Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

a cikin yaran gidan. Ko bi ta inda suke batayi don hatta da Yaya Khalifa da Mu'azzam sun daina amsa gaisuwarta. Ruqaiya da Zainab ne kawai basu canja mata ba watakila kuma don su din yara ne basu fahimci me ke faruwa ba.



Ana saura kwana biyu daurin auren ne Hajiya tace ta shirya Mallam Adamu ya kaita gida. Duk da ba taron biki zasuyi ba anan amma tasan acan 'yanuwanta baza su kasa yin yinin biki ba.



Bata debi wasu kaya ba sai kayan data ware zata bayar. Koda tayiwa su Ummie sallama ba wacce ta kalleta a cikinsu.



Ta iske gidansu a cike da mutane, su kam hidimar biki sosai sukeyi. Tana shuga aka fara mata guda ana ga amaryara ta iso. Ita dai yake kawai takeyi.



Dakin Goggo ta shiga gaba daya jikinta yayi sanyi. Sai yanzu data ga mutane a gidan ta kara yarda bikinta akeyi. Har ga Allah baso aurennan takeyi ba to amma bata da yanda zatayi, bazata iya cewa Hajiya bata son danta ba bayan dukkan abinda ta mata ga kuma Babanta da bayada wani buri bayaga na ganin aurenta.



An daura auren Ja'afara Bello Danmaliki wato Daddy da Aisha ranara asabar da misalin karfe biyu da rabi anan kofar gidansu dake garin gaya. A bangaren ango dai ba wasu mutane bane da yawa suka halarta don bazasu wuc mutum goma ba har shi angon.



An shirya nr akan cewa da an gama daurin aure za'a wuce da amarya. Mutum biyu ne aka shirya zasu raka Aisha gidanta duba da yanayin da bikin yazo musu.



Sosai Babanta yayi mata nasiha ya nuna mata cewa kyakkyawan halinta da nagartarya ne suka saka Hajiya yin sha'awar hadata aure da danta don haka yana so ta cigaba da portraying kyakkyawar dabi'arta ta rike yaran mijinta da amana.



An fito da ita tana kuka sosai don har yanzu ta kasa yardarwa kanta wai itace aka daurawa aure da Daddy. An sakata a motar da dama don tafiya da ita aka zo tare da 'yan rakiyarta.



Sun shiga gidan ana kiran sallar magriba. Ita dai banda faduwa babu abinda gabanta keyi. Tana lullube a cikin mayafi aka shiga da ita cikin gidan.



Gidan shiru babu kowa sai Hajiya da suka tarar a parlour. Ita tayi musu jagora zuwa dakin Aisha dake a sama. Bayan fitarta ne su Yaya Huwaila da Yakumbo Dije ( kanwar Babanta) da suka kasance 'yan rakiyarta suka fara haramar yin sallah.



Yakumbo Dijevce tacewa Aisha ta tashi tayi sallah. Sai a lokacin Aisha ta bude idonta, dakin tabi da kallo. Dakin da Mami take saukar bakinta ne sai dai an canja kayan ciki. Gado ne da wardrobe da madubi kirar italy.



Dama Babanta ya fada mata cewa Hajiya tace ita zatayi mata kayan daki, da gani babu tambaya don tasan Babanta bazai iyayi mata irin wannan kayan ba.

CIGABAN LABARI


UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ
'YA'YAN MIJI
๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ

Na Umm Asghar

15

Tsaye take a kitchen tana shirya abincin dare. Tuwon semovita takeyi da miyar kuka. Ta gama tuka tuwon ta kwashe a cikin warmer ta kada miyar kenan Farida ta shigo kitchen din hannunta rike da farar roba irin wadda ake zuba yaji, tukunyar miyar ta bude ta juye abinda ke cikin robar.




Kallonta kawai Aisha ta tsaya yi tana mamakin irin wannan hali na Farida. Ganin zata fita daga kitchen dinne yasa ta mata magana tace "miye wannan kika zuba mini a miya Farida?" Murmushi ta saki wanda da an gani an san na mugunta ne tace "oh wannan, wani spice ne da zai karawa miyarki dandano, shinshina robar kiji" ta tura mata robar hancinta tana dariya.



Cikin takaici Aisha tace "wai lalle nebkika zuba mini a girki Farida". Dariyar shakiyanci tayi sannan ta juya ta bar kitchen din. Tsabar takaici Aisha ji tayi kamar tayi kuka.



Wulakancin Farida ya fara isarta, idan banda wulakanci ya za'ayi ta zuba mata lalle a cikin abinci da gangan. A yau dai kam bazata kyaleta ba don ta lura shirun da takeyi musu ne yasa suke yi mata abinda suka ga dama.



A yau dai kam sai taji dalilin irin wannan cin kashi da suke mata. Kashe cooker din tayi ta nufi parlour don taji dalilin Farida nayi mata abinda tayi.



Turus tayi ganin Daddy tare da duka yaran a cikin parlour din. Bata san cewa ya dawo gidan ba. Sannu da zuwa tace mishi a yayin da take karasawa cikin parlour. A takaice ya amsa mata da yauwa ba tare da ya dago ya kalleta ba.



Komawa tayi kitchen ta hado ruwa da kemo ta dora akan tray hadevda cups ta kawo mishi. Sida stool ta janyo gabanshi ta dora tray din akai tare da tsiyaya mishi ruwan a cup. Tana dagowa taga yaran duka na banko mata harara.



Dauke kanta tayi ta samu wuri ta zauna cikin sanyin jiki. Tana jinsu suna hira shi da yaranshi tamkar babu ita a wutin haka sukayi mata. Dama kuma idan da sabo yaci ace ta saba don idan suna wuri tazo ta zauna yi sukeyi tamkar basu san da zamanta ba.



Cikin muryar shagawaba Farida tace "Daddy me ka sayo mana ne tun dazu nake hararar ledojin daka shigo dasu", gaba daya suka saka dariya. Mu'azzam yace "eh wallahi nima dai hankalina yana kan ledojinnan". Murmushi yayi jin abinda suke cewa, mika musu kayan yayi yace gashinan kowa daya. Ga matan dai laces ne ya saya musu mazan kuma voile.




Gaba daya suka hau murna hade da yi mishi godiya. Duk da kyautar da aka musu idanun Farida na kan ledar dake aje a gefe. Cewa tayi "Daddy wannan kuma fa ko naka ne" a yayin da take daga ledar don taga abinda ke ciki.



Laces ne a ciki guda biyu sai dai da gani a idon ansan babu tambaya yafi wanda ya basu kyau da tsada. "Daddy nidai wannan nake so don yafi wancan kyau ko kuma ka hada mana gaba daya kawai". "Ajiye Farida wannan na Auntynku ne" yace mata.



Wani banzan kallo ta watsawa Aisha sannan tace "please Daddy wallahi tunda naga wadannan naji sun shiga raina don Allah" cikin murya irinta shagwababbun yara tayi maganar.



To shikenan ku dauka ita sai a saya mata wani" yace a lokacin da ya mike don hawa sama. Ihun murna Farida ta saka suka tafa da Ummie suna murna.



Ummie tace "amma gaskiya Farida kin burgeni ni ai bazan iya abinda kikayi ba, ko da yake dama ke Daddy's pet ce he never says no to you shi yasa kikeyin abinda kika ga dama".



Ta wani kada idanunta ta juyasu sannan tace "ato da ni din ta wasa ce, ai wallahi yarinya kadan ma ta gani idan dai nice. Ita har ta isa ta saka wannan lace din shima Daddy da taya bera bari. Ban gaya muku na kara mata maggi da gishiri a cikin miyarta bako, ai yau zakuci delicious".



Sai a likacin Aisha ta tuna da abinda Farida ta mata. Tashi tayi ta koma kitchen din don ta hada wata miyar tunda dai waccan ta lalace bazata ciwu ba. Tana jin Farida na gaya musu ai lalle ta zuba mata a cikin miya suna dariya.



A ranar wata asabar da dare ne suna zaune gaba dayansu a parlour suna kallo. Ita dai Aisha homework taje koyawa Zainab. Daddy ne ya shigo da sallama. Dukansu suka amsa suna mishi barka da shigowa. Ledar dake hannunshi ya ajiye akan center table yace yana mai kallon Aisha "ga nan nama" "mun gode Allah ya saka da alkhairi" tace mishi.



Bai zauna ba sama kawai wuce. Yana hayawa Farida tayi zirif ta dauke ledar naman ta nufi kitchen, tashi Ummie tayi tabi bayanta. Kwalowa Ruqaiya kira sukayi, tashi tayi taje amsa kiran da sukayi mata.



Sai gata ta dawo da plates guda biyu a hannunta ta mikawa Yaya Khalifa da Mu'azzam sannan ta koma ta dauko nasu ita da Zainab. Tare suka fito dasu Ummie suma da nasu plate din a hannu.



Wato kenan su sukayi rabon naman ta kuma tabbata basuyi rabon da ita ba. Ko kallonsu batayi ba ta tashi taje ta hada kayan abincin Daddy ta nufi sama don bata tsammanin zai kuma saukowa.



Bata sameshi a parlour ba don haka ta wuce cikin dakin. A kwance'akan gado ta iske shi. "Daddy ga abincinka" tace mishi a lokacin da take ajiye tray din a kasa. Tashi yayi zaue sannan yace "kinga kwashe abincinnan ki kawo mini tea kawai sai ki hado mini da naman".



Tsaye tayi a wurin ta kasa gaba ta kasa baya ta kuma kasa gaya mishi cewa babu naman ya kare. Cikin daga murya yace "kinyi mini tsaye a ka bazaki kawo mini bane ko me"?



Cikin fargabar abinda zaice tace mishi "babu naman ne ya kare". "Ban gane da babu ya kare ba, kina nufin gaba daya kuka cinye ba tare da kin dibar mini ba. Ke wacce irin yarinya ce kwata-kwata bakida common sense baki san abinda ya dace ba".



Ta inda ya shiga ba ta nan yake fita ba, fada kawai yakeyi kamar dama irin kiris dinnan yake jira. Sai da ya gaji don kanshi sannan yayi shiru. Hakuri kawai ta bashi ta sunkuya ta debi kwanukanta ta fita daga dakin.



Ajiye kayan tayi ta bude freezer ta fito da naman rago ta yankashi sirarata wanke ta dora a wuta. Sannan ta fito da dakakken kuli-kuli da tomatoes da attaruhu da albasa ta gyara. Tsiren tukunya ta hada mishi sannan ta dafa tea ta zuba a flask ta shirya cikin tray tana jiran naman ya karasa ta sauke.



Koda ta duba taga ya nuna sai ta sauke ta zuba a cikin bowl ta hada akan tray din. Tana cikin wanke tukunyar da tayi amfani da ne taji muryar Ummie a bayanta tana cewa "Farida gane mini ikon Allah, wai matarnan nama tazo ta gasa don bata samu taci wanda Daddy ya kawo ba.



Farida ce ta karaso kitchen din tace "ai kinsan duk wanda bai taso cikin arziki ba idan ya sameshi daga baya cin kwan makauniya yakeyi mishi". Hannunta ta kai zata dauki naman, Aisha tayi caraf ta rike hannun tace "wannan ne kuma baki isa ba, kun rabe wancan a tsakaninku kun cinye ban tanka muku ba ba kuma zakuzi kuce zakuci wannan ba. Duk wacce take so ta bude fridge ta dauka ta dafa amma ba wannan ba".



"Samun wuri, ke nan har kin isa muna son abu kice baza mu dauka. Naga dai ubanmu ne ya sayi kayan ba na wani ba" cewar Ummie kenan. Aisha dai ta kankane namanta ta hanasu tabawa tacec"kome zakuce ku fada nama ne dai bazaku taba mini ba".



Suna cikin hayaniya ne suka ji gyaran muryar Daddy. Gaba daya sai suka shiga taitayinsu don fuskarshi sam babu annuri. "Lafiya kuke mini hayaniya a gida da darennan, ke kuma bazaki kawo mini tea din bane" yace yana maida kallonshi ga Aisha. "Kayi hakuri yanzu zan kawo" tace tana mai daukar tray din.



Ya juya zai bar kitchen din kenan Farida tace"Daddy kaga wai nama muka gani muna so wai bazata nbau ba". Juyowa yayi ya kalleta yace "nama wane iri ba kince babu ba kun cinye". Cikin muryarta mai sanyi tace "eh wancan babu wani ne nayi maka dama".



Yace "kuma shine bazaki basu ba alhalin suna so, to a wanne dalilin. Ku dauka kuje kuci ni bana ci" yace wa su Farida. Bayan ya fita daga kitchen dinne suka kyalkyale da dariya Ummie tace "wayaga cusa kai babu kwarjini".



Ajiye musu bowl din naman tayi ta wuce ta kai mishi kayan tea din ranta a matukar bace. Don takaici a daren har kuka sai da tayi.



UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ
'YA'YAN MIJI
๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ

Na Umm Asghar

16

A safiyar litinin ne bayan ta gama shirya su Zainab ta hada musu abincin break ta sallamesu zuwa school. Nasu breakfast din ta shirya a table sannan ta wuce zuwa dakinta ta yi wanka ta shirya a cikin doguwar rigar material, bata daura dankwali ba sai siririn gyale data yafa a kanta. Turaren ladies ta fesa a jikinta sannan ta fita zuwa dakin Daddy.



Da sallama a bakinta ta shiga dakin. Yana tsaye a gaban wardrobe yana fito da kaya yana ajiyewa a kan gado. A bakin gadon ta zauna bayan ta gaisheshi. Trolley ya dauko ya ajiye sannan yace mata "shirya mini kayannan tafiya ta kamani zuwa abuja zanyi kwana hudu, bari na shiga wanka". Tashi tayi ta shirya mishi kayan daya fitar cikin akwatin sannan ta hau gyaran dakin.



Bayan ta gama ne ta koma parlournshi na nan sama ta zauna, tv ta kunna ta kai tashar mbc2. Bawai kallon takeyi ba sai dai zaman shirun ne ya isheta. Tayi kusan mintu talatin a zaune kafin ya fito. Tashi tayi ta karbi akwatin hannunshi sannan tabi bayanshi suka sauka kasa. Ajiye akwatin tayi a gefe sannan suka nufi table don yin breakfast.



Kasancewar su Ummie suna hutu yasan suna can suna bacci ba da wuri za suyi breakfast ba yasa daga ita sai shi ne a table din. Sau tari tafi sakewa a irin wadannan lokutan da daga ita sai shi ba tare dasu Ummie ba don sukam idan suna wuri sai sunyi sanadin da Daddy ya bata mata rai.



Bayan sun gama breakfast dinne ya mika mata kudi wrpper 'yan dari biyar wato dubu hamsin kenan. Mikewa yayi yana mata sallama akan cewa sai ranar juma'a zai dawo. Har wurin mota ta raka shi tana dauke trolley din, sai bayan taga tafiyarsu ne sannan ta koma gida.



Colonel Ja'afar Danmaliki na kwance akan gadon dakin hotel din da yayi masauki a garin abuja a daren daya samu kwanaki biyu da barin gidanshi. Mamakin kanshi kawai yakeyi yanda tun barinshi kano ya kasance cikin kewar yarinyar.



Bai taba tunanin cewa zaiso wata diya mace a bayan Zainab ba sai gashi yanzu ba tare da yasan lokacin da hakan ya faru ba ya samu kanshi cikin soyayyar 'yar karamar matar tashi.



Yasan harda hakurinta da sanyin halinta wajen taimakawa wurin assasa mishi soyayyarta a zuciyarshi. Muryarta kawai yake so yaji ko zai samu nutsuwa sai dai kuma abin haushin shine ko numberta baya dashi.



To ko a wurin Khalifa zai nem number nata idan yaso sai ya fake da kira don jin lafiyarsu yaji muryarta. Kai a'a da kunya gaskiya ya nemi numberta wurin Khalifa sai dai ko a wurin Hajiya.



Kai yasan abu ne ma da bazai yiwu ba ya nemi numberta a wurin Hajiya idan dai baso yake ya bata mata rai ba. Kawai dai hakuri zaiyi har ya koma gida ai nan da kwan biyu ne babu wani dadewa. Sai dai kuma ganin kwanaki biyun yakeyi kamar watanni biyi koma shekaru don tsayi.



Ya dade a kwance yana juyi ba tare da ya iya yin bacci ba sai tunanin Aisha da ya sakashi a gaba. Da kyar bacci barawo ya lallabo ya saceahi, sai dai baccinnashi ma a cike yake da mafarkanta.



A safiyar alhamis ne Aisha ta tashi jikinta yayi matukar zafi zazzabi ya shigeta. Koda ta tashi ji tayi jiri yana dibanta, komawa tayi ta kwanta. Wayarta dake ajiye akan bedside drawer ta janyo ta kira Lami.



Ko mintuna biyar ba'a rufa ba Lami ta hayo, daga bakin kofa ta tsaya tana sallama. "Shigo Lami" Aisha tace bayan ta amsa mata sallamar. Karasowa ciki tayi sannan ta gaida Aisha.



Bayan sun gama gaisawa ne tace mata ta hadawa su Ruqaiya abincin makaranta sai kuma ta shirya breakfast saboda bata jin dadi bazata iya tashi ba.



Komawa tayi ta kwanta bayan fitar Lami daga dakin. Tana cikin bacci taji an yaye quilt din data rufa a jikinta. Koda ta bude ido Farida ta gani a tsaye a kanta tana huci. "Lafiya" shine abinda tace mata.



Cikin daga murya tacev"eh kin tambayi lafiya mana tunda kin samu wuri har kin nade akan gado kina bacci, idan banda kin samu wuri Lami zaki saka tayi mana abinci. Kevtunda kike a gidannan kin taba gani munci girkin 'yan aiki. To wallahi tun wuri gara ki tashi ki girka mana abinda zamuci idan ba haka ba na sanarwa Daddy".



Quilt dinta kawai taja ta rufa sannan tana daga ciki tace mata "idan kun ga bakwa son na Lamin sai ku shiga kitchen din ku girka amma ni yau bazan iya saukowa ba don kuwa bani da lafiya. Idan kin fita kija mini kofar".



Mamaki ne ya kama Farida don kuwa bata taba zaton Aisha zata iya maida mata martani ba. A nata tunanin shirun da Aishan keyi mata ta dauka tsoronta takeji bata san cewar tsabar rashin son fitina ne yasa take kyaleta.



Cikin sanyin jiki ta fita daga dakin. Dole hakanan abincin Lamin suka ci tundaha na safen har na rana dana dare. Da daren ne Farida ta dauki waya ta kira Daddy don ta kai mishi karar Aisha.



Yana daga wayar ko gaisheshi batayi ba ta fara mishi korafi tana cewa "Daddy karar matarnan na kawo maka yau throughout bata bamu abinci ba sai Lami ce ta girka mana kuma munyi mata magana tace idan baza muci ba mu barshi wai ita ta daina girka mana abinci".



Ajiyar zuciya ya sauke sannan yace "jinan Farida, hakanan Aisha bazata hanaku abinci ba ko dai akwai abinda kukayi mata, nasan halinku fa". Jin abinda abinda Daddy yace ne yasa ta fara matsar kwallar karya tana cewa "wallahi Daddy babu abinda mukayi mata kawai dai bata ga damar yin girkin bane kuma fa dama Daddy kaine bakasan halinta ba amma ba kirki ne da ita ba".



Har cikin ranshi yaji baiji dadin kalamin Farida akan Aisha ba. Hakuri kawai ya bata yace idan ya dawo zai tsawatar mata.



Washegari ma Aisha a kwance ta yini a ranar ma kuma sai Lami ta saka tayi mata girkin gidan. Kasancewar a ranar Daddy zai dawo ne yasa ta daure ta tashi duk da jiri dake dibarta amma a haka ta shiga dakinshi ta gyara ta wanke toilet sannan ta jona turaren wuta a burner.



Dakinta ta koma tayi wanka ta shirya a cikin atamfa super holland kalar blue da ratsin yellow a jiki. Mai kawai ta shafa sai turare data fesa a jikinta ta sauka kasa. Tea ta hada tasha sannan ta fito da naman kaza ta wanke ta dora duk a kokarinta na hadawa Daddy abinci sai dai kuma dauriya kawai takeyi don tsayuwa ma neman gagararta takeyi.



Kamshin tafasar naman ne ya bugeta a take taji amai ya taso mata. Kafin tayi wani yunkuri aman ya taho gaba daya. Anan wurin ta durkushe ta hau sheka amai. Lami dake wanke-wanke a sink ta taho da sauri ta riketa tana mata sannu.



Bayan ta gama aman ne ta kuskure bakinta Lami ta kamata ta maidata daki sannan ta koma ta gyara wurin. Komawa tayi dakin ta tambayeta me take da niyyar dafawa taje ta girka. Cewa tayi kawai tayi shinkafa da miya da salad. Sanin cewa ba lallai ne ya ci ba yasa tace tayi shinkafar don tasan baya cin abincin masu aiki.



Ya shigo gidan ne wajen karfe bakwai da rabi. Bai tarar da kowa ba a parlour kasa don haka ya wuce sama maybe kuma suna dakunansu. Dakinshi ya wuce, sai da yayi wanka yayi Sallah sannan ya fito don yaci abinci. Zuciyarshi fal da tunani Aisha yana mamakin abinda ya hana ta zuwa yi misgi sannu da zuwa. A take maganr da Farida tayi mishi jiya ta fado mishi a rai.



Baiyi wata-wata ba ya nufi dakinta don ganin lafiya. Tunda taje gidanshi a matsayin matarshi bai taba shiga dakinta ba sai yau. Tana kwance a kudundune cikin quilt. Da sallam a bakinshi ya shiga sai dai ganinta a kwance ta lulluba har kanta yasa bai san lokacin da ya karasa gaban gadon ba yana cewa "lafiya Aisha kika kudundune cikin bargo a zafinnan gashi ko fanka ko ac baki kunna ba".



Jin muryarshi ne yasa ta yaye rufarta bude idonta da suka kada suka yi jawur. Tsikar jikinshi ce yaji ta tashi hada idon da sukayi. Zama yayi a bakin gadon sannanyace "baki da lafiya ne, tun yaushe ne bakida lafiya" ya tambayeta yana mai kai hannu jikinta.



Da sauri ya janye hannunshi jin yadda jikinta yayi zafi. "Bari na canja kaya sai muje asibiti" yace a yayin da ya mike daga kan gadon. Baifi minti biyar da fita ba ya dawo yana sanye da shadda getzner kalar light brown dinkin tazarce.



Bargon ya janye sannan ya saka hannu ya dagota. Zaunar da ita yayi ya janyo hijabinta dake ajiye akan sallaya ya saka mata ya mika mata takalmi ta saka ya mikar da ita.



Tana rungume a jikinshi suka fita. Har sai da ya zaunar da ita a cikin mota sannan ya zagaya ya shiga ya tashi motar suka fice. Asibitin da suke da family folder suka je.



Ba wani bata lokaci suka sami ganin likita. Tambayr ta yayi abinda ke damunta tace mishi zazzabi ne sai jiri da take fama dashi sai kuma tashin zuciya. Test ya rubuta ta malaria da kuma ptegnancy test yace suje lab ayi yanzu su kawo mishi.



Bayan sunje sunyitest dinne sun kawo mishi result din ya duba yace "its as i suspected she's 12 wks pregnant sai dai kuma akwai malaria a jikinta. Wani irin farinciki ne ya ziyarci Daddy jin cewar zai samu Baby.



Gaba daya fuskarshi ta cika da annuri har mamaki ya dinga bawa Aisha don bata taba ganinshi a cikin farinciki kwatankwacin wannan ba. Bayan sun karbi magungunanta ne suka tashi suka tafi.



Motsi kadan idan Aisha tayi sai yayi mata sannu, mamakinshi ne kawai ya kamata don bata taba sanin wannan side din nashi ba.



UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ
'YA'YAN MIJI
๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ

Na Umm Asghar

17

Akan Aisha Daddy yayi watsi da policy dinshi na cewa iyalinshi bazasu ci abincin masu aiki ba don kuwa a yanzu kowa na gidan girkin Lami suke ci don laulayi ya sako Aisha a gaba komai taci sai ta amayar dashi.



Sosai take ganin kulawa da tarairaya a wurin Daddy abinda ya kara assasa wutar kiyayyarta a zuciyar yaran don sosai suke bakin cikin ganinta da ciki tun ma dai ba Farida ba.



Sai da cikinta yayi watanni hudu sannan ta samu saukin laulayin. A lokacin ne kuma ta karbi hidimar gidanta duk da dai Daddy yaso ta bari Lami ta cigaba da kulawa da komai amma ta dage akan zata iya don haka ya kyaleta.



A kwance take akan gadon Daddy sai shagwaba take zuba mishi wai jikinta na mata ciwo. Shi kuma ya biye mata yana mata tausa hade da yi mata mitar aikin da take yi ne ya saka mata ciwon jikin shine kuma dalilin da yasa tun farko ya hanata yin aikin taki ji.



Tun tana mamakin kulawar da take samu daga Daddy har ta dain don da farko ma kasa sakewa tayi dashi sai da taga dai da gaske yake janta ajikinshi sannan ta sake ta bar yin dari-dari dashi.



"Um Daddy kana jina" tace mishi cikin muryar shagwaba. Bata fuska yayi yaja kunnenta kadan yace "bana hana ki ce mini Daddy ba, ni ba Daddynki bane Daddyn baby ne" ya fada yana mai shafo cikinta. "Gara ma tun wuri ki daina kirana Daddy nan don banaso, kirani da sunana Ja'afar yafi mini, ok".


"Owch da zafi fa Dad... ow sorry, nifa gaskiya bazan iya kiran sunanka ba gatsau, haba ai babu ma tsari wallahi" ta fada tana mai cuno baki.



Sunkuyowa yayi yay kissing din lips dinta lightly sannan yace "to ki kirani da wani sunan amma ba Daddy ba". Tace to shikenan zanyi tunani, ni kasa na manta me ma zance maka, yauwa dama so nake nace'maka inason zuwa gidan Hajiya na gaisheta".



A take ya bata fuska yace "nifa bana son yawo, ke da baki da lafiya wane fita kuma zakiyi. Ina ce'kuma kusan sau uku Hajiyan tana zuwa dubaki bare kice kin dade baki ganta bane yasa kike son zuwa".



Jikinta ne yayi sanyi jin abinda yace sai dai kuma bazata iya mishi musu ba don kuwa bata saba musu dashi ba komai yace da to take amsa mishi. Sai dai kuma har cikin ranta bata ji dadi ba don har fuskarta sai da ta nuna bacin ranta.



"Fushi kikayi don nace bazaki fita ba" tace "a'a me ka gani" yace "gashinan kin bata rai kin daina

Please Login or Register in order to submit comment