Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

21

A yanzu da akayi wa su Farida aure Aisha bata da wata matsala a cikin gidanta don sosai Ruqaiya da Zainab ke yi mata biyayya kuma dama dai a yadda yaran suka taso tare da ita bata da matsala dasu.




An gama biki da sati biyu Daddy ya kwashi Aisha da yaranta masu watanni biyar suka tafi umrah sai Zainab da Ruqaiya kasancewar Yaran na hutu.



Mu'azzam kawai aka bari a gida don har lokacin Daddy ba wai ya huce daga fuahin da yakeyi dashi bane. A lokacin da Daddy yayiwa Aisha maganar tafiyarsu Umrah sosai tayi murna sai ta tuna lokacin da Farida tayi ta mata kafafa akan zasuyi tafiya su barta to itama yanzu gashi nata lokacin yayi don dama komai yana da lokacin.




Sosai Ruqaiya da Zainab ke taimaka mata wajen rainon twins, duk da Daddy na fadan yawan bawa yaran twins da take yi wai kar su kada su. Idan yana fadanshi kawai sai dai tayi dariya tana mamakin son 'ya'ya irin na Daddy shi komai a harkar yaranshi idonshi yana kai.



Sai dai ta sakawa ranta cewa ita kam bazata yadda ya bata mata yara ba irin yadda yayiwa su Ummie shine kuma dalilin da yasaka suke taka kowa ba tare da fargaba ba don sun san komai sukayi a wurin ubansu ba laifi bane.




Sai da sukayi sati uku sannan suka dawo gida nigeria, gaba daya a wannan lokacin Aisha ta canja ta kara yin kyau saboda kwanciyar hankali data samu ga uwa uba soyayya da kulawar mijinta data samu.



Bayan sati daya da dawowarsu ne Daddy yace ta shirya ta rakashi gidajensu Ummie yaje yaga dakunansu don tun da akayi auren bawai yaje bane.



Tayi shirinta cikin atamfar super exclusive kalar navy blue da ratsin fari da light yellow a jiki sai tayi amfani da farin mayafi da takalmi. Bata dauki jaka ba sai wayarta data rike a hannunta.



A gida ta bar twins qurin masu rainonsu kuma ganin su Ruqaiya na gidan yasa bata damu sai ta fita dasu ba.



Gidan Farida suka fara zuwa, Daddy yace ta shiga ta sanar musu da zuwan shi. Ta shiga cikin gidan da sallama, a main parlour su ta tarar da uwargidan Faridan tare da yaranta da maigidan.



Cikin girmamawa sosai matar ta karbeta duk da cewa zata iya girmewa Aisha. Bayan sun gaisa ne Aishan ke tambayar Farida tace mata tana dakinta ta saka yarinyarta ta raka Aisha.



Kafin su wuce ne Aisha ke sanar musu cewa tare da Daddy suke ai kuwa maigidan naji yayi hamzarin tashi yana cewa bari yaje ya shigo dashi.



Ta shiga dakin Farida tana ta kwala sallama amma ba'a amsa ba don haka ta zauna a parlour tacewa yarinyar ta shiga dakin ta yi mata magana. Ta shiga babu dadewa ta fito ta ce mata wai gata nan zuwa.



Tayi zaman fiye da mintuna goma kafin Farida ta fito tana yatsina fuska ta zauna. A dakile tace mata ina yini, lafiya kawai Aisha tace mata tace "tare muke da Daddynku yace na rakoshi yaga gidanku so yana kasa idan kinga dama kina iya zuwa ki gaisheshi".



Jin cewa yare suke da Daddy ya sa tayi saurin tashi ta fita. Ta dan jima kafin ta dawo, kamar bazata yiwa Aisha magana ba sai kuma tace mata "Daddy yace kije ku tafi" mikewa tayi ta ajiye mata ledar tsarabarta tace mata "to Allah ya bamu alkhairi" bata jira amsawarta ba ta fice.



Daga gidan Farida gidan Ummie suka nufa. Anan ma Daddy bai shiga ba. Ita kam Ummie ta karbeta da mutunci da murnarta har tana tambayarta twins tana cewa me yasa ba'a zo dasu ba.



Bayan sun gaisa ne take sanar mata cewa tare suke da Daddy. Sosai tayi murnar jin Daddy yazo gidanta. Tashi tayi ta shiga part din maigidan ta sanar mishi, babu wani dadewa kuwa ya fito.



Har kasa ya tsugunna ya gaida Aisha sannan ya fita don ya shigo da Daddy. A parlourshi ya saukeshi don haka can Ummie ta bishi ta gaidashi. Sun danfi dadewa a gidan Ummie sannan Daddy yace ta fito su tafi.



Itama ajiye mata tsarabarta tayi sannan sukayi sallama ta fita. Har wurin mota suka raka su sunata godiya. Ummie na rokon Daddy don Allah ya bari su Ruqaiya suzo mata don tunda akayi auren ya hanasu zuwa.



A hanyarsu ta komawa gida ne ya biya da ita grand square sai dai be yadda ta shiga ba, bayan ya fito ne ya miko mata leda mai dauke da turaruka designers guda uku. Sai kuma chocolates da biscuits na yara.



UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ
'YA'YAN MIJI
๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ

Na Umm Asghar

22

Tunda ta tashi yau bata zauna ba. Aiki takeyi kamar bazata gama ba. Ita kam wannan abu ya isheta ace aikin kenan kullum ta tashi bata da hutu, tace tana bukatar cook ance a'a ta bukaci house help nan ma yace mata a'a. Gashi yanzu ya kawo mata aikin girki wai zaiyi baki bayan duk wannan wahalar data keyi ta kuma san ba appreciating zaiyi ba don kullum tayi girki sai ya kushe. Ita kam har ga Allah bazata iya ba don ko a gidansu bata saba da aikin wahala ba kitchen kuwa kwata-kwata basa shigar shi da sunan girki.



Yanzu wannan aikin abincin ya zatayi dashi fisabilillahi tunda dai yasan ba iyawa tayi ba. Tana tsaye a kitchen din ta tasa kayan aikin a gaba tana kallo ya shigo ya kare mata kallo ganin yadda ta doka tagumi tana kallon kayan ya kara bata mishi rai. Tsaki yayi abinda ya maido da hankalinta gareshi. Cikin dakewa yace mata "su Maryam zasu zo su tayaki aikin amma na yau kawai, gara tun wuri kisan me kike ciki don bazan dauki wannan sakarcin ba. Ace kina 'ya mace amma baki iya komai ba, I've had enough of ur nonsense. Duk yadda zaki yi ki koyi tsaftar muhallinki da girka abincin gidanki kije kiyi don na gaji da barnar Kudina kina mini asara" wani tsakin ya karayi kafin ya fita ya bar mata kitchen din.



Har cikin ranta taji dadi da yace su Maryam suzo su tayata aikin sai dai kuma bata san ya yake so tayi ba wajen koyon girki. Ita yanzu wa zata samu da zata na koya mata girki har ta iya, mts ita fa harka da kitchen ma kwata-kwata batayi mata ba. Ita kam Farida taji dadinta wallahi komai tana kwance za'ayi mata shi amma ita nan gata an saka ta a gaba kullum cikin fadan wani kuskure nata yake.



Da taimakon kannenshi Maryam da Amina suka hada lafiyayyen lunch inda suka yi musu arabian zirbiyan da farfesun kayan cikin rago da potato salad sai zobo drink din daya wadatu da cucumber da kayan kamshi.



Sun shirya table tsaf sannan suka kara kimtsa gidan sukayi wa Ummie sallama cewa zasu koma gida don suna zuwa islamiyya. Sosai taji dadin aikin da suka mata, da zasu tafi ta musu kyautar kayan kwalliya da turare.



Tun bayan tafiyarsu take tunanin abinyi akan matsalarta, kamar tace musu su rinka zuwa suna koya mata abubuwan da suka danganci girki sai kuma taji kunyar yin hakan kannen mijinta nefa, to ko Farida zata kira ta bata shawarar yadda zatayi. Kai a'a tasan halin Farida sarai bawai zata bata wata shawarar arziki bane.



Idanunta ne taji sun cika da hawaye, sai yau ta kara tabbatar da tayi rashin uwa don kuwa da Mami na nan tasan da bata shiga cikin matsalar da take ciki ba yanzu tasan babu yadda za'ayi ayi aurenta ba tare da Mami ta koyar da ita kula da hidimar gidanta ba.




Ta jima tana kuka kafin ta rarrashi kanta tayi shiru, gashi Abdulhalim tunda suka ci abinci da abokanshi suka fita bai dawo ba. Wayarta ta janyo ta kira Yaya Khalifa.



Yana amsa wayar ta saka mishi kuka, sosai ta tayar mishi da hankali jin kukanta. Da kyar ya lallasheta tayi shiru sannan ya bukaci yaji damuwarta. Cikin rishin kukan ta sanar dashi duk abinda Abdulhalim yace ta karasa da fadin "ni bansan ya zanyi ba Yaya Khalifa wallahi na gaji komai nayi a gidannan baya appreciating sai yayi ta fada bayan kuma yasan cewa ban iya ba".



Shiru Khalifa yayi ya ma rasa me zaicewa Ummie, ganin shirun shi bazai taimaketa da komai ba yada yace mata "why not da bazaki nemi Aunty Aisha ba ina ganin idan har kika gaya mata zata san yadda zata bullo wa al'amarin kuma kinga catering ta karanta so ko ita ma ai zata iya koya miki girkin, amma
ke me kike gani".



Tasan Aunty Aisha bazata ki koyar da ita ba to amma tana jin kunyarta ganin irin rashin mutuncin da suka dinga mata. Jin tayi shiru bata amsa ba yasa Khalifa yace "bafa nace lallai ne sai kin nemeta ba na ga ne kamar ita yafi dacewa ki nema don ina ganin bazata ki taimaka miki ba".



"Banki ta taka ba Yaya Khalifa kawai dai ina jin kunyarta ne akan abubuwan da suka faru amma zan kirata a waya In Sha Allahu, nagode Yaya Khalifa". Sosai yayi mata nasiha kan hakuri da juriya a dukkan al'amuranta.



Ta jima tana juya wayarta tana contemplating kiran Aisha a waya ko kar ta kirata. Daurewa kawai tayi tayi dialling number, bata jima tana ringing ba taji amsawarta da sallama.



Cikin dauriya sosai ta iya amsa mata sallamar sannan ta gaisheta tare da tambayar lafiyar twins dasu Zainab. Da kyar ta iya yi mata bayanin dalilin kiran datayi mata. Shiru Aisha tayi tana saurarenta ba tare da ta katse ta ba har saida ta lura cewar ta gama maganar sannan tace mata "ina ganin abinda za'ayi shine ki nemi izininshi sai ki rinka zuwa gida muna yin girkin tare har ki kware batun gyaran gida kuma Ummie dole ne ki cire lalaci da kyuiya ki zage damtse kike gyaran muhallinki, kuma ma idan banda abinki ke da ba yara gareki ba ya za'ayi ki dinga barin gidanki yanayin datti ai bazai yiwu kice wai sai gidanki yayi datti sannan zaki gyara shi ba. Idan kina kula da gyaranshi akai-akai ko ace wata rana zaki tashi baki gyara ba ba za'a gane ba don yana samun kula. Kiyi kokari ya barki kina zuwa gidan sai ku tsara ranakun da zaki na zuwa idan d weekends ne to idan kuma ranakun aiki ne ma dai duk ina gida amma ina ganin kamar weekdays din zaifi tunda lokcin yana wajen aiki sauran bayani kuma sai kinzo gidan".



"Nagode sosai Aunty Aisha Allah ya saka da alkhairi In Sha Allahu zanyi mishi maganar nasan ma bazai ki ba duk yadda mukayi kuma zan kiraki a waya sai na shaida miki".



Sosai taji dadin maganar da sukayi da Aunty Aisha, In Sha Allahu kuma zata gyara al'amuran gidanta don kuwa tana son mijinta sosai bata so tana yawan bata mishi rai kuma ita ma tana so taga tayi abinda zata burgeshi har ya yaba mata.



UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ
'YA'YAN MIJI
๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ

Na Umm Asghar

23

Kusan sati biyu kenan kullum da safe Ummie ke zuwa gida wurin Aisha don koyon girki. Zuwa yanzu kam Alhamdulillahi tana iya shiga kitchen tayi girkin abincin kuma a cinye ana santi. Ita kanta tana jin dadin yadda kullum tayi girki Abdulhalim ke yabawa don tun baya yadda cewa ita keyi har ya yadda don Aunty Aisha tana directing dinta ne kawai amma komai ita keyi aikin Aisha kawai ta saka ido.




A yammacin wata talata ne Aisha na zaune tare da Daddy a parlournshi na sama, yana karatun jaridar daily trust ne ta ranar ita kuma tana kallon tashar Africa magic hausa sai dai ba duka hankalinta ne akan kallon ba tana kula da twins da suke wasa.




Zainab ce ta shigo parlour da sallama sannan ta durkusa tacewa Aisha "Mummy Yaya Farida ce tazo tana parlour a kasa", jim Aisha tayi cikin tunanin lafiya Farida tazo yanzu da yamma don magriba ma ta kusa kuma ita din tun bayan aurensu zuwanta gidan baifi a kirga ba shima kuma bata fin mintuna goma take tafiya.



Tashi tayi ta sauka zuwa parlournsu na kasa. Farida na zaune akan kujera double seater ta hada kai da gwiwa. Koda Aisha ta shiga parlour bata dago ba ga alama bata ma san ta shigo parlourn ba har saida Aishan ta mata magana sannan ta dago kanta. Fuskarta tayi jajawur alamun taci kuka ta koshi.



Ganinta a haka gaba daya sai Aisha ta rude cewa takeyi "Farida lafiya wani abu ya faru ne ko baki da lafiya, ina maigidan? Me ke faruwa ne, kiyi mini magana mana". Gaba daya Aisha ta manta wacece Farida da irin zaman da sukayi tare yanayin data ganta a ciki ya sanyayar mat da jiki sosai.



Ita dai Farida banda kuka babu abinda takeyi tun Aisha na bin kanta don taji damuwarta harta gaji ta kyaleta. Suna zaune a wurin akayi kiran sallar magriba don haka Aisha tace mata "ko meye yake damunki hakuri zakiyi ki fawwalawa Allah al'amuranki ita wannan rayuwar da kike gani hakuri shine jigonta dolene ki koyi hakurin zama da mutanen da Allah ya hada ki dasu. Yanzu ki tashi kiyi sallah in yaso sai ki samu Daddy kuyi magana".



Bata jira jin amsawar Farida ba ta haya sama don yin sallar magriba. Sai da ta fara shiga parlour Daddy ta dauki 'yanbiyu ta mika su wurin nannysu sannan ta wuce dakinta tayi sallah. Koda ta idar bata tashi ba sai bayan da tayi salkar isha sannan ta fito.




Ta samu su Zainab da Ruqaiya akan table suna jiransu don yin dinner amma har lokacin Daddy bai fito ba. "Zainab je ki kira Farida tazo taci abinci" Aisha tace mata. Tashi tayi ta nufi aiken da akayi mata, dawowa tayi tace mata wai tace ta koshi.




Cewa tayi da yaran suci abincinsu kawai ba tare da sun jira Daddy ba. Bayan sun gama cin abincin ne ta koma sama don ta tambayi Daddy ko akwai abinda yake son ci ta mishi don tunda taga bai sauko dinner ba tasan ba cin abincin zaiyi ba.




Koda ta shiga parlour ta iske shine tare da Farida tana zaune a kasa akan rug din tsakiyar kanta a sunkuye a kasa sai dai hakan bai hana kukanta fitowa ba. Juyawa tayi zata bar parlour Daddy ya tsaida tare da cewa "ya zaki fita ko ba wurina kika zo ba" yace yare da kashe mata ido daya๐Ÿ˜‰.




Murmushi kawai tayi amma sosai Daddy ya bata kunya. Cewa tayi "na gani ne dama baka sauko kayi dinnwr ba shine zan tambayeka ko akwai wani abu da kake so na shirya maka kafin dare yayi". "Thanks for the gesture amma bana bukatar komai sai tea sai ki hada mini da cake, ai akwai ko?" tace "um akwai" ta juya ta bar parlour.




A lokacin da suka zo kwanciya ne Daddy ke fada mata dalilin zuwan Farida wai mijin ne ya korota saboda tana da matsala da matarshi da yaranshi yace bazai iya zama da matar da bata son 'ya'yanshi ba. Ita kuma Farida tace wai yaran ne keyi mata rashin kunya kuma wai uwarsu ke saka su ba kuma tayi magana ba sai yace ita fitinanniya ce bata son zaman lafiya shi yaranshi nada tarbiyya baza suyi mata rashin kunya ba.




Shiru kawai Aisha tayi bata ce komai ba sai dai cikin ranta cewa takeyi alhaki ai kwikwiyo ne hakanan kuma sharri dan aike ne duk inda yaje zai dawowa maishi. Tana tuna yanda Farida ta takura mata a zaman gidannan ta kuma yi sa'a komai tayi daidai ne a wurin Daddy bata laifi yanzu gashi abin ya dawo kanta.




Sai dai bazata iya fitowa ta gayawa Daddy hakan ba don haka tace mishi "to yanzu wanne mataki zaka dauka don kasan bazai yiwu ja yanke hukunci ba tare da kaji ta bakin maigidanta ba ko", yace "hakane nayi tunanin kiranshi muyi magana sai naga dare yayi amma In Sha Allahu gobe zan nemeshi don naji ta bakinshi amma idan har abinda tace mini gaskiya ne shima bai kyauta ba ai yaran yanzu ba abin yarda bane bazai yiwu ka bashi shaida ba farat daya".




Wannan rayuwar da abin mamaki take, shine kawai abinda Aisha ke cewa a cikin ranta don sosai Daddy ya bata mamaki jin cewar da yakeyi wai mijin Farida bai kyauta ba tunda yabi bayan yaranshi bayan shi dinma haka halinshi yake akan yaranshi sam su basa laifi sai dai kai ka saba musu amma badai su suyi maka ba.



Washegari ne bayan Daddy ya dawo daga office mijin Farida yazo. A parlourn bakinshi ya sauki surikinnashi. Sai bayan sun gama gaisawa ne sannan suka fara tattaunawa akan maganar inda yake shaidawa Daddy cewa Farida bata so ko yaya taga yaranshi sun rabeshi sai ta hau harare -harare tana zare musu ido shine yasa ma ko dakinta basa shiga haka nan kuma ta raina matarshi ko gaisheta batayi gashi sai tace wai bata yadda yayi hulda da matarshi ba shi kuma ya gaya mata cewa yana son matarshi bawai ya daina sonta bane yasa ya aureta shi kuma baiga diya macen da zai aura ya wulakanta Matarshi akanta ba, idan taga bazata iya zama da ita ba to sai dai ita ta fita ta bar mata gidanta.




Shiru Daddy yayi yana saurarenshi sai dai ranshi idan yayi dubu ya baci da rashin arzikin da Farida keyi a gidanta don kuwa shi ta zubarwa da mutunci don duk wanda yaji abinda takeyi a gidanta zaice ne bata samu tarbiyyar arziki ba a gidansu.




Hakuri ya bawa mijinnata yace mishi kuma In Sha Allah hakan bazai kuma faruwa ba don sosai zai ja mata kunne akan hakan. Sun rabu akan cewa sai gobe zata koma gidan.

*****

Kuyi hakuri da wannan wallahi kaina ciwo yakeyi dauriya kawai nayi nayi typing wannan, sannan kuyi hakurin rashin jina kwana biyu bana samun caji ne a wayata kusan kullum a kashe take yini lokacin dazan samu cajin kuma dare yayi.



UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ
'YA'YAN MIJI
๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ

Na Umm Asghar

24

Ranshi a bace ya shigo gidan. Tun daga kasa yake kwalawa Farida kira. Gaba daya jikinta ne ya dauki rawa jin yanayin da Daddy yake kiranta. Allah yasa dai ba wani laifin tayi ba don tun jiya dama a tsorace take da Daddy ganin bai wani bata goyin baya ba akan rikinsu da maigidanta.




A kasalance ta fito daga dakin don zuwa amsa kiran Daddy. Bata taba zaton akwai wata rana da zata ji tsoron haduwarta da Daddy ba irin yau don yanayin kiran da yake mata sosai ya kidimata. A bakin kofar dakin sukayi kacibis da Aisha da tazo kiranta. Ce mata kawai taje Daddy na kiranta ta wuce zuwa dakinta.




Da kyar Farida ta iya jan kafafunta ta wuce zuwa parlour Daddy. A hankali tamkar bata so tayi sallama, sai bayan daya amsa sallamar ne ta shiga cikin parlour. Durkusawa tayi tace "Daddy ina yini, gani ance kana kirana". Shiru ne ya ziyarci parlour tamkar babu kowa. Shi dai Daddy kallon Farida kawai yakeyi yana mamakin irin halayen yarinyar da abubuwan da mijinta yace tana yi mishi. Sai dai kuma yasan shine babban mai laifi a duk wani hali da Faridan ta kasance a ciki.




Tun tasowarta ya kasancevmai nuna bambanci tsakaninta da 'yanuwanta baya son laifinta ko kadan komai tayi a wurinshi daidai ne. Wani irin so yake yi mata da baya yiwa 'ya'yan daya haifa. Sosai yake tausayinta da maraicinta yana ganin duk duniya bata da sai shi tunda bata san ubanta ba. Kullum cikin nuna bambanci yake tsakaninta da 'yanuwanta don ko abu ne ya hadasu to baya taba bata laifi koda kuwa itace bata da gaskiya sai yace au aukw tsokanarta.




Akan haka sun sha samun sabani da Zainab don tana yawan gwada mishi cewa ba daidai bane abinda yakeyi. Bazai yiwu tayi tsokana ba sannan a bawa wanda t tsokana laifi ba wannan ba adalci bane amma sai ya rufe ido ya hau fada yana cewa don ba 'yarta bace yasa take ganin abin da yakeyi a kanta a matsayin rashin kyautawa amma da 'yarya ce yasan ko daga kai baza tayi ta kallesu ba.




A duk sanda irin haka ta faru sai tace mishi "wannan sangartawar fa da kake yiwa Farida ba gata ne kake yi mata ba domin kuwa ita din 'ya mace ce kuma wata rana gidan aure zata je, babu kuma mijin da zai dauki rashin da'a da rashin tarbiyyarta. Wannan wacce irin rayuwace ace yaro duk abinda yayi daidai ne baza'a mishi fada ba idan nayi magana kace na takura mata saboda ba 'yata bace nana tausayin maraicinta".




A yau ga wata rana din da Zainab ke yawan gaya mishi tazo gashi miji ya koro mishi Faridanshi akan halayenta marasa kyau. Allah ya jikan Zainab yayi mata Rahama, har kullum yana jin kewarta tana damunshi ya sani a zamansu bai kyuata mata ba don kuwa bai bata dama tayiwa yaranta irin tarbiyyar da take so ba. Dagowa yayi ya kalli Farida da jar lokacin take a durkushe tana sharar hawaye. A lokacin daya shigo daga ganawarsu da mijinta ranshi a matukar bace yake shine ma dalilim da yasa ya shigo yana kwala mata kira abinda ya fito da Aisha daga kitchen tana tambayarshi lafiya. Zaunar dashi tayi ta kawo mishi ruwa yasha sannan tace mishi bawai zai samu Farida da fada bane, nasiha zaiyi mata ya nuna mata cewa baya son munanan halayenta baiji dadin yadda take tafiyar da al'amuran gidanta ba a cikin nutsuwa ba wai da fada ba.




"Yanzu maigidanki ya bar nan mun kuma tattauna akan yanayin zamanki dashi da kuma iyalinshi. Banji dadi ba yanda yace wai bakya girmamashi bakya girmama matarshi sannan kuma bakya son 'ya'yansgi ba kyaso kiga yana kyakkyawar mu'amala dasu. Wanne irin sonkai ne dake Farida, yaya zakije gidan mata da 'ya'yanta kice wai mijinta bazai yi hulda da ita ba, to a ina aka taba irin haka.




Ai kema kinsan bakiso a zauna lafiya ba. Kin kuma dauki hanyar nesanta kanki ne da mijinki don ko ni nan bazan taba son matar da bata son iyalina ba. Don haka ina horonki da idan kin koma gidanki ki sake tsarin mu'amalarki da maigidanki da kuma iyalinshi.




Dole ne kiso 'ya'yanshi ki kuma yi kyakkyawar mu'amala dasu domin kuwa jema 'ya'yanki ne tunda kina auren ubansu kuma idan har son gaskiya kike yi mishi dole ne kiso duk wanda ke tare dashi don haka tsakaninki da matarshi girmamawa ne ban yarda naji ance kin raina ta ba.




Sannan kuma Farida dole ne ki kasance mai yin biyayya ga dukkan wani umarni na mijinki idan har bai kasance sabon Allah ba. Rashin da'a da tsiwa ba zai sa ki samu soyayyar mijinki ba sai dai ma ya nesanta ki dashi don haka inaso ki ajiye duk wani hali naki marar kyau ki aro kyawawan halaye ki yafa don kema ko zama tauraruwa a wurin mijinki.




Idan kinyi hakan kuma ba wani kika mutunta ba saini don wannan zai nuna cewa kin fito daga gida na tarbiyya tunda gashi kinyi ba daidai ba an gyara miki kuma kin dauka. Allah yayi miki albarka ya albarkaci rayuwar aurenki, tashi kije sai ki shirya gobe In Sha Allahu zaki koma gidanki".




Tunda Daddy ya fara magana Farida ke kuka har lokacin daya sallameta. Tashi tayi ta koma daki ta kwanta. Maganganun Daddy ne kawai suke dawo mata a ranta. Ta sani tana son mijinta sai dai kuma tana tsananin kishinshi da ko yaranshi bata so taga yana basu lokacinshi bare uwarsu.




Gashi kuma akayi dace yaran ba da'a ne dasu ba wannan ne yasa ta karaji yaran basuyi mata ba. Kasancewar ta saba a gidansu komai take sobshi take samu yasa tayi tunanin a gidan mijinta ma haka ne zai kasance sai taje ta tarar kwata-kwata rayuwar ba iri daya bace.




Mijinta wani irin mutum ne me son kanshi, bata usa tace anyi mata wani abu ba kama daga yaran har uwarsu sai ya rufe ido ya hau zazzaga mata masifa yana cewa bata isa ta rabashi da familynshi ba don sune rayuwarshi. Kuma fa sunayi mata

Please Login or Register in order to submit comment