Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

na basu purnishement tunda suka wahalar mini da Mamita".


Sun dade suna hira da Mami kafin sukayi sallama. Tashi tayi ta kaiwa Hajiya wayarta sannan ta zauna suka cigaba da kallon da sukeyi. Ji tayi Hajiya na magana don haka ta dawo da hankalinta gaba daya wurin Hajiya. "Na'am Hajiya me kikace" tsaki Hajiya tayi sannan tace "fadan Maminku nakeyi wai gaya mini takeyi ta gaji hidimar yara tayi mata yawa. Dama ni tunda suka yi maganar tafiya Ummara da yara banji sun saka dake ba shiru na musu ban yi magana ba tunda sun riga sun gama tsarinsu amma ko don ki tayata da hidimar yara ai da sun tafi dake. To shi Jafaru wani irin baudadden hali gareshi abinda yasa kanshi shi yakeyi ni kuwa ban cika son shiga sha'anin gidanshi ba. Ita kuma Zainab tsoronshi takeyi duk abinda yace ko baiyi mata ba bata iya musa mish. Yo dama wadannan malalatan yaran nata me suka iya bare har su tayata da rainon yara, su da basa iya tsinanawa kansu komai bare suyi wa wani".



Aisha dai shiru tayi tana sauraren Hajiya ba tare da ta tanka mata ba.sai dai cikin ranta mamaki ne takeyi wao kenan har Hajiya ma tasn halin Daddy na rashin son mutane su rabeshi, sai dai kuma ba abin mamaki bane tunda itan mahaifiyarshi ce. Ita kam ta sani ko ita karfin zamanta a gidannan Mami ce da don tashi ne da tuni ta dade ba barin mishi gida.



A ranar da tayi sati biyu a gidan Hajiya ya kama washegari su Mami zasu dawo ta shirya ta tafi gidan don ta gyara duk da dai akwai masu aiki a gidan to amma gyaran sama gaba daya aikinta ne 'yan aiki basa gyara musu dakunan barcinsu.



Aikin da tayi ya dauketa tsawon lokaci kafin ta gama. Gidan Hajiya ta koma ta kwana gari na wayewa ta koma gidan din ta shirya musu abinci. Fried rice tayi da coleslaw hade da peppered chicken sai tuwon alkama miyar kubewa busashiya da tayi saboda Daddy yafi son abincin gargajiya fiye da komai.



Karfe biyar da kwata na yamma su Mami suka shigo harabar gidan tare da Mallam Adamu da yayi kanin yini a airport yana jiran saukarsu. Aisha najin tsayuwar motarsu ta fito da sauri tana murna.



A guje Ruqaiya da Zainab suka taho suka rungumeta. Ita ma farincikin ganinsu duk ya cikata. Rike hannuwansu tayi ta karasa wurinsu Mami tana yi musu sannu da zuwa. Gaba dayansu suka dunguma zuwa cikin gida. Dukansu a parlour suka zauna sai Mami da Daddy ne kawai suka haya sama.



Ruwa da lemuna Aisha ta kawo musu tana yi musu sannu. Tana zama Zainab da Ruqaiya suka sakata a gaba da labari. Farida da Ummie kam kujera kowaccensu ta hau ta kwanta yayinda Yaya Khalifa da Mu'azzam suka wuce dining area don cin abinci.



Sai bayan kusan minti talatin sannan Mami ta sauko. Ga alama wanka tayi don ta canja kayan jikinta zuwa doguwar rigar atamfa. Table din ta nufa tana bude kwanuka.



Tashi Aisha tayi ta nufi table din. Durkusawa tayi ta gaida Mami tare da yi mata barka da dawowa. Bayan sun gaisa ne Mami kece mata "sannu a kokari Aisha Allah ya biyaki, duk ke kadai kikayi wannan aikin?" Dariya kawai tayi tace "amin Mami". Hada abincin Daddy Mami tayi sannan ta dauka ta koma sama ga alama dai yau a saman zaici abincin.



Da dare ne bayan anyi sallar isha'i Aisha taja Zainab don ta rakata ta gaida Daddy. A parlournshi na sama ta same shi yana kishingide akan doguwar kujera. Ganinta baisa ya tashi zaune ba. Durkusawa tayi ta gaisheshi tare da yi mishi barka da dawowa.



A dakile ya amsa mata gaisuwar da lafiya. Tashi tayi ta fita ta bar Zainab da tun shigarsu parlourn ta nufi wurin Babanta ta zauna.



Washegari da safe ne Mami ta bata tsarabarta. Dogayen riguna ne masu kyau guda biyu daga Mami sai wani agogon hannu inji Daddy. Sosai Aisha tayi murna da tsarabar da aka bata.



Ruqaiya da Zainab ma matetial suka bata sai Ummie da ta bata kayan bacci riga da wando. Yaya Khalifa kuma ya bata takalmi sai Mu'azzam da ya bata agogo, ta tashi da agogi biyi kenan.



Farida kam ko kallonta batayi ba bare kuma tasaka rai da tsarabarta. To ita dinma bata saka rai tunda dai tasan tsakaninsu da Farida, amma kuma duk ma'aikatan gidan babu wanda batayi wa tsaraba ba har masu gadi.



UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ
'YA'YAN MIJI
๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ

Na Umm Asghar

12
A kwana a tashi nmbabu wuya wurin Allah. Gashi har Aisha ta gama dalilin da yasa ta cewa Mami tana son zuwa gida don kuwa ta dade bata jeba. Sati biyu taso yi amma sai Mami tace tayi sati daya don bata son tana yin nesa da ita. Ba don taso ba ta amince sai don bazata iya musawa Mami ba.



Bayan kwana biyu ne ta shirya ta tafi gaya. Sosai mutanen gidan sukayi murnar ganinta. Goggo ta sauketa da fura da nono da danwaken wake da rogo mai dan karen dadi.



Sosai taci danwaken don ta dade rabon da taci. A kano basayin danwake don yaran gidan duk basa so shi yasa Daddy yace a daina yi tunda babu maiso.



Tana gama cin abincin ta haye gadon Goggo ta kwanta barci inda ba ita ta farka ba sai da la'asar. Bayan tayi sallar ne ta fita zuwa gidan yayarta Huwaila wacce ta kasance babba a gidansu haka kuma 'ya a wurin Goggo.



Da murnarta ta tareta, bayan sun gaisa ne ta kawo mata kunun aya mai dadi tasha kasancewar sana'arta ce saida kunun aya. Suna cikin hira ne ta sako mata maganar aure tace "amma dai zuwa yanzun kin tsaida miji ko don tun dadewa ya kamata ace an aurar dake".



Yake Aisha tayi tace "Yaya Huwaila kenan". Hade rai Yaya Huwaila tayi tace "ban gane da ni kenan ba, kina nufin har yanzu baki tsaida miji ba Aisha kin kuwa san yadda Baba ya damu da batun aurenki? Shiru fa kawai yayi don yana jin nauyin Hajiya bayaso ya nuna musu ikonshi akanki amma banda haka ai da tuni yayi magana akan zamanki a haka don ba so yakeyi ba ko karatun da kikayi don babu yadda zaiyi ne amma da don tashi ne da kina gama secondary school za'a aurar dake".



Gaba daya jikinta taji yayi sanyi jin cewar Baba ya damu da zamanta haka babu aure. Banda abin Baba ma dai miye abin damuwa don takai yanzu ba tayi aure ba tunda dai ba wai ta wuce lokacin auren bane bare ace ta rasa miji. Shine fa dalilin da yasa wasu lokutan bata cika son zuwa gida ba don kuwa idan tazo an dunga yi mata surutu akan rashin aure kenan.



Bata bar gidan Yaya Huwaila ba sai bayan da tayi sallar magriba taci abinci tukunna. Koda ta koma gida ta tarar Baba bai dawo daga masallaci ba kasancewar idan ya fita sallar magriba baya dawowa gida sai yayi isha. Tana shigowa gida ana yin kiran sallar isha don haka ko zama ba tayi ba dauki buta tayi alwala sanna ta gabatar da sallah.



Tana zaune akan sallaya taji shigiwar Baba. Bayan kamar mintuna biyar da shigarshi dakinshi ne ta tashi ta bishi. Da sallama ta shiga dakin sannan ta zauna akan tabarma. "Sannu Baba ina yini" tace tana mai russunawa. "Lafiya lau Aisha, kinzo lafiya" "lafiya lau Baba". "Madalla, ya wajensu Alhaji Jafarun dasu Hajiya duk suna lafiya dai ko?" tace "duk lafiyarsu lau sunce a gaisheku" yace "Masha Allahu, to ya karatunnanki babu dai wata matsala ko".




Tace "Alhamdulillahi, ai Baba harna gama ma" yace "to Masha Allahu, Allah ya bada sa'a. Sai batun aure kenan ko tunda Allah yasa kin gama karatu". Shiru tayi tare da sunkuyar da kai. "Ya kika yi shiru Aisha, ko har yanzu mijin bai samu ba" cikin sanyin murya tace "kayi hakuri Baba".



Shiru ne ya ratsa na wasu 'yan mintuna zuwa can Baba yace "kina jina ko Aishatu, ni da kike ganina bazan yi miki dole ba hakanan kuma bazan zuba miki idanu kiyi ta zama babu aure ba don haka idan har kinsan akwai wanda kika tsayar kiyi gaggawar turoshi idan kuma babu to ki tabbatar da kin samu zaki gabatar dashi dimin kuwa har ga Allah zamannan naki a haka ba sonshi nakeyi ba".



Tace "In Sha Allahu Baba bazan baka kunya ba". Daga haka suka shiga hirar duniya. Bata bar dakin Baba ba sai kusan karfe sha daya. Dakin Goggo ta shiga tayi shirin kwanciya sannan ta kwanta.



Tunda ta fita da safe yawon gaishe-gaishe bata dawo gida ba sai gaf da sallar magriba. Sosai take cikin gajiya. Ko don ta dade ba tayi yawo irin haka ba gaba daya sai taji jikinta yana mata ciwo.



A ranar da ta kwana biyu da zuwa gida wurin karfe sha biyu na rana suna zaune da Goggi, gyaran zogalen da Goggo zatayi dambu takeyi. Yarone ya shigo yace wai ana sallama da ita. Mamaki ne ya kamata, waye kuwa zaiyi sallama da ita da safennan. Ita wa ma ta sani da har za'azo wurinta.



Ganin bata da niyyar amsawa ne yasa Goggo tacewa yaron kace tana zuwa sanna ta cewa Aisha "tashi kije ki ga waye, ai ba'a san inda za'a dace ba". Kasancewar tayi wanka tun tashinta, sanye take cikin atamfar Holland dinkin riga da zani. Hijabi kawai ta saka ta fita don ganin mai sallama da ita.



Mallam Adamu ta gani zaune cikin mota. Cikin sassarfa ta karasa wajenshi, tana zuwa ki gaishe shi batayi ba ta tambayeshi lafiya. Murmushi yayi sannan yace "lafiya lau Mami ce tace nazo na daukeki" "Mami fa kace kuma lafiya Mallam Adamu ka tabbata" ta tambayeshi fuskarta dauke da mamakin jin cewar Mami tace a zo a dauketa ganin sun rabu ne akan zatayi sati daya kafin ta koma. Yace "lafiya lau kawai dai tace ne nazo na daukeki". To ina zuwa tace mishi sannan ta juya zuwa cikin gidan.



Sanarwa da Goggo tayi batun tafiyarta. Itama Goggo tarrarrabi takeyi cewa anya kuwa lafiya. Daki Aisha ta shiga ta hada kayanta sannan ta fito tayi sallam da Goggo tana cewa ta fadawa Babanta batun tafiyarta idan ya dawo. A sosron gidan sukayi kacibis da Baba, kafin tayi Mayans ya rigata da cewa "naga Mallam Adamu yazo daukarki ko, Allah ya kiyaye hanya ki gaida mutanen gidan. Tace "amin Baba fatana dai Allah yasa lafiya" yace "lafiya lau kawai dai bata ji dadi bane Mamun taku amma yace jikin da sauki".



Sallam Ragusa Baba sannan ta wuce mota suka dauki hanyar kano. Hakanan taji gabanta na faduwa don haka ta fiddo da AlQur'ani daga jakarta tana karantawa. Sai da suka isa kano sannan ta rufe AlQur'anin ta mayar cikin jaka.



Suna shiga layin gidansu taga cincirondon motoci a kofar gidansu. Mummunar faduwar gaba ce ta sameta, cikin rawar murya tace "Mallam Adamu me je faruwa ne, don Allah ka gaya mini". Cikin dakewa Mallam Adamu yace mata "sai dai muyi hakuri Aisha Hajiya Mami Allah yayi mata rasuwa jiya da darea sanadiyar ciwon ciki".



Sandarewa kawai Aisha tayi a zaunen da take ta rasa gane ne kunnuwanta suka jiye mata. Wani irin kuka ne yazo mata, kifa kanta kawai tayi akan cinyoyinta tana kuka. Mami wai Maminta ce ta rasu. Mamin data tafi ta bari cikin koshin lafiya ashe bazata dawo ta tarar da ita ba. Wannan rayuwar abar tsoro ce, wato tsakanin rayuwa da mutuwa dan takin kalilan ne ( Allah yasa muyi kyakkyawan karshe, Amin).



Ta dade a zaune cikin motar kafin tayi karfin halin fitowa, gidan a cike yake da mutane 'yan karbar gaisuwa. Ta kofar kitchen tabi ta shiga cikin gidan. A parlour ta tarar dasu Hajiya da Hajiyarsu Mami da wasu daga cikin 'yanuwanta. Durkushewa tayi kawai a wurin tana wani irin kuka, mutanen wurin gaba daya suka hau bata hakuri.



Da kyar ta iya tsaida kukan tayiwa su Hajiya gaisuwa sannan ta tashi ta haya sama zuwa dakinsu. Su Ummie ne a dakin tare da kawayensu. Tana shiga Ummie ta taso ta rungumeta tare da fashewa da kuka, itama Aisha kukan takeyi.


UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ
'YA'YAN MIJI
๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ

Na Umm Asghar

13
Mutuwar Mami ba karamin girgiza al'ummar gidan tayi ba tun daga kan maigidan zuwa yaran gidan da ma'aikatan gidan gaba daya. Ga Aisha kam ko mutuwar mahaifiyarta bata shigeta haka ba ko don lokacin da mahaifiyarta ta rasu bata mallaki hankalinta kanta ba.



A cikin kwanaki bakwai da akayi ana karbar gaisuwa sunga tururuwar jama'a 'yan zuwa ta'aziyya. Kodayake Mami ta mutane ce, fata dai a koyaushe shine halinta na gari ya bita.



A bangaren Aisha ma Babanta da Goggo da Yaya Huwaila ne suka zo musu ta'aziyya don Goggo ma da Yaya Huwaila zama sukayi har saida akayi sadakar uku sannan suka koma.



Bayan anyi sadakar bakwai ne kowa ya watse sai suka ji gidan yayi musu fadi. A wannan lokacin ji sukayi mutiwar ta dawo musu sabuwa tamkar a lokacin akayi ta.



Sauki daya da suka samu shine da Hajiya bata koma gidanta ba taci gaba da zama dasu to sai dai suma sun sani zamanta dasu ba mai daurewa bane.



A ranar da Mami tayi kwana ashirin da hudu da rasuwa ne Aisha na tare da Hajiya a dakin da Hajiyan ta sauka. Man zafi take shafa mata a kafafunta kasancewar tana fama da larurar ciwon kafa.



Daddy ne yayi sallama ya shigi ckin dakin. Amsa mishi Aisha tayi sannan ta gaisheshi ta tashi ta fita. Zama yayi a kasa ya jingina da jikin gadon sannan yace "Hajiya barka da dare an yini lafiya" "lafiya lau Alhamdulillahi" Hajiya ta amsa mishi "ya hidimomi, yanzu ka dawo hala?"



Yace "eh Hajiya komai lafiya lau mun gode Allah. Ya kafartaki, tana matsa miki ne har yanzu ko sai kun koma asibiti". Lankwashe kafafuwan tayi tace "a'a basa mini wani ciwo ai naji dadin maganin da aka canja mini a asibitin, sai dai dama akwai maganar da nakeso muyi".



Gaba daya ya tattara nutsuwarshi zuwa ga Hajiya don daga yanayin yadda ta mishi magana yasan maganar da zata fada mai muhimmanci ce sosai.



"Kana jiko dama akan maganar yarinyar nan ne Aisha, da iyayenta suka zo gaisuwa mahaifinta ya bukaci da ta koma gabanshi tunda ta gama karatu gashi uwar rikonta Allah yayi mata rasuwa. Ta na dai ce mishi ya dakaceni kadan In Sha Allahu zan nemeshi akan maganar".



Ta dan numfasa sannan ta cigaba da cewa " ni ina ganin mai zai hana ka aureta ta maye maka gurbin Zainab ko babu komai kasanta kasan halinta tunda tarbiyyarkuce kuma zata zamewa 'ya'yanka uwa tunda akwai shakuwa sosai a tsakaninsu, bama dai Ruqaiya da Zainab don sunfi sauran bukatar uwa amma kasancewar su da Aisha maraicin da zasuyi kalilan ne".



Tunda Hajiya ta ambata mishi aure yaji wata iriyar zufa ta keto mishi hankalinshi ya tashi yawun bakinshi gaba daya ya kafe ya rasa mai zaicewa Hajiya. Da kyar ya samu ya tattaro dauriya yace " Hajiya wani irin aure a yanzu kuma da yarinyar nan Aisha, ai 'yata ce kamata yayi ace ni zan aurar da ita ba wai ni na aureta ba".


Tsuke fuska Hajiya tayi ta bata rai sannan cikin kausashiyar murya tace "wace irin magana ce kakeyi haka, haram ne auren Aishar ko menene, kuma da kake maganar aure yanzu wuri yayi maka ko me. Idan bakayi aure yanzu ba sai yaushe zakayi. Kasan dai ni bazan cigaba da zama maka a gida don na kula maka da yaraba dole suna bukatar uwa bama dai kananun kuma a ganinka akwai wacce tafi dacewa da zame musu uwa fiye da Aisha ne. Yarinyar da tun haihuwarsu take faman hidima dasu. Kuma ni nayi maka sha'awar aurenta ne saboda yarinyar mutuniyar kirki ce sosai zakaji dadin zama da ita don bata da raini kwatakwata bata da rawar kai irin ta 'yanmatan yanzu. Amma bazan tursasaka akan abin da bakayi niyya ba tunda bakaso shikenan fatana Allah ya hadaka da abokiyar rayuwa ta gari, Allah ya jikan Zainab"




Tunda ya sunkuyar da kanshi ya kasa dagowa don gaba daya sai yaji mutuwar Zainab ta dawo mishi sabuwa, rashin Zainab da yayi ne yasa har Hajiya keyi mishi maganar aure a cikin kasa da kwana da talatin da mutuwarta kuma auren ma da karamar yarinya 'yar cikinshi da bata wuce sa'ar Mu'azzam ba danshi na biyu bama Khalifa ba.



Tunda ya mallaki hankalin kanshi bazai iya tuna wata rana da yayiwa Hajiya musu akan wata bukatarta ba don haka bazai fara daga yanzu ba.



Aure tace tana so yayi to In Sha Allahu zaiyi da kuma yarinyar da takeso. Kamar yadda tace ne yaranshi sunyi sabo da yarinyar sosai, sai dai har cikin ranshi yasan zaiyi auren nan ne kawai don farin cikin Hajiya bawai don yana ra'ayi ba, shikam matarshi daya ce Zainab babu wata diya mace da zata iya maye mishi gurbinta.



Dauke kai Hajiya tayi tayi tamkar bata san da dashi a zaune ba. Ta san har ga Allah bada wani abu tace yayi aure ba sai don sanin cewa auren ne zai sama mishi nutsuwa ya dauke mishi damuwar da yake ciki ta rashin Zainab.



Kuma da tace ya auri Aisha tasan itace kawai zata iya hakurin zama da yaranshi tunda ba yau suka fara zama tare ba amma mawuyacin abu ne yayi dace da matar kwarai da zata kula mishi da yara tsakaninta da Allah bare da ya kasance mai ido ne shi akan harkar yaranshi ba kiwacce mace bace zata iyayin hakuri da halinsu ba amma Aisha fa tasan halinsu ta kuma iya zama dasu tunda duk tsawon zamanta dasu ba'a taba jin kansu ba ta kuma dade da sanin cewa ba dadin zama dasu take jiba tun ma ba Farida ba da Mu'azzam dama kuma sune fitinannun.



Ganin shirun bazata kai msihi ko ina ba nevya sashu amsawa Hajiya da bukatarta. Farin ciki ne ya lullube Hajiya sosai, dama dai tasan da wuya ya tsallake maganarta ko da kuwa baya so. "In Sha Allah sai kayi alfahari da auren Aisha don kuwa yarinyar arziki ce ita, Allah yayi maka albarka yasa 'ya'yanka suyi bika fiye da yadda kake bina".


UMMASGHAR
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ
'YA'YAN MIJI
๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ

Na Umm Asghar

14
Babu bata lokaci Hajiya ta nemi Baban Aisha da maganar auren da take son kullawa tsakanin Daddy da Aisha inda anan take ya amince da shawarar Hajiya don dama zaman Aisha a haka babu aure ba dadi yakeyi mishi ba.



Ba wani dogon lokaci aka yanke wa auren ba, sati uku kawai aka saka zai kama bayan anyi arbain din Mami da sati daya kenan. Za'a daura auren acan gaya sai a dauko amarya daga can.



Ita kam Aisha bata san wainar da ake toyawa ba har sai da ya rage saura kwanaki goma daurin auren sannan Hajiya ta sanar da ita.



A razane ta dago ta kalli Hajiya da kwata-kwata bata lura da halin da takevciki ba ta cigaba da yi mata nasiha akan hakuri da karbar kaddara aduk yanda tazi mata.



Sai dai sam Aisha bata san me take cemata ba don gaba daya kwakwalwarta daina aiki tayi na wucin gadi, bata san cewar hawaye takeyi ba sai da taji Hajiya ta tabata sannan taji danshin hawayen a fuskarta.



"Kuka kikeyi Aisha, bakiyi na'am da maganata bane yasa kike kuka? Idan kina ganin akwai damuwa sai a fasa don bazanso inyi abinda zan cutar dake ba domin kuwa ke din amana ce a wurina. Ni dama nayi sha'awar kasancewarki madadin Maminku ne saboda kyawawan halayenki da nagartarki zanso ace kin kasance tare da Jafaru ki zame mishi mace ta gari uwa ga 'ya'yanshi don nasan ke kadai zai aura da 'ya'yanshi bazasuyi maraicin uwa ba".



Cikin sheshekar kuka tace "kiyi hakuri Hajiya bawai ina kuka don banyi na'am da maganarki bane sai don ina ganin idan akayi haka tamkar naci amanar Mami ne data rike ni da zuciya daya tamkar 'yar data haifa, tsawon zaman da ita bata taba bambantani da yaranta ba.


Amma ya za'ayi na kasa bin umurninki bayan dukkan abin da kikayi mini a rayuwata komai zan zama a rayuwa kece sila ya kuwa za'ayi na kasa yin abinda kikeso.



In Sha Allahu zaki sameni mai yin biyayya ga dukkan umurninki matsawar bai sabawa Allah b, Allah ya tabbatar mana da abinda yafi alkahiri".



Sosai farinciki ya lullube Hajiya cewa takeyi "nagode Aisha In Sha Allahu alkhairi na tattare da rayuwarki, Allah yayi miki albarka ya azurtaki da zuri'a ta gari".



Har lokacin shocj bai saketa ba abin daure mata kai yakeyi yadda Hajiya tayi yunanin hada wannan auren sai dai bata bari Hajiya ta gane tana cikin damuwa ba tayi kokarin ganin ta saki fuskarta, sai dai bata iya cigaba da zama a dakin ba sallama tayiwa Hajiya ta koma dakinsu.



Tana shiga dakin toilet ta wuce ta rufe kanta a ciki ta fashe da kukan tausayin kanta. Ita kuma tata kaddarar kenan ta auren mutimin da yayi 'ya da ita. Ta jima cikin bandakin sai da taji ana knocking sannan ta wanke fuskarta ta bude kofar ta fita.



Farida ce a tsaye a bakin kofar. Tsaki ta mata sannan tace "wani sabon salo ne wannan ki shige bandaki ki rufe kinaji ana knocking kinyi banza da mutane".



Ko kallon Farida batayi ba ta wuce ta hau kan gado ta kwanta. Tunda taji maganar aurenta da Daddy ta koma wata sukuku da ita gaba daya ta rasa walwalarta. Kullum Ummie cikin tambayarta abin da ke damunta take amma amsa daya take bata itace babu komai.



Yaya Khalifa ma saida ya kirata yayi mata nasiha akan rashin walwalarta don a tunaninshi mutuwar Mami ce har lokacin ke nukurkusarta sai kawai ta bishi akan haka dinne.



Bata san a wurin wa su Ummie sukaji maganar ba a lokacin saura kwana shida durin auren. Farida da Ummie ne suka shiga dakin suka sameta tana shirya musu kaya a cikin wardrobe. Ummie ce tace mata "Aisha wacce magana naji anayi a cikin gidannan akanki da Daddy?"



Gabanta ne taji ya fadi jin maganar data fito daga bakin Ummie. Daurewa tayi ta amsa mata da "wacce magana kenan kikaji". Wani wulakantaccen kallo tayi mata sannan tace "kina nufin kice bakida masaniya akan batun aurenki da Daddy". Shiru Aisha tayi don bata san amsar da zata bata ba.



Shirun da Ummie taji tayi mata ne ya bata tabbacin cewa maganar da taji ba karya bace kenan da gaske ne Daddynsu Aisha zai aura, wannan wane irin cin amana ne Aisha tayi musu ta rasa mijin aure sai mahaifinsu.



Shi yasa dai mutane ba abin yarda bane, da uta ce maijin haushin yanda Farida ke treating dinta ashe dai akwai abin da Farida ta hango da yasa ta kasa yarda da ita.



Zamewa Ummie tayi ta zauna a kasa don ji tayi kafafunta baza su iya daukarta ba jikinta gaba daya rawa yakeyi.



"Mtsew... ni dama na dade da danin crwa wannan mai kama da bararon zamanta a gidannan ba alkhairi bane, kune dama kuka daukaketa kuka maidata wata tsiya. Na kuma tabbata ita tayi kulle-kullen da har Hajiya tayi tunanin hada aure tsakaninta da Daddy. To wallahi tun wuri kije ki kwance kullin da kikayi wa Hajiya don bazamu taba aminta dake a matsayin matar Daddynmu ba".



Haka suka saka Aisha gaba sunata yarfa mata rashin mutunci amma har sukayi suka gama bata daga kai ta kallesu ba. Ta sani cewa dolene ta aro hakuru ta kara akan nata don wulakancin da zata gani a wurinsu ba kadan bane.



Ko kadan kuma abin da sukayi mata bai bata mata rai ba don tasan dolene suji babu dadi akan sabon matsayinta a wurinsu itama ba dadin take ji ba don dai babu yadda zata yi ne to amma ya kamata su fahimci cewar itama ba yin kanta bane kuma komai yana tafiya ne akan kaddararshi.



Idan har Allah ya kaddara mata auren Daddy bata da yanda zatayi ta guje mishi hakanan idan har babu shi a cikin kaddararta babu abin da zaisa aurensu ya kasance.



Tun daga wannan ranar Aisha ta koma mujiya

Please Login or Register in order to submit comment