." Dariya Abba yayi sosai, cikin zolaya irin na iyayen zamani yace
"Ka matsu ne?" Salem sunkuyar da kanshi kasa yayi yan dariya,
"Ai kayi kokari...35 ba wasa bane..in badai kana..." Da sauri Salem ya girgiza mashi kai
"Never.. Abba" yafada kanshi kasa, saida kunyan tadan sakeshi sannan yace
"Amma Abba there is one more problem.."
"OK..na meye?" Ahankali Salem yafara cewa
"Abba maminta bata son hausawa" dariya Abba yakarayi
"Me hausawa sukayi mata"
"Wai Abba cewa take basu da rike aure..." Dariya Salem yafara yana
cewa
"Yau aure gobe babu" yafada a irin muryan mami, Abba dariya yayi.
"In-law to be dinka kake yiwa shakiyanci ko..babu ruwana..amma maganan ta ba karya bane..saidai ba duka aka taru aka zama dayaba.. Besides we are not hausas"
"Ai Abba dukkan mu Hausa ake cemana"
"To ba matsala bane, zamu nuna masu muma muna da rikon aure"
"Insha Allah" mikewa yayi ahankali,
"Abba inason in goma gidana na nan" kai Abba ya girgiza mashi
"Kayi zamanka nan tukunna"
"OK" yafada amma badon yasoba, donshi mutum ne maison privacy, har ya kai bakin kofa Abba yace.
"Mijin Yoruba..ka kokarta kafara cin abinci don kar ayi tunanin wani ciwo gareka" murmushi jin dadi Salem yayi
"Insha Allah Abba" sannan yafita, yana fita yaga majed ya taho da wani work phone
"Sir wani nason magana da kai" fuska daure Salem yace.
"Waye?"
"Nigeria head of NGO "
"Baka fada mashi ina holiday ba?"
" Sir na fada mashi..amma yace is about family din matanka...." Bai karasa ba Salem ya tureshi yana juyawa yana kallon kofa part din Abba don ya tabbatar babu Wanda yaji abinda majed
"Kana haukane?.. Don't you know secrecy?..Dalla bani wayan.." Yafada yana kwace wayan daga hannun majed, yana amsa waya na tsikewa, fuskanshi murtuke yayi dialing number, mutumin na picking yace
"Alh ya akayi ne?" Daga chan bangaren akace
"Sir wallahi iyalen alh umar Adam gezawa ne suka addabeni..wallahi yanzu nan Matan har kuka tayimin awaya wai tunda ameera ta bar gida basu ji daga garetaba..uwar har cewa tayi tana da feeling something bad is happening to her.."
"Indeed" Salem yafada kasan makoshin shi sannan yacigaba da sauraren Abinda ake fada mashi
"Sunce basu da contact dinka shine suke son in sada su da kai..." Sai yayi shuru, Dan karamin tsaki yaja
"Wannan long story... Kawai say some body want to speak to me..is better... Connect me to them" yafada lokacin da ya karasa kofan part dinshi, bude mashi kofa akayi ya shiga ya samu wani kujera ya zauna ya dora kafa daya kan daya lokacin wayan nata ringing, muryan dad ameera yaji yayi sallama, amsawa yayi sannan yace
"Alh ya akayi ne?.." Ahankali dad ameera ya gaisheshi, ya amsa yakara cewa
"Ya akayi ne?"
"Sir kuna lafiya?"
"Lafiya.. Ko kaji rashin lafiya ta?" Da sauri dad yace
"No sir.." Ahankali yacigaba dacewa
"Ya ameera?" Yayi maganan kaman an fixgota daga bakinshi,
"Lafiya..." Bai gama magana ba yaji kaman an amshe wayan, saiji yayi ance
"Hello uncle.." Cire wayan yayi daga kunnenshi ya kalli wayan sannan ya maidata kunnenshi
"Uncle..." Ahankali Salem yace
"Sir who is this?"
"Sir nine affan...sir please am missing anty ameera... Please I want to talk to her..." Yana kaiwa nan ya fashe da kuka, Salem sai yaji duk jikinshi ya mutu, affan yacigaba dacewa
"Mom..is also crying every day.. Please sir..I want to see my anty.. Ameera..." Salem lumshe idanuwa yayi da affan yace mom dinsu tana kuka kullum, yasan hannunka baya rubewa ya yarda
"What the fuck have been doing keeping people's child.. Ina ruwana da rayuwan ta..." Ya fada cikin ranshi
"No don't say that... She deserve to be taught a lesson of life time.. .." Ji yayi affan nacewa
"Uncle are you there?.." Da sauri Salem yace
"Yes...but am not hearing what you are saying... Because you are crying... Guys don't cry..right?" Yafada kaman ba shiba, kallon shi nayi nace kaima kwananka shida babu ranar da baka kuka
"Yes sir " affan ya amsa mashi
"Don't worry you will talk to your ANTY...but please ka yimin hakuri sai gobe cos ina yola itakuma tana abuja..." Da sauri affan yace
"Yeeeeee...thank you sir..."
"No p...and tell mom not to worry gobe in na koma gida zan kai mata waya..,"
"Sir..daman bata da waya?" Salem dariya yayi
"Ai bata fadamin bata da wayaba so ban saniba...that means bata damu dakuba" yafada yana shuumin murmushi, ahankali affan yace
"Sir daman haka take but we can't do without her..."
"No matsala.. Now tell me ya karatu..."
"Fine..sir...na fadawa class mates dina sir Salem Yusuf sulaiman ne

Please Login or Register in order to submit comment